ᎠᎪႮᏞᎪᎻ BIYU _The Historical_ ~BOOK ONE~ Bismillah Rahamani Raheem *Sadaukarwar taki ce! Maman ABUNA! Kince na rage masarautan Jordan ko💝💞🤩 Uwata ga book dinki sukutun da guda na baki domin ke* '''Tukwaici gareku Batul Ghana And Mom Sayeed My Juwairiya Nasir And Mom Ases And Maman Khadijah da Sadeeq Har abada kuka raina💝 Gaisuwarki ce Aunty Safiya Danjuma Jos 💞''' Page 1.. Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama... Ya rasu a shekara 632 ran takwas ga wata june,(malaman tarihi zaku iya min karin bayani idan nayi kuskure ba laifi bane 💞) Bayan rasuwar shi Asahaba suka shiga tattaunawa, inda aka daura Sayyiduna Abubakar, bayan shekara biyu Allah yayi mishi rasuwa sakamakon zazzabin da yayi fama dashi. Bayan shi sai aka bawa Sayyiduna Umar wanda yayi shekaru biyar zuwa bakwai, ya rasu. Lokacin Sayyiduna Usman yana kasar damascu na syria ya tafi fatauci. Aka bashi bai sani bashi khalifancin. Wato Amirul Muminina kenan. Shima bai jima ba, Allah ya amshi rayuwar shi aka bawa Sayyiduna Ali shima ya rike na wani lokaci kafin ya rasu, amma har zuwa lokacin gwamnatin Musulunci bata fad'adda ba. Iyakarta jazziratul Arab ce, wato yankin. Madina, macca, da wasu sassan jazziratul Arab. Bayan wasu lokuta. Aka bawa Khalifancin Rashidu. Lokacin khalifancin yayi da'awa amma shi bai kafa daula ba, yayi dai lokacin da inda wasu daga cikin ayarin shi suka yi ta kama karya tare da zalinci. Sannan shi ya shigar da al'adun larabawa zuwa ga maguzawan larabawa. Daga nan Umayyad ta kafa daular ta, daga shekarar 661, 750 Umayyad itace daular musulunci da tayi fadi da tsayi, domin tayi girman ban mamaki, Umayyad ta mamaye yankin jazziratul Arab baki daya. Idan muka duba inda Ta mamaye sune. *Makka* *Madina* *Damascu na ƙasar Siriya* *Kuifa* *Istanbul* *Carboda* *Falasɗinu* *Kairomam* Da wasu yankunan jazziratul Arab, Sannan bata samu damar shiga Farisa da Girka ba, a wannan lokacin khalifancin Umayyad ba a takura wanda ba Musulmi ba, asalima tsarin su ya banbanta da na Khalifancin Rashidu. Haka ya janyo hankalin wadanda ba musulmi ba shiga addinin Musulunci. Zunzurutun karfin mulkin Umayyad tasa aka fara rade radin zai d'aga hedkwatar musulinci da yake Madina zuwa damascu, tilas yasa shi dawowa Madina gudun faruwar juyin juya halin Musulunci. Dan haka sai ya zamana an sami hedkwatar musulinci guda biyu, daya a damascu daya kuma a Madina, wanda haka yaso tab'a kimar musulinci a lokacin. Shekara 750- 1258 Abbasiyyah ya kafa tashi daular lokacin wafatin Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama, yana da shekaru daular abbasid yayi rolling. Wanda shi kuma ya mamaye yankin guf baki daya har zuwa nahiyar Turai. Daga cikin yankin da Daular Abbasid suke mamaye akwai. *Farisa* *Andulus* *Hindu* *Asia* *Iraq* Da wasu sassan kasar Afrika, ita ba su libya, Morocco, Algeria, da tsallaken kogin blue nel. Sannan musulinci ya tsallako har bakin gabar tekun maliya, zuwa sudan kenan. Daga nan kuma ya karaso sauran yankunan kudancin Afirka da sahara. Wanda ya shigo har kasar Masar. ---- Babban hedkwatar Abbasiyyah tana Baghdad, a Lokacin wadanda ba muslmai ba, suna biyan haraji me suna jizyah,2.5% wanda dashi ake raba charity. (Ban san me zan ce da Hausa ba! Amma ana kiran shi da haddaya da larabci) Tsarin sarrafa mulkin daular abbasid yayi wani irin karfi wanda shi da Umayyad aka ce sune mafi girman daular musulunci daya shekara dubu daya da dari hudu da ashirin da biyar. Sannan daga baya wasu daga cikin dangin Umayyad, sun koma Andulus inda suka kafa daular Larabawa a gurin, wasu kuma suka kafa daular Ottamah A Istanbul na kasar Turkiyya. Shi kuma Abbas ya kafa daular Abbasid a tsakanin. Daga baya wasu daga cikin mukararaban Abbasid sun dawo Samanid da wasu bangare na yankin suka kafa daular Abbasid a gurin. Mafi girman Daular da ta gagari kowa a lokacin, tana da dinbin dakarun soji, sannan a lokacin ta hana kowani harshe sai labarci, bayan haka an yi sarakuna shida a cikin Daular. Bayan Abbasid da kuma wasu mabiyan shi. Sannan sai ana cikin shekaru ba 1355 Hijrah Manzon Allah daga Makka zuwa Madina, Turawan Mulkin Mallaka suka shigo cikin lamarin daular Larabawa. Suka dagula musu lissafi, inda suka nuna musu mace tana da damar yin mulki, kamar yadda yake faruwa a wasu nahiyoyi kamar kasar hindu, ana samun magajiyar sarauta, sai kasar Sin, suma ana samun magajiyar sarauta, a turance(Empress, a larabci kuwa ana kiranta Sultanah) Wato ita (Empress) ana samunta ne sakamakon kasancewar matar Sarki ko Kwarkwarah sarki, ko kuyangar sarki, sannan matsayin da yake kaita zuwa Empress haihuwar d'a namiji. Sanan ba a damu ba, koda kuwa matar sarki ce ta ta samu wannan damar, burinta kawai ta sami d'a namiji, wanda zai zame mata garkuwa. Daga lokacin da aka ce matar sarki ta samu juna biyu, toh akan Nimo duk wani me maganin cikin masarautan ya bincika lafiyarta, idan kuma kuyanga ce. Toh zata kasance a killace. Gudun kar a bata guba ko abinda zai kashe d'an cikin ta. Tunda turawa suka basu wannan tsarin ya zamana, an sami sarakuna, suka shiga mutuwa, basa cika shekara daya za a wayi gari sarki ya mutu, ko a samu matar shi itama ta mutu ko idan tana da d'a namiji ya mutu. Sai da ta kai daular Samanid manyan mutanen cikin gidan sarautar kowa gudun mulkin yake, kuma wani abun da yake damun crown prince, sun fara tsoron zama a matsayin Sultan a cikin daular. ^^^ Abdus Samad bin Hubaish bin Aamaan al Muktum. Shine Sultan na tara a daular Samanid, kuma ya rayu tsawon shekaru goma sha biyar, Yana auren Yar daya daga cikin crown prince na masarautan wato Fazilatul nisa, mahaifinta me suna. Hood bin Abdul munaf bin Basra, almuktum yana cikin jerin manyan masu jiran gado, dan haka lokacin Sultan Abdus Samad yana shekara biyar a karagar mulki, ya hada shi aure da yarshi duk da Sultan din yaƙi, sabida tsoron kar ta samu ciki a kasheta. Tunda daular ta zama kamar akwai cultist curse. Koda aka aura mishi ita, babu abinda ya tab'a hadasu asalima Sultan kauracewa yayi tare da dauko balagoron dole zuwa kasar Carboda, inda a can ya hadu da wata baiwa me suna. Hoyam, Ya daukota har daular a boye, daga shi sai narmin baiwar shi ce, a hannunta ya taso, lokacin da ya kawo mata Hoyam. Yarinya ce da bata wuce shekara goma sha shida ba, dan haka ya manta da ita, sai bayan wasu shekaru marasa rata. Ya tuna da ita, lokacin yana fama da rashin haihuwa, dan da farko bai damu ba, sai daga baya da aka matsa mishi musamman sultana Fazilatul nisa, abin ya d'aga mishi hankali. Har zuwa wani lokacin da ya nemi Hoyam, tunda Sultan ya nemi yarinyar nan ya daina niman Sultana. Hankalinta yayi mugun tashi san haka tana da wani amintattun bayinta me suna Shairah da Narjis, ita Narjis mace ce Shairah kuma namiji ne wato d'an daudu. Duk wata mace baiwa da take cikin masarautar shi yake shayarda ita maganin gyaran jiki, tare da mata duk wani abinda zai gyarata. Narjis kuma itace ke tare da Sultanah duk abinda za a aikata da saninta itace kashin bayan dukkanin aiyukan Sultana, Yawo take a tsakar d'akinta sanye take da wani shegen gown, me dauke da duwatsun jauhari, kanta da wuyarta dauke yake da kambun lu'lu'u. Shafa wuyarta tayi sannan cikin wani irin yanayi me cike da mugun mulki tare da Izzar da suka tattaro a cikin idanunta tace. "Taya aka yi Abdus Samad ya ajiye baiwa a cikin masarautan nan ban wani ba?" Zuɓewa suka yi akan gwiwar su, tare da kaskantar da kansu, suna faɗin. "Mun tabbata asararru marasa albarka, tunda zaman mu a gare ki bai zama me amfani ba, Sultana mun bayarda kawunan mu da gangan jikin mu sadaukarwa ga b'acin ranki kinsaka takobin ki, ki.sare kawunan azzalumai irin mu!" Wani irin iska taja, kafin ta juya musu baya tace.. "Narmin!" Jikin Narjis na rawa taficce da sauri, har shashin bayi wanda yake can hanyar fita cikin masarautan. Ta buga kofar Narmin. A tsora ce ita da Hoyam suka kalli juna, sannan ta juya ta boye Hoyam, kafin ta bude kofar. Turata dakarun da suka taki Narjis suka yi sannan suka shiga duba d'akin, cikin tsananin bincike suka samota sakamakon atishawar sa tayi. Wani iri daraja kan Narmin, dan haka aka sako su a gaba, babu wanda yace kala. Lokacin da suka isa shashin Sultanah, zuɓewa suka yi akan gwiwar su. Tana kishingide akan wata kyakyawan darduma, tare da wasa da tufar hannunta. Kusan rabin awa, kafin ta kalli Shairah. Cikin wani yauki ya kalli Narmin. "Toh azabar Allah ya tabbata akanki. Da cin amanar da kika yi! Yau naga abinda ya hana mata gemu yaba maza!" "Hmm!" Sultanah tace, "Toh ai sai ki tashi ki bar mana nan domin Sultanah zata yi magana da abinda kike b'oyewa!" Mik'ewa tayi kanta a duke sannan tace. "Kaina da gangan jikina, mallakar Sultan Abdus Samad ne, haka ma Hoyam mallakar shi ce,.ina niman afuwar Sultanah da karta cutar da Hoyam. Yarinya ce da bata san kome ba." Sake tufan da yake hannunta tayi, sannan ta juya tana kallon Narmin. "Ni zaki koyawa abinda na taso a kai?" Sake zuɓewa tayi akan gwiwar ta, zata yi magana aka bankad'e kofar shiga d'akin. Aka shigo,. sanye yake da doguwar riga, me ruwan goro sai gashin da ta sauka har gadon bayan shi. Kallonta yayi cikin nutsuwa. kowa fita yayi daga dakin aka bar Hoyam da take durkushe gaban Sultanah da ta hasala. "Abdus Samad! Meye nufinka da wannan kaskantacciyar baiwar? Shin tafini nasaba ne? Nawa ka saye ta na fanshe ta." Mik'ar da Hoyam yayi yana kallon Sultanah, sannan ya d'aga haɓɓar Hoyam wacce take kuka kamar ana yagar namar jikinta dan ta gama tsorata. "Bar kuka gani nan a tare dake! Kinji ki fita Narmin tana jiranki." Ya faɗa mata. A hankali ta janye jikinta tare da barin d'akin, ta nufi hanyar waje, tana shashekar kuka. A bakin kofar tafi ta gamu da Narmin, ta riko hannunta suka fara tafiya,.harsuka iso shashin kuyangi. Kallon su tayi sannan ta sunkuyar da kanta sakamakon irin kallon da suke mata, suna magana kasa kasa. Akan itace sultan mafi soyuwa a zuciyar shi. Kishin ta yi kama su, sosai musamman da suka ganta sanye da tufafi masu kyau irinta kasar yamma. Haka yana nufin Sultan yana ji da ita kenan. Tunda suka isa dakin su, take kuka cike da tsoro. "Narmin ina jin tsoron kar su, kuma zuwa." "Karki damu Sultan ya san da batun ba zai tab'a barin a cutar dake ba, domin yana sane dake. Ki bar kuka;" Gyada mata kai tayi, sannan ta kalle ta cikin damuwa. "Me yasa takira mu?" Banza da ita tai tana hada kayan da aka wargaza d'azun. "Baki ce min kome ba?" "Sabida har yanzun daular nan babu wanda yake da yakinin Sultan zai samu d'a namiji, tunda har Kwarkwarorin shi ba haihuwa suke ba, sannan na hore ki da karki yarda wani ya baki abu kici. Domin cin abu a hannun wani tashin hankali ne, karki yarda wani ya shayar dake wani abu, yin haka hatsari ne." "Sabida Me yasa kika min doka?" "Sabida zasu iya samun damar saka ki cikin jerin mutanen da ba zasu sami haihuwa da Sultan ba. Duk ranar da kika samu ciki da Sultan ranar zaki daina amsa sunan baiwa ko kuyangar sarki, sai dai magajiyar sarauta, isa wannan matakin kuma shine rayuwa da mutuwa, domin.". Buga kofar dakin aka yi, da sauri tazo ta bude. Sultanah ce tana huci tare da kallon Narmin. "Ina munafukar take? Wani tsafi kika yiwa Sultanah da yake cewa kinyi mishi ya zab'e ki a matsayin kuyangar shi, ki gaya min nawa ne zan biyaki!" "Sultanah! Kuyangi suna jinki karki bada mata, zasu samu abin gulmatawa!" Shiru tayi tana kallon Narjis gyada mata kai Shairah yayi tare da cewa. "Sultanah!" A fusace ta juya tare da barin gurin, tana isa shashin kuyangi, tace. "Shairah ka dauko min Hoyam, nan." Da sauri ya kalli Sultanah. Kafin ya juya inda suke, aka tawo da Hoyam. Tana kallon Yarinyar cikin tsana da tsangwama tace. "Zan shayarda duk wacce Sultan ya keb'e da ita, duk wacce Sultan ya gayyaceta turakar shi bata gaya min ba, sai na shayar da shi nono mahaifiyar shi a karo na biyu." Huci tayi sannan ta kalle su, ta juya bayanta, tare da d'aga hannunta. "Darda, ka zane mana Hoyame!".... *Book one free ne, book two da three na kudi ne 200₦ ta bank 0472282105 ki katin mtn ta wannan Number +2347035133148 ko ta wannan Number 08130269641 Insha Allah 13/2/2021 xan cigaba da Posting* #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: https://www.wattpad.com/1019331921?utm_source=android&utm_medium=link&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=Mai_Dambu&wp_originator=EhMWxWcs3%2BXBPmJ9Mx4VmYNMNPNLwAtXfRCgGgL0YhnfgfEGgGb%2BS6%2FL2PAUJxT95YPPst3m3dR%2FtnwJ0kHvOKhC0Kwru7g1GiqVx5gpeoIWEc8eNdkpZWokeVl8WEgB *_ᎠᎪႮᏞᎪᎻ BIYU_* _The Historical_ ~BOOK ONE FREE~ Bismillah Rahamani Raheem Page 2.... Kamar wacce aka aikowa wahayi ta juya tare da dakatar da Darda, ta tako har gaban Hayom. Tana huci musamman da taga yadda yarinyar take mata kallon kurilla. Dauketa tayi da mari, tana tuno abinda yace mata. --- "me ka ɗauke ni? Ka maida Ni wata bita can, mmm sultan yaushe rabon ka da ka gayyace Ni turakar ka? Ashe ka ajiye wata a can gefe ne, ka saba duk macen da zaka nima a cikin Kwarkwarorin ka kana turo min a shirya maka su, ashe ha'intana kake? Meye na rage ka dashi da zaka boye yar wannan yarinyar?" Karamin murmushi yayi sanan yace mata. "Idan kin gama zan fita?" Ya gaya mata hankalin shi yana kan zoben hannun shi, a rikice tace. "Sultan!!!" Juyawa yayi tare da tura kofar zai fita. "Meye na rage ka dashi?" Cak ya tsaya kafin ya juya yana kallonta, sannan yace. "Ke zab'in Kawuna ce! Ita kuma abinda zuciya ta ke so ce, dan haka koda ban bata gurbin Matana ba, zan ajiye ta a matsayin Kuyangar da nake so! Kuma na rantse da Allah, wani abu ya same ta, dole na rage miki matsayin ki daga Sultanah zuwa Ameerah." Sake baki tayi tana kallon shi har. Yana gama fadar haka, ya fice abinshi daga d'akin, ihu ta saka tare da zuɓewa a gurin. Bayan fitar shine ta fito domin cikin mutuncin Hayom. "Sultanah, karki yanke hukunci cikin sauri, ki barta a sannu zamu yi maganinta, yanzun kuma kika yi haka tankar zubda kimar ki ce, kuma kuyangi na kallonki, kiyi nazarin abu mana." Inji Shairah, Juyawa tayi tare da barin gurin, ranta a b'ace, tana shiga turakarta ta shiga watsi da kome na dakin, hatta mudunin dakin. Cikin wani irin ihu tana kuka. "Burina! Burin zuri'a ta, zama magajiyar sarauta, yau an wayi gari Sultan yana shirin ture min. Shairah kayi min iso ga mahaifina." Yana bakin kofar ya d'an duka kad'an yace. "Allah ya huci zuciyarki Sultanah" Zama ta cigaba da yi tana, domin abin da mugun ciwo, na ha'intar ta da Sultan yayi. --- bayan tafiyar ta, kallon Hoyam sauran matan gurin suka yi tare da cewa. "Ke kan Azabar Allah ya tabbata akan ki, tunda kika b'atawa Sultanah rai." Mik'ar da ita Narmin tayi tare da kaita, dakin da zata zauna, tana kuka. Ta kasa magana. "Kiyi shiru, yau zaki fara zuwa turakar Sultan kuma yana da kyau ki kiyayye abinda zan gaya miki, babu ruwanki da kowa." "Ni babu inda zani!" "Hmm!" Narmin tace mata, sannan ta juya tare da shiga dakin wanka da yake cikin dakin. Ta haɗa mata ruwan wanka tare da turarukan wanka ta larabawan asali. Sannan tazo ta sakata a gaba suka shiga ban ɗakin. Sai da ta dubata sosai sannan taga babu abinda ya sami yan matancinta. Kafin ta barta a ban dakin tafito. ^^^Wani shashi ce me matukar girma da wadatuwa, ga kyau da tsarin, ya tsaya a bakin kofar shiga cikin gidan, yace a mishi iso da Amir Hood Abdul Munaf. Shiga cikin gidan Bafaden yayi can bayan dakikai talatin ya fito tare da mishi iso, a hankali yake tafiya har ya shiga cikin gidan, ya sami manyan manyan hannun damar Sultan Abdus Samad. Gaishe su yayi sanan ya kalli Mahaifin Sultanah Fazilatul nisa, ya d'an duƙa kadan ya yace. "Zan so na gana da kai a keb'ence." "Karka damu ina sauraren ka."inji Amir Hood, "Sultanah tana cikin damuwa da tashin hankali, sakamakon yankar bayan da Sultan yayi mata." Shiru yayi sannan yace mishi.. "Shairah ban fahimci me kake nufi ba!" " Eh toh abin nan ne da ake kira d'an wanken zagaye, ko nace asirin ciki sai hanji!" Ya kuma aure Amir Hood. "Kasan matsala ta da kai kenan, dabaibayi, sai ka kulle mutum ka barshi a waje." Kallon sauran mutanen yayi sannan ya kuma kallon Shairah, baya son abinda zai kawo rashin yarda da mutanen da yake niman hadin gwiwa dasu ne, yafi son ya samu yarda da aminci a tsakanin su, domin cimma muradun karni. "Ka fito ka gaya min meke faruwa?" Ya faɗa cikin dakakkiyar zuciya dan ya fahimci tunda Shairah yake iya zagaye zagaye abin babu dad'i. "Eh toh kamar dai koda yaushe ko wani alazi da nashi amanun, haka yau ma. Idan da sai an kawo su ake fansarwa Sultan wannan karon da kanshi yaga kyakyawan barewa ya daukota zuwa cikin gidan sarautar ya ajiye ta, yana ciyar da ita, daga cikin dangin albarkatun da Allah ya bashi." Lumshe idanun shi Amir Hood yayi sannan, ya juya ga Yayan Fazilatul nisa,me suna Abdul Mannan. Mik'ewa yayi tare da nufar hanyar waje shi da Shairah. Dake dukkan su larabawa ne ma'abota Balaaga, take suka fahimci abinda Shairah yake nufi. Sai dai duk sun ajiye haka a ransu. Sannan suna mamakin taya aka yi har ya iya samun damar ajiye baiwa domin kanshi ba tare da an kawo ta an tantance ta ba. Domin abisa masarautar duk macen da za a kamo a yaki ko a sayota toh wajibi ne, ta kasance a gurin Narjis da Shairah su bincike lafiyarta amma, kuma ya iya samun damar daukota har cikin masarautan. Amir Ansas ya kalli Anir cikin mamaki yace. "Ya Abdus Samad zai mai damu mutanen banza? Taya zai dauko baiwa ya keb'ance ta?" Ya fada tare da kafe sauran mutanen gurin da ido. "Wato abinda Sultan yake nufi ya fi karfin yayi tarayya da sauran kuyangin da aka ajiye mishi sai yaje ya nimo baiwa da kanshi bayan gasu nan a cikin masarautar idan ma baya muradun su, akwai y'ay'an mu!" A zabure Amir Hood ya kalle yi sannan ya narke kamar ba zai magana ba, kafin yace musu. "Ina ganin ai ba wani abu bane, Sultan ne guda yana da ikon zab'ar abinda rashin yake so, ba sai an mishi dole ba, sannan ban ga wani abin d'aga mishi hankali ba. Na tura Abdul Mannan ne domin ya rarrashi Kanwar shi, kusan abunka da mace, amma babu kome wallahi." "Ai maganar da Fujai yayi gaskiya ne, duk nan babu yaro kuma ai ya sab'awa dokar masarautan nan wanda magabata suka saka hannun su. Haka rashin adalci ne." "Amir Kaisan ya dace kayi mishi magana, tunda kaine mabiyin mahaifin shi idan bai ji naka ba, zamu mishi magana dole ya hakura da ita Baiwar." Cikin kwantar da kai Amir Hood yake rarrashin su, karshe suka yi fushi akan bai san me yake yi ba, gaskiya bai ji dadi ba. Amma kuma ya zai yi dole haka zai hakura, ---- lokacin da suka isa sun sami abinda ya faru, ya baza cikin gidan sarautar, duk inda Abdul Mannan ya wuce bayi da bararo gulmar su ake, haka ya rintsa idanun shi zuciyar shi tana tafasa. Har suka isa turakar Sultanah tana zaune tasha kuka har ta godewa Allah, kallon ta yayi da sauri ta mike tare da fadawa kirjin shi. "Yan uwana, zan mutu Sultan ya ajiye baiwa a wani shashin wai Ni zab'in Kawun shi ce, ita kuma zab'in abinda zuciyar shi ke so ce!" "Shiii! Ya isa zan samu Abbu da maganar karki kuma kuka, akan kishi kike kuka? Waya ce miki ana kuka sabida kishin namiji, yaki muke mu kashe zaratan maza, ba kuka muke a filin daga ba, mahaifin mu kowa yasan shi da tsagwaron jarumta, da dakakkiyar zuciya, karki yarda mace ta saki kuka bayan kina da yayu maza biyu uku a raye. gani Abdul Mannan, ga Raheeb, ga kuma Lukman." Rarrashin ta yayi, tare da bata baki karta yi kuka tunda suna tare da ita, kuma mahaifin su zai zo da kanshi. Bayan ta share kwalla ne suka shiga hira, tare da tattaunawa akan abubuwan da sune suke faruwa, a cikin masarautan musamman rashin haihuwar ta, anan abin ya dame ta, da ta tuna inda har bata haihu ba, tabbas sauran crown prince zasu fara batun su badda yaran su mata.. Kallon d'an uwan ta tayi cikin tashin hankali. "D'an uwana me zamu yi?" "Babu abinda zamu yi sai abinda Abbu yace" Yana fadar haka ya mike tare da rike kafad'arta, yace. "Karki damu, zamu san abin yi!" Daga haka mata sallama ya fice daga d'akin, Tunda ya fita take zullumi, cike da damuwa, tare da hana kowa shigowa dakin ta. Abincin dare na bata ci. : Taje mata gashinta Narmin take, tare da kallon yadda take gyara fuskarta, murmushi tayi tare da cewa. "Kuma idan naje me sanyi wa Sultan?" "Idan kika je zaki gani." Cikin danyen yarinta tace mata. "Amma zan kwana ne a can?" "Idan kika je zaki gani." Tura baki tayi, sannan ta kalli Narmin daga cikin madubi tace. "Amma Sultan yana Kwarkwarori da yawa, kuma naga suna tsoron Sultanah." "Ke baki tsoron ta ne?" Ware idanu tayi sannan tace mata, "Tab wallahi mugun tsoronta nake ji!" "Yayi kyau haka nake bukatar ji daga gare ki." Tana gama shirya ta, ta rike hannun ta, suka nufi shashin Sultan, ta tsaya daga bakin kofar shiga shashin sa, tare da yiwa fadawan da suke jikin kofar magana. "Bakuwar Sultan ce!" Bude mata kofa akayi wanda yayi dai dai da isowar Sultanah, kallon juna suka yi ta kalli yadda Hoyam ta diriri ce. "Sultanah Fazilatul nisa tana niman Iso Sultan!" "Sannan Baiwarka Hoyam tana nan itama!" Dake ciki akwai wani Bafaden me suna Rizwan.. "Ka sallame Sultanah, Hoyam nake son ganawa da ita" . "An gama ranka shi dad'e!" Ya fadi haka tare da ficewa daga dakin karatun Sultan. ."ranki shi dad'e, yace ba yau zai gana sake ba, Hoyam yake son ganawa da ita!" Cikin mugun fusata ta yi yunkurin zata shiga. "Ranki shi dad'e, Sultan baya son ganawa dake, da Hoyam yake son ganawa!" Ya fadi haka ne sakamakon yadda take kokarin lallai sai ta shiga cikin shashin Sultan, shi kuma yasan halin Sultan sama da shekaru talatin idan ya tsaya akan abu toh babu makawa ba zai canza ra'ayin shi ba, idan kuma aka sami akasin haka, zai iya sanyawa a sare kan mutum. Dan haka ya nunawa Hoyam hanyar shiga. Ai kuwa Sultanah Fazilatul nisa taja rigarta sai da tayi baya zata fadi. "Sultanah! Zata rena ki fa!" Sake rigar tayi, sanan ta juya tare da barin gurin, ranta na kara b'aci, wato itace ba zai gana da ita ba, tana shiga shashinta ta fashe da kuka tare da cewa. "Shairah maza ku nima min iso ga Abbu na!" Da sauri suka fita shi da Narjis, kallon juna suka yi. "Me kika fahimta?" "Me kuwa ban fahimta ba" "Wai nan alƙawarin Allah za a dakatar?" "Zai dakarun kuwa! Tunda sun shiryawa haka ba iya ita ba, jimawar da Sultan yayi akan mulki bana wasa bane, sannan kuma sauran barorin shi ba Haihuwa suke ba, balle ace zasu zama magadan sarauta. Idan ka duba a cikin masarautar mutane da yawa suna jiran kujeran can, da ake fada akan shi waye zai sake ya rasa shi? Waye zai yarda ya rasa shi." "Kedai inda ranka kasha kallo. Muje zuwa." Shairah ya faɗa tare da kallon hanyar gidan su, Amir Hood. Bayan sun shiga suka sami mahaifinta, yana ganin su ta fahimci al'amarin ya girmama, dan haka ya taso da kanshi. ... Tunda suka iso ya same ta yashe a kasa tana kuka, zama yayi a kusa da ita, yana shafa kanta, tare da sake murmushin takaici. "Albasa bata yi halin ruwa ba! Ina nan ina yaki domin ke, ashe Ni kike kunyatawa a cikin masarautan? Ina ƙoƙarin ganin mun sami karfin jama'a ashe kina nan kina b'ata min aikin da nake, bani nace kiyi hakuri ba! Bana ce ki dauke Kanki akan shi ba? Toh indai Ni ne Sarkin yakin Samanid kar na kuma jin kinyi tari Barsu muga iya gudun ruwan su." Gyada kai tayi tare da share kwallar ta. Mik'ewa yayi sannan yabar shashin, yana jin wani duhun bakin ciki a ranshi, dole ya dakatar da kome kafin lokaci ya kure mishi. Idan lokacin ya kure sai dai a zab'i wata hanya na daban. - Zaune suke dukkan su,.suna kallon juna. "Koda ace mun dakatar da Sultan bamu da hurimin hana shi abinda yake so! Dan haka kawai mu yi abinda muke ganin shine dai dai, amma kusan Abdus Samad bai da dad'i idan muka takura shi." "Toh Fujai Matsalar... Littafin kuɗi ne.... #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: *_ᎠᎪႮᏞᎪᎻ BIYU_* _The Historical_ ~BOOK ONE~ Bismillah Rahamani Raheem Page 3... "Karka ce zaka yi wani yunkurin! Masarautan nan cike yake da baƙar siyasa, idan ka sake wani shirme ya fito daga gare ka, zai zamewa kabilar mu abin kunya!" Inji Amir Anas, Murmushi yayi sannan ya gyara zama, kafin yace. "Kasan har yanzun bai gama gano meye silar mutuwar Sultanah Afeefah ba, dan haka kayi ƙoƙarin gano inda." "Amir Hood yana shigowa!" Inji Bafaden da yake bakin kofar shiga zauren tattaunawa, nasu na yarimomi masu jiran gado. Babban tashin hankalin su, kawo Baiwa da Sultan yayi cikin masarautar shine damuwar su,.idan so samu ne a fitar da ita daga jikin shi, domin suna da yakinin duk macen da ta fito ta jikin sarki karshe bala'i take zamewa masarautan, sannan kuma tana iya baza mulkinta na son ranta, dan haka suka fara nazarin yadda zasu tunkaro Sultan. *** Kallon fuskarta yaƙe, yadda kwalla suka bushe a a saman fuskarta, shafa fuskarta yayi cikin nutsuwa, yana murmushi musamman yadda take ajiyar zuciya. Shi kanshi yasan cewa yayi mata bazata, domin ya saka mata karfi ainun. "Hoyam!" Gyara kwanciyar ta tayi sannan ta kuma lumshe idanun ta, sabida barcin da yake cike a idanunta. A hankali ya mike tare da barin gadon, ban daki ya shiga ya shirya kanshi. Sannan ya fito, jin Rizwan yana buga mishi kofar shi ne ya sashi cewa. "Hmm!" Shigowa yayi sannan ya gaida Sultan. "Manyan dattawan Fada suna son magana da kai. A zauren tattaunawa." Bude wata takarda yayi ya dauki alkalami ya fara rubutu, yana gamawa. Ya mikawa Rizwan. "Akwai wani mahayi zai tafi kasar Carboda ka bashi." Mik'ewa yayi tare da saka alkyaba, sannan ya saka kai zai fita, ya sami Narmin tana bakin kofar shashinsa, tare da wasu manyan masu tsaron lafiyar shi. "Narmin ki kula da lafiyar ta." Dukar da kai tayi sannan tace mishi. "An gama Sultan." Suna barin shashin, ta shiga cikin da sauri, ta hango Hoyam, tana barci. Tashinta tayi ta fashe da kuka. Fita Narmin tayi tare da samun Shairah ta gaya mishi, zaro idanu yayi waje. Sannan ya kuma juya tare da niman Narjis ya gaya mata, take aka nimo masu kula da lafiyar matan masarautan, suka nufi har dakin Sultan, anan suka taimakawa Hoyam aka gyara ta sosai, sannan aka kuma dauketa zuwa Chamber na musamman, sakamakon ita din Zab'in Sultan ce. Sannan aka Narjis da Shairah suka nufi Shashin Sultanah suka gaya mata, murmushi tayi hawaye na zuba mata, tace. "Ki bata bayi yan mata da zasu zauna da ita, kuma ku saka ido akanta, karku yarda ku.." "Na'am Sultanah!" Sannan suka fita, suna komawa aka duba bayi da kunyangi aka saka Narmin ta zab'esu sannan aka kai su Chamber din Hoyam, wacce take barcin gajiya domin babu abinda ba ayi mata na kulawa ba. Abinci ne kuma ana kawowa tace ta koshi a barta barci take ji. ** Murmushi yayi tare da dauke kanshi, kafin ya kalle su kasancewar fuskar shi babu burbushin fara'a. "Idan na fahimce ku, na zare ta daga cikin rayuwata, bayan kusan haka ba sauki ne a gare Ni ba, sannan kun dauko min labarin karni masu yawa, wato babban karni, na rabu da Hoyam sabida karta haifi namiji ta kwace masarautan ko ba haka ba?" Maida kanshi yayi sannan ya kalli Ubaidullahi. Aminin shi na kut da kutt, ya kuma lumshe idanun shi, sannan ya ce mishi. "Ubaidullahi! Me zaka ce?" Shiru suka yi sannan yace. "Ai duk abinda ka zab'e naka ne, kuma muradinka ce, dan haka umarni zaka bani." "Rizwan me kace?" "Rayuwata da kome na, mallakin Sultan ne! Umarnin ka ya wadattar dani." "Fujai, Kaisan, Hood, Anas, Abu Yusr, Abdul Muxxalib, ina jin ku me kuka ce akan zab'ina" Had'iye yawu suka yi, sannan suka dukar da kansu,.tare da mubayi a, wannan itace dokar shi.. Idan kuka ja, ya kuma ja. Toh abinda zai faru gaba wasan takobi da jini ne. Mik'ewa yayi sannan ta bar su a gurin, cikin jimamin abinda zai iya faruwa gobe. ** Tunda aka sanarwa Sultanah, Cewa Sultan yana gayyatar ta, turakan shi, take kwalliya. Tare da gyara wasu abubuwan ta, sannan ta shirya ta fita, ana take mata baya, isowa babban falon cin abincin kuyangi, ware idanunta tayi tana niman inda Hoyam take tayi, bata ganta ba. "Shairah ina Hoyam?" "Tana shashinta, bata cin abincin da sauran matan" Ya faɗa kan shi sunkuya, "Akan me?" "Ai tafi su daraja!" Gyada kai tayi sannan ta wuce zuwa shshain sultan. "Sultanah ta iso!" Aka gaya mishi, kallon Rizwan da Ubaidullahi yayi sannan yasa su, suka nad'e aikin da suke, sannan suka fita. Kafin ta shigo cikin falon shi me dauke da kayan tarihi na sarakunan larabawa. Zama tayi a falon, ganin yadda yake ta shirya abubuwan shi. Ita nan zata ja mishi aji ne, sai ta lura shi karshen aji ne, dan tunda tayi sallama, Sultan bai d'ago ya kalle ta ba, amma kuma ya amsa mata. Tashi tayi tare da zare alkyabar jikinta, sannan ya rage daga ita wata rigar barci ruwan hanta, wanda ya tsaya iya cinyarta. Takowa tayi zuwa bayan shi, tare da mishi matsar kafadar shi. A hankali tana sauke ajiyar zuciya, tausayi ta bashi. Ya jingina kan shi a kan cikinta, sannan ya juya yana kallonta. Zaunar da ita yayi akan cinyar shi yana shafa fuskarta a hankali. Daukarta yayi, zuwa turakar shi, daga nan ya kwarkwance mata, tare da kiran sunan Hoyam, cak farin cikin da take ji tare da jin dadin da yaƙe yawo a ranta da gangan jikinta, suka tsaya, kokarin datakar dashi ta fara, amma fir yaki sai da ya biya bukatar shi, sannan ya kyale ta, wani irin kuka take babu shiri ta maida kayanta, tare da barin d'akin shi. Sam ya kasa fahimtar me ya faru, kawai dai yaga tana kuka ne, dan haka ya share batun ta. ......Kwanaki ƙalilan ya kuma niman Hoyam, a lokacin aka gaya mishi tana cikin fashin sallah. Dan haka aka nimo mishi wata yar kasar Masar me suna Alima, kyakyawa ce yarinya ce kamar Hoyam, amma kuma sai dai ita tun kafin a kawo ta cikin masarautan, ta samu matsalar fyade. Dan haka lokacin da Sultan ya haɗa shimfid'a da ita, sai yaji ya rena mata, musamman yadda ya tuna Hoyam, matar shi ma ya rena mata balle kuma Alima. Dan haka koda ya gama da ita, a daren ya sallame ta, amma kuma sai dai kash. Yarinyar ta faɗa kaunar Sultan, dan haka take ji koda Bala'i sai ta haɗa alaƙa da Sultan. Bayan haka, ba zata iya zama a matsayin baiwa ba, shi yasa lokacin da Shairah ya gaya mata zai kaita dakin Sultan tayi ta murna, koda ta kasance dashi abinda ya kuma d'aga mata hankali Hoyam. Itace kalmar da take fita a bakin Sultan. Dan haka taji ba zata iya barin shi ba, dole itama yayi mata wannan son da yake ma, Hoyam tana son ya mallaka mata zuciyar shi. Dama Chamber din Hoyam babu ruwa, kuma tayiwa Narmin magana har tasaka bayin su kawo mata ruwa, ashe basu kawo ba. Dan haka tana ganin babu ruwa ta shirya sannan ta nufi hanyar ban dakin kuyangi, bata da matsala, amma yadda aka tsaneta abin har tsoro yake bata. Dan haka tana isa ban dakin ta saka bayinta suka mata kome cude mata baya suka fara. Alima da ka gaya mata ai Hoyam tana ban Dakin. Tana zuwa tasa ka mikar mata da bayin ta shiga dukar su, abinda yabawa kowa tsoro har da Hoyam cikin dariya tace musu. "Uwar dakin ku bazata iya taimakon ku ba, to bari kufa yadda zan mata." Haka ta kunce tawul din wankar da yake daure a kirjin Hoyam, suka shiga mata dariya suna dukarta, kafin kace me sun mata taron dangi, sun mata dukar Bala'i. "Ranki shi dad'e, uwar bayi. Alima ta daki Hoyam fa" da sauri suka kalli Juna da Shairah, tare da Narmin da take gurin a tsaye, bata jira abinda za ace ba, ta wuce da sauri zuwa ban ɗakin, ta sami Hoyam akwance ta suma, Alima tana murmushi, tare da kai mata duka, a cikinta tana faɗin. "Jaka! Ke har kin isa ki mallaki zuciyarshi, toh na aiki lahira kafin na sami Sultan kowa ma na mai dashi bawa na." Ture ta Narmin tayi lokacin da Narjis ta shigo, ta kuma kifa mata mari. "Lallai kina cikin azabar da tafi ta wuta Bala'i. Maza ki saka kayanki kafin Sultan Abdus Samad ya nime ki." Da sauri aka shirya Hoyam, aka fitar da ita zuwa shashinta sannan aka kira masu kula da lafiyar matan shashin, kafin kace me, maganar ya yadu har Chamber Sultanah. Tayi farin ciki, amma kuma ta danyi shakkar abinda Alima tayi, dan haka tasa aka kama Alima, tun kafin Sultan yaji labarin. Sai dai abinda basu sani ba, kawai sai ganin Sultan aka yi yazo Chamber din Hoyam. Ganin halin da take ciki. Ya fusata shi ainun. Dan haka ya saka aka kawo mishi Alima, kallonta yayi sannan yace mata. "Meye kika aikata?" Zubewa tayi a gaban shi tana kuka, tare da kallon Narmin. "Sultan na cancanci mutuwa, amma kafin nan ina son na fadi wacce ta sani aikata wannan ta'asar," ta kuma rushewa da kuka.sannan ta fito da sisin gwal, a cikin wani san karamin jaka, ta zuba. "Sai da nace miki Narmin ba zan iya ba, kika sani na dake ta, toh gashi kin sani zan sadaukar da Rayuwa ta. Sultan Narmin ce ta sani." Cikin tsananin tsoro Narmin ta zaro idanu waje, sannan tace. "Kiji tsoron, Wallahi ban aikata kome ba" Kafin kace me, Narmin ta faɗa cikin maganar, kallonta Sultan yayi sannan ya nuna ta hanyar fita, tare da saka masu tsaro su tafi da ita, ita kuma Alima a mata bulala talatin ladar aikata abinda aka sata, ita kuma Narmin kar a mata kome sai an gama bincike, Hoyam kuma kulawarta ya koma hannun Narjis, tare da Shairah. Dan haka duk abinda zata yi kar a takura mata. Bayan an gama shara'ar, Sultan ya tafi da ita shsshin sa taci abinci sannan yace daga lokacin da ta ji yunwa a shashinsa zata ci abinci, kuma ta amince. --- "Amma, Shairah baka tunanin akwai wani abu a kasa, taya Alima zatayiwa matar da muma mun same ta da aikinta haka?" Inji Narjis. "Yau naga abinda ya fi zare tsayi, Yo ku mata kaidin ai sai a hankali, kawai tayi haka ne sabida dalilin kanta, tayu kuma sakata akayi, tayi kuma ita tasaka kanta." Kus-kus suke maganar, har na wani lokaci, sannan suka isa shashin Sultanah, kallonta suka yi ranta a b'ace. "Waye a cikin ku ya saka Alima aiki?" "Sultanah tuba muke, amma babu wanda zai saka Sultanah aiki akan wani dalili mara hujja," Inji Shairah, "Kuma kawai anyi haka ne dan a rushe Yardan mu ne a ranki." "Toh waye? Waye ya sakata aikata haka?" Ta faɗa da karfi. Shiru suka yi, tare da sunkuyar da kansu, suna jiran hukuncin da ya dace da. ** Istanbul. Daular Umayyad Salmanu Abul Hassan Bin Abrad. Shine Sarkin wannan daular, kuma ana mulki bisa ka'ida da adalci, sannan su masarautan basu da fitina da tashin hankali, bayan haka kuma basu da magadar mulkin, sabida basu tsarin Magajiyar sarauta, wato (Empress Mother of King) kenan. Tattaunawa suke akan Taron da suke halatta duk shekara, a babban hakwatar musulinci da take garin baghdad. Sannan Sarki Abul Hassan tana son isar korafin shi ne akan yadda Daular Abbasid, suke kwashe bayi karfi da yaji, sannan kuma suna kai hare haren wulakancin ga talakawan da suke iyakar su, daukar Umayyad basu da tashin hankali. Domin suna yin kome tsarin addinin Musulunci ne, shi yasa talakawan da suke wajen iyaka suke ta dawowa cikin daular. ** Daular Abbasid. Kukan da take mishi ya tsaya mishi a ranshi, rike hannun shi tayi tare da cewa. "Sultan Narmin ba zata tab'a sawa a cutar dani ba, don Allah ka sake ta ni na yafe matar ina bukatar ta!" "Toh bar kuka haka, zaa saketa, sannan ki kula" Gyada kai tayi, tare da mikawa ta shiga ban daki tayi wanka, zata fito shima ya shigo." Dan haka suka kuma komawa cikin ruwan wankan wanda aka janyo mishi kamar wata korama, a cikin ban dakin shi... Tana fita, ta nufi shashinta, sannan ta koma gurin Sultan, ta sha ruwa. A hanyan da zata gidan tsaro, suka bangaji juna da Alima, ai kuwa ya ta yanki jiki ta fad'i. Tana shure shure. *Shin wacece ta fadi Hoyam ko Alima* BANI DA SALO! Amma ina da chakwakiyyoyi🤫🤨 #Paidbook #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: https://www.wattpad.com/1030677648?utm_source=android&utm_medium=link&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=Mai_Dambu&wp_originator=UAFVn6IqJPyhet8kdMafauzI6wppA5jaY51yBCvSwl%2FcN4uLk7Q7lAmpMHMD0fir5Z6QacntpbxI11YFe%2Fi%2BDwUpDABGp7ATfdvnLZHFieJDX6S1r%2FtPBG4sMaCfMkGe *_ᎠᎪႮᏞᎪᎻ BIYU_* _The Historical_ ~BOOK ONE~ Bismillah Rahamani Raheem Page 4... A razane Hoyam take kallon Alimah da ta yanki jiki ta fad'i. *Me take nufi?* Kafin ta bawa kanta Amsa, Alimah ta danna wani irin ihu da yaja hankalin masu kula da shsshin su, shigowa da gudu. Jini ne ya b'ata inda take da jikinta, kuka take tare da nuna Hoyam. Wani irin tsoro ne ya kamata, dan dole ta zuba mata ido, haka Narjis da Shairah suka saka Bayi mata suka dauke ta. Ita kuma Hoyam aka tasata keyarta, zuwa gidan Yarin, domin ta aikata laifin zubda cikin jikin Alimah. Kafin kace me har sun ririta alamarin zuwa babban al'amarin da har ya kai kunnen Sultanah. Take tasaka aka kamo Hoyam, aka kai ta Fadar Sultan, aka fadi abinda tayi aka kuma kambama al'amarin da yana cikin tsinuwar da aka yiwa masarautar akan Sarki ya b'oye. Dole aka tura Hoyam horo me tsannanin na tsawon sati biyu. Tare da hukuncin ba zata kuma zama babban shashin ba, sai kebantaccen shashin dake wajen masarautan, a can zata yi wa'adin da aka diba mata. Wannan abun da suka yi yayi mugun fusata ta, dan haka tana kallon Sultanah irin kallon sai na miki kwatankwacin abinda kika min, sai na rama sama da abinda kika min. Bayan tafiyar Hoyam, Sultanah Fazilatul nisa tasaka aka kama Alimah, tare da dauketa cikin masarautan baki daya, tare b'atar da ita baki daya. Bayan sun mata wulakancin na fitar hankali, aka mata barazanar kada ta kuma dawowa cikin masarautar idan ba haka ba, zasu kashe ta. * Bayan an rufe Hoyam, bai hana Sultan Abdus Samad zagawa gurin Hoyam yana rage daren shi a gurinta har ta gama kwanakin da aka diba mata. A hankali kome yake tafiya har bayan wata biyar, aka sami labarin Hoyam tana da ciki, wannan shine dalilin da yasa aka dawo da ita cikin masarautan sannan aka bata shashi me girma irin na Sultanah Fazilatul nisa. Tunda Hoyam ta sami cikin ta shiga bada wani irin umarni wanda shi kanshi Sultan. Ya kasa magana akan haka, emirate councilors sun so dakatar da ita, sai ya kasance Sultan ya bata kariya, A hankali cikinta na girma matsalolin masarautan na kara girma, har cikin ya isa haihuwa. Wata daren ƙaramar sallah ta haifi Yaronta namiji kyakyawa dashi, tun da aka d'ago mata yaron ta ganshi, aka kuma fitar dashi gurin Sultan, ya mikawa babban Limamin masarautan, yayi mishi huduba. Bayan Sultan ya gaya mishi sunan shi. ** Tunda aka fara shagalin suna sai da akayi sati Daya ana abu daya, sannan aka tsagaita. Matsalar da aka fara samu, shine Sultanah Fazilatul nisa, tana masifar kawo tarnaki akan Aamaan, wanda har ya kaita tayi tuntuben harshen cewa. "Tunda ka zaɓe ta sama dani, sai naga bayanka har ita ɗin." Akan wannan furucin, sai da aka dakatar da mahaifinta, wanda haka ya fi mishi sama da ace baiwa ce ta kori yar shi daga cikin gidan da yake saka ran shine zai mulke ta nan gaba. Haka Hoyam ta cigaba da baza mulkinta har ta kai, ta sauke wasu gwamnoni na cikin yankunan kasar, ta dauko yan ƙabilar ta, ta daura. Kasancewar itace mahaifiyar Crown prince yasa babu wanda ya dakatar da ita sai Sultan. "Hoyame! Bana son kina shiga sha'anin mulkin na, nasan d'anki shine zai zama sarki anan masarautan, dan haka ki bar shiga harkokin cikin masarautan!" Cikin kirsa da kisisina, tace mishi. "Toh shugabana, duk abinda ka bukata haka zanyi, tuba nake ya shugabana!" Yadda take maganar tana matse kwalla yana cikin abinda yake masifar sosa mishi rai, dan haka ya rungume ta, yana gaya mata sabida akwai masu Niman bayan su ne, idan aka ce yau tana shiga harkan mulkin shi tabbas zasu ga gazawar shi. Shi kuma baya fatan samun haka, kafin kace kwabo Sultan da Hoyame, sun lula wata duniya na daban. *** "Amir Ansas! Baiwar Sultan tana min kama da wani anan masarautan." Inji Amir Fujai, "Bani daya na fahimci haka ba, ba kowa bane sai Ghanim, wannan Mutumin.." Da sauri yayi shiru, tare da juyawa yana kallon Inuwar mutum ya juya da sauri, take yasa aka bi bayan mutumin babu shi babu dalilin shi. *"Hmm! Ina sane da abinda yake faruwa, amma kuma taya kuke ganin zamu kawo karshen Abdus Samad, sannan taya zamu iya samun damar mulkin kasar nan bayan shi kanshi yana da magaji, sanan itama Hoyam din ba kyaleta zai yi ba" Kallon Abdul Mannan suka yi sanan suka ci-gaba da cewa. "Dole zamu bada damar canja wurin da kome, amma Sultan kan dole mu idda aikin mu akan shi, koda taimako ko babu taimako, sannan.yadda aka wulakanta mana mahaifi dole mu tsaya domin kare mutuncin shi." Haka suka bar wannan batun tare da tsayawa ka'in da na'in, kowani kusurwa na masarautar kowa burin shi ya zama shine magajin Izzah, dan anyi Mamakin yadda Sultan Abdus Samad yakai wannan lokacin. Ba tare da an sami matsala ba. Sanan kuma wani abun da ya d'aga hankalin mutanen da suke harin karagar, ba kome bane. Sai wayen gari da akayi Sultan Abdus Samad yana maida duk wani kundin tsarin mulkin ƙasar tare da da saka sunan Aamaan shine sarki na gaba. Tare da maida wasu abubuwan da ya kasance nashi izuwa na Hoyam da Aaman. Babu wanda ya saka baki ko ya nemi dakatar da Sultan, sai dai daga kulawar da ake bawa, Hoyam da Aaman. Sultan ya gayyace Yan uwan shi a wani liyafa. Wanda ya bayyana Hoyam a matsayin Matar shi da zai aura, wannan shine mafi kololuwar tashin hankalin. "Na gabatar muku da ita ne domin kuwa gobe Insha Allah zan aureta, kuma itace Sultanah Hoyam." Kallon shi suke cikin fusata, amma babu wanda ya isa bayyana fushin sa, tare da gabatar da b'acin ranshi bisa ra'ayin shi. Amir Kaisan yace. " Ya kai d'an dan uwana, kasan kuskuren da kake cilla rayuwarka ciki kuwa? Wannan shawarar bata dace da wannan tunanin ba, kayi min afuwa amma tabbas akwai abinda Hoyam take nufi da ta shigo rayuwarka! Ita din Y'ace ga Ghanim, mutumin da ya ciyar da Sultan Aamaan dan uwana, tare da matar shi Sultanah Sajiyah guba, ga ta nan tambaye ta.?" Juyawa yayi yana kallon Hoyam,. wacce kwalla ya shiga zuba mata. Dakyar ta bude baki tace. Sultan! Baka yarda dani bane? Kai ka sayo ni, kuma ka..." " Ya isa tashi kije zan zo yanzun." Tana tashi ta rungume D'anta tana kallon su baki daya, sannan ta lashe bakinta, hawaye na zuba mata. Tabar gurin. Tunda ta tashi aka fara cacar baki tsakanin Sultan wanda shi kan shiru yayi musu, duk abinda suke fada ana jin su, karshe haka suka mishi barazanar zasu kashe shi, idan bai dakatar da auran Hoyam ba. Fita yayi daga cikin su ya dawo shashin Hoyam, a daren ranar ya rubuta takardan dakatar da duk wanda ya gayyata aka ci abinci dashi. Haka ya kwana zuciyar shi babu dad'i. Sannan wani abun da zai baka mamaki, ya washi gari yana tashi bayan an dakatar da mutane, sai ya bawa Hoyam damar tayi magana, tunda ake a tarihin masarautan ba a tab'a cin zarafin emirater councilors ba sai a wannan lokacin. Haka suka yi hakuri tare da ɗaukar abinda yazo musu, dole suna shiga kyakyawan shiri akan Sultan da Hoyam. Wai akace wanda ya shirya ya shirya wanda bai shirya ba dole ya fadi, domin an daura auren Sultan da Hoyam, wanda ya sanya Sultanah Fazilatul nisa. Haukacewa kamar ba me cikakken lafiya ba. Abu goma da ashirin, an dakatar da mahaifinta, sannan ana cikin wannan yanayin aka kuma bankad'o wani abinda ta aikata, wato koran Alimah daga masarautan. Da kuma saka Alimah yiwa Hoyam sharrin ta zubda mata cikin karya. Wannan abun shi ya kara dagula mata lissafi, Domin Sultan ya bawa Hoyam damar tayi duk abinda ya dace. Amma banda kisan kai. Dan haka tace. "Zunubin da suka aikata zai kawo su gabbar da za'a hukunta su" wannan abun da take yana masifar burge Sultan Abdus Samad. Abinda yayiwa Sultanah ba wani abu bane sai haramta mata shiga duk wani abinda ya shafi cikin masarautar kasancewar ta yar magajin sarauta yasa aka d'aga mata hukuncin. Aikuwa Sultanah ta fusata tana faɗin. "Sai na kashe ka Abdus Samad, tunda kasaka wulakantacciyar Baiwarka ta wulakantani. Insha Allah matukar ina raye sai na kashe ku. Sai na tozarta ku, sai na dasa muku bakin ciki a rayuwarku, ke kam wallahi ki kiyayye abinda zan miki, domin zan sanya miki bakin cikin da yafi guba illa," da ace Sultanah Fazilatul nisa ta san Illar abinda take cewa, da tai hakuri ta kyale su. Dan haka suka fitar da ita tana, ihun tare da ɗaukar alwashin sai ta girgiza masarautan baki daya. Sam haka bai dame su ba,, domin a hankali Hoyam ta juya kome ya koma nata, ya dawo karkashin kulawar ta, sai da takai ta kawo Sultanah Hoyam ita ke umartan Sultan wanda shi kuma ya fara goce mata. Haka ya matukar girgiza mata zuciya domin bata kawo hakan zai tab'a ta ba. --- bayan wata biyar Sultan ya fara rashin lafiya, wanda ya haɗa da tarin jini, abinda na daga mata hankali kenan, domin ana kiyayye abincin shi da na shanshi. Asalima baya cin abincin kowa sai dai ya girka da kanshi. Hoyam aka fara zarga, shi da kanshi ya wanke ta, domin tunda yake da ita bata tab'a ko dafa ruwan zafi ba, dan haka ya wanke ta Sosai. Duk da ta kasance da tana jin haushin sa amma haka bai tab'a sakawa ta cutar dashi ba. Haka ya cigaba da jinya, wanda aka yi nasarar fahimtar an kawo mishi kyautar wasu kayan alfarma a jikin su aka sami gubar, dan haka aka fara binciken mutanen da suka kawo kayan ba a same su ba. Dakyar Allah ya kwace shi daga wannan gubar. Yasha jinya sosai, lokacin Saman yana da shekara daya a duniya. Dan haka suka dauki soyayyar duniyar nan aka daura mishi. Gefen yan uwan Sultan da ita kanta Sultanah suna shan alwashin kashe ahalin sultan Abdus Samad. Dan haka cikin murdaddiyar yanayi aka wayi gari. Tare da kama Sultanah Fazilatul nisa a dakin Sultan da katon wuka. Hannunta duk jinin shi, tayi mishi kisar gilla, wanda ya fusata Hoyam da ta rasa mijinta, take aka fidda Sultanah daga cikin masarautan, sannan wani abun da ya daurewa kowa kai yadda take rantsuwa wallahi bata kashe shi ba. Ba ita bace tayi kisar, itama ta samu bai cika bane tayi kokarin cire wukar amma ba ita bace. Lokacin da aka fara bincike, masu tsaron kofar shi sun tabbatar da ita ce ta shiga. Dan haka babu wanda ya shigo kafin ita, amma sam taki yarda..dole aka kaita haramtacciyar Fada aka ajiye ta, tare da Alimah da Narjis da Shairah,. Wacce itama aka samu itace tayi sanadin kawowa Sultan kayan da yake da guba, Sannan aka rufe kundin tarihin su.. Ranar da akayi jana'izar Sultan ranar Hoyam ta canza duk wani tsarin masarautan, aka yi garambawul da wasu abubuwan, ta kwaso kabilar ta. Ta watsa su cikin tsarin mulkin masarautan. Sannan Yan uwan Sultan da suna ki mishi mubayi a, suka mata. Sannan tare da goyan bayan mulkinta. Bayan sun yi haka da wasu kwanakin aka tsinci gawarwakin su, sakamakon zasu yi juyin mulki, Dakarun Sultanah Hoyam suka bude musu wuta. *** Birnin Kisra. Babbar kasa ce da suka shahara a harkan sihiri da tsafi, dan haka suke Baje kolin baiwar su. Guri babban bokan kasar Amir Hood da Amir Kaisan tare da Fujai, suka zube a gaban shi. Dariya yayi sannan ya kalle su, sanan ya nuna su sa yatsa. " Ba zaku tab'a mulki ba, ba zaku tab'a dakatar da wanda ya shirya yaki ba, amma zaku iya samun damar shiga tsarin mulkin ta karkashin kasa, shima lokaci ne zai baku damar haka. ...kai Fujai da Kaisan, mutuwa zaku yi irinta wulakanci da kaskanci, kai Kuma zaka yi dogon zamani, amma bakin ciki zai kashe ka. Kamar yadda ake mutuwa a cikin sahara idan ruwa da guxirin suka kare, haka idanun kowa zai bude, shekara bayan shekara zata bayyana kanta, babu alamomi ta, amma tabbas wannan mulkin mallaka zaku rasa shi, za a shafe kome zai zama tsarin Ubangiji shine sama da kome. Kamar yadda kuka zalinci kanku haka kome zai zo, ya faru... Acct: 0472282105 Ramlat Abdulrahman Manga GTBNK! +2347035133148 zaku iya tura shaidan ta Number Zahran Adda Ramlat, #Paidbook₦200 nafi son ta bank, katin mtn 300₦ #Mai_Dambu. [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: https://www.wattpad.com/1031122018?utm_medium=link&utm_source=android&utm_content=share_published 🐾*_ᎠᎪႮᏞᎪᎻ BIYU_*🐾 _The Historical_ ~BOOK ONE~ Bismillah Rahamani Raheem Page 5... "Karya kake mushiriki! Karya kake Azzalumin mutum, Ni ba zan yi mutuwar wulakancin ba, nawa Amir Hood ya biyaka? Ni zaka kalla kace mutuwar wulankanci zamu yi?" Murmushi kazugumin bokar yayi sannan ya cigaba da cewa. "Kaisan ka haifi d'a namiji! Amma ba zai hana ka mutuwa ba, haka kai ma Fujai." Hawaye ne ya zubo daga cikin idanun su. "Mafi yawancin ku, zaku mutu ne da tabon cin amanar juna, ku kiyayye abinda kuka aikata, kai ma Hood baka tsira ba, domin gwara su mutuwa zasu yi, kai kuma kaskantacciyar rayuwa zai ayi har lokacin da zaka sami damar sarrafa abubuwan da dama, zaku iya tafiya." Silalar zinari suka bada, sannan suka bar gidan, zuciyar su cunkushe da tashin hankali, musamman Fujai da Kaisan, da zaka tsaga jikin su, zaka samu babu jini sai zunzurutun tashin hankali. Babu abinda suke tunawa sai bayansu. Wato yaran su, tashin hankalin da yake nukuskusa zuciyar su ba a fada. Amma tabbas suna tsorace da abinda zasu je su tadda a gida ba. Dan haka suka kalli Amir Hood. "Tabbas daga yanayin da muke tinkarar Daular mu, na Fahimci akwai tashin hankali a cikin shi. Duk da bamu san meke faruwa ba, amma don Allah ga Yarona da baida Uwa sai ni ne Ubanshi nine Uwar shi, na haɗaka da Allah ka sanya min ido akan rayuwar shi." Inji Kaisan yana zubda hawayen bakin ciki, haka ma Fujai ya bada d'an shi da matar shi. Suna kuka suna kome haka suka iso birnin Samaind, suna shiga kofar masarautan, aka zagaye su. Tare da kama Amir Kaisan da Fujai, aka tafi dasu. Shi kuma Amir Hood aka wuce dashi fadar Sultanah. Wacce take zaune bisa kujeran mulkin masarautan. Yana shiga ya zube a gabanta, yana cewa. "Rayuwata da kome na mallakar ki ce Sultanah Hoyam, kiyi duk abinda kike so koda kuwa sare kaina zakiyi ina shirye na sadaukar da numfashina domin ki" Sai da tayi shiru na wasu dakikai, kafin ta tsura mishi ido, sannan tace mishi. "Kuskuren ku daya ce, na bincike akan wanda ya shirya yaƙi? Dan haka ba zan hana walwala ba, domin barin makiyi a raye shima wata nasara ce da Ni'imar rayuwa, zan Barka ka rayu a cikin yanayi mafi kaskanci, ga dai mulkin ina kanyi amma babu wanda ya isa dakatar dani. Dan haka kuyi hankali dani, domin zan iya shafe dukkan larabawan wannan daular na zuba kabilata" D'aga haka tayi alama da hannu a dauke shi ya bar mata fada. Da wannan damar Sultanah ta cigaba da mulkinta, har tsawon shekaru masu yawa cike da zalinci da azabtar da duk wanda yaki mata mubaya'a, sanan ta kuma kange danta da kowa, domin ko cikin mutane bata barin shi ya shiga ita ke tare dashi. *** Aaman na da shekaru goma, aka gina wata (castly) kamar gidan sama ne kamar me, mafi girma da tsawo, wanda ita kanta Sultanah tayi shine sabida D'anta, ta kuma yi nasarar nisanta shi da al'ummar mutanen kirki. Sai ma wasu Yara irin shi aka kawo Darakshan da Kuma Fudail, duk da an kawo su, iya kansu. Akan abinda zai yi ne ba yaki, bayan nan basu da hurumin shiga koda babban falon shi. Kuma duk da kasancewar su a cikin gidan bai saka ya kalle su a cikin masu sanya shi farin ciki ko abokan hira ba. A hankali ya tashi cikin kaɗaici sosai, bai da abokin tarayya bai da abokin hira, ya tashi cikin wani irin miskilanci da mugunta, domin an zuba mishi dakaru sama da dubu dari shida masu kula da lafiyar shi, sannan a gurin ake bashi horon yaki na fitar hankali. Domin an cire mishi wata shashi na musamman, domin horon yaki. Yana da shekaru sha tara, aka fara mishi gwajin lafiyar shi na d'a namiji ta hanyar kawo mishi yan mata, masu rufaffen fuska, yana kwanciya dasu. Shi kan shi daga lokacin ba zai iya tuna me ya faru ba, amma sam bai da ra'ayin kasancewa da mace, bai san yawan yan matan da ya kwanta dasu ba. Sai dai kuma wani abu da ake zargin shi musamman Sultanah Hoyam. Wato mahaifiyar shi. Shine idan aka kai yan matan, haka zai a fita dasu, dan wani lokaci yana gaya musu bai da lafiya, ya fara wannan salon ne daga lokacin da ya hadu da yarinya take gaya mishi don Allah kar ta mata kome ita makauniya ce, satota aka yi, itace yarinyar da ya kyale ta, bawai dan yana tausayin ta ba, sai dai wani irin yanayi da yake jin yana cikin koshin lafiya ya rasa macen da zai kwanta da ita, sai miskiniya. Haka kawai ya saka kyamar kwanciya da Yan matan, daga karshe aka fara zargin ko yana luwadi ne, kuma masu kula da lafiyar shi basu tab'a ganin shi da namiji ba. Haka Ya tashi babu abinda ya sani sai mugunta, domin kuwa idan aka kawo mishi matan, hana su shigo mishi turaka yake. *** Bayan shekaru talatin da biyar, "Wai ku nan zaku iya ja ne da Sultanah Hoyam?" "Khabir baka da hurumin magana akan Iyakokin mu, ku sa kuke da lusarin magajin sarautar ku,sannan ita kanta Sultanah Hoyam din wacece ita? Ko ance muku bamu sami labarin irin mulkin mallaka da take yi bane? Dan haka karka fara shiga iyakokin kasar mu, sannan bakin haure da suke shigowa ba zamu dakatar da su ba, sabida son zuciya irin naku, idan kuna son mu tsaya akan ra'ayin ku, ku sauke mace a mulkin ku" "Zulushimalain! Karka gaya min maganar banzan kai waye kai." Cikin fusata fadawan daular Umayyad suka far musu sai da suka kashe su, sannan suka bar Khabir. "Ga sako nan! Ka kaiwa wancan Yarinyar, ka gaya mata mun shirya tsaf domin kare kasar mu, idan ta kuma ihu kamar kare zamu mata kisar gilla." Bayan sun gama suka sari cinyar shi tare da daura shi bisa raƙumin da tarin dukiya, suka kuma hada da Zungurerren takardan cin mutuncin da fusatar zuciya. Lokacin da magatakardan masarautan ya fara karanta lafuzan da aka rubuta a takardan, wani irin tsoro ne ya mamaye zuciyar shi da ruhin shi, zuɓewa yayi tare da fashewa da kuka yana fadin. "Kaicona na shiga uku na lalace, me yasa suka rubuta abinda ba zan iya karantawa ba, na tuba shugabana kiyi min rai ki karamin nisan kwana." "Hmm!" Tayi mishi alamar ya cigaba da karantawa, haka yana rawa tare da makarkata, yake karanta labarin yana zubda hawayen, har ya gama karantawa.mikewa tayi tare da barin dare bata ce kome ba. Sai da aka kwashi kwana goma ana zubawa Sultanah ido akan abinda zata aikata, kawai tasa aka tura musu da sakon. *Ya kai karamin mutum! Kazo daulata ka bani hakuri tare da durkusawa a gabana, Ni kuma Sultanah Hoyam Ghanim zan maka afuwa na yafe maka! Rashin bin abinda nace zai iya zama tashin hankali a dukkan Daulolin guda biyu* Wannan wasikar kaskancin da aka tura ga Sultan Abrad, yayi masa zafi domin bai san abinda ya faru ba, kawai shima ya saka aka rubuta mata na cin zarafin ta tare da bakakken magana da har suka kira ta, da koriyar macijiya. .... Wannan dalilin ya saka aka fara shirin yaki, inda Sultanah ta shirya dakarun miliyan uku da dubu dari tara,. Lokacin da yan leken asirin Daular Umayyad suka sami labarin, take suka tura. Aikuwa dole hankalin mutane ya tashi aka korafin babu yaƙin da za aje kodan Albarkacin mutanen da suke zuwa niman mafaka, Sultan Abrad ya duba maraicin su ya nime sulhun. A take ya shiga niman taimako yankunan jazziratul Arab emirate, su bashi hadin kai domin yakin da Sultanah, duk suka ki, karshe Sarkin Yeman Abul Hassan shi ya turo mishi da wasikar cewa ya nime sulhu.. dan haka ya shiga niman hanyar da zasu dai-daita. Dan haka ya shiga niman.mutanen da zasu tsaya mishi. Karshe Amir Abdul shakoor na kasar Dubai, shi ya gayyace su, tare da wasu sarakunar larabawa, aka shiga tabirin sulhu, dakyar aka samu Sultanah ta sauko dake ta tura wakilanta ne da yadda zasu ja, kafin aka yarda. Suka dai daita inda suka nime Abrad ya bada Kanwar shi Azizatul Nissah. Bayan nan kowa ya kama gaban shi. Hankalin Sultan Abrad ya tashi ainun, domin baya kaunar ya bada Kanwar shi, dan haka sukayi ta tattaunawa. "Bamu da zab'i! Bamu da iko! Dole mu dakatar da Iran, zubda jinin ya isa haka, Jama'ar mu!" Ya karshe maganar a raunane yadda zai fahimtar da kai yana cutuwa daga halin da al'ummar shi take ciki. Cikin nutsuwa mutum min da yake gefen shi ya sunkuyar da kan shi yace. "Allah ya taimaki Sultan Abrad! Ina gani ka basu ƙanwarka tayu a kawo karshen rikicin dake tsakanin masarautu biyu!" Watsar da kayan dake yake gaban shi yayi, tare da rintsa idanun shi kan mutumin da yayi maganar cikin tsawa yace. "Murad kayi hauka ne? Ka haukace ne? Toh bari na gaya maka, wannan yarjejeniya ce idan baka sani ba, ba zan tab'a daukar kanwata Almira Ashnah na bawa wancan Mahaukacin ba! Kasan me suke nufi idan muna son a janye yakin dake tsakanin mu? Na basu kanwata su mai da ita baiwa, akan me zan taso daga daulata nazo nan Dubai nimar baiwa da zata dace da gidan mu. .... Ruwanka ka zab'a min kyakyawa! Ruwanka ka barni na zab'a da kaina. Amma ka tuna Daular Larabawa sunki taimaka mana, sabida kowa yasan kasar Farisa da fitina.!" Daga haka ya saka kai zai fita, aka kwankwaso kofar dakin. Kallon Murad yayi, da sauri ya buɗe kofar dakin wani mutum sanye da kaya fuskar shi a rufe ya shigo dakin. Kallon Juna suka yi da Sultan Abrad, shi kuma ya kalli Murad ya fita da sauri, har yana tuntube. Rufe kofar yayi sannan ya zuba mishi ido. "Har yanzun baku nime hanyar sasantawa da kasar Farisa ba ko? Toh kuwa yaki zai ci kasar ku, dubanin dukiyoyin dake cikin masarautar zata lalace, kasa zata sha jini. Sannan mata zasu zama zawarawa, yara zasu zama Marayu. Bamu son ƴa me yanci! Baiwa muke nima! Baiwa muke so! Idan kuka bamu ƴa ba zata iya zama shiru ba, bamu bukatar sarauniya a cikin masarautan, sarki kawai ya ishe mu!" Mik'ewa mutumin yayi zai fita, Abrad ya rike hannun sa, cikin damuwa. "Ka taimake ni! Idan ban sami baiwar ba ya zanyi! Wallahi bana son azubda jini a daulata!" murmushi mutumin yayi sannan yace. "Ina da wani dan Safara a nahiyar Afirka yanki yammacin su, akwai kyakkyawan mata a gurin, amma ba asalin kyakyawa muke bukata ba, domin bamu son soyayya ta tsaga tsakanin zukatar mutanen masarautan." Wani wawan ajiyar zuciya ya sauke, sannan yace mishi. "Toh! Waye shi?" "Yana kasar Andolus! Shaibaan. Dan kasar Saudiyya ne," Cikin yarda da ƙaddarar su, Abrad yace. "Yau ashirin ga watan Agustan, Insha Allah kafin watan goma na wannan shekarar, zan turo muku ita cikin daular ku. Indai haka zai kare zuciyar da take cike da kaunar Juna, nayi alƙawarin haka." Ya faɗa tare da jaddadawa akan shi abinda yake da Muradin faruwar shi. Bayan fitar mutumin da basu san fuskar shi, take suka fara hada shirgin su, tare da jin sun rabauta daga wannan yanayin. Dan haka suka nufi daular su cike da kwarin gwiwar abinda zasu iya aikatawa. ** Gezira Sudan. Wata karamar gari ce, wacce take tsakanin blue sea, gari ce da a da can baya ake kiran ta da. Jazira, daga baya aka maida ta gezira, mafiya yawancin mutane yankin makiyaya ne, masu kiwon shanu da rakumai, kasancewar garin yana tsakanin ruwa ne, kuma ga shi ana hidimar cigaba ga lambuna da kuma inda makiyayya sune kiwon su. Babu tashin hankali sai yawaitar Arziki da cigaba, dan wani lokaci idan akwai tashin hankali babu Cigaba da ake samu. ..... Watsa min ruwa yayi na sake murmushi, tare da kallon shi, girgiza kai nayi ina wanke tufafin Baffana. "Ikram!" D'ago idanuna masu kalar ta mage nayi na kalle shi, "A duk lokacin da na kalle ki tsoro kike bani" Mai kai na nayi tare da cigaba da aikina. Dawowa yayi gabana ya amshi wankin hannuna, "Ikram! Ina ji a raina wata rana zamu kasance tare, amma bana jin zamu yi tsawon rayuwa a tare." Nan ma ban kula shi ba, sai da na gama dauraye kayan na nafi gurin shanya. #paidbook #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: https://www.wattpad.com/970384685?utm_source=android&utm_medium=link&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=Mai_Dambu&wp_originator=l43AacEqBsPiLlYx5dhUheB%2F6jOni0C%2FxhyeNcS9TpekWSOB8YCl6xXvPHaqW4bRGWROavXnJPdrwFm8rAjS2tmZwTvI3QQgXPSh3Q6sUDHNdzt%2FH%2BdwCgongFSjFBz5 ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 _The Historical_ ~BOOK ONE~ Bismillah Rahamani Raheem Page..6 Sake shan kaina yayi tare da cewa. "Zuciyata tana yawan bugawa idan na kalli kwayar idanun ki! Ina ji a raina ban cancanci." "Noman!" Na ambaci sunan shi a sanyayye, kafin na cigaba da aikina. "Ikram!" "Me kake so nace? Ina kowani abu ne dan kare kai na kimar mahaifina, baka ga yadda Matar shi ta mai dashi ba? Ina ma zan iya goge zanen ƙaddara ta da kake hangowa! Ina ma zan iya fuskarta Gobena da kake hangowa. Banda sakewa na baka kai na shine abu mafi muni da Zubewar kimata,Noman kai ne mutum mafi kusanci da ni, don Allah ka bar azabtar da ruhina" Amsar kayan yayi a hannu na, tare da kallon cikin idanun ta. "Sirrin kyanki yana cikin kwayar idanunki, ba kowani cikakken mutum bane zai fahimci ainihin sirrinki, Ikram ina miki kaunar rai da rai ne, wallahi na rantse da Allah babu macen da zan iya sadaukar da rayuwata akan ta ba sai ke!" A hankali ya tako gabana, har numfashin mu yana jauraya da juna, yana kallon cikin idanuna. "Tsarki ya tabbata ga Allah madaukakin sarki, da ya halicce mace mafi kyawun idanun a cikin wannan nahiyar tamu, Ikram kina tattare da sirri na musamman." A hankali ya lallubo hannuna, ya kai saman fuskar shi. "Ba dukkan mutane suka san meye So ba, so yana karewa. Amma kaunar da nake gani cikin kwayar idanun ki, ya ishe ni." A hankali na zare hannuna, tare da amsar kayan hannun shi, na bar gurin. Tare da tattara kayan baki daya. Ina tafiya yana bin bayana. Tare da wakokin yabo da wasu baitoci.. (Yawwa toh wallahi zanyi waka. Kar kuma ce muryan ba dad'i 😻 _So da kaunarki ya mamaye zuciya da ruhina_ _Mafarkin zuciyata ke ce!_ _Muradina taki ce_ _Kece kaunar zuciyata_ _Ruwa da iska, dare da rana_ da kaunarki nake kwana_ _Abar kaunata... Kin zame mini farin wata na! Farin ciki na, maganin bakin ciki na_ _Murmushinki maganin bakin cikina! Dariyarki maganin kuka na!_ _Abar kaunata ki kaunace Ni Ko zan samu daman kiran kaina namijin Soyayya_ Juyawa nayi ina dariya, sannan nace Mishi. "Kana da kyan hali, kana da dadin mu'amala, kana da kyakkyawar alaka da mutane. Rayuwata fansa ce ga rayiwarka! Amafin rai a ji dadi, amfanin numfashi na, fansan ranka, murmushin ka magogin bakin cikina, Rayuwata da duniya ta zan tattalin shine domin ka, Mu gina rayuwar mu da kaunar mu, har karshen rayuwar mu" Haka kawai naji kwalla na zuba min, tare da kara yawan shi. Takowa yayi tare da kallona. "Idan akwai abu mafi daraja da nasamu kece, na same ki a lokacin da nake bukatar ki." Saka hannun yayi tare da gogen min kwalla, da sauri muka juya sakamakon kirana da Airan take. Da sauri na dauki sandar da nake kiyo dashi, tare da kora tumakan da na tawo dasu, tare da wankin Baffa. "Noman sai mun hadu a makarantar dare." Da sauri na bita, tare da koran dabbobin. "Airan lafiya." Tana haki, "Baffa!" Da gudu muka rufa hanyar gidan mu, muna isa muka same shi a kwance, cikin kazamta domin ya b'ata jikin shi. "Mamma baki ga ya b'ata jikin shi bane?" Cikin wani irin kallo.tace min. "Na gani, kawai ban gadama na gyara shi bane." Haka na fito jikina sabule, na koma dakin shi na saka Airan, ta kawo min ruwa a wani katon mazubi, sannan na shiga goge shi, tare da kwashe kayan ta fito, taga garin ya fara duhu,kwalla ce ta zubo min, ina kallon yadda garin. A hankali nake tafiya har na isa bakin rafin na fara wanke kayan, ina gamawa na dauki kayan da sauri na dawo gida, dan a tsora ce nake da gurin, kasancewar nasha samun labarin an tare yan mata a gurin an musu Fyade, sai abin ya bani tsoro. * Ikram Almustapha, shine cikakken suna na, mahaifina makiyayyi ne, kuma bakin Balarabe ne, kasancewar muna da alaka da larabawa, yasa dabi'ar mu sak da bafulatanin daji, sabida kakana da ya haifi Mahaifiyata Yazeed Balarabe ne na kasar meroccon, Dan haka Mahaifiya ta fara ce sol, mahaifina ne bakin fata, mahaifiyata ta rasu sakamakon dogon nakuda, ta barni da kanwata Airan, sai ni Ikram. Bayan rasuwar ta ne ya auri Mamma me sunan Kanwal, tunda ya aurota matar nan ta daka rayuwar mu, uku ta kuntatta mana, amma a haka muke rayuwa. Mahaifin mu yana da hakuri, tare da kauda kai. Shi yasa matarshi take cutar mu, sai dai yace min. "Kuyi hakuri, Allah zai duba maraicin ku, Ikram Insha Allah ba zaki gushe ba, sai Allah ya duba miki rayuwar ki, duk inda kika yi Allah sai ya kare ko da karfin ikon shi. Kayu hakuri Allah zai albarkaci rayuwar ku." . Wannan shine kalaman shi a kullum, lokacin da Baffa ya aureta yana da dabbobin shi, amma daga baya duk ya kare, ba tare kwashe su tass. Mu biyu Baffa suka haifa shi yasa yake nuna min lallai duk wuya duk rintsi kar na sake na rabu da Airan. --- koda na dawo na shanya kayan, na duba madafi babu abinda zamu ci sai guntun tsakin alkama, ita na watsawa ruwa ba wanke tare da hada wuta na turara shi, bayan na samu yayi..na juye mana, wani kwano na dauka me dauke da maikon mai. Na zuba mana a cikin na juya, tare da ɗaukar kwanon na kawo daki, a hankali na shiga hurawa Baffa ina bashi. Sai da ya koshi, sannan na raba mana, nida Airan muka ci sauran. Tare da kallon ta, dan abincin babu yawa, kawai sai na tsame hannuna na bar mata, nasha ruwa na kwanta. Noman Anwarulkharim, shine sunan saurayi na, mahaifin shi ne hakimin garin mu, Noman shine d'a na uku, a gidan su. Yana da yayu mata biyu da kanen biyu, Babbar Yayar su, Malikah, Ajeebah, sai shi. Kanen shi, Quraibah, Saghirah. Noman yana da ilmin addinin musulunci, da kuma ilimin duniya, domin duk cikin yankin mu babu wanda ya tab'a fita wata duniya yayi karatun su, sai shi. Duk da dai daidai gwargwado ilimin addinin mun iya kuma muna yaki da jahilci. Noman malamin mu ne a makarantar masu jan kunne, duk da a lokacin mun iya Rubutu da karatu, a yanzun haka na kusan hada Alqur'ani, a gefe guda. Ma ina da ilimin litattafan addini, burin Baffa na kenan. Dan yace min Mahaifiyata, tana kamata ta haɗa Alqur'ani, dan haka nima nayi ƙoƙarin haka. Shi kuwa Noman wanda nake yawan kiran da Sayyid, mun hadu ne a wani hatsarin da ya kusan faruwa dani, matasan larunga, wasu irin matasa ne masu shegen rashin kunya da rashin mutunci, sannan sun addabi kauyen mu, bamu isa fita kiwo babu namiji ba, duk inda zamu dole mu sami rakiyar namiji, domin idan suka kama mace suna cin mutuncin ta ne, na fitan hankalin, toh ranar tun asuba Mamma ta kore ni kiwo, ina fita bakin rafi lokacin matasan sun tawo ayari guda, dan haka suka shiga ƙoƙarin rabani da mutuncina, har Allah ya kawo min shi, Tun lokacin nake kokarin b'oye kaina, amma ya nuna min shi bai san kome ba, sai so. Ya nuna min so ne yake tare shi, dan haka abinda yazo min dashi kenan, kuma nima na amshe shi a matsayin mutumin da ya dace da rayuwar. Duk da matar Mahaifina bata kaunar shi dani. Wannan shine tarihina, a hankali na juya, na saka hakarkarina. "Ikrammmmmm!" Baffa ya kira sunana. Da sauri na mike daga kwanciyar da nake na nufi gurin shi. "Baffa gani!" "Ruwa nake so zan sha!" Juyawa nayi na fita daga dakin, na dibu mishi, d'aga kan shi nayi na bashi ya sha, har zan cire ya kuma maida kanshi. Naji tsoro ya kamani, kallona yayi dukda hasken dakin na aci balbal ne, haka ya kura min ido. Kiftawa yake yana kuma kallona, abu yake son fada amma ya kasa, cewa kome. Kallon kwayar idanun shi nayi na fahimci akwai abinda yake son fada, amma bani da yancin Sanin abinda yaƙe cikin ranshi. #Mai_Dambu#Paidbook ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 _The Historical_ ~BOOK ONE~ Bismillah Rahamani Raheem Page 7.... *SAMAIND* Kallon Khabir tayi babban hannun Damarta, ta gyara zama tace mishi. "Hmm!" Zuba gwiwar shi yayi a kasa, sannan ya kai hannun shi kirjin shi yace mata. "Sultanah, mun daidaita dasu. Har sunyi mana kyautar bayi, masu yawa. Akan ki huce!" Dauke kai tayi tare da mik'ewa daga inda take zaune, ta nufi gaban tagar da yake hango mata haramtacciyar fada. "Bana jin haka da kuka yi da wata alfanu, ina ji a jikina yarda zai haifar da cin amana! Kafin kai nasan halin mutane da yawa, dan haka karka yarda ka ci Amana ta, ya kuka yi da Abrad?" Jikin shine yayi sanyi sannan ya sunkuyar da kai. Muryan shi na rawa yace mata. "Sultan Abrad zai badda Kanwar shi!" Ya faɗa a tsorace, Ta dauki lokaci tana share hannunta, sannan ta koma mazaunin ta,ta kalle shi. "Idan na kashe ka, zasu zuba idanu akai na, idan na Barka zasu kuma jin wata magana daga gare ka? Dan haka kayi tafiyar ka, idan zaka fita ka dauki wancan sakon ka tafi dashi." Jikin shi na rawa ya zube a gabanta. "Abinda kika ce shi zanyi" Mik'ewa tayi tare da cewa. "Ka kula da harshenka, domin zai iya kai ka, hanyar da ba zata dawo da kai ba. Kuma bana son na fahimtar da kai wacece ni" Tunda ta shiga shashin duk masu kula da lafiyar shi, har dasu Darakshan da Faduil. Kallon shi tayi na wasu dakikai, sannan ta debi abincin a cokali ta kai bakin shi. Buge hannun ta yayi, sannan ya dauke kan shi akan Abincin. "Aaman!!!" Kamar da dutse take magana, yaki ko kallonta. "Me yasa baka amsar tayin da ake turo maka, dukkansu bayi ne babu." Mik'ewa yayi tare da, gyara zaman alkyabar yayi cikin wani shegen miskilanci, wanda ya zame mishi kamar rayuwar shi ce, zai bar shsshinta "Aamaan ko baka da lafiya irinta maza ne?" Cak ya tsaya sannan ya gyada mata kai, alamar eh. Daga haka ya bar shashin, Indai haka ne toh tabbas akwai matsala ta wani gefe,. Wani ƙasaitacciyar murmushi ta sauke lokacin da hasashenta yazo mata dai dai dan haka a ranta taji ba zata iya daukar nauyin kula da lafiyar shi ba, dama tayi kokarin tasan ko yana da matukar bukata ga Y'a mace ne, sai kuma ta Fahimci shi irin mutanen nan ne da basu cika damuwa da mace ba, ko da yake ai baida lafiya ce ta kawo haka. Tunda ya shiga babban filin da yake hawa na biyu na castly din ya shiga juyi tare kallon Fudail. Takobi ya dauka tare da yin kan Fudail, da azabben sara, cikin wani irin zafin nama..ya goce. Cikin mugunta da mugun nufi ya shiga kaiwa Fudail sara da suka.. Tun yana gocewa har ta kai baya iya gocewa sai kare kanshi yake, "Sultan Aaman mun tuba Mehra" Cak ya tsaya, tare da cillar da takobin yana huci. Kallon kwari yayi tare da ɗauka. Cikin b'acin rai ya dauki bakar ya haɗa. Tare da sakewa inda yake koyan horo, yi yake yana kuma yi, idanun shi sun yi jajjur. Kalmar da Mahaifiyar shi ta gaya mishi ne yake kara azazzlar shi. Bai san dadin abota ba, kallon kowa yake da wata zuciya duk cikin su bai yarda da kowa ba, sai Darakshan. Domin yasha ganin shi yana yawan shiga damuwa, yazo yayi ta mishi magana, kuma har yau bai tab'a ko da cewa Darakshan sannu ba,, duk abinda yake cikin, matukar zai gan shi a gurin sai yaji ya sami nutsuwa a ranshi, domin dukkan su masu kula da lafiyar shi,. Darakshan ne ya iya mu'amala da shi.. a hankali ya juya da a sanyayye kamar wanda ya rasa lakar shi ya haura saman gidan shi. Kallon juna suka yi, tare da sunkuyar da kai. Babu wanda ya isa yayi magana sabida ko tari ba ayi a cikin gidan. Magana me tsayi basu yin shi, sai dai hiran kurame. Kasancewar manmallakin gidan baya son hayaniyar mutane, idan kaji hayaniyar mutane, toh wasan takobi ake anan ne zaka samu yana sarrafa takobi kamar wanda ya kware a filin daga. Tunda ya haura zama, ya koma tagar dakin shi, ya zauna yana kallon yadda rana take tafiya zata fadi yamma. Bai tab'a ganin yadda ake rayuwa a waje ba, shi kawai abinda ya sani ya zauna a sama, sai idan ya najin nishadi ya dauki takuba. Lumshe idanun shi yayi tare da buɗewa, ya sauke ajiyar,. Sauke kanshi yayi kasa, yana kallon tsohon fadar da ba a amfani da ita, har ya nuna alamar babu wanda ya damu da ita. Kallon wasu tsuntsaye yayi ya ga sun nutsu suna shawagi, kallon su yake yadda suke rayuwar su, sai yaji haka yayi mishi dad'i ina ma da zai sami sabon rayuwa, tabbas zai yi yawo kamar yadda yake so, shi mutum ne da yake son rayuwar bude ido, kisan shi.yana zaune a guri daya ne, Amma da ya sami damar fita kamar kowa tabbas zai zama wani abin alfahari a gurin shi ** Haramtacciyar fada. Kallon kanta take a jikin wani tsohon madubi, me dauke da yanar gizo da kura. A hankali ta taka har gaban madubin. "Sai da soyayya ake iya cin Amana, idan babu soyayya babu wanda zai yarda da wani! Shairah, madubin nan yana faffutikar ganin ya tuna min gobe na! Shairah har yanzun da sauran lokaci ko? Tabbas zan rama shekaru talatin da biyar suna cike da zuciyar da aka yasar da ita ?" Inji Sultanah Fazilatul nisa, Sunkuyar da kai yayi sannan yace mata. "Ya shugabana, duk abinda kika ce haka za ayi, amma ki cigaba da tausar zuciyar ki." "Narjis! Kinji abinda Shairah yace, wai na kara hakuri anya zan iya." A hankali narjis ta kalli. Darda, "Zaka iya shigowa." A hankali ya shigo, cikin nutsuwa ya nufi kusa da Sultanah Fazilatul nisa. "Sultanah kome ya tafi yadda kika tsara." Rabonta tayi murmushi tun ranar da aka kawo ta dakin. "Insha Allah, sai na fanshe bakin ciki na, sai na murza mulkina. Sai na hana kowa suku ni." Dariya take tare da kallon su, tana dariya tare da zama tace. "Ku dauki gwala-gwalai na ku raba a tsakanin ku, ku dauki kome na mallaka, ku kai cikin garin ku rabawa al'umma. Kuyi kyauta da sutura ta, ku kwashe kayana, ku raba karku bar min kome, Burina da muradina ya kusan cika, Alhamdulillahi." Zuba gwiwar ƙasa tayi, tare da fashewa da kuka. Tayi kuka ta kuma, tare da komawa gefe ta cusa kanta a tsakanin cinyoyin ta. Ajiyar zuciya take saukewa, sannan ta cire kanta, tana kallon su tace musu. "Wallahi ban kashe Sultan Abdus Samad ba." "Sultanah mun zan ba zaki kashe shi ba." Share kwallar tayi da bayan hannunta, kamar yarinya ƙarama tace. "Toh me yasa baku gaya musu." "Sultanah idan muka gaya musu ba yarda zasu yi ba, kuma karshe hukuncin kisa zasu yanke mana." Gyada kai tayi, sannan tace. "Zaku taya ni wannan yakin?" "Sultanah zamu tayaki matuƙar ya kama daukar fansa ce, bayan haka ba zamu iya taimaka miki da abinda ya wuce haka ba " Kwalla ne ya zubo mata, tayi ta gyada kai tana share kwalla, kafin tace. "Har raba ni da dangina suka yi" "Allah zai baki dama akan su." Haka suka yi ta rarrashin ta, tare da bata baki. *Damascu* Yau kwana uku kenan, yana zaune a fadar shi, kallon shi Sheikh Saiful Badarr, ya gyara zama sannan yace musu. "Karku ha'incin masarautan Samaind, sabida sun fimu karfin mulki, sannan koda aka ce zamu gwabza yaki dasu mune a kasa, ku basu abinda bakin ka ya faɗa, tunda kace Almirah Azizatul Nissah zaku basu." Dakatar dashi Sultan Abrad yayi, da sauri. Yana kallon mutanen fadar. "Bahhas ka tabbatar yau kun dauki ayari zuwa Andulus, karku manta ku zab'a mana mace mafi daraja, karku damu da tsannanin kyau, kawai ku nima musu wacce zata jure duk wata wahalar su." "Insha Allah, Rabbi." Haka suka juya zasu fita, yace musu. "Karku manta ku nimo musu wacce zata zame mana fansa ga kanwata. Tun bayan mutuwar Dariya bana fatan kanwata da Y'ata su kuma fadawa Matsala." "INSHA Allah." Mik'ewa Sultan Abrad yayi, tare da barin fadar, yana shiga cikin gidan sarautar ya wuce dakin da Kanwar shi take, ya same su tare da yarshi, suna zaune sai hira suke tare da yar shi, a hankali ya shiga cikin dakin, yana jin duk wata nutsuwa yana sauko mishi. Wato da ya Kuskura ya sake Kanwar shi ta shiga cikin wancan gidan, akwai matsala domin kuwa zai rayu cikin bakin ciki da tashin hankali har karshen rayuwar shi. Shi yasa da wancan me rufin fuskar ya kawo shawara ya amince. "Abbi!" "Yaya!" Murmushi yayi sannan ya tako gaban su da sauri, ya rungume su. Dariya suka saka tare da kara rungume su. "Almirah!" Murmushi tayi sannan tace mishi. "Yayana, naga farin ciki da bakin ciki a fuskar ka?" Ta tsura mishi ido, zama yayi kusa da ita, sannan ya bata labarin abinda yake faruwa. "Amma da baku amshi tayin wancan mutumin ba, idan ya kasance shi din munafuki ne fa?" Ta tambaye shi tana kallon shi. Shiru yayi sannan ya sunkuyar da kanshi kasa, kafin yace mata. "Mafita nake nima! Kuma ba lallai bane idan aka tura baiwar a sami biyar bukata, ki bani haɗin kai don Allah karki bari wani abu ya dame ki..." Mu hadu a next page Insha Allah.. #Mai_Dambu #Paidbook [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: https://www.wattpad.com/1032132293?utm_source=android&utm_medium=link&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=Mai_Dambu&wp_originator=a7uCjjAvUSJSKPRj92lkHRqYhhrfYA3lHRyw28GFKsPFnIgz2LhKAsyWyZ%2FT4tyTFv%2FZXjTsoXVfLCBqiF0Z9D8z7QeQxtX2I1QXt6H6fQgMzsSw37mphWhiwp71eIKk 🐾ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜🐾 _The Historical_ ~BOOK ONE~ Mai_Dambu Bismillah Rahamani Raheem Page 8 2in1 "Ba mafita ka nima ba," Zuba mata ido yayi sannan yace mata, "Mafita ce, domin suma basu bukatar Y'a! Baiwa suke nima, idan aka basu Y'a zasu wulaknta ta, amma baiwa a wulakance zata rayu" Murmushi tayi sannan tace mishi. "Allah shi ya halicce mu, sannan a cikin zukatar mu ya sanya mana, juriya da hakuri. Ita baiwar wata rana Allah zai." Mik'ewa yayi tare da shafa kan Yarshi, ya bar d'akin dan matuƙar ya cigaba da sauraron ta,zata iya sanya mishi karamin ciwon kai. Fatar shi mutanen da ya tura Andulus su kawo mishi abinda yake son kare martabar Daular shi. *** GIZERA Haka yayi ta kallona, sannan ya riko hannuna cikin nashi, yace min. "Ikram! Airan!!!" Hawaye ne suka shiga sauka daga idanuna, sannan na rike hannun shi. "Ikram Airan" Juyawa nayi na kalleta, tana barci a saman tsumar mu, cikin kwanciyar hankali. Ajiye shi nayi tare da kofin ruwan, na juya na nufi gurinta, tashinta nayi. Koda na tashe ta, muka dawo gurin shi, kallon mu yake tayi, hawaye na zuba mishi. Ita dake barci yaci karfinta, haka ta jingina da jikina. Hada hannun mu yayi da ita, tare da cewa. "Insha Allah, sai kin zama mace mafi daraja a duniya!" Daga haka ya lumshe idanun shi, hawaye na zuba mishi, juyawa yayi ya kwanta, a hankali yake sauke ajiyar zuciya. Wanda yake nuni da cewa yana jin jiki. Kwantar da ita ayi a kan gwiwata, A haka muka kwana, da asuba na mike tare da dibo ruwa. Nayi mishi alola, duk yadda naso ya tashi yaki, wani irin tashin hankali nake ji yana cika min rai, da gudu na nufi dakin Mamma, na burmu. Kwance na same ta da wani mutum. A firgice suka farka, tare da kallon na suna rufe jikinsu. "Yar mijinki ce?" "Eh Jonah!" Murmushi yayi sannan yace mata. "Kina da kayan dukiya kike b'ata lokacinki?" Wani irin rawa jikina ya dauka, "Mamma Baffa baya motsi fa" Na fada ina ja da baya sabida yadda mutumin yaƙe kokarin riko hannuna, da gudu na fita. "Allah ki duba abinda nace, yarinyar zata yi cire ki a halin talaucin da kike cikin shi?" "Amma taya?" Inji Zariya! "Ta hanyar sayar da ita, a kaita babban birnin kasar nan, tayi aikatau." "Sayarwa kuma? A'a sai dai na baku kuna biyana kuɗi" Matseta yayi sannan yace mata. "Karki damu, za ayi haka." Jin Ihun mun yasa mutumin banzan ya bar gidan, da sauri tare da niman hanyar tsira, yana fita ta samu ta shigo, daga nan ne fa ta fahimci, mutumin da take wulakantawa ya ya koma ga mahaliccin shi. Sai lokacin ta samu damar saka hannu a kai ta fasa ihu. Tare da fitowa waje tana kururuwa, Kafin wani lokaci zuwa sallah asuba, har an shirya Baffa. Ana kai shi matar nan ta saka aka kwashewa dabbobin da muke kiwo, ban san yadda zance ba, amma bayan zaman makokin Baffa mun koma kamar zamu mutu, Noman ne yake kawo mana abinci, yau na tashi da wani irin tashin hankali, haka kawai naji rai na bai kwanta da bakin da muka yi tun daren jiya ba, sun sauka a dakin Mamma. Ina wanke kayan da suka b'ata, tare da wanke na wankewa, Airan kuma ta fita da dabbobin Mamma, ni kuma ta dakile ni a gida dan tasan bana kaunar Airan ta fita da dabbobin. Sallamar Noman naji a kofar gidab mu, na leka. "Ina Matar Baffan ku?" Kallon shi nayi sannan nace mishi. "Tana cikin gida!" "Kice ina magana da ita" Da sauri na juya, dauke kai yayi idanun shi na cike da kwalla. Noman fari ne ba can ba, yana da kira irinta sadaukai, sannan yana da matukar kwarjini da haiba. Sau dayawa a cikin garin mu, muna kiran shi sa Maza gudu. Shi yasa Yan mata suke kishin akan nice kawai nayi sa'ar samun shi. .... Fitowa Mamma tayi suka yi magana, ba tare da wani dogon tashin hankali ba, tace min. "Ki bishi ki kado min Dabobbina, ita kuma karamar ƙaruwar ku dawo da ita." Duk da ban fahimci abinda take nufi ba, amma sai da naji kamar zuciyata zata bar gangan jikina. Ban iya motsin kirki ba, haka na bi bayanshi har bakin rafi inda ake kokarin nimo Airan a cikin ruwa, ga dai alamar inda aka yi mata ta'asar, ya b'aci da jini. Jikina na rawa lokacin da na sami takalmin ta, da sandarta sai zaninta wanda ya b'aci da jini kamar anyi yankan rago, wani irin kuka nake me mugun sanyi, amma babu ko digon kwalla a idanuna, dakyar aka samo ta cikin ruwan, dayawa sun dauka ta mutu ne, sai da suka. Ji bugun zuciyar ta a jikin hannunta suka ce. "Tana raye!" Duk sai na rikice na rasa abinda zan yi, daukar zanin. Indela tayi tare da daura mata, aka nufi gidan me magani, Tunda muka kaita, matar nan take gaya min magana akan ita ba zata tab'a d'aga kai ta duba ta ba, sai mun bata silalar kudi me yawa. "Ki dubata zan biya." Inji Noman. "Ko Anwarulkharim ba zai sani nayi abinda banyi niyya ba, dan haka ku ajiye min kudi na dubata." Haka yafita ina gurin ya nimo kudin ya kawo, tace. "Ba zan dubata ba, kudin yayi min kad'an" Sake fita yayi, can sai gashi ya kuma dawowa, dakyar dai ta duba mu. Muna tsaye Mahaifin shi yazo. Kallon mu yayi sannan yace min. "Ina rokonki da Allah, ki rabu da shi, bai tab'a min sata ba sai akanki, ku ba mutanen kirki bane kuma bana son na rabaku da karfin tsiya, amma bari na miki misali, a hankali da kanwarki take ciki zaki iya kome saboda ita ko Bazaki iya ba!" A hankali na zuba mishi ido, sanan nace mishi. "Zanyi idan ta kama wasar rayuwa ko mutuwa." "Alhamdulillahi, toh don Allah idan kina son na barku ku cigaba da zama a wannan yankin, ki fita a rayuwar shi. Idan ba haka ba, zan sanya a muku koran kare." Daga haka yaja hannun shi zai tafi dashi. Kai na a kasa Noman ya rike hannuna, “ina tare da ita Abba ba zan iya binka ba" Kallona Abban shi yayi, sannan yace min. "Kiyi mishi magana mu tafi!" "Ka bishi mana," Ina fadar haka na juya mishi baya, ban kuma kallon shi ba, har suka bar gurin mu. Isowar Mamma da wadannan mutanen ya sani kallonta. "Ya jikinta?" " Ana kan duba ta" Murmushi tayi sannan tace min. "Toh babu damuwa,;" Sannan suka bar gurin, tunda aka gama kula da Airan, nake bin gida gida niman sadakar abinda zan ci, babu wanda ya bani. Dakyar na hadu da wani abokin Noman ya bani gurasa, na nufi gidan me magani, ina shiga na samu Airan tayi fitsari ko nace wanda yake fita a jikinta kowani lokaci. Haka na bata na wanke kayan, sannan na zauna naci guntun. Kwanan ta biyu a gidan matar ta kore mu, dan masu zaman jinya sun gudu wai masifa ce zata shafe su. Masu zuwa ganinta kuma suka daina, haka na dauke yarinyar na sakata a bayana, duk inda muka bi sai anyi mana, ihu da atule. Allah kadai ya kai mu gida. Shekarun Airan goma sha uku ne, wannan waki'ar ta same ta, haka nayi ta kula da ita, ga jikinta kamar lalacewa yake, haka zanyi ta wanke ta da ruwan zafi, har sai ta daina kuka. Sannan na saka mata tsuma na rufe mata gurin sabida fitsarin da yake zuba mata. Muna kwance da daddare, Mamma ta shigo dakin. "Ikram! Dama nazo ne na baki shawara ko zaki dauka akan ciwon Airan!" Zubur na mike, ina zare ido. "A cikin bakin da nayi ne tace min ko zaki shiga birni ne domin aikatau? Kinga idan kika tara kudin sai mu kaita asibitin a can." "Na amince, indai zata sami lafiya zanje." Murmushi nayi sannan ta nufi dakin ta, ta gaya musu, a daren ranar muka nufi babban birnin Sudan. ** Baya bata kaɗan. Bayan tafiyar su, Mamma ta fito da kudin da aka bata, ta shiga dakin Airan take kwance, daukar ta tayi tare da nufar gidan me magani, dan dama itace tayi sanadin faruwar kome, tun daga fyaden da kin basu kulawa ta sayar da Ikram ita kuma Airan zata meda ta karuwa tana samun kudin shiga , dake Airan din bata tafiya dole ta goyeta. Tana isa kofar gidan Airan tayi mata nauyi, kamar an daura mata shirgi. Koda ya shiga da ita gidan, matar ta dubata ta, girgiza mata kai tayi alamar yarinyar ta mutu, tashin hankali ta shiga tare da niman taimakawa aka mata wanka akan gobe da safe za a kaita makwancinta na gaskiya.... (Me karatu wannan shine mafarin tafiyar mu🏇🏽) *** *Andulus* Yau kwanan su tara kafin suka iso babban birnin kasar, kallon juna suka yi sannan suka nufi gurin wasu yan daudu, gaisawa suka yi sannan suka tambayi. "Kais! Muke nima?" "Ai shugaban mu, toh sannunku yan samari, kuzo mara ba da manyan sadaukar kaga wani labcecciyar kirji me hana mata sukuni." .suna magana tare da nuna su da yatsa, har cikin wata gidan alfarma suka shiga, sannan aka musu iso. Suna shiga suka zauna, a kujeran da ya nuna musu. Zama suka yi tare da cewa. "Muna buƙatar?" "Aidah ki kawo musu bayin nan duk da na yammacin Afrika basu iso ba." "Toh shiga ba, an gama!" Yadda yayi maganar kamar wani mace, Fita yayi, bayan kamar minti goma sai gashi dauke da wasu yan mata, tsirara suka nufi cikin dakin. Juyawa suke tare da nuna musu su. "Ya sunyi?" "A'a sunyi shekaru dayawa, bamu son me yawan shekaru!" "Toh zaku yi mana hakuri nan da kwana goma kayan mu zasu iso. Kafin nan kuyi shagali!" "Bashi bane a gaban mu, abinda muke bukata idan zamu sami kayan takasance babu wanda ya kutsira." "Duk abinda nake ina yi da lissafi! Duk da bani da lissafi, amma ina fahimtar kidaya. Ku jira nace" Da haka suka amince da shawaran shi. **((Page 9))) Muna isa da asuba, babu batun sallah, bakin tekun aka kai ni, inda aka yi ta zuba mutane a cikin wani abu ana rufewa. Fita mutumin Mamma yayi da matar da muka tawo da ita, suka tafi wani guri can sai gasu sun fito suna dariya. "Toh Ikram Allah ya ƙaddara saduwar mu, matar Babanku ta sayar mana dake, ita kuma kanwarki zata cigaba da mata karuwanci," Ashe kuka rahama, ce dan bana iya cewa kome, sai ajiyar zuciya. Haka suka jani zasu wurgani cikin abun, na shiga ihu tare da cewa. "Ba zaku tab'a sayar dani ba, idan na fito sai na kashe ku. Mugayen banza mugayen wofi." Ina ji ina gani aka watsani cikin abun aka rufe mu. Daga nan muka suka karasa sauran aikin tare da d'aga jirgin ruwan. Wato ban san me zan gaya muku ba, tafiya ce wacce bamu san inda muke tafiya ba, bamu ganin juna, Bama fahimtar saye a kusa damu,.sai dai da zaran mutum ya.mutu da yinwa da ƙishirwa zasu bude mu, a cire shi a jefa cikin Teku. Ban san iya adadin mu ba, amma a yadda nake jin hiran masu kuzarin cikin mu, muna dayawa, basu bamu abinci sai munyi kwana biyu, sannan a watsa mana gurasa, da dambe ake daukar shi. Sannan kuma yawan mu bamu da karfin haka, tafiyar kwana goma, a cikin shi sau biyar muka ci abincin. Mafiya yawan mutanen cikin mu, sun mutu an zubda su cikin ruwa, kafin muka isa, cikin talatimin dare, haka ayi ta zuwa ana fidda mu. Har aka gama sauran kuma aka kai su tsakiyar ruwa aka zubda su. Idan ka ganni nayi da kan da kan, na kode babu abinci. Muna shiga gidan kais aka turo mana katon tire da abinci, haka muka shiga warwaso, duk warwasonka za a kara maka, sai dariya ake mana. A hankali muka nutsu tare da cin abincin, me dad'i. Ina ci ina kuka tare da tunowa da Airan, har muka koshi. ---- bayan mun haka aka kai mu wani katon daki daga nan muka yi wanka, sannan aka bamu wani dan kamfe, muka rufe gaban mu, kafin aka nuna mana hanyar fita. "Ba zan fita da wulakancin ba, tsirara?" Buge min baƙi su yi, tare da jana da karfin tsiya,. suka nufi babban falon Kais, aka watsar dani, da sauri na kare kirjina, tare da dunkulewa guri guda. Sauran yan matan haka, suke tsaye. Tasowa yayi tare da kama gashin kaina, ihu na saka tare da kai mishi duka, "Ya kuka ganta!" "Eh toh har yanzun gaskiya da sauran domin bamu ga fuskarta ba, ba zamu iya sayan!" "Wallahi sai na kashe ku, Idan kuka saye ni!" Na fada ina zare musu ido. "Tayi!" "Me yasa kace haka?" "Ban sani ba, amma tana da kyauta na musamman, ka duba kwayar idanunta!" Haka ya ture ni sannnan yace. "Dinari, dubu sau dubu." "Mun kara maka da bugun tsabar dinari. Yau zamu koma" "Wallahi ba zaku dauke ni ba." Muka fara kokuwa dasu, wata yar riga aka saka min tare da daukata aka fice dani, ihu nake ina gaya musu sai, sai na kashe su, Akan idanuna akayi ciniki na,.tun daga Sudan ake saka min furashi. Tafiyar asuba muka yi, dake zasu sauka a Askandariya. Dole kafin mu isa can dare zai yi. *** Sultan Abrad. "Yau saura kwana tara su dawo, bana son kome ya kuma jagulewa ba a cimma matsaya guda ba." "Insha Allah zasu dawo nan da bada jimawa ba!" A bukatar shi, idan aka kawo baiwar a cikin kwana biyu, zai sallame ta.a yadda yace Kenan. *** *Masarautar askandariya* Ihu take tare da kai musu duka, tana tirjiya, su kuma samudawan matan suka dauke ta da karfin tsiya, suka makata da kasa, wani irin ihun take sauran matan suka fashe da dariya, suna ihu. "Kai kuyi mana shiru. Gidan sarautar mu ba a hayaniya da ihu." Inji wata mace wacce take da matsakaicin shekaru, yanayin fatar jikinta me duhu ne. "Ku sake ni mugaye Azzalumin mai nice ajalin Sultan Abrad sai na shayar dashi gubar mutuwa. Sai na lalata kome nashi." Buge mata bakinta aka yi, ta fashe da wani irin shakurarren kuka, lokacin da ta ji suna duba yan matancinta, sannan suka sake ta, tare da wurga mata towel ɗin ta, ta rarruma, ta daura tare da mik'ewa akan diga dudduginta. Wani sabon kukan ne ya kuma kwace mata. "Ki daina wannan haukar? Domin gobe zamu wuce dake Oman." Had'iye yawun tayi, cikin kuka tace. "Me yasa zaku kai Ni Oman bayan kunce Sultan Abrad ne ya saye Ni? Wai ma waye su?" Wucce ta suka yi, basu bata amsa ba, daga bayanta aka ce mata. "Ke yar Afrika bakar fata, wani izza kike ji dashi?" Cikin zafin rai ta juya tana kallon su, gyara tsayuwar ta yayi, sannan tace. "Ismi Bilqis ALMUSTAPHA! Wata ta kuma kirana da bakar fata sai na yanke harshen shi." "Toh munji baiwa bilqis!" Cikin zubda kwalla, ta kalle su. Cikin kuka ta dauki duk wani abu ne hannunta ta shiga buga musu, suna gudu. "Wayyo Allah na, meye nayi muka da zafi kuka rabani da ahalina?" "Ke ki mana shiru! Ku kuma yan mata mu fita," Haka suka fito suka bar bilqis a cikin ban dakin tana kuka da ihu, yar kimanin shekaru goma sha bakwai. Wadannan samudawan matan suka fidda ita da karfin tsiya, suka kai ta wani dakin da ake ajiye ta, tare da wurga mata kayanta. Zama tayi tare da sake kuka me mugun cin rai, tana kallon yan matan da suke dakin..matsowa kusa da ita wata yar budurwa tayi, tare da daura kanta bisa kafad'arta. "Yar uwa!" Kuka ne ya kuma kwace musu, tare da rike junar su. "Kiyi hakuri!" "Sun saye ni kamar dabba, sun raba Ni da kowa nawa, sun mayar da rayuwata mata amfani!" "Meye nayi musu? Meye na katse musu? Allah ya saka min." .na Cigaba da kukana haka matashiyar yarinya ta Cigaba da rarrashina, tana bata hakuri. "Gobe zasu wuce damu Oman!" Wani irin kwalla ne ya shiga zuba min, ina kallon yarinyar. "Wallahi ba zan tafi Oman ba, ko zasu kashe ni sai na gudu" Na faɗa cikin tabbatarwa kaina zan aikata abinda na faɗa, shiru dakin yayi, babu wanda yayi magana. ~~~ A fadar Sultanah Amrah na kasar Askandariya. Dan dukawa suka yi, sannan suka ce mata. "Muna godiya Sultanah Amrah da bamu masauki gobe Insha Allah zamu wuce Oman, mun gode ainun." Ƙasaitacciyar murmushi tayi sannan tace. "Tsakanin mu da Sultan Abrad akwai yarjejeniyar sulhu da zaman lafiya, sannan babu amfanin hana ku masauki. Dan haka dukkan abinda kike bukata langesa zasu muku!" "Mun gode ranki shi dad'e, mun sami kome ma!" Ya kuma fada a karo na biyu, jinjina kai tayi sannan ta d'aga musu hannu. Babu musu suka fita, daga cikin fadar. "Nawwas, akwai matsala fa?" Kallon shi wanda aka kira da nawwas yayi sannan ya cigaba da tafiya. "Yarinyar nan!" "Me ya faru?" "Ta tabbatar da zata gudu gobe" "Allah ya nuna mana goben.," Ya faɗa tare da murmushin mugunta. Haka suka karasa dakin su, bayan yan matan gidan sarauta sun zo debe musu kewa, da yan kad'e kad'e da raye-raye. "Kana tsoron kar ta gudu ne?" Gyara zama Zur yayi sannan yace. "Ban ga rashin tsoro a idanunta bane," Murmushi Nawwas yayi sannan ya cigaba da wasa da hannun shi yana faɗin. "Zuciyarta a kone yake" "Kamar ya?" Inji Zur, "Daga yadda take iya sarrafa harshenta da fushinta!" "Kasan ban lura da haka ba, domin nasan dai." "Akwai ciwo a ranta wanda yasata kasa boye b'acin ranta, idan ta cigaba da sarrafa fushinta har aka kai ta Samaind, sunanta gawa. Sai dai yanayin kaddara idan ta sauya." Ya faɗa haka yana kallon, wata da take rawa. ** Gezira. Kurawa mahaifin shi ido yayi cikin wani irin kaduwa. Bakin shi ya gaza furta kome, sakamakon kukan da mahaifin shi yake, "Noman na cuci kaina, gashi saboda son zuciya na cutar da Yaran da babu ruwan su. Gashi ba aje ko ina ba, anyi.... #Mai_Dambu... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: https://www.wattpad.com/1032581704?utm_source=android&utm_medium=link&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=Mai_Dambu&wp_originator=6I7W6FRqTxinGtl9jgfvth%2BS5iQWEYUprgoAPgiWur5smXqzWL5Ee8uUktHwu3iZ2WdtcLySltEgKfb2Jk1Kb0GbW3xpNIkEcvn7jurBV9R91%2BsJQqQzRV5V0rw3oBhA 🐾ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜🐾 _The Historical_ ~BOOK ONE~ Mai_Dambu Bismillah Rahamani Raheem. Page 10.... Wasu irin kwalla ne suke kokarin sauka daga cikin idanun shi amma ya dakatar dasu. "Abba me yasa kayi min haka? Ka cutar dani ka cutar da Yaran da Babu ruwan su? A sanadin haka Har Airan ta rasa rayuwarta. Yau gashi nan abun ya faɗa kan mu" Ya fada a sanyayye, gwanin ban tausayi. Share kwalla yayi sannan yace mishi, "Wallahi ban tab'a ganin Muguwar mata irin matar Malam Almustapha ba, ka yafe min ka yafe min abinda nayi muku." Mik'ewa Noman yayi, tare da barin gurin mahaifin shi, gidan su Ikram ya nufa, tare da shiga kai tsaye. Ya sami gidan kamar ba ayi mutuwa ba. Domin ya cika makil da yan iska, sai karta ake ana ta sharholiya. Kwallo ya shiga yi da kayan gidan, tare daka musu tsawa. "Ku fita kafin na ci mutuncin ku" Ganin yadda ya koma kamar wani zaki ya sa kowa ya shiga barin gidan, a tsora ce. Takowa yayi idanun shi jajjur gaban Mamma, "Ina take?" Murmushi tayi sannan tace mishi. "Bana tunanin tana raye ma, domin ko ta mutu an wurgata cikin ruwa ko kuma tana can cikin Sudan tana aikatau." Da sauri ya juya tare da barin cikin gidan.. ** Askandariya. Tunda aka kawo mana wani kunun alkama da madarar rakumi, sai wani dan fai-fan abu kamar burodi, dashi muka karya, a hankali na mike tare da gyara zaman rigana, dan sabulewa yake. Sannan na daure gashin kai na, da kyau na mai dashi tsakiya, sannan na koma na zauna. "Baki gaya min sunanki ba?" "Inam!" Yarinyar ta amsa min. "Me yasa zaki gudu?" Dauke kai nayi sannan ta cigaba da gyara rigana bayan na yaga kasar shi. Daukar igiyar nayi sannan na daure k'uguna dashi yadda rigar zata zauna min, guntun igiyar na daure wuya ta fashi. Can kuwa sai ga dakarun Oman. Haka suka tasa keyar mu, muna fita waje inda zai fitar damu daga garin. Nace musu. "Ko ku barni na yi tafiya ta ko kuma na kashe kai na," Caaaa suka min da takuban su. Aikuwa na, kuma sheke wuyata. Sake jan igiyar nayi, kuma duk muna cikin gidan sarautar Askandariya, ganin da gaske kashe kaina zanyi suka shiga ƙoƙarin hanani, Ni kuwa damar guduwa nake nima toh sun zagaye Ni. ..... "Toh mun gode, Nawwas idan har ka isa Oman ka sanarwa Sarkin ku, nagode sosai abisa yarda da yayi dani." Inji Sultanah Amrah. "Godiya muke!" Daga haka suka fita bayan sun yi sallama da ita, yana fitowa farfajiyar masarautan ya hango yadda ake da Ikram, a hankali ta taka tare da ratsa dakarun shi. A hankali ya saka hannun shi a saman wuyarta, zuɓewa tayi a jikin shi ta baya, zuciyar shi ce ta shiga wani irin bugawa, da sauri ya ture ta, tare da barin gurin su baki daya. A lokaci guda haki da wani irin yanayi na fitan numfashi ya taru mishi, sosai yake jin bugun zuciyar shi. A hankali ya juya tare da kallon yadda aka dauke ta, za a fita da ita. Duk da ya ganta babu kaya a jikinta, bai ji wannan yanayin ba, sai yanzun da ta haɗu da jikin shi. Lallai zuciya baka da ikon sarrafa sai yadda ta sarrafa ka. ** *SAMAIND* "Narmin! Ban san me yasa nake jin babu dadi ba!" Inji Sultanah Hoyam. Gyara tsayuwa dattijiwar tayi sannan tace mata. "Ina ga yana nasaba da." Buga mata kofa aka yi, ta kalli Narmin, fita tayi ta sami Khabir, Shigowa suka yi, tare da gaida Sultanah Hoyam. "Kina da baki Sultanah." Kafe shi tayi da ido, "Gwamnonin yanki nan baki daya ne suka tawo" ya faɗa mata. A hankali ta mike tare da saka alkyaba ta fito. Tunda ta shiga fadar suka mike baki dayan su, har da Amir Hood. Suka gaishe ta. "Sannunku!" Zama tayi ta daura daya akan daya,. tana kallon su. "Sultanah mun zo da wani batu ne, da fatan zaki fahimce mu, Gyara zaman ta, tayi sannan ta zuba musu ido. Daya daga cikin gwamnonin wanda ya kasance shugaban su baki daya yace mata. "Sultanah ne sunana Mir Kamshad, ina rike da yankin arewacin kasar nan, Sultanah mun zo da batu me girma ne." Ya zuba mata ido,.yana kallon yadda take sauraron shi. "Kasancewar kin jagoranci dogon lokaci akan karagar mulki, shine muke rokonki, da kibawa D'anki dama sultan Aamaan Bin Abdus Samad Bin Aamaan Almaktum, damar jagorantar mu! Sanan munyi mubaya'a baki dayan mu akan jagorancin mu." Kallon su tayi baki dayan su, cikin wani irin juriya da jarumta, murmushi tayi sannan tace musu. "Sai me?" Mik'ewa wani gwamnan yayi tare da cewa. "Suna Mir Umdatuddawla, ina jagorancin yammacin kasar nan, Sultanah a labarin da muke samu, sultan Aamaan ya san Y'a mace, bayan kuma Daular nan an san cewa duk basaraken lardin nan dole sai ya bayyana cewa yayi tarayya da Y'a mace.!" Fasali yaja tare da kallon ta, ya cigaba da cewa. "Abisa ka'idar daular nan, dole ko baiwa aka kawowa sarki yayi tarayya da ita dai ya shaidawa duniya haka domin muna sakan ran zamu sami magajin shi." Yana kai aya ya zauna, tare da zubawa gwamnan kusa dashi ido. Mik'ewa yayi sannan yace. "Suna na Mir Ihsanul Hak! Sunana na, Ni ne gwamnan kudancin kasar nan, Sultanah abisa al'ada kafin ki kasance shugabar mu sai kin kasance a matakin tanttancewa. Amma saboda kaunar da Abdus Samad yake miki, kika sami damar zama Sultanah, dan muna koron a shigar mana da jarabawar zama Magajiyar sarauta a cikin wannan daular kamar yadda aka yi shekarun baya, sannan shima Aamaan din muna bukatar ya fito ayi mishi jarabawar zama sarki na gaba." Yana gama fadar haka ya zauna, "Suna na Mir Fawwaz, ina rike da wasu abubuwan na shige da ficcen na kasar nan, dani aka tafi Baghdad, akan sulhu. Sultanah Hoyam tabbas kin rike daular Abbasid fiye da yadda suka rike Daular Umayyad, amma maganar gaskiya shine sun janye ne sabida Yawan dakarun mu, miliyan uku da rabi. Yayinda suke da dakarun miliyan daya da rabi.. a takaice zamu iya shafe daular baki daya, amma sabida yadda suka kawo sharuddan su, sai da suka yi magana akan mulkin da kike yi bayan kin hana d'anki damar mulki, sannan suka ce su yar su ba zata zama baiwa ba, matukar zata zama baiwa toh zancen zai iya zama na kasa da kasa." Zama yayi sannan Amir Hood ya mike, "Ya shugabana, batun su haka yake, sannan abisa al'ada muna bada daman ayi jarabawar zama sarki da matar sarki, idan har aka sami damar haka toh muna, iya fuskatar tozarci a gurin wasu sarakuna. Ba laifi bane bawa mace mulki, amma mafi muhimmanci shine ta sauka ta barwa namiji damar haka." Zama yayi sannan wazir din ta ya mike me suna Burhan ya mike. "Zamu duba wannan batun, sannan Sultanah zata tabbatar da tayi yadda kuke so." A hankali aka shiga kus-kus, tare da jin eh ta amshi kuskurenta kuwa ko. "A yafe Ni! Da zuwa a makare. Sunana Mir Rahil, ni ne me shige da fice na masarautan nan ta harkan haraji, Sultanah Hoyam ana fitar da dukiyar al'umma ba tare da sun gani a kasa ba, sannan an tsawallawa talakawa haraji, Sultanah muna gudun abinda ya faru lokacin Margayiya Sultanah Safrah ya kuma faruwa a wannan lokacin,. Idan da hali a duba maganar nan" Dake mace ce lokaci guda suka hade mata kai, tare da nuna mata lallai sai ta sauka ta bawa D'anta. Har suka gama magana babu abinda tace. Karshe sai da safe tayi musu, tare da barin fadar. Tunda ta shiga cikin turakarta, take kwance, ta kasa cewa kome, kallon Abubuwan da ya faru take, a hankali ta fita ta kofar shashinta ta baya, tare da nufar inda wani sirtacceen d'akin ta shiga bayan ta zauna. "Zaki dawo dama?" "Tuba nake!" "Ai kinyi kuskuren! Ki tafi abinki, kamar yadda suka yunkura haka zaki hakura sannan kuma akwai wasu gaba, d'anki nan dai dole kiyi hakuri da shi. Kamar yadda kika." Mik'ewa tayi da sauri ta bar cikin ɗakin, wani irin bala'i take ji, kamar zuciyarta zata buga, komawa dakin tayi, sannan yace mata. "Ni na amince zaki ce!" Ajiyar zuciya tayi sannan tace. "Sai me kuma!" "Kije kawai!" Wani irin dariya ta sake tare da cewa. "Ni Sultanah Hoyam." *** A hankali na bude idanuna, na kalle ni a daure. "Kan Uba! Ku dabobbi, shegu mugaye Azzalumai marasa imani, ku sake ni ku gani idan ban kashe ku ba, yan iska mugaye." Ihu nake ina zagin su, tunda muna yankin mu larabci muke yi, kuma suna fahimtar abinda nake fada. Takowa yayi gaba na, ya saka d'an mukulin ya bude ni, zubur nayi tare da kai mishi duka ya tare hannuna, tare da hada ni da jikin jirgin na bugu. Riko gashin kaina yayi, "ki iya harshenki, idan ba haka ba wallahi zan baki mamaki, karki kuma d'aga min murya." Cikin fusata na kalli idanun shi. Dauke kan shi yayi da sauri. "Bar kallona da shegen idanunki nan masu kama da na aljanu." Sake fusata ni yayi na cigaba da kallon shi. Sauran bayin suna kallon mu, sake daka min tsawa yayi ban dauke kai na akan shi ba. A hankali ya saka hannun shi ya keta min rigana har ƙasa, rungume shi nayi, tare da cusa kaina cikin kirjin shi. Wani irin mutuwa jikin shi yayi tare da kasa aiwatar da kome. Cire rigar samar jikin shi yayi tare da rufa min, kan shi ya kai dai dai kunne na, yace. "Ki daina taurin kai." Sannan ya yankince ni daga jikin shi ya ficce. Faduwa nayi tare da bin bayan shi da ido, ina huci, gyara zaman rigar nayi a jikina. Abincin da suka kawo min, bai min ba nayi kwallo dashi. "Ni bazan ci wannan abincin ba!" Na fada da karfi. Dauka Inam tayi ta haɗa da bata aikuwa na shiga musu diban albarka. Haka ya kuma shigowa da wata riga ya wurga min, sannan ya durkusa a gabana. "Kin san me? Zan kunya taki a gaban jama'a! Idan baki son haka ki ci abinda aka baki." Tofa mishi yawu nayi, tare da cewa. "Idan ka fasa ka rena Uwarka da Ubanka, meye ya rage min kun sayo ni domin ku maidani baiwa ko? Toh nice ajalin Sarkin ku." Goge fuskar shi yayi, tare da mik'ewa yasa aka kawo min, abincin shi. Ihu nayi tare da kiran daya daga cikin dakarun shi nace mishi. "Kai kare! Zoka ga babban jaki ya kawo min abincin shi." Basu kula ni ba, haka na ci abincin na turawa sauran matan, aikuwa suka cinye abincin. Tsiya kala kala, nayi musu Iskanci kuwa da nake yiwa Nawwas da Zur Allah kadai ya sani, amma a duk lokacin da na tuna da kanwata Airan, idan ba fara kuka. Duk sai sun ji babu dad'i, dan suka rasa me zasu iya min nayi shiru. Dan haka idan suka ga ba shiga damuwa, ina kuka sai su shiga min kid'a. Wanda suke ganin kamar haka zai sanya ni, saukowa da wuri. Idan na gama kukan kuma, na shiga tsula musu Iskanci duk sai sun kasa yin kome. A hankali tafiyar kwanaki ƙalilan, ya jamu kwanaki sama da goma sha biyar, kafin muka isa. Dalilin b'ata lokacin ma Nawwas ne yake hana su tafiya da sauri. Da safe muka masarautan, a hankali muke tafiya, jama'ar garin suna kallon mu, sai nuna mu suke. Lokacin da muka shiga cikin farfajiyar, mun samu ana ta hidimar mulki kawai, haka muka zama yan kauye muna kallon yadda aka zuba dukiya me tarin yawa aka gina daular. A hankali nake juyawa, ina kallon ko ina. "Nawwas! Nifa idanun yarinyar nan tsoro yake bani!" Murmushi Nawwas yayi sannan yace masa. "Babu abun tsoro fa,sai dai yau zata iya bazawa Sultan Abrad halin ta, zan so naga yadd..." Kallon juna suka yi sannan Nawwas yace. "Kasan me?" "Amirah Sariyah matar Sultanah da tarasu, wallahi kamar su daya." Sai lokacin Nawwas yayi murmushi, sannan.... 🙄🤭 Sultanah Hoyam? Nawwas? Ikram? Shuwagabannin yankunan kasar SAMAIND? Sultan Abrad? Amir Hood? Fazilatul nisa? Sultan me jiran gado.... *Alqur'an akwai matsala 🤔🤣 Chakwakiyya zalla 👌🏼* #Paidbook #Mai_Dambu *Book one free ne, book two da three na kudi ne 200₦ ta bank 0472282105 ko katin mtn ta wannan Number +2347035133148 ko ta wannan Number 08130269641* Happy weekend 💞💝 [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: https://www.wattpad.com/1033128340?utm_source=android&utm_medium=link&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=Mai_Dambu&wp_originator=0hWPUPP4EB2me9%2Bvw5nt7Z%2FDqwYO3s4%2BGS7vBQWXokANARTOhHKVLw8%2Bp%2BHOFoec1Edf8fruBacauoAQ5%2FkXjvfowuFI57CvmlYdViv1eM0F4E%2Fap5Mu3ehqgtdE1I%2BO 🐾ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜🐾 _The Historical_ ~BOOK ONE~ Mai_Dambu Bismillah Rahamani Raheem. Page 11... Sake baki Zur yayi tare da kallon Nawwas, girgiza kai yayi tare da karawa gaba, tare da juyawa yana kallon hanyar da aka tura bayin. .. tunda muka nufi hanyar, jikina yayi sanyi, dan na fahimci akwai sassauci game da wannan masarautan, muna shiga aka nuna mana cikin inda zamu zauna. "Ya ku yan mata, zaku iya wucewa ban daki kuyi wanka tare da sauya kayan ku!" Inji wata babbar mace. Tsaki nayi tare da dauke kaina, na nufi hanyar da aka nuna min,.tunda muka shiga kowa ya cire kayan shi amma naki cire nawa, ina tsaye kamar gumki. "Ke ba zaki cire naki bane!" Juyawa nayi ina kallonta kafin nace mata. "Ni ba dabba bace, balle ki ce na tsaya na cire kayan jikina." D'ago kai tayi tana kallona, cike da mamaki. Cikin rawan jiki ta bar ban ɗakin, siririn tsaki naja tare da komawa gefe na hade daya akan daya. Can sai ga ta sun shigo da wasu matan, haka suka yi ta kallona, kafin suka kama ni da karfin tsiya, suka min wanka dan tsakani da Allah nake son basu ciwon kai. Bayan sun gama tare da buge min bakina, duba mu suka shiga yi,suna ware wasu yan matan. "Ban da munafunci meye yasa kuke ware mu?" Kallona suka yi sannan d'ayan su tace min. "Duk wanda kika ga an ware ta, toh zaki samu ta tab'a daukar namiji ne, duk." Sake baki nayi ina kallon ta,kafin nace mata. "Idan ta dauki namijin ina zata kai shi?" Cike da al'ajabi suke kallona, kafin suka share ni. "Kuna nufin ba zaku gaya min gaskiya bane?" Banza suka ba ajiya na, Inam ce ta riko hannuna. "Suna nufin wadancan sun tab'a kwana da maza ne!" Da sauri na rufe mata bakinta, jikina har yana karkarawa. Su kansu sai da suka fahimci a tsorace nake, kafin wani lokaci na fashe da kuka. Airan ce ta fado min, kuka nake har da shasheka. Dakyar suka duba gaban mu,tare da sallamar mu. Kasancewar mu yan yankin nahiyar Afirka, mune muka fi yawa a wurin, sai muka sami saukin abubuwan, babu kyara ko hantara, dan yadda na Fahimta, kamar suna son zama da d'an Afirka. Ba yabon kai ba, duk inda dan afirka yake zaka same shi yana zaune ne dan niman na kanshi, zai yi wuya kace bai san aikin shi ba. Kaya aka mika mana, tare da nuna mana yadda zamu saka, sannan suka ce muje wani daki mu gyara gashin kan mu, tunda muka shiga dakin muka shirya. Abinci muka ci a nutse, sannan suka ce mana. "Idan kun gama zamu kai ku shashin Sultan Abrad, "Toh!"muka ce musu. Muna gama cikin abinci kuwa, suka tawo, tare da bamu mayafai muka rufe fuskar mu,.sannan muka nufi babban dakin hutawar shi. Babban burina bai wuce na gaya mishi bakar magana ba, yadda zai ji haushin yadda yasa aka sayo ni,.muna shiga kuwa yana zaune. Tunda muka shiga bai d'ago kai ba, har matar ta nufi inda yake tayi mishi magana, ko a jikin shi. Bai mata magana ba ya cigaba da abinda yake yi. Mun gaji da tsayuwa, kawai na sake musu tsaki. Me shegen karfi. A fusace ya d'ago kai, ba iya shi ba dukkan su wai nima na suke,. "Wacce mara mutunci ce tayi tsakin?" "Nice!" Cikin zafin nama, tazo ta finciko ni, sai da na zube akan gwiwata, zuba min ido tayi, kafin ta fita zai gata tare da dauko wasu fadawa, suka zo da bulalar su. Nan suka shiga zane ni, bakina bai mutu ba, kuma ban fasa abinda nake yi ba, domin bakar magana nake gaya musu, tun maganar baya shigan shi, har ya d'ago kai tare da kafe ni da ido, nima shi nake kallon da idanuna jajjur. "Sai na kashe ka! Wallahi." Na fada da idanuna jajjur. "Ya isa haka?" Ya dakatar dasu. Mik'ewa yayi tare da isa inda yake sakale da takuba, biyu ya ciro tare da wurgo min, sai tawo a hankali yace min. "Tashi gani ki kashe ni" Cikin zafin rai, na mike da gudu sai da ya bari na dauki takobin nazo da gudu, ya goce tare da saka min kafa na fadi. Murmushi yayi sannan yace. "Idan kika yanke koda rigar jikina zan bada jirgi a mai dake garin ku, da dukiya me yawa. Idan kuma Ni nai nasara akanki, zaki zauna a cikin masarautan nan har zuwa lokacin da yayi min ki bar masarautan." Cikin kwarin gwiwa, na kuma mik'ewa, kai naga mugu na karshe da yasan cewa ba iya kashe shi zanyi da sauki ba, shine ya shiga bani wahala, tare da mai dani abin wasar shi. Idan na kawo mishi sara haka zai goce ya make keyata, ko kuma yaja Jelar gashina. A takaice dai haka ya mai dani kamar wata mage da b'era, musamman idan ta sami Bera mara wayo, haka yake ta min rashin mutunci. Karshe janyo ni yayi gaban shi, tare da saka hannun shi a gefen cikina, daya hannun kuma ya rike tare da takobin, cikin jin haushi na fara kiciniyar kwace kaina, yana ta juya takobin da hannuna, karshe ganin na takura mishi da juye tare da make shi da take mishi kafa ya ture ni gefe, yayi tafiyar shi. Yana murmushin mugunta. "Bakin mugu Azzalumi, sai kinyi kukan da nayi." Da sauri matar da ta kawo mu, tazo tana faɗin. "A kul da wannan maganar da kike mishi." D'ago kai nayi ina kallonta, sai lokacin ta lura da hannu na da yayi jajjur, sabida hada hannun shi da nawa, d'ago ni tayi muka bar shashin. ... Tsaye yake gaban wani tangamemmen hoton da aka zana da wasu irin kallon launi, mace ce tsaye, sanye da tufafi masu nuna alamar itama yar babban gida ce. "Sariyah! Na yarda da ana mutuwa, shi yasa na amince da hakan, amma yau ganin me kama dake ya kuma dagula al'amurra na, sama da kome." Gyara tsayuwar shi yayi yana kuma hango kaman ta da Baiwar da tace zata kashe shi. ** *SAMAIND* Shigowar ta fadar kenan, ta kalli mazaunin duk wasu masu fada aji na masarautar yau basu nan, ta nemi guri ta zauna cike da mamaki. Ita gwamnonin nahiyar ta zasu juyawa baya, a hankali ta mike tare da kallon Khabir. Sannan tace mishi. "Ka duba min a ina suke" "Ki gafarce ni, suna can gidan Amir Hood." "Akan me?" "Sabida jiya kinki magana" Lumshe idanun ta tayi tare da gyad'a kanta. "Ka kashe min su" "Ranki shi dad'e, ba zai yiwu ba. Sabida idanun kowa na kanki, mafi alkhairi a gabatar da Sultan Aamaan." "Umarni kake bani?". Tambaye shi a tsawace, Sunkuyar da kanshi yayi tare da cewa. "A'a ranki shi dad'e, shawara nake baki!" "Idan baki fa?" Ta tambaye shi, ranta a harzuke. "Ranki shi dad'e, ki Fahimci wani abu, guda." Takowa yayi gabanta sosai, yayi mata maganar da yasata sake murmushi, sannan yace mata. "Sunci amanarki, kuma ba zai tab'a barin ransu ba, dan haka ki duba magana ta." Murmushi take tare da gyada kanta kamar kalangariya, sai wani irin dad'i take ji, ** Sultanah Fazilatul nisa. Rike take da bulala take, idan yarinyar tayi kuskuren kad'an sai ta watsa mata bulalan. Har sai ta ce. "Auch!" "Jasra!!!" Ta daka mata tsawa, "Idan baki nutsu ba, zan baki mamaki. Ki Fahimci Abu daya muke son yaka, fansar jinin Mahaifinki." Inji Sultanah Fazilatul nisa. "Amma Sultanah! Ita daya ba zata iya aikin ba." "Ina sane da hakan!" Ta bawa Shairah amsar a takaice. A hankali take nuna mata yadda zata yi tare da daura mata darasin rayuwar masarautan, Jasrah Abdul Mannan, shekaru goma sha biyar kenan da aka kashe mahaifinta, abisa kama shi da aka yi da munafurci sosai abin ya tab'a mahaifin shi Amir Hood, domin yana ji yana gani ana salwantar da rayuwar yaran shi, amma saboda dauke kan da yayi yasa har yau baa taɓa jin tace sai an kwace mishi hakkin shi a gurin Sultanah ba. Ita kanta tasan ya kai kololuwar hakuri, amma ba haka bane bukatar ta, dole idan zaka yi yaki kasan da wanda zaka yi. -- Amir Hood. Shiru yayi yana sauraren su, sannan ya mike dai dai lokacin da aka bude kofar da Sultanah Hoyam zata shigo. Murmushi yayi sannan ya tashi a inda yake ya nuna mata inda zata zauna. Zama tayi sannan ya koma bayan kujeran ta ya tsaya, murmushi tayi sannan tace musu. "Kifar da mulki na rabo ne na zubda jinin mutane, dan haka ga damar da zan iya sakewa, Ni Sultanah Hoyam Ghanim, na sauka kujeran mulkin na bawa Yarona Zakina ya cigaba da mulkinsa fiye da lokacina." Ta faɗa tare da kallon su, dukar tabirin tayi, aka bude kofar. Sanye yake da wata riga da wando, bayan shi wata mayafi ne me hade da rigar. Kyakyawa ne dogo me yalwan doguwar gashi, wanda ya sauka har dokin wuyar shi. Gashin giran shi a tsatsaye yake, gashin idanun shi kuwa idan ya lumshe idanun shi, sai ya sauka akan fuskar shi, tsabar tsayin su. Hancin shi ya daidaita akan fuskar shi. Sarki ya tabbata ga Allah madaukakin sarki. Mik'ewa dukkansu, suka yi domin kayan jikin shi kawai zaka kalla ka tabbatar cewa sarki ne sukutun da guda, Fudail da Darakshan sune suke take mishi baya. Dukka manyan mutanen fadar sai da suka mik'e, a hankali ya karasa inda aka ware mishi kujeran shi, Fudail ya isa gurin kujeran ya tsaya tare da dubawa sannan yaja shi baya, Aamaan ya zauna. Kafin kowa ya zauna. Tunda ya zauna bai d'ago kan shi ya kalle kowa ba. Haka zalika bai ce kome ba, Darakshan da Fudail, zuciyar su cike take da farin ciki zasu ji muryan shi, tsawon shekarun da suka yi a tare bai tab'a musu magana ba. Tunda ya zauna yake wasa da zoben hannun shi, kamar yadda yake cikin karamin yatsar shi. "Yanzun dai kin hakura, duk da haka zamu iya cewa za a rantsar da shi nan da kwanaki, sannan mu gwamnonin nahiyar baki daya zamu turo Yaran mu nan da shekara me zuwa, domin halartar bukukuwan murnar cika shekara daya a kujeran mulkin shi tare da zab'ar matan da zai rayu da su, me kuka gani akan hakan?" Kura mishi ido suka yi, ganin yadda fuskar shi take nuna bai yi na'am da abinda suke bukata ba, yasa suka kuma cewa. "Mun baka nan da wata uku, bayan baka saurautar." Dunkule hannu yayi tare da kallon me maganar. Sunkuyar da kai Mir Umdatuddawla yayi. "Afwa Sultan Mehra!" Ya faɗa, kallon su yayi sannan ya mike, tare da barin su a gurin. Suna kiran shi da Mehran kasancewar shine Aamaan na biyu da ya amshi masarautan, kuma Sarkin su na gaba. Tunda ya fita Sultanah Hoyam ta mike tare da cewa. "Na bawa namiji mulki kamar yadda kuke bukata saura me?" "Saura ki zare hannunki a cikin mulkin shi, idan kika barshi yayi mulkin shi cikin nutsuwa zaki samu kwanciyar hankali, idan kuma kika shiga cikin wannan lamari. Zamu yi wasan zubda jinin al'umma, wanda haka kuma zai iya kawo juyin juya halin a daular Abbasid." Ya fada cikin Izza da mulki. Murmushi tayi sannan tace. "Mir Rahil ni kake gayawa magana kai tsaye?" "Na gaya miki magana ne a matsayin namiji, wanda yake da karfin al'umma a kasa shi, Hoyam!" Wani irin kallo take mishi tare da gyada kanta. Irin zamu hadu nan gaba. *Ku danyi hakuri kai na yana ciwo wallahi*😢 *Alqur'an akwai matsala 🤔🤣 Chakwakiyya zalla 👌🏼* #Paidbook #Mai_Dambu *Book one free ne, book two da three na kudi ne 200₦ ta bank 0472282105 ko katin mtn ta wannan Number +2347035133148 ko ta wannan Number 08130269641* Happy weekend 💞💝 [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: https://www.wattpad.com/1008832612?utm_source=android&utm_medium=link&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=Mai_Dambu&wp_originator=hV0o6BRzWV9PE%2FPSkh1CA2aeSMIhkctp%2FU0dOLVFW44lHA944Is10c8h8lv2s34K68eKo39RK%2FCg10dJp4XTqTiWBApgP0IPngp9nByELBwl9t%2FKYgEJ0qvROFec78bS ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 Book 1 Mai_Dambu BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM ```HAPPY BIRTHDAY To You MUHAMMAD KARIM, Ubangiji ya karo shekaru masu Albarka``` 🍦🍰🥧🎂🍭🍮 Page 12.. Murmushin da ba zaka iya fahimtar na me ba, ta sake tare da gyad'a kanta. Har ta nufi hanyar cikin gidan shi. A hankali take takawa kasancewar gidan ya dauki shiru, baka jin ko motsin rai. Abinda ya faru tsakanin su da Aamaan yake kuma dawo mata a rai, lokacin da tazo Mishi da batun ya amshi mulkin shi. Tun da ta fara magana yake wasa da wata kofin da kayi shi da karo me hade da danyen azurfa, matar inda karon yake. Kaskantar da kanta tayi cikin sanyin murya da rarrashin, tare da kalamai masu laushi da taushi me hade da tsantsar siyasa da hikima tace mishi. "Mehran! Yau gani gare ka, da kokon barana akan wannan zaman da kake ya isa haka!" D'ago kai tayi tana kallon shi sannan ta sunkuyar tare da cewa.. "Mehran, duk duniya bani da gatan da ya wuce kai, Mehran Daular Abbasid sun dauke min Ubana sun dauke min Uwata! Mehran ga mahaifiyarka tana zubda kwalla tare da niman ka amshi mulkinka domin na fara fuskarta juyin juya halin dangin ka." Matse kofin karon yayi sai da karfen azurfan ta suke shi jini na d'iga daga hannun shi. Ya kafeta da idanun shi masu kama da na mashaya, har wani hazo hazo suke, idanun ya bude su kuwa wani irin kyali suke tare da tara ruwa. Ƙwayar idanun shi kuwa dauke take da wata irin ruwan zinari ko zaiba za a ce, tsakiyar idanun kuwa d'igon ruwan toka ce, me shegen kyau. Matukar zai kura maka idanu, kaifin idanun shi sai Yasaka ka sunkuyar da kanka, a sanyayye tayi kasa da kanta. Baya jin zai mata magana, dan haka ya dauke kanshi tare da wasa da jinin da yake d'iga a hannun shi. "Mehran! Sunci mutuncina, sun wulakanta ni, yanzun kuma suna ƙoƙarin kwace mulkin ka da karfi, idan suka sami nasarar haka, tozartani zasu yi, Mehran" D'ago zafaffan idanun shi yayi, ya zuba mata su. Fuskar shi babu alamar wasa ko sauki akan shi. Dauke kai yayi tare da mata alamar tayi tafiyarsa kawai. Mik'ewa tayi a hankali ta tako gaban shi. Tare da kama hannun shi ta sumbata. "Allah yayi maka tsawon rai da albarka, ya bamu ikon rike mulkin kasar nan a tare." Kai hannunta tayi kanshi, lumshe idanun shi yayi abinda ya rasa kenan, shekaru masu yawa. Yau gashi ya same shi, duk da bai son magana sai dai Allah yayi mishi wani irin dabi'a, shi mutum ne me mugun bukatar kulawa. Ko yayya ka nuna kulawar ka akan shi toh bai da damuwa zai iya zama da kai. Shima zaman na kurame, dan har sun saba da halin shi. Na rashin magana da shiga sabgar kowa. Sai dai yana da mugun dabi'ar da ya kasa rabuwa da shi,ba kome bane sai idan dare yayi yana shan barasa,idan ya sha haka zai kwana a duk inda ya hantsila, sai dai Darakshan da Fudail su kinkime shi zuwa makwancin shi. A hankali ya zare hannun ta akan shi, tare da kallon kofar, babu musu ta juya ta fita. Sunkuyar da kai yayi sannan a ranshi yake cewa. *Bayan shekaru da dama yau zan fara fita waje? Hmmm"* Ya faɗa yana me juya al'amarin, a hankali ya tab'a wata karfe, take karar ya cika falon, ko minti biyu ba ayi ba, Fudail da Darakshan, suka shigo. Kallon dakin shi yayi, da sauri Darakshan ya wuce, shi kuma Fudail ya nufi waje can sai gasu tare da wani tsoho, yana zuwa ya fara kunce kayan hannun shi, a hankali ya ciro kayan aikin shi. Cire kwalbar karon yayi tare da wanke ciwon sannan ya saka mishi magani, kafin ya mike tare da cewa. "Sultan Allah ya baka lafiya!" *Allah?* Ya tambayi kanshi, a iya sanin shi bai tab'a jin wannan kalmar ba, sai a bakin tsohon likitan masarautan. Watsar da abin yayi tare da kallon su Rakshan yayi, sannan ya mike, dakin shi ya nufa. A hankali ya shiga ban daki, wata katon kwarmin wanka ya gani cike da ruwan zafi, wanda aka zuba mishi turarruka, a hankali ya shiga tare da zama. Bayan ya cire kayan shi. Daura kan shi yayi inda ake tanada wani matashin kai me laushi. A hankali yake bude jikin shi ruwan na ratsa shi, ya jima yana jin dumin ruwan, tare da jin amon kalamun Mahaifiyarshi, --- "Sultanah! Dole Sultan Aamaan zai bukaci bayi mata, masu rawa, masu kula da saka mishi kaya, hada mishi ruwan wanka!" Inji Narmin, Cike da jin zafi abinda ya faru, kallon shi tayi sannan ta daidaita nutsuwarta tace. "Bayin da za a kawo daga Oman zasu zo dai-dai lokacin da ake bikin nadin sarautar shi, sai mu zab'a mishi wanda muka ga sun dace da zama a shashin sa." "Kuma Kinga kome zai zo miki da sauki!" Kurawa Narmin idanu tayi. "Ba dai dai bane, domin ai kowa yasan Abrad ya bada Kanwar shi, bayin da zata zo dasu zasu tashi a matsayin namu ne, rashin kunyar da yayi min,Kanwar shi zata fuskance shi. Dan sai na tozartata, na wulaknta ta, abu daya nake so.kar a yarda Sultan yaji wannan kazamin labarin" Gyada mata kai tayi sannan tace mata. "An gama ya shugabana" "Idan kin fita ki kira min Khabir"inji Sultanah, Bayan fitar Narmin,sai ga Khabir ya shigo, kallon juna suka yi, sannan ya gaida ita. "Ka san inda Alimah take?" "A'a Sultanah, sai dai na saka a miki cigiyarta!" Alamar ya tafi tayi mishi, aikuwa da sauri ya bar dakin mu. "Akwai abinda Alimah ta sani? Wanda yaja Sultanah koranta. Tabbas sai inda karfina ya kare, domin sai na nimota a fadin duniyar nan!" ** Oman. Yau kwana hudu kenan, da zuwan mu. Ina zaune aka kirani, a hankali ya mike tare da saka takalma na, na fice. Ina bin bayan wacce tazo kira na, wani katon fili ne, yana tsaye rike da takobi yana, kara bawa wasu horo. Tsaki nayi a hankali idanuna ya sauka akan wata yar karamar wuka. Me kyau na cin tufa. Dauka nayi a hankali na bi ta bayan wasu ganye masu tsayi, ina isa inda yake..na wurga mishi wukar. Kamar wanda yake gani na,kaucewa yayi wukar ta sami daya daga cikin mutanen da suke daukar horon ya'ki. A tsorace nayi baya, zan gudu. Ji nayi an damke ni. Fito dani aka yi tare da wurgani gaban shi. Sai lokacin na lura Ashe su uku ne, Zur da Nawwas, wukar ma yar banza Zur ta samu. Takowa yayi gaba na, ya zauna. Diban kasa nayi tare da watsa mishi zan gudu, ya damki hannuna tare da, rike wuyata zuba min ido. Jikina ne ya mutu, nayi kasa da kaina,.a hankali na fara ƙoƙarin kwace kai na, watsewa su Zur da Nawwas suka yi, kura min ido yayi cikin jin dadi. "Har yanzun kin kasa kwatar kanki, da kin kashe ni zaki iya tafiya ko yanzun." Tashi nayi da sauri na ɗauki wukar, Dariya yayi sannan yace min. "Amma da alamu yarinta yana damunki. Maza zo nan" Kasa motsi nayi ina kallon shi yadda yake dariya, a hankali na sulale kasa na zauna. Sai a lokacin na sami damar zubda kwalla. "Tashi." "Ba zan tashi ba!" Mik'ewa yayi tare da ɗaukar wukar ya iso gaba na. Zama yayi muna kallon juna, a kura min ido yayi cikin nutsuwa. "Me yasa kike son komawa gida?" Kallon renin hankali nake mishi sabida yadda tambayar shi ta zama ta renin hankali, mik'ewa nayi zan bar gurin. "Har yanzun kina da'irar birnina, dawo ki zauna." Zama nayi ina kallon kasa, tare da wasa da kasa, A duk lokacin da na lumshe idanuna, Airan ce a cikin shi. "Wacece ke" "Ka kirani ne dan kaji tarihina?" "Ban Kiraki dan naji tarihinki ba, sai dai ina jin a jikina baki cancanci zama baiwa bace!" "Idan kuma zanen ƙaddara ta ce fa?" Na tambaye shi, "Babu shakka, ba zan yi sake reshe kama ganye ba, dan haka wacece ke?" "Ni ba mutum bace, ko baka ga kwayar idanuna bane?" Gyada kai yayi sannan yace min. "Haka ma yayi." Idanuna na kan wukar shi, dan haka burina d'aya na yanka shi ko ta halin k'ak'a, mik'ewa yayi nima na mike tsaye, tare da wukar, ya bude baki zai min magana kawai, sai jin kaifin wukar yayi a gefen cikin shi. Kura min ido yayi, cikin mamaki. "Meye kika aikata?" Sai lokacin na sake wukar, tare da kwala kara, jikina yana rawa, shigowar Nawwas, tare da wasu manyan fadawa guda biyu, ya sani fashewa da kuka, tasani suka yi a gaba, har kurkuku. Shi kuma Nawwas ya rike shi suka nufi cikin gidan sarautar, tunda ya zaunar dashi bai, iya cewa kome ba, har Azizatul Nissah da Yar shi Ilham suka zo, sun same shi ana gyara ciwon. "Bata da laifi, ni na sakata yin haka!" "Yaya meke faruwa ne?" Kafin yayi magana Nawwas ya rigashi, kura mishi ido tayi sannan ta bar d'akin, duk da yana kiranta bai sanya taji a ranta zata kula shi ba, can kurkuku ta nufa, tare da sawa a dauko mata Ikram. Tunda aka fito da ita, take kallon ta, cike da mamaki. Yadda tayi mugun kama da Mamar Ilham, dauke batun tayi tare da sawa a dauko bulala, ana kawowa tasa a shiga dukarta. Cikin mugun kiyayya nake kallonta, haka itama. Dukda dukar da ake min bai sani dauke kai na akanta ba, har sai da suka min dukar da ko kai na kasa d'agawa. "Kuyi ta azabtar da ita har sai ciwon jikin Yayana ya warke." Haka ta faɗa tare da barin gurin, suka jani zuwa cikin kurkukun. Inda aka shiga azabtar dani, duk taurin kai na, sai da nayi sanyi, bana iya kuka sai na zuci. Amma izuwa lokacin zuciyata tana gida. Dan haka duk abinda ake min gani nake domin lafiyar kanwata ake yin shi. Sai da na kwashi kwana goma sha daya, sannan yazo da kanshi. Kallon juna muka yi, sannan na wuce zan bar inda yake. Dawo dani yayi tare da kallona. "Me yasa baki da hankali?"ya tambaye ni, Shiru nayi tare da juyawa zan bar gurin ya riko hannuna, ya ratsa cikin gidan dani, sannan ya fito dani ta babban kofa. Kwace hannuna nayi, ina hararar shi. "Me yasa kika tsani kowa? Me yasa ba zaki yi mu'amala da mutane ba? Ke kin fi son kullum." "Kasan me? Idan baka da abin fada na juya na koma cikin gidan" na fada ina kallon shi. Shiru yayi sannan ya bude baki zai min magana na juya abuna, zai bini,. Nawwas ya rike shi. "Kai fa Sultan ne? Sannan tun daga lokacin da kayi arba da ita ka watsar da kome naka. Sannan karka manta akwai matsala a gaba, yau saura kwana biyu rak, a kai su SAMAIND, me kake nufi Sultan?" Ajiyar zuciya ya sauke tare da kallon Nawwas, girgiza kai yayi sannan yace. "Tunda na hadu da na ganta na rasa kome, ji nake kamar ni ba Basarake bane, Nawwas bana jin zan iya barin ta haka ba, bazan iya bawa SAMAIND kyautar da Allah ya bani ba. Ba zan iya basu ita ba." Shiru Nawwas yayi tare da kallon shi. "Amma yarjejeniyar sulhu tsakanin mu da su, kai kace ka badda kanwarka domin sulhu,.kenan zaka badda Azizatul Nissah ce, a rufe kofar tashin hankali ko kuma zaka sallama musu Ikram?" Lokaci guda kome ya tsaya mishi, "Ba zan bada su ba dukkansu. Koda kuwa hakan yana nufin share daular Umayyad ne baki daya, ba zan iya sake musu mata masu daraja..." "Sultan Abrad!" D'agawa Nawwas hannu yayi tare da barin gurin, ran shi na b'aci sosai. Koda Nawwas ya koma fada, nan ya tara manyan mutanen fadar ya musu bayanin halin da ake ciki akan Sultan yaki mai da hankali, kuma nan da kwana biyu zasu cika alkawarin su. Amma ya gwammace ayi yaki da ya bada daya daga cikin Matan da yayi magana akan su. Nan kuwa suka tasa, maganar a gaba... ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 Book 1 Mai_Dambu BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM Page 13 Bai iya kare kan shi ba, sai dai kuma ya kasa furta musu koda kalma daya ce, kallon su yake tare da jin tashin hankali sama da kome a rayuwar shi. "Yanzun kuna ganin na basu Ikram?" Yadda yayi maganar a raunane sai da suka sunkuyar da kansu. "Ba sauke kai nace kuyi ba, ina son ta ne, zan nime wata baiwa ta maye gurbin ta, ita kuma ta tafi a matsayin baiwar da take kula da lafiyar wancan, bayan haka." "Sultan Abrad ba zai yiwu ba, kowa yasan halin Daular Abbasid, kowa yasan yadda suke iya sarrafa makami a hannun su, idan suka fahimci anci amanar su. Daular Abbasid ba kamar nan daular Umayyad bane, muna da saukin mulki da iya mu'amala da kowa, kasancewar sauƙin mu yasa duniya take mana kallon matsorata. Ba tsoro bane muna da dinbun al'umma da suke zaune dan niman na kasu. Muna da masaniyar yadda suke gudawa daga yankin da aka farmaki su, zuwa yankin mu. Dan haka kayi ƙoƙarin gano shin wadannan talakawan naka sun cancanci a zubda jinin su ko basu cancanta ba. Karka manta miliyan uku da rabi na dakarun yakin SAMAIND, su kadai zasu tashi daular Umayyad." Inji Sheikh Saiful Badarr, Shiru kowa yayi, cikin takaici ya mike, tare da barin fadar. "Sultan!" "Ayi duk abinda ya dace, amma banda aurin aure." "Suma basu bukaci haka ba, duniya kawai suke son tasan halin da ake ciki." Yana shiga ya zamu, amintacciyar baiwar shi Nagar, yace mata. "Ki kawo min Ikram turakata." Yana jin wani irin tashin hankali, jin yaƙe kamar yayi wurgi da zuciyar shi. -- Ina wanke kayan da ake girkin kurkukun aka kirani, tashi nayi tare da nufar gurin. "Kizo" Ba musu na bita, cikin gidan sarautar muka shiga, inda ta haɗa min ruwan wanka, tare da turaren wanka, haka nayi sannan na fito tare da gyara jikina, bayan na gama ta bani turare na shafa na shafe jikina da man zaitun wanda aka hada da turaren joda. Ina gamawa ta mika min wata riga iya gwiwata, me tsantsi. Irin yadin kasar Sin, hannun rigar kamar igiya haka yake, sai gaban rigar da yake shara Shara, kana iya hango kirjina da yadda suke tsaye. Gasu a cike suke tam, daura min wata abaya tayi, sannan muka nufi shashin Sultan. Tana kai ni bakin kofar ta buga aka ce ta shiga, tare muka shiga sannan ta juya abinta, rufe kofar tayi. Juyowa yayi yana kallona, sannan ya tako gabana, rike hannu na yayi. A hankali ya jani har bakin gadon shi. Zare abayar yayi sannan, ya kalli jikakken gashin kai na. Ajiyar zuciya yake saukewa tare da matsowa kusa dani, yana cigaba da zare rigar jikina. Rike hannun shi nayi. "Karka tab'a min alfarma ta, domin na, abokin rayuwata ce." Fincike rigar yayi,.idanun shi ya dauka akan kirjina. A hankali ya sake labulen gadon. Sannan ya jani cikin gadon, a hankali tare da nutsuwa, yake gabatar min da kanshi, ban san me aka bani, amma tabbas na kasa fahimtar kome akan shi. Juyar da kai na, nake tare da lumshe idanuna. Abinda ya faru da Airan yake yawo a cikin idanuna, sakamakon jin hannun shi a tsakanin cinyoyina, mai da hannun shi yayi kirjina, wata irin ajiyar zuciya na sauke, tare da saka hannuna dukka biyu na ture shi na ja,. mayafin na rufe jikina. Kuka na niman kwace min, kamar sakarai haka ya tawo min, ture shi na fara ƙoƙarin yi. Ya murɗe ni da karfin tsiya. "Ina da ikon nayi yadda nake so dake, amma burina nayi da yarda ki, don Allah ki Fahimci sakon zuciyata." Ya faɗa min. "Ba sakon zuciya bane, shaawa ce zallah don Allah karka raba Ni da kimata. Kana da kanwa da Y'a!" Hannun shi ya kai lausassan nonuwarta, ya matsa a hankali har zuwa kan su. Kan shi yana saman wuyana, lasar wuyana yake har zuwa kunne na. Ina jin yadda halittar shi take motsawa, ya sani rikicewa da kuka. Cizon kunne na yayi, tare da cewa. "Zaki tafi kasar SAMAIND, aiki zaka min. Idan lokacin Barinki kasar yayi zan zo gare ki, Ikram ki saka ki ajiye domin ni naka halicce ki, karki kuskura wani ya tab'a min kimarki" A hannun shi ya kai kasata,.yaji yadda ruwa yake sauka. Wani irin a jiyar zuciya ya sauke sakamakon yadda yaji gurin ya jike sosai, dan haka ya shiga wasa da gurin, wani irin rawa jikina ya dauka,.ta k'amk'ame shi, ji nake kamar zuciyata zata fado, juyar dani yayi tare da cewa. "Ba zan rabaki da dukiyar ki ba, amma zan sauke ajiyar da yake jikina..na shekarun kewar mata ta" Yadda yake aikin tare da maganar yasan ya jikina yayi wani irin mutuwa,domin kuwa ba zan iya cewa Sultan Abrad ba karshe bane, domin yasan yadda ake sarrafa mace irina me shegen taurin kai, Wani irin mika nake tare da tura mishi jikina.. murmushi yayi yana jaddadawa kan shi, Tabbas narga tayi amfani da turaren miski domin kashe karfin jikin Ikram, wanda shi yake azzazala mata sha'awan ta. A hankali yake goga yar jamiyar wandon shi, a jikina inda suka haɗu da ruwan jikina da na shi, suka bada wani yanayi na daban... (Bari nayi nan) Duk da bai shiga jikina ba, amma na fahimci shima sai da ya sauke kayan nauyin shi sannan ya rungume ni, yana shafa bayana, Noman nake hangowa a idanuna. Hawaye na zuba min. A hankali barci ya dauke ni, a jikin shi. Sake shigar dani yayi jikin shi, yana shafa bayana a karo na babu adadin. Dole ya yayi wani abu. ** SAMAIND Kallon yadda dabbobi suke rayuwar su yayi, cikin yanci da walwala, shi kuwa an saka mishi sassari tare da nauyin wasu al'ummar da bai shirya dasu ba, *Me yasa duniya take cike da masu son kai ne? Me yasa ba a bani damar.* "Sultan Mehran!, Akwai baki daga yankunan gabashi kasar nan sun zo maka mubaya'a!" Inji Rakshan, Bai mike ba, kuma bai amsa ba ya cigaba da kallon dabbobin da suke shawagi a lambun ne, Rakshan zai Kuma magana Fudail ya dafa kafadar shi. Girgiza mishi kai yayi tare da mishi alamar yana sane da abinda kace. Sauke ajiyar zuciya yayi, tare da kallon Fudail, A takaice sai da suka kwashe awa daya a gurin kafin ya mike dan kanshi ya fice daga lambun suna bin bayan shi, mutum ne da bai son hayaniya, shi yasa yake keb'ancewa daga hayaniyar. Yana fada ne a zaune suka ishe shi da surutu ya, bar fadan yanzun kuma zuwan baki daga wasu yankunan yasa zai je. Koda ya shiga ya samu har lokacin suna magana, akan tsarin lallai duk budurwan da zata shigo masarautan dole ta zama tana budurci idan ba haka ba, toh sai dai a sauke Sarkin. Sannan kuma ita a kashe ta, wannan shine gaskiyar maganar da suka yanke, dan haka sauran gwamnatocin da suke ikirarin zasu bashi Ƴaƴan su mata, su san da tsarin. Wannan sakon Sultanah Hoyam ce. Kuma manyan fadan sun amince da shawaran ta. "Muna gaisuwa da sabon Sarki wanda za ayi bikin bashi sarauta nan da kwanaki biyu, Sultan Aamaan Mehran na biyu, Rahab itace yankin da nake jagoranta. Sannan muke da alhakin sarrafa, sulkin yaki Sultan ga mafi Nagartan Sulken yakin da muka sarrafa da hannun mu,.ka ka amshe shi da farin ciki. Mikawa Rakshan aka yi ya mikawa Fudail, juyawa yayi sannan ya mikawa Sultan Aamaan Mehran na biyu, a hankali ya sake rigar ta fadi kasa, Yasaka kafa ya taka. Gyada kan shi yayi sannan ya Kalli Rakshan. Dauka yayi sannan ya ajiye a gefe, su kansu manyan fadar. Kallon mamaki suke mishi musamman yadda yake magana da idanun ko da hannu, sannan idan bai son abu, karara suke ganin baya bukatar shi a kwayar idanun shi. "Sultan Mehran! Wannan kansakalin yaki ne, Sultan shine abu mafi daraja da muka sarrafa shi..ka amsa da farin ciki." Murmushi Amir Hood yayi sannan yace. "Sultan Mehran yana godiya abisa wannan kyautar da ake bashi." "Sultan Mehran! Ga takobin da tafi kowacce takobi daraja, da ita akayi yakin Birnin Quzai, kuma da ita aka yaki Ranvagalas, Sultan Ni nake jagorancin garin, Wurta sannan wannan takobin ita daya ce garkuwa ga Mutanen wannan yankin,. Bamu da kyautar da ta wuce wannan, kasancewar muna cikin Sahara ce.. gata nan sai jajjayen Rakumai guda dubu tara da muka kawo." Kallon mutumin yayi sannan ya kalli magatakardan masarautan, wanda yake ta rubuta abinda ake kawowa. Kafin ya kalli Rakshan cikin idanu.sannan ya shiga wani irin motsa hannun shi, yana haɗawa. Kana ya Kuma hada hannun shi har sau biyu. _Kace ya maida garkuwan su da dabobbin su yankin su. Shekara me zuwa ya cika min dabbobin ya kai dubu goma_ Kallon mutumin yayi, sannan ya kalli Sultan Mehran! Tare da sake ajiyar zuciya yace. "Mir Jazib.. idan na fahimci sakon Sultan Mehran yace ka mai da garkuwarku yankin ku, sannan shekara me zuwa ka tawo mishi da dabbobin nan guda dubu goma." Gyada kai Mir Jazib yayi tare da komawa ya zauna. Kallon Rakshan mutanen fadar suka yi suna mamakin yadda ya iya fahimtar lamarin Sultan Mehran. A hankali suka gama gabatar da kansu..kafin Mir Umdatuddawla ya mike tare da cewa. "Sultan Aamaan Mehran, mun gama kawo yadda za a shigar da batun yan matan da zaka aura. Abinda muka yanke, shine bamu yarda a kawo wata mace daga yankin da ake samun yar tsama dasu ba, sannan bamu amince Sultan ya shigo mana da baiwa cikin masarautan nan ba, Bamu amince ya bawa wata mace damar Sultanah ba, har sai ta haifi d'a namiji, Sannan Sultan yana da ikon zartar da abinda yake bukata amma shima sai ya nime shawaran Mahaifiyar shi, Sultanah Hoyam. Sannan dole ne Sultan ya bayyanawa masarautar nan yayi tarayya da Ƴa mace ko yar waye, Sannan." Dakatar dashi Sultan Mehran yayi, tare da mik'ewa a gajiye yana nuna alamu da Rakshan yaji da kome. Bayan fitar shi Mir Rahil ya mike cikin fusata. "Meye Mehran na biyu yake nufi? Ba zai bude baki yayi magana ba, sai abinda kuka ce." "A wannan lokacin na mulkin sh, dole kubi abinda yake nufi, kuma dole mu yanke hukunci ga duk wanda ya nime bijire mishi, Sultan Mehran baya magana, bayana nufin shi kurma bane ko bebe, shi mutum ne da magana bata shiga bakin shi ba, idan yayi muku, bismillah" Daga haka ya juya suka bar fadan. "Dole mu saka shi yayi magana, dole yayi magana, ya zama wajibi yayi magana, matukar ina raye zan saka shi yayi magana.!" "Babu wanda ya isa ya samin Yarona yayi magana!" *** Oman Kallon Ikram yayi sannan yace. "Babu wanda ya isa rabani dake!" Inji Abrad, *** Gezira. "Insha Allah babu wanda ya isa ya shiga tsakanin mu sai Allah, Ina tafe niman ki!" *Alqur'an akwai matsala 🤔🤣 Chakwakiyya zalla 👌🏼* #Paidbook #Mai_Dambu *Book one free ne, book two da three na kudi ne 200₦ ta bank 0472282105 ko katin mtn ta wannan Number +2347035133148 ko ta wannan Number 08130269641* [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: https://www.wattpad.com/1033847662?utm_source=android&utm_medium=link&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=Mai_Dambu&wp_originator=U%2BKxfjj9pAp6lNBwOKTrL0n8IZodUh1%2Fi4kPauenrACA5g3CpBPg2XKNYbJz2ZMOPcIzyi5QVLlSuzMupzKMqu6w439ysIbmau4%2FPRE%2F5MsqRS%2F8ngta9Wj%2FVEanIgc3 ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 Book 1 Mai_Dambu BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM Page 14..... Har ila yau, baya jin zai iya rabuwa da Ikram, shi yasa yake makale da ita, kamar wacce aka bata bamju. Barci take akan gadon, har ya shigo da Narga ta gama zagaye fuskarta da wani bakin abu, musamman gefen fuskarta na dama, sannan ya sallame ta, ya cigaba da hadinta. Yau da ya haɗa jikin shi da nata, yaji abinda yake son ji. A hankali ya sauke idanun shi kan babban yatsar hannunta. Wanda yake dauke da wata yar karamar chindo sak irin Sariyah, wannan kama da mugun yawa take. Mikewa yayi tare da barin d'akin, ya nufi lambu ya zauna, tare da tuno abubuwan da suka faru, daga auren shi. Har zuwa rasuwar ta, bar mishi yarinya. *Ban farka ba sai kusan Magarib, a hankali na bude idanuna tare da kumshe su. Abubuwan da suka faru yana dawo min daki daki. Dafe goshina nayi tare da tattara zanin gadon na tashi zaune. Hada kafaffuna nayi tare da daura kaina a saman gwiwa ta. Wani irin bakin ciki nake ji, ban san me ya shiga kai na ba, har nayi kokarin raba kimata ga wannan bakin azzalumin. Turo kofar da yayi ne ya sani kallon shi, sake mai da kai na nayi cikin matsanancin kunya, takowa yayi har gabana, ya zauna a kasa yana me jingina jikin shi da gadon. "Ikram Wacece Airan?" Ware idanu nayi ina kallon shi, kafin na dauke kai na, tare da cewa. "Meye matsalar ka da son sanin kome akai na ne? Abinda kayi dani bai isheka bane sai ka kuma sanin sirrina!" A sanyayye ya mike ya dawo saman gadon, zuba hannun shi yayi saman kafana yana matsa min su. "Ban san me yasa kake son tab'a ni ba, kai baka da kawazuci ne?" "Ina dashi mana, haduwa ta dake ya sani jin zan iya yakince wancan yanayin na zauna da ke." Tsaki naja tare da mikewa na nad'e jikina da mayafin gadon, fisgo ni yayi tare da warware mayafin, ya mai dani gadon shi yana me kwanciya a sama na, kallon idanun juna muka yi tare lokaci guda. Goga min hancin shi yayi a saman nawa, tare da matsa min kirjina zuwa cikina. Buge hannun shi nayi tare da watsa mishi harara, dariya yayi yana me sake naushin shi a kaina. "Da alamu baki kalli fuskar ki ba, don Allah karki cire kome na fuskarki, bana son ki samu matsala da kowa ne Kinji." Dauke kai nayi, amma dake ya san kan mugunta ya kuma jibga min nauyin shi. Dole na bude baki zanyi magana, sai jin harshen shi nayi cikin nawa, ware idanuna nayi akan shi, cike da tsoron Allah.(wallahi kuwa tsoron Allah kaca-kaca a ranmu 🤣) "Don Allah d'aga ni!" "Ikram! Babu namijin da zai baki tsoro, ina son mace irinki don Allah karki yarda wani dalilin rayuwa yasa mu rasa junan mu!" "Kai sarki kake ko Sultan? Na tab'a gaya maka ina sonka ne? Ko nace maka ina kaunar ka ne? Babu abinda ya dame ni, ni mallakin Noman ne, kuma Insha Allah." Cizon lebbena yayi tare da lasar bakin zuwa wuyana. "Ina da kishi amma bai hanani na bar mace tayi abinda ta zab'a ba ba, don Allah bar kiran sunan namiji a gaba na." Ya faɗa min. "Matsalar ka ragagge ne, Ni bani da matsala da wannan tunanin, wanda nake so yana can yana jirana na. Zan iya mutuwa domin so, amma ba zan tab'a mutuwa akan so ba, dan haka koda zan mutu domin so na mutu, bana fatan na mutu akan so." Daga haka na ture shi tare da nufar ban dakin ina jan zanin lulluben, haka na shiga ban dakin nayi wanka sosai, sannan na fito da alola. Mika min tufafin mata yayi na gabatar da sallar da ake bina, sannan na daura wanda aka yi lokacin. A hankali na gyara jikina tare da cire kayan na dauko wanda nazo dashi zan fita. Yana zaune yana kallona. "Da zaki iya da kin hakura da fitar na sai gobe!" Juyawa nayi tare da kallon shi a takaice, sannan na saka kai zan fita naga wajen turakar da duhu sosai. Dole na juyo da sauri tare da komawa dakin shi na haye gadon da mugun sauri. Murmushi yayi tare da kallona yana cewa. "Lallai baki da dama, haka kike tsoro dama?" Murguda mishi baki nayi tare da cewa. "Ba dai mugunta bane halinka zaka gani a kwaryan cin abincin ka !" "Toh tashi ki koma mana ai bani na dawo dake ba?" "Da baka dawo dani ba, amma ai ka tsorata ni" "Bana son sharri, Ni ban dawo dake ba, kawai dai baki fita da zuciya daya bane" "Toh waye yace ka sara min baki, Ni bazan kwana a daki daya da kai ba, dan Ni ban." Tashi yayi zaune, tare da kallonta sannan ya zuba tagumi, dan ya fuskanci ga baki daya rashin kunyarta ba wani damunta take ba, "Me yasa baki da kunya? Me yasa duk abinda zai fita daga bakin ki baya zama me dad'i?" Jikina ne yayi mugun sanyi, kwanciya nayi, tare da lumshe idanuna.ban kuma bashi amsa ba, sakamakon barcin da yayi gaba dani. *** SAMAIND A hankali suke shigar da sabon tsarin da aka shigar dashi masarautan. "Sultanah Hoyam, a da can baya kafin zuwan ki. Bayin da ake kawowa cikin daular nan,.toh akan fidda tsarin mu'amala da bayin ne! Mukam zab'e kyawawan cikin su, ga sarki tare da saka musu alama a hannun rigar su. Bayi kenan, Mataki uku zuwa huɗu ne. Kuyangin sarki ana basu wani ƙaramin kambu ne, su daura akan su. Sai bayi na biyu ana tura su shashin Sultan da Sultanah, domin su dibe musu kewa. Da kade kade da raye-raye. Sai mataki na uku. Akan tura su madafi tare da nasu girki. Sai matakin karshe ana tura su, aikin a cikin masarautan baki daya, tare tura wasu gefen tsohuwar fada." Matakin farko banbancin su shine suna da kambun azurfa, na biyu suna da jan zare a hannun rigar su. Mataki da uku suka da koren zare a wuyar su, sai mataki na uku akwai kalar rawaya. A jikin rigar su. Sannan sai matakin horar da wacce zata iya zama Kwarkwarar sarki, zata kasance ba a hada ta da sauran." Kurawa Narmin idanu tayi sannan tace mata. "Wannan ba zai zama matsala ba, dan haka. Jeki kawai zamu yi magana daga baya." Narmin na fita ta jingina kanta da hannunta, karfin hali take amma tabbas tana jin kamar zuciyarta zata kama da wuta. * "Dole ki hadu dashi yau, tare da nuna mishi murnan zama sarki na gaba. Jasrah karki sani jin kunyar kai na, ki bi duk abinda zasu saka ki." Gyada mata kai tayi tare da, fita tare da nufar kofar da zata fita. ,--- tunda ta fita take bin zomo har gurin shan iskar da Sultan Aamaan Mehran yake zaune shi daya. "Kai mavisha, katsa min mana karka gudu ka bar ni! Don Allah ka tsaya min." Aikuwa dan zomon na zuwa ya shige cikin kujeran da Sultan Aamaan Mehran yake zaune akai. Tunda ta shiga gurin take kallon yadda lambun ya haɗu, a hankali idnun ya sauka akan wani kyakyawan halittar Allah. Gyara tsayuwar ta, tayi sosai tana kallon shi cikin al'ajabi, tunda take jin labarai irin na hikaya da al'ajabi bata tab'a jin ko ganin mutum me kyan halitta irin shi ba. Tun d zomon ya shigo, yake sane da shigowar ta, sai dai wani abun mamaki, shine kamar wanda aka gaya mishi ana cillo wani abu, da sauri ya saka kafar shi ya kwashe ta, aikuwa sai ga dogon mashi an wurgo mata ta bayanta. Haka yaje ya faɗa kan itaccen tuffa, ihun da tayi yaja su Fudail da Darakshan, suka shigo lambu. Da sauri suka ce mata. "Kwanta, karsu kuma wurgo miki wani abu!" Kamar wanda suka sani aikuwa su ga wasu an kuma cillowa, dakyar suka kare yarinyar tare da turata hanyar gida, bayan kaman minti biyar, sai ga wasu ruwan kibbau, fauce takobin hannun Fudail. Ya nufi inda ake wurgo musu mashin, tunda ya nufi gurin Fudail suka rufa mishi baya. Suna shiga suka tadda wasu gungun mahayan kisa ne. Suna shiga suka musu kawanya. Kallon yake, kafin ya kalli kayan fadar hannun su, tankar wasu dakaru. "Da farko Sultan yana shirin yi muku afuwa, dan haka ku bar nan kafin ya iya sauya ralayin shi." "Kai shafaffe mara amfani, mu da uban gidan kare muke ba da kare ba, karka yarda na fusata. Domin zan koyawa wannan yaron da wuyar shi bata gama yayye shi ba, bari na nuna muku yadda ake gudanar da aiki cikin salama." Cikin ihu suka nufe su, domin su musu ribdugu, sai dai ance ba a san maci tuwo ba sai miya ta kare, domin cikin zafin zuciya, Sultan Aamaan Mehran ya tare su, lokacin guda aka fara faffata wani irin azazzaben yaki wanda ya sanya kura ta turnuke sararin samaniya. Lokaci guda aka fara cin kasuwar jini da gawargaki ake cikin su., kafin su ankarar da abinda yake Faruwa, Mehran ya musu muguwar barna, domin a cikin kankanin lokaci, kasa ta sha jinin ta koshi. Baka jin kome sai karar takuba da Gatari. Dama ina nan na muku alƙawari...... Paid book. Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: https://www.wattpad.com/1034092544?utm_source=android&utm_medium=link&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=Mai_Dambu&wp_originator=GuO7QZMwU%2FP%2FXoEqsI0M1logOSHj%2B72o1vXIXR4Es5gqGkIQneuqZrg8irRFHx0MjVmpoIEb6MkTxTKSDYI8Yq60uLbQaYeOzkw8wbglg3C2gM1zL10iGPO104Nmoyng 🐾ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜🐾 _The Historical_ ~BOOK ONE~ Mai_Dambu Bismillah Rahamani Raheem. Page 15.. Su goma sha huɗu aka Turi su, kafin kace me Sultan Mehran yayi musu rubdugu, ya dargargaje su na fitan hankali. Kura Mishi ido Rakshan da Fudail suka yi zuciyar su tana wani irin bugawa, zunzurutun tashin hankali ta tsoron shi da shakkar shi ne ya darsu a zukatar shi. Tabbas sun san an hora Sultan Mehran a cikin castly din shi, amma basu tab'a tunanin horon yakin ya kai inda zasu razana haka ba. Domin lokacin wasu mutane biyu suke zuwa horar da shi, daya dan kasar Hindu ne daya kuma ɗan ƙasar Sin ne. Mutanen biyu sun shahara a fagen yaki da dambe, kwararru ne a iya sarrafa takobi da kwari da baka. Sannan idan aka kuma ce za ayi tawo mu gama ne da hannu sunyi zarra. Dan haka kafin su gama nazarin waye Mehran, tuni ya haɗa gawarwakin mahayan kisan, ya zauna akan su irin zaman sadaukai. Ila mutum daya da ya bari a raye. Isowa gurin Rakshan yayi tare da marin mutumin yana tambayar shi. "Waye ya turo ku?" Dariya mutumin yayi sannan ya tofa mishi yawu me hade da jinin bakin shi. Wasa da takobin Sultan Mehran yake cikin shiru da nuna alamar lallai fa su tambayi mutumin. "Kai Solobiyo, dan daudu. Ko kai mata maza ne? Ai ashe baka da lafiyar maza, haka fa aka gaya min tsoron ka nunawa mata Jarumatar ka a gado kake ko?" Ya fashe da wata irin dariya sannan ya ja fasali yana huci. "Ko baka san muna da labarin cewa, kai lusari ne baka iya kome ba sai bin maza ta baya?" Bai d'ago kai ba, amma tabbas maganar tana dukar shi sama da harin da suka kawo mishi. Kallon shi yayi tare da dauke kan shi daga kallon shi. "Saura yan awani ka zama sarki ko? Toh tabbas saura awani ayi bikin mutuwar ka, na rantse sai sun shafe tarih.." Jifan shi yayi da takobi sai da duk suka razana, sabida yadda takobin ta raba kan shi gida biyu. Sai lokacin ake buza kansakalin yaki. Ko minti biyar ba ayi ba, dakarun masarautan suka musu kawanya, a fusace. A hankali ya mike tare da ratsa su, suna bashi hanyar,. Lokaci guda suna zuɓewa akan gwiwar su, hannun su dayansu akan kirjin su. Kan su a sunkuye. Haka ya wuce su bai ce kala ba..duk inda ya gifta dai dai ka ga zaratan maza suna zuɓewa a kasa ana jinjina mishi. A haka har ya isa fadar shi wanda yake cike da dattawa, tun kafin ya shiga cikin fadar an wanke shi da ruwan danyen madara. Wanda aka tatsota daga jikin saniyar, da dumin jikin saniyar, cak ya tsaya, basu fasa wanke shugaban su da madaran ba, sabida sunyi imani da cewa Sultan Mehran na daya haka ya tab'a faru dashi, yau gashi jikan dan shi ya maimaita, dan haka yana tsaye suka zuba Mishi ruwan zuma, ana wanke Mishi jikin shi. Tare da yin Imanin tabbas Allah ya kawo musu Sultan domin ya tsaya musu. Sannan koda zai kasance mara imani, tabbas gaba zai iya sadaukar da farin cikin shi domin Al'ummar shi baki daya. Kuma koda ya zasu fidda matar da zai aura a matsayin magajiyar sarauta wato (Empress) kenan, zata iya kasancewa sa'ada a gare su. Kuma zasu sami sukunin rayuwar su da walwalar su cikin tsarin Ubangiji. Bayansa ina zuba Mishi zumar sannan suka bishi da ruwa me kyau suka wanke shi tass, sannan suka yayyafa Mishi ruwan turaren miski. Tun kafin ya isa gurin zaman shi an shimfid'a mishi wata kilishi me shegen kyau da ɗaukar idanu. Kujeran shi kuwa an saka mata wata yadi me tsantsi ruwan gwal, cikin jarumta da dakakkiyar zuciya ya zauna a saman kujeran da yake nashi ne shi dayan shi, tare da da dunkule hannun shi na dama a k'ugun shi. Hannun shi na hagu akan gwiwar shi, cikakken Basarake ya fito sak. Mik'ewa duk manyan mutanen da suke fadar suka yi tare da cewa. "Mun bika munyi mubaya'a!" Shigowar Rakshan da Fudail rike da kan Yan tawayen da suka kawo mishi hari yasa kowa ya firgita. Wanda yayi dai dai da shigowar Sultanah Hoyam da sauri dan har labarin harin da aka kaiwa Mehran ta ya isa gare ta. "Sultan Mehran. Wannan kan mutumin zamu bincika muga daga inda ya fito, domin mun gano tutar kasar Carboda,Sultan idan muka yi bincike muka gano wanda yake da hannu." Dakatar da Rakshan yayi tare da mik'ewa ya bar fadar. Yana fita manyan fadan suka mik'e. "Sultanah Hoyam! Kowa yasan daga yankin Carboda kika fito meye kika sani akan wadannan maharan?" Wani irin kallo takewa Mir Rahil cike da mamaki da al'ajabi. "Kuna nufin nice zan farmaki Mehran?" Ta tambaye su cikin tsananin zafin rai, "Ko baki farmaki Mehran ba, alamu ya nuna da na jikin Mehran ake son cutar da shi. Dan taya aka san yana can keb'entaccen lambun shi?" Inji Mir Umdatuddawla, Ga baki daya suka hade mata kai, tare da niman laka mata sharrin ita ta farmaki D'anta domin an sanya ta, ta bashi mulkin da take kai. Kasa magana tayi sabida zuciyarta tayi wani irin nauyi tare da tashin hankali, bata san lokacin da ta juya ba, domin suna bukatar amsawarta ko ta tinzira tace wani abu, domin su daureta da harshenta, sai dai kuma tasan halin su. Ba iya su ba cikin gidan sarautar baki daya tasan abinda zatayi ta cimma nasara akan su, ta kuma san abinda zata yi ta lalata musu kome nasu shi yasa da ta Fahimci zasu sakata tayi magana shine ta bar fadar. Bata tsaya a ko'ina ba, sai gurin Mehran, tana shiga falon shi ta zube a kasa tana kuka tare da gaya mishi yau ita ake zargi da yunkurin kashe shi, wani irin kuka take tare da rantsuwa, kura mata ido yayi sannan ya tako har zuwa gabanta, d'agata yayi tare da saka kanta a gefen kirjin shi yana rarrashinta. "Wallahi Mehran kaji na rantse maka bani na turo su ba, Don Allah ka yarda dani" *Wallahi? Na rantse? Toh me Ammu take nufi? Don Allah? Toh waye ne Allah nan?* Shiru tayi sakamakon yadda yake buga bayanta, a hankali ya janye jikin shi, fuskar shi cike da tambayoyin Waye Allah? Sai dai yadda yake din nan bai da cikakken lokacin da zai yi tambayar waye Allah? Dan haka ya juya tare da niman komawa gurin zaman shi yana wasa da tuffa. "Mehran! Don Allah kace wani abu mana?" Shiru yayi yayi tare da dauke kanshi akanta. "Mehran shekara ashirin da bakwai rabon da naji muryan ka?" Idanun shi ne suka yi jajjur, yana tambayar kanshi. *Wacece ta bukaci na rayu babu wani kusa dani? Kece? Dan haka yadda kika daura Ni haka zaki hakura dani! Babu shakka kin cutar dani Ammu!* Ya faɗa dan shi kanshi ba zai ce ga ranar da yayi magana tun ranar da ta dauko shi ta kawo shi cikin gidan, yana kuka da ihu ba dai zauna ba, har ta b'acewa ganin shi. Bata kuma dawowa gare shi ba, sai bayan shekara biyu, tazo ganin shi. Lokacin ya saba da kadaici. Baya son yanayi sai ko idan yana karb'an horon yaki. Lokacin da ta fara kawo mishi yan mata ba zai ce ga fuskar su ba, amma tabbas ya fahimci abinda take nufi a lokacin. "Mehran don Allah ka bar azabtar da ni, da shirunka wallahi ba zan iya jure wannan yanayin ba. Nasan nayi kuskuren tafiya na Barka amma wallahi ban yi dan kai na ba, sai dan kai. Mehran masarautan nan cike yake da tashin hankali, dole na keb'ance ka domin ka samu horo na musamman. Mehran wannan lokacin da ban dauke ka ba, haka zaka zama sarki babu wani girmamawa, babu shakkar ka a idanun su, Mehran ni!" "Ki je kawai" A birkice ta d'ago kanta tana kallon shi wani irin kuka ne ya kwace mata, da sauri ta je ta zube a gaban shi tana kuka tare da cewa. "Mehran nice kayiwa magana, Allahu Akbar Allahu Akbar Ubangiji nagode maka, Mehran nagode, Mehran!" Dakatar da ita yayi tare da kallon hanyar kofar, tashi tayi hawaye na zuba mata. Tana fita ya bi bayan ta da ido, yana jin zafin da zuciyar shi take, amma bai saka yaji digon tausayinta ko soyayyar ta, asali zuciyarshi ta bushe ne. Kwanciya yayi a dogon kujeran tare da lumshe idanun shi, yana kad'a kafar shi tare da zurfaffa tunanin shi. *Waye Allah?* *Toh a ina yake?* Wadannan sune tambayoyin da yakewa kanshi. *** Gezira Sudan. Huci yake tare da sheke wuyarta. "Zaki gaya min ina kuka kai min Ikram?" "Noman! Saketa zata fada abinda dole ta?" Inji Mahaifin shi, Dariya ta saka tare da kallon su. "Ai ta tafi kenan har abada, kuma nayi imani ba zata dawo ba, kaga wannan shine dalilin da yasa na kore su. Idan da zata san waye ita? Shima mahaifin su yasan wacece Zaituna matar da ya aura uwar Yaran shi, sai ya mutu sau dubu bayan dubu, dan haka nayi haka ne domin kome ya lalacewa Ikram. Akan me zan zauna da yarinya da Taurarenta yafi na kowa, kai ma idan ka shiga rayuwar ta, tabbas zaka iya zama makaho domin kuwa a tsakanin zuciyar mu akwai abinda muke kokarin dannewa domin biyar bukatar kan mu" Dauko itace yayi tare da dauje yar banza, yana ji kamar ya kashe a ya huta. "Noman! Na maka izini ka shiga duniya niman ta, idan ka same ta, ga wannan takardan ka nufi kasar Istanbul ka zauna a can da ita, kuyi auren ku, karka yarda ka dawo nan sai da jikokina. Akwai Abokina a can me suna hizran karka manta ka rike shi da amana, Insha Allah zaku rayu cikin salama." Gyada kan shi yayi tare da barin gurin, ya nufi gidan su ya shiga hada kayan shi, da zai yi tafiyar dashi. Shigowa abokin shi na yaranta yayi me suna Sarwat, ya daki kafadar shi yana faɗin. "Mara mutunci, kasan duk duk garin nan bani da kowa sai kai shine bari ka tafi ka bar ni, don Allah ka tafi dani." "Toh amma!" "Don Allah ka tafi dani!" "Shi kenan, amma ban san ta inda take ba" Gyada mishi kai yayi sannan yace mishi. " Sai mu nime ta mana." Haka suka hada kayan Noman, sannan suka nufi gidan su Sarwat suka hada kayan shi kasancewar shi daya ne a gidan kuma Maraya ne bai da kowa, shi yasa Noman ya amince su tafi tare ko babu kome zai su ji dadin tafiyar tunda sun san juna. Guzuri suka diba me yawa, da ruwa wanda zai taimaka musu sabida tafiyar da zasu yi a yankin sahara idan sun tsallaka teku. Da haka suka yi sallama da kowa na garin tare da niman albarkan iyayen shi. (Saduwar Alkhairi) ** Oman Washi gari. Sanyin asuba ce ta tashe ni daga barcin da nake, a hankali na zuba mishi ido, babba ne babu laifi. Amma kuma Ni duk haushinsa nake ji, a hankali na janye jikina daga gare shi tare da nufar ban daki nayi wanka, sabida jiya ma haka ya gama jagwalgwala ni, sannan ya samu barci. ...ina fitowa yana tashi shima. Dauke kai nayi tare da saka kayana nayi kokarin gabatar da sallar asuba. Ina idarwa yana tadda na shi sallah. Ina zaune a gurin nayi shiru, ina kewar Airan ne, kewarta nake sosai a raina. Dan haka ina kallon ya idar da sallah ya matso kusa dani, sannan yace min. "Don Allah Karki cire abin fuskar ki, ki barshi haka kinji" Janye idanun na nayi akan shi tare da kallon kofar dakin shi. Shima zubawa kofar yayi ido, sannan ya mike ya rike hannuna. "Don Allah Karki yi abinda zai kusanta ki da wasu mazan, kinji bana son na.." "Rasani kawai kasa a ranka zaka rasani ne, domin kuwa ina ji a jikina Jarumina yana nan tafe." Damke hannuna yayi sannan yace min. "Na rantse da Allah, duk wanda ya Kuskura ya bibiyeki zan kashe shi." Kuyi hakuri...... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: https://www.wattpad.com/1034332478?utm_source=android&utm_medium=link&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=Mai_Dambu&wp_originator=ZG1SK2xVFREr7hRhBhywpRJFGcG%2FU04IT0c4iD2112GhzLOAlOkhgZul%2BFXxbRvW%2B5B65PK0%2FIBcXT7tIPL5xgrIrj4qJCiAhPQYYo%2F9B%2FvjAek8Z02xB3mvkJTKj6qe ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 Book 1 Mai_Dambu BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM Page 16... Wani irin kallon nake binshi da shi daga sama har kasa, kafin nace mishi. "Yana da kyau ka manta dani, ka kuma manta da abinda ya haɗa mu, domin kayi iya na kudinka sauran kuma ka ajiye zan amshe shi da hannuna." "Me yasa baki da tsoro da hangen nesa?" Kallon shi nayi a kai kaice, kafin na tabe baki na, sannan nayi gaba abuna, "Ba zaki tsaya muyi sallama ba?" "Iya wanda kayi da jikina bai isheka bane?" "Ya ishe ni kan, amma ba haka nake bukata ba" "Toh sai ka cinye ni, ko kuma ka boye ni sabida rashin adalci." Na fada ina bashi amsa a takaice. "Kina min kama da wata shashin rayuwata!" Ya fada dai dai na rike hannun kofar, "Wannan kuma matsalar ka ce, ba iya shashi ba ko rayuwar kace bai tikani da kasa ba, balle naji zafin jiki na." Ina bude kofar, muka yi idanu biyu da Nawwas, kura min ido yayi sannan ya dauke kanshi. "Barka dai mara dariya!" Na fada ina kallon shi. Tab'e baki nayi tare da matsawa zan wuce. "Meye sirrinki?" Cike da al'ajabi na kalle shi, murmushi nayi sannan na bar gurin ina tafiya cikin nutsuwa,nasan ba a haife ni cikin gidan Sarauta ba, amma kasancewata cikin gidan sarauta yana sani jin kamar an haife ni ne domin mulkin baki daya. Duk inda na wuce bina ake da mutuntawa,har na isa kofar da zata sadani kofar bayi. "Ke bakar fata? Ba a gaya miki cewa dake za a tafi daular Abbasid ba?" Kallonta nayi domin bani da amsar bata, yaushe aka shirya wannan tafiyar ba a sanar min ba, daki na shiga na sami su Inan suna ta shirya mana kayan mu. Dauke kai nai sakamakon yadda bayin suka zuba min ido, sabida kamshin turaren Abrad, matsowa Inam tayi sannan tace min. "Yar uwa jiki kin kwana a turakar Sultan ko?" Murmushi nayi mata sanan nace mata. "Eh!" "Don Allah ya jiyar dake dadin da." Kallonta nayi tare da kallon sauran bayi matan, "Sirrin mu ne, bana fatan na zama mara sirri." Daga haka Narga ta kawo min abin karyawa tana faɗin. "Ana son gobe da asuba mu isa SAMAIND Insha Allah, dan haka ki shirya cikin sauri" "Bai zai yiwu ba, idan gaggawa kuke toh kuyi tafiyar ku, ni ba a tilasani cin abinci ban shirya ba, kuma ba a sani cin abinci da zafi, kuma idan ya Huce dole a nimo min wani." Na fada cikin daurewar fuska, ina bude abincin. Sak kamshin abincin da naji a shashin Sultan Abrad da alamu abincin shi ne. --- Bin bayan ta yayi da ido, zuciyar shi kamar ta diro kasa, wani irin kishinta yake ji yana cika zuciyar shi, dan haka koda Sultan yayi mishi izinin shiga cikin dakin, ranshi a sose ya shiga, asalima wani irin kallo yake bin gadon da suka tashi daga barci, kasa kasa yake kallon dakin kafin ya maida idanun shi kan Sultan Abrad da abinda zai fada. "An gama shirya kome, ku a ke jira Ikram din ma." "Eh toh gaskiya dole a jira ta, dan naga bata gama shiryawa da wuri ba. Tunda bata fita da wuri ba!" Murmushin takaici Nawwas yayi tare da kallon shi, shima ya fice. ... Kutuful aka yi da tiren abincin gaba na, ban tab'a jin wulakantani da aka yi ba sai yau, kallon Azizatul Nissah nayi cikin al'ajabi, kai hannun ta tayi tare da kai min mari na rike da sauri, mik'ewa nayi domin ba zan yarda da duka ba. Cillar da hannunta nayi tare da kallonta, "Ba zan lamunci duka ba, sayata Abrad yayi ba yana nufin mallakata yayi ba, kika mare ni zaki ga abinda zai dame ki." Cikin fushi da b'acin rai ta kai min dukar da gaske, aikuwa nayi maza na make mata gefen cikinta sai da ta zube a kasa, ihun da tayi ne Dakarun da suke kula da lafiyar ta suka shigo. Zasu fita dani sai ga Abrad da Nawwas, sun shigo. Ganin Dakarun zasu tab'a ni ya dakatar dasu. Cikin kuka take gaya mishi abinda nayi mata, ba tare da ya tambaye ni ba, kallon kasar dakin yayi yace mata. "Waye yace ki zubda mata abincin ta? Sannan meye ya kawo ki shashin bayi? Bana son haka kar na kuma ganin ki a nan, sannan kiyi maza kishirya kayanki, domin dake zamu nadin sarautar Sultan Aamaan Abdus Samad Aamaan na biyu." Juyawa tayi tana kallona, na dauke kai na, tare da mik'ewa zan fita ya d'an buge hannuna. Juyawa nayi na kalle shi. "Ki shirya." "Zan tafi babu abinci ne a cikina." "Toh zasu baki!" Nawwas ya bani amsa a takaice, Tab'e baki nayi sannan nace mishi. "Na koshi ma" Daga haka na bar gurin baki ɗaya. * Askandariya Kallon waziriyarta tayi cikin sanyin jiki, tace mata. "Zaki wakilci masarautan nan zuwa birnin Samaind, ba zan sami zuwa bikin sarautar Aamaan na biyu ba." "Toh ranki shi dad'e, Ubangiji ya cika miki burinki na sarari da na boye, ya warkar dake ciwon da yake damunki na tsawon shekaru, Sultanah Amrah. Allah ya kara miki hakuri da dangana." Murmushi tayi sannan tace mata. "Amin Ya Allah, babu kome ya wuce zanen ƙaddarar mu ce a zane a gurin." Kwalla Waziriya ta goge cikin tausayin Sultanah yadda ta amshi kaddarar su hannu bibbiyu, bata tab'a kawowa wata rana zata saka ayi mata duba ko tsafi. Har yau tana saka ranta zata kuma niman damar. "Toh Yalqoot karki damu, Insha Allah Ubangiji yana ki yana gani zai kawo karshen kome." Cikin karfin hali tace. "Insha Allah." Ta faɗa tare da matse kwalla. .... Bayan barinta fadar Sultanah Amrah, a hankali ta isa gidanta ta shirya kayanta, sannan ta fito ta bar yankin baki daya. Dan su zasu iya isa bata yi magana ba. ** Garin SAMAIND ya cika makil da al'umma, maza da mata. Kowani kusurwa na yankin ya cika da al'ummar Annabi. Tun safe akewa garin tsinke dan haka suka zuba dakaru dubu dari bakwai a cikin garin..sannan daga wajen gari akwai dubu talatin da bakwai. Kasancewar an rigada ansan da zuwan baki Karku ga yadda aka tsara garin ya koma mafi girma da kyau, gashi yan kasuwan su suna baje kolin su. Wani irin cigaba aka samu na Kasuwanci a cikin birnin. Daga can katangar masarautar, wasu mutane ne tsaye, suna ta hidiman su. ..... Tun jiya ake raba kyauta tun daga masarautar har zuwa wajen masarautan, kyautar tufafi da abinci ake badawa, * Madinatul Mah. Wata karamar birni ce me dauke da mutane bazasu wuce dubu talatin ba,. kasancewar su musulmai kuma manoma. Sannan shugaban yankin me suna Hilali Bin Mahfuzur. Mutumin kirki ne, kuma yana dauke da adalci a cikin yankin shi. Kasungumin mayaki ne, wanda ya jima yana aiki da dakarun Samaind, kafin haka kore shi sabida ya nuna halin gaskiya da gaskiya. Wata matashiyar budurwa wacce ba zata wuce sa'ar Ikram ba, yake bawa horon yaki, cikin zafin nama da kwarewa yake kai mata sara. Amma yarinyar tana karewa. Fitowa tayi dauke da kwando, tana kallon su. Har yau bata cire burinta da tsammanin zama wata a cikin daular Abbasid ba, kallon yarta gudan jininta take, cikin tsananin kaunar ta tace. "Mahlika!" Da sauri yar ta juya tana kallon uwar, sannan ta kare sarar da mahaifinta ya kai mata. "Anne, kirana kike?" Murmushi tayi tare da kallon Hilali. "Mijina karka kai mata sarar, kyale sarauniyar GOBE!" Sake takobin yayi tare da cewa. "So nake tayi iyakan kokarinta, ta wanke miki zuciya a birnin Samaind." Wani murmushi tayi sannan ta zauna, tana kallon shi. "Idan kuma ta fadi ba?" "Zata yi nasara!" "Na fadi sabida cin amana, kana ganin yanzun ma zan kuma samun nasara?" "Idan kika yi aikin alkhairi zaki yi nasara, dole ki sami Hoyam!" Ya fada mata kai tsaye yana kallon ta, Girgiza kai tayi tana faɗin. "Hoyam! Ba zata yarda dani ba, zata iya kashe ni ma." "Kai Anne wanda yace zai kashe ki ai sai inda karfina ya kare." Ta faɗa tana kallon iyayenta. "Mahlika, karki damu da yarda Allah sai mun amfana dake." Wannan kenan. ** Tafiya ce da suka gajarce mana ta jirgin ruwa, akwai wata baiwar Azizatul Nissah, me suna maimana. Kallona tayi sannan tace min. "Sultan Abrad yana kiranki." "Kice ba zan zo ba" Na fada kai tsaye, Dafani Inam tai tana kallon yadda na hade fuska. "Don Allah tashi kije" "Dake nasanta da mugun tsoro mik'ewa nayi tare da bin bayan Maimana, Dake jirgin ruwan babba ne, ba na wasa ba. Ina Binta har wani babban falo. Yana tsaye da takobi guda biyu a hannun shi. Muna shiga ya wurga min daya. Kallon shi nayi ina kuma kallon takobin. "Zama a cikin Samaind sai da d'igon jarumta da kuma kirsa da kisisina, uwa uba makirci, kasuwancin da tafi karɓuwa kenan, dan haka dauka na fara koya miki yadda ake kare kai." A hankali na kalle shi sannan nace mishi. "Waye ya gaya maka ni abinda zai kai ni cikin masarautan kenan? Ko ce maka aka yi ni munafuka ce? Bana son damuwa." "Ki dauki takobin." Ya fada min haka cikin lalluma, ganin yadda ya kwantar da kai, ya sani dauka. Ina kallon shi, Jan takobin yayi tare da kirana, murmushi nayi sannan na juya takobin kafin nayi kanshi da sauri. Tare da bin shi zan sare shi. Buge takobin yayi tare da buge kafana da kafar shi. Faduwa nayi sosai. Durkusa yayi gaba na, tare da dafe goshin sa. "Kin san yadda na tsani faduwar ki nan! Sabida nasan gobe zaki amfana da wannan yanayi, tashi zaki sami wanda zai baki horon yaki Insha Allah. Akwai mutumina a cikin masarautan, ba zan gaya miki sunan shi ba, dan ba hankali ne dake ba." Haka ya cigaba da bani, horo har dare ya raba, muna abu daya sallah da abinci muke ci, mu cigaba da faffatawa, na gaji tilis faduwa nayi ina haki. "Toh tashi muje ki kwanta," gwalo idanu nayi tare da kallon shi fuskana a murtuke nace mishi. "Haila yazo min yanzun!" "Baki da kunya ce?" "Ai babu kunya a tsakanin ku, idan na barka abinda zaka min ko kunyar rayuwata ba zaka ji ba" Na mike ina barin falon, bin ta yake da wani irin kallo, tare da jin kamar da ruhinshi take tafiya, ** Karfe uku na asuba muka isa bakin gaɓar tekun SAMAIND, mun sami kome da kuma kowa, a hankali muka shiga sauka har inda suka tanada mana Dawakai da leken dawakan, sai sauran bayin irin su Inam da zasu shafo da kafa. Ni na shiga keken Abrad ne, tunda na shiga cikin keken zance na shiga uku, domin kamar tsohon mayye haka ya takura min, har Addu'a nake, Allah ya rabani da kazugumin mara mutunci nan. Karfe hudu saura muka isa gidan bakin da aka sauke mu, muna shiga kowa ya kama gaban shi, fitowa nayi sakamakon mantuwan da nayi, zan wuce naji an fisgo ni, tare da kai kanshi wuyana. "Baki san Yakana da kawaici nake miki bane? Ko baki ga zanen da take cikin kwayar idanuna bane? Baki Fahimci dalilin dauke kai ba bane? Kina azabtar dani, kuma wallahi zan iya lamunci na ga wani ya rab'e ki ba, idan kuwa haka ta faru. Wallahi sai na raba mutum da numfashin sa." "Toh sake ni, tun baka kashe kowa akai na ba, zaka kashe ni. Wai ku meye matsalar ku da rayuwata ce? Shi wancan ya gama abinda zata yi kai ma ka dasa daga inda ka tsaya, ba zan fasa gaya muku ba ina da wanda nake so! Ina da abokin Rayuwata." Daga haka na juya zan bar gurin, muka hadu da Azizatul Nissah. Kallon juna muka yi zunzurutun kishi na addabar ta, bata san lokacin da tace min. "Karya mara daraja!" "Babu damuwa, sirrina ne maza suyi yaki a kaina, martaba ta ce duniya ta bagwaza akai na, Alfahari na ne, zaratan maza su tsaya a bayana. Daukaka ce na zama kalabi tsakanin rawuna!" Na fada ina kallon ta, d'aga hannu tayi za.... #Mai_Dambu ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 Book 1 Mai_Dambu BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM Page 17... Marina zatayi Nawwas ya rike mata hannu. "Kana jin tana gaya min magana akan idanun ka?" Ta faɗa a fusace, "Meye a cikin shi? Gaskiya ta gaya miki, ita din kalabi ce a tsakanin rawuna, karki d'aga mata hankali, ki barta a zauna lafiya." "Akan wata banzan yar karamar kasa? Wacce take fatar..." "Wai meye haka?" Inji Abrad wanda ya fito, kafin Azizatul Nissah tai magana, Nawwas ya mishi magana tare da nuna mishi babu kome, riko hannuna Abrad yayi ya wuce dani. Wurga ni yayi saman shimfid'ar shi. "Meye kike bukata? Ba zaki nutsu ba ke kenan fada kamar wata kar.." "Abrad nice karya?" "Ba haka nake nufi ba!" "Lallai kuwa." Mik'ewa nayi da sauri zan fita ya riko hannuna, kwacewa nayi tare da fita daga dakin, zunzurutun raina ya b'aci sosai, ko kallon gabana bana yi. Ban tsaya ba, na nusa dajin dake cikin birnin, sai da nayi tafiya me nisa, sannan na fara jin maganar mutane kasa kasa. "Dole gobe na idda nufina, Sabida na rantse babu nada shi da zasu yi. Kuma nasan dole zai fito ran gadi cikin satin nan matukar ban kashe Mehran ba shege." Ji nayi an rufe min baƙi daga bayana, tare da juyar dani, kallon juna muka yi, cikin wani irin murya da zan iya rantse da Ubangiji da ya Halicce ni, ba mutum bane, ya saka min hannu a bakina, tare da kai kanshi kunnena, yana sauke wata irin numfashi, rike rigar shi nayi sakamakon jin da nayi kafaffuna basu iya daukata. "Karki yi ihu!" Wani irin abu naji ya daki zuciyata, lokaci guda naji ina kokuwa da numfashina, a hankali yake janye fuskar shi daga kunnena na, zuwa wuyar shi. Sai ga d'an kunne na ya rike rigar shi, wani irin numfashi naja tare da damke shi, a hankali ya d'ago hannun shi, kamar wanda ake koya mishi aikata kome ya kai kunne na, ya zare dan kunnen, sannan ya ya kalli fuskana da take rufe, da sauri wanda yake hade da sanyin dabi'a, ya janye a jikina, sannan ya rankwafa yana ƙoƙarin d'ago kai na, ina kauce wa, shafa bakina yayi da yatsar shi, yana kallon gurin mutanen, a hankali yakai hannun shi kan takobin shi, a tare muka kalli juna, hasken farin wata hade da reshen biya yayi mana iya ka da kallon kwayar idanun juna. Hancin shi ya goga akan nawa, wani irin abu muka ji kamar an watsa mana ruwa, ala tilas ya janye hancin shi, lokaci guda ya tab'a wuyana. Daga nan ba san kome ba, kuma ba zance na san yanayin fuskar shi da kome nashi ba, abu daya na sani shine muryan shi wacce take bugawa kwalkwalawa ta, da zuciya ta wani irin yanayi. A hankali na bude idanuna, akan Abrad, wanda ya damu sosai. Kallon su nayi naga nima kallona suke, tashi nayi zaune tare da cewa. "Nayi gamo ko?" Na tambaye su. "Bamu sani ba, amma mun ganki a kwance gefen ki kadan an kashe wasu mayakan kisa!" Zubur nayi ina kallon su. "Wallahi aljani ne, ban tab'a jin ko ganin irin shi ba, don Allah ku nimo min malam ruki'a su duba ni!" Zaro idanu suka yi, lokaci guda na birkice musu, kalmar *Karki yi ihu* yake yawo a kunne na, aikuwa ban san lokacin da na shiga zunduma musu ihu ba, ana tare tare dani, lallai sai sun yarda na gamu da aljani. Dakyar suka danne ni, aka yi ta min Addu'a, kafin na sami barci, me cike da mafarkai masu mugun ban tsoro. Tafiya nake a sahara, ruwana da guzurina ya kare. Har dare ya cimmani, a hankali nake tafiya hango wata alkarya nayi tana ci da wuta. Ga Abrad da Noman suna ƙoƙarin riko ni. Gefe guda kuma gawarwakin mutane nake tsallakawa, har na iso alkaryan. "Ikram!" Naji muryan Ammyna. Juyawa nayi tare da kallon su. Zuciyata suke da murna na fara isa gare su. Mika kofi tayi na amsa, amadadin ruwa jini na gani a cikin shi. "Ammyna!" "Rayuwar Duniya cike take da faffutikar ganin samu da rashi, wannan ruwan shan shi ba zai miki sauki ba, amma kuma zaman shi a cikin ki zai fi kome baki wahala. Idan da hali ki kashe wancan wutar da ta taso cikin wancan alkaryan." Juyawa nayi tare da kallon alkaryan, zan basu amsa suna b'ace min, hango wani mutum nayi a tsaye hannun shi goye a bayan shi, yana gaban wata kujeran mulki, wanda take zubda jinin da yake gangarawa ta wani gurin yana isa alkaryan wutana na kara kama cikin alkaryan. Da sauri na ajiye kofin na shiga ƙoƙarin tona rami, ina jin kukan mutane da dabbobi kamar suna kiran. "Ikrammmmmm!" Wani irin rudewa nayi, sakamakon jin kiran da nake, gashi ina ƙoƙarin toshe hanyar tafiyar jinin nan. Sai rike hannuna aka yi tare da d'agani cak, ina ganin mutumin nan ya juya abin shi, daukata aka yi da kofin ruwan jinin nan aka kawo ni bakin alkaryan aka ajiye ni. "Ikram!" Juyawa nayi ina kallon su. "Kizo mu koma nahiyar mu!" "Ikram ina kaunarki, kizo mu koma daulata." "Ikram!" "Ikram! "Ikram! "Ikram!" Haka suka yita kiran suna na, suna biyo ni duk na birkice sakamakon yadda suke zubda jini, sake kofin hannuna nayi tare da fasa ihun da ta saka. Na farka a tazame jikina yana rawa, haka Abrad ya rungume ni, wani irin kuka nake tare da cewa. "Na haɗa ka da Allah ka mai dani gida, wallahi ba zan iya zama a nan ba mutuwa zanyi." Kifa kaina yayi a kirjin shi, tare da shafa bayana. "Kiyi hakuri, zaki min aikin shekara daya ce, da izinin Ubangiji zan dawo daukarki kinji , ki taimakawa Kanwata don Allah." A hankali yake shafa bayana, tare da lallashina, har na sami nutsuwa, sannan na kalle shi. "Ina jin yunwa kuma banyi sallah ba " Da kanshi ya kai ni ban daki tare da cewa. "Dama kina sallah kika hana ni sukuni dake a cikin jirgin ruwa ranar?" Share shi nayi, sannan nayi uzurina na fito, ina idarwa naci abinci tare da sallah sannan na koma na kwanta, sabida bazan iya fita koda nan da kofar gidan ba. Ina ji ina gani suka fita suka barni. Har da bayi. ** Masu shirya sarakunan masarautan na musamman aka kawo, domin shirya garnakaki. Ana shirya shi ana kuma kara fitar mishi da haibar shi. Wani irin kyau da kwarjini ya kuma sosai, musamman da suka saka mishi wani kambun azurfa, a saman rawanin shi. Wanda ya kuma fidda shi na musamman. A hankali suka sunkuya tare da daure mishi zaren takalmin shi, sannan suka nufi hanyar fita bayan sun gama. Zama yayi tare da kallon Rakshan da yake murmushi. Shigowar Fudail yayi cikin hanzari, tare da karasawa kusa da Sultan ya gaishe shi sannan yace mishi. "Sultan Mehran! An kawo hari dajin da yake wajen masarautan amma an dakile faruwar haka, bayan an musu kisar gilla, Sultan abin mamaki mutanen nan ba a san daga inda suke zuwa ba, sannan akwai masaniyar za a kai hari gurin maka wankar sarauta." Watsa hannun shi yayi tare da mik'ewa, ya nufi kofar fita, yana tare idanun shi yana yawo cikin al'ummar castly din shi. Sai zuɓewa duke tare da kwasar gaisuwa, shashin mahaifiyar shi ya nufa, har ya isa cikin gidan tana tsaye ana shirya ta, yana shiga duk masu aikin suka fito, Mika mishi hannu tayi wanda yake cike da gwala-gwalai, ya sumbata. "Allah ya tayaka riko Mehran!" Murmushi yayi sannan ya juya zai zauna ta rike hannun shi, suka fito daga cikin ɗakin, a hankali take takawa yana gefen ta, Khabir da Fudail da Darakshan,suna bin bayan su. Dakarun kimanin dubu biyu suka bin bayan su, koda suka isa farfajiyar masarautan, kimanin dakaru sama da dubu dari shida suka kewaye su. A hankali ya isa inda keken dokin da zata kai shi filin da za a bashi mulkin yake, yana shiga Darakshan da Fudail, suka hau dokin su, Fudail a gefen dama, Rakshan a gefen hagu. Ga jerin gwanon dakaru, masu iya sarrafa takobi, suna baya, masu aiki da kibbau suna gaba, masu iya sarrafa Gatari suka tsakiya, sannan masu sarrafa nashi suna tsaka tsakiya, nasu amfani da majajjawa suna karshe. Sannan suna tafiya tare da kiran "Mehran" Tafiyar da bazata wuce minti goma kacal ba, sai gashi ta kwashe minti talatin da wani abu, kafin suka isa gurin, sannan a saman katangar gurin akwai da karu sama da dari hudu suna jiran kota kwana. Wannan shirin duk na kare lafiyar Sultan Mehran ne. .sarakunar larabawa da wasu sakarunnan wasu alkaryoyin duk sun halarta, zaune suke ana gabatar da kome, bayan Rakshan ya sami babban limamin kasar ya kora mishi jawabin waye Mehran, shiru yayi sannan ya cigaba da gabatar da abinda yake gaban su. ** Kwalin kwal kamar mayya suna barni a gidan, dan haka ina tashi na nufi ban daki nayi wanka, sannan na fito na shirya cikin wata riga da wando kayan maza ne, sai yar mayafin da na rufe fuskana, kallon shigar nayi cikin tunanin kar na fita na janyowa kai na fitina, sai na sauya tare da barin fuskana a yadda aka samun wannan bakin abun na fito. Na sami dakarun suna gadina, dole nayi musu bayani, sannan na nufi inda na je jiya. A hankali nake tafiya ina raba idanuna, har na isa gurin da naga yasha ambaliyar jinin, sai karnin jini yake tashi, kasa jurewa nayi na fara amai, tare da wani irin jiri. Faduwa nayi a gurin, ina jin gurin na juya min, a hankali idanuna suka rufe, ban kuma farkawa ba, sai bayan wasu lokuta kafin na farka a cikin wata yar bukka. "Sannun!" Tashi nayi zaune tsoho ne tukuf, me yalwacce da farin gashi. "Ayya baba,.yaushe nazo nan" Murmushi yayi sannan yace min. "Idan na canka dai-dai, sarauniya bilqisul Ikram nake magana da ita ko?" Tankwashe kafaffuna nayi, tare da kallon shi. "Ko kai ma aljani nine?" Murmushi yayi sannan yace min. "Ko daya! Ni bawan Allah ne kamar ke, saba'in ke kina rayuwa ce a kasan wasu ni kuma ina rayuwa ce a karkashin mulkin Ubangiji na." "Eh toh ba zan ce ba, kuma ba zan iya zartawa ba, amma ba makawa wata dalilin ya sanya nake nan a zaune ko?" Cikin murmushi yace. "Ita dabi'a koya ake, al'ada mutane ke samar da ita, halayyarka kuwa halitta ce a jikin ka, manuniya kadai ke isar da sakon zuciyar mutum" "Ban fahimci Hikimar ka ba?" "Zamowa ko zartawa daga ahalin babban gida yake samuwa, sai dai ina kuka da kukan da zaki yi! Ina tausayin tausayawa da zaki yi, dole haka zata faru domin zanen ƙaddara bata karya kuma bata shiga gamin gambiza." Kallon shi nake cikin mamaki wallahi duk na kasa Fahimtar abinda yake nufi. "Alkarya tana ci da wuta! Zakwakurai suna huci da sunanki! Duniyar ta cika da gawarwaki, ƙishirwa a cikin zafin sahara! Duk baki Fahimci hikimar Ubangiji ba. Toh shikenan. Ga wannan sarewar ko koyi bisa shi wata rana zaki nemi idan halin haka ya samu." "Baba! Baka gaya min sunan ka ba!" Juyawa yayi ya kalle ni, sannan yace min. "Uwaisul Qarni!" Kallon shi nayi sannan nace mishi. "Sunan mutumin da Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama yace Sayyiduna Umar idan yana nan lokacin da uwaisul Qarni zai bayyana toh yayi kokarin rokon shi akan ya roka mishi Allah ya gafarta mishi. Lallai Baba sunan ka me daraja ne, dukda ban san kome akan ka ba, sai dai zanyi fatan Alkhairi a rayuwar ka. Nagode." Daga haka na mike zan tafi, yace min. "Bilqisul Ikram! Baki dauki sarewar ba, karki manta jiya ba gamo bane, aiki zakiyi da zuciyarki da karfin ki, ki ajiye batun Soyayya, kiyi aikin da duniya zata yi alfahari dake. Kuma karki zauna jiran sai an koya miki kare kanki, kiyi hakuri da inda zaki zauna da koyarwa. Dabi'arki bata karamin kofa bace, muna da masu ilimin duniya suna ganinki zasu iya fahimtar da magautar Daular nan a rufe tarihinki..... *Kun dai ji! Abinda yace! Gashi tayi gamo! Ga Chakwakiyya sai kara habaka yaƙe! Ga mafarkin da tayi! Ga wasu zantuntuka da Tsoho Uwaisul Qarni yayi! Karku manta duk yadda ka tafi a labarin zaka dawo domin karnin baya aka koma! Like kwarkwarah 💝💞😹🤣🤭* *ABIKRAM* *NOKRAM* *NAWKRAM* *MALAM GAMO baka da team* Littafin na kuɗi ne!. #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: https://www.wattpad.com/1034823697?utm_source=android&utm_medium=link&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=Mai_Dambu&wp_originator=MsMwT9n73chbpIbB7ZAzir6cYIsdC0zoLvn6XiQp94WiQ2YNqavnWKJP6fWtpJwKQ1bQOgzPnEIGILQaW8foUCMbMUkPgQHUkffR474WwVSFVgpsHqKpB8v5o%2BYVwY2O ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 Book 1 Mai_Dambu BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM *Toh ni dai ban san me zance muku ba! Musamman Yan team din Abrad 😹! Noman Anwarulkharim da Nawwas basu da team ko? Toh wanca kurman fa! Gaisuwa ta ga Yan team din Kalabi tsakanin Rawuna Wato Bilqisul Ikram💝💞* Murmushi nayi sannan na juya ga tsoho Uwaisul Qarni, kallon shi nayi sannan cikin nutsuwa na koma bakin inda na zauna, sannan na dauki sarewar. "Na gode sosai baba!" Murmushi yayi sannan yace min. "Karki damu da yau, goben ki zaki duba, shine kafin ya iso miki zaki fahimci girman ƙaddara da soyayya, asa'ilin zaki Fahimci soyayya ba kome bane matukar zaka sadaukar da rayuwarka domin mutanen da suke jin ƙishirwa domin ka. Ba mamaki Mahaifiyarki tasaka miki Bilqisul Ikram ce dan kanta ba mamaki kuma ta saka miki ne kawai dan soyayyar sunan ko kuma ɗan kasancewar gobenki tayi kyau." Murmushi nayi ina kallon shi domin zantuntukarka shi bai wani dame ni ba, amma kuma ina kan auna shi. Kafin nace mishi. "Baba zan tafi!" "Toh Sultanah Bilqisul Ikram!" Kallon shi nayi tare da cewa. "Baba Sultanah kuma? Ina Ni ina wannan matsayin sai jinin sarauta" Na fada ina murmushi, kallon tausayi tare da jinjina yayi min, sannan ya ce min. "Allah ya ƙaddara saduwar mu." Murmushi nayi sannan nace mishi. "Amin Ya Allah!" "Karki manta ki rike ibada da Addu'a domin itace makamin mumini, kuma bata tab'a shaida mutumin kirki sai da Ibadar shi. Addu'o'in kuma su tamkar Sulken yaƙi ce, duk yadda makiya suka kawo miki hari matukar Allah ya amsa miki addu'ar, babu abinda ya isa ya miki. Sai dai su kare da makircin su. Karki sake tsanani ya sa ki manta Allah, ki tuna dashi ki rike shi a ranki yana sane dake, gwabzawar ba karama bace, kasadar babba ce, zanen ƙaddara kenan, a haife ka a cikin mutane ka mutu a cikin dokar daji, karki sake wani ya sauya miki alkibla yin hakan zai iya targada miki nakasunki. Ikram ki tsaya akan kanki karki tsaya akan ra'ayin kowa." Daga haka ya nuna min hanya, yana biye dani, amma kuma bakin shi bai fasa kiran Allah ba, har ya fidda ni bakin hanyar da zata kai ni masaukin mu. Yana min addu'ar dacewa. ** Wato a cikin birnin Samaind kuwa, an rantsar da kurma injin yan majalisan shi. Lokacin da aka bashi damar yayi magana, a hankali ya tako gaban amsa kuwar, yana kallon miliyoyin al'ummar da suka kasance jama'ar shi. Kallon su yake tare da jin kuncin rashin abokin hira da raba damuwar juna. mahaifiyar shi bata bashi damar zama da kowa ba, su kansu mutanen da suke kewaye da shi kawai an basu damar kula dashi ne. Bawai su shaku dashi ba, rasa abun da zai ce yayi yana kallon su, suna kallon shi. Toh me zai ce musu? Bai san abinda zai iya fada ba, kawai tsintar kanshi yayi da sake musu murmushin jin dadi. Daga haka ya sauka daga inda zai yi maganar. Dariya Abrad yayi tare da cewa Nawwas. "Kaga lusaranci, maganar ma ya kasa sai dai mabiyan shi suyi, a haka zan dauki kanwata me daraja na bashi ita. Wani abun zai mun isa liyafar dare." Shi kuwa Nawwas wani irin haushin Abrad yake ji, musamman da yasan yadda yake kaunar Ikram, wani irin kallo yayiwa Abrad. "Ba lusaranci bane, mulki ne yayi mishi yawa, Sultan Aamaan bai da lusaranci, ko kafin muzo shekaran jiya an kai mishi hari, shi.daya yaji da tawagar mutanen da suke yakar dakaru dari da yan kai..a kira shi lusari? Allah ya nuna mana lokacin da zai nuna bajintar shi." Daga fadin haka ya mike domin an bawa Sultan Mehran mulkin tare da saka mishi wata alkyaba, daga nan aka mika mishi takobin da suka gada tun daga kan tub daga Abbasid. Ga baki daya ya gaji an hana shi sukuni, dakyar yake d'aga kafarshi, har aka gama taron lafiya. Sannan suka fito. Haka kawai ya juya tare kallon Fudail da Darakshan. Cikin sauri suka saka shi tsakiyar su. Tafiya bata yi nisa ba. Kawai sai ji suka yi an sake ruwan kibbau. Take garkuwan yaki suka kare su, nan aka shiga guje guje, domin ceton rayuwar al'umma. Sake sakewa suka yi aka samu aka tura Sultanah Hoyam cikin keken doki, wasu dakaru kimananin dari biyar suka kewaye ta, tare da barin gurin da ita, A hankali ya zare takobin yana janta a kasa, bai cire kome na shi ba. Takobin kawai yake ja a kasa, tare da d'aga hannun shi yana kallon dakarun shi. "Ku ajiye makaman ku, ku barni na kare kujerar mulkina" Yadda yayi maganar cikin wani ɗan karen murya me mugun dadin sauraro, yasa duk suka dare. Zunzurutun mugunta da mugun hali yake ji yau a ranshi sama da koda yau she. Kallon Rakshan yayi dan maganar da yayi yanzun ya sashi jin gajiya tsakanin wuyar shi da kai shi. Kallon dakarun yayi. "Dakarun Samaind su koma can, maharan kuma, Sultan yace idan kuka yi nasarar kwarzanin shi yayi alƙawarin zai zube a gaban jama'a ku sare kanshi." " Kai lusari, munyi alkawarin koda zaka shafe wasun mu, sai mun share tarihinka da izinin Ubangiji, dan haka a gwabzawa kawo." Da sun san waye yake tsaye a gaban su, ba zasu yi kokarin cimma shi da karfi da yaji ba, amma ina basu da hankali, sun makance da son lallai sai an shafe shi. Wato yadda suka tawo da mugun gudu, suna ihu. Bai saka ya d'ago kai ba, balle yayi musu shirin kota kwana ba, suna isowa dab dashi suka mishi wani irin zobe, yadda zasu dargargaji dan banza.(Masu karatu kuyi hakuri domin gaskiya wannan labarin yazo da sabon tsari, babu domin akwai abubuwan da dole sai na tafi dashi domin labarin ya tafi min yadda nake so. Dan haka ba wancan labarin da za'ayi soyayya bane a tashi labari ne me matukar bukatar fahimtar bai ɗaya) Yadda suka mishi rumfar nan, haka bawan Allah nan yayi ta girbe halittun Allah cikin kwarewa da zafin nama,.kafin minti talatin da biyar, ya tara gawarwakin su ya jibge su. Sannan ya koma ya haura saman su..ya. Zauna tare da suka takobin shi a jikin su..yayi irin zaman sarakuna masu shegen izza da takama. Take Al'ummar kasar shi suka fara ihu tare da murnan sun sami mai ceton su. Ya jima yana zaune a gurin tare da su Fudail. Yana jiran daga ina sauran zasu fito. Ganin babu kowa yasa shi sauka akan su, ya wuce gaban dokin shi da ya dace ya fita ayi rangadi tunda anyi nadin sarautan, sai dai babu inda za shi domin yana bukatar nutsuwa da ruwan zafi. Bai cika son magana ba, amma daga lokacin da aka tabbatar zai zama sarki yake cikin duhun damuwa, kowani dan banza nima yake lallai sai ya kashe shi. Koda suka nufi cikin gidan sarautar, hankalin Sultanah Hoyam bai kwanta ba, sai da ta ganshi, sannan tayiwa Allah godiya. Zata addabe shi da magana yayi wucewar shi abin shi dan baya son hayaniya. --- Kallon Juna suke shida Nawwas, cike da al'ajabi. Kafin yace mishi. "Na yarda da lokaci ne zai tabbatar da lusaranci da Jarumta, yau naga wani irin yanayin da ban tab'a gani ba, Nawwas kalli yadda yake musu kisar gilla, kamar bai tab'a jin tausayi ba a rayuwar shi?" Yar karamar dariya Nawwas yayi sannan yace. "Har na tausayawa ranar da zai fahimci yaudaran shi ake, kaga yadda ya tinkari mutanen hamsin babu shamaki babu kome, kuma ya girbe su cikin ruwan sanyi." Gyada kai Sultan Abrad yake tare da jinjina al'amarin a ranshi. ** Lokacin da na dawo har zuwa lokacin basu dawo ba, kwanciya naso yi amma na Fahimci lokacin sallah azzahar yayi tashi nayi tare da alola nazo na gabatar da sallah ina idarwa na kwanta. Tuni barci ya dauke ni. Ban tashi ba sai da la'asar, ina tashi na same su duk sun dawo, tashi nayi tare da gabatar da sallar la'asar, ina idarwa ya shigo min dakin. "Ina kika je? Dakarun sun gaya min kin fita?" Banza nayi dashi tare da Cigaba da cin abincina ina kallon ruwan gaba na. Dauke abincin yayi tare da gaya min bakar magana. Mik'ewa nayi cikin zuciya nace mishi. "Da kasaye ni nace zan zauna da kai dan dole ne? Aikin da zan maka ko ance maka ban san yafi sayata da kayi hatsari ba, idan da biyar bukatar ka ce ka..." Marina yayi tare da rike gashin kaina, "Abrad sake ni! Ka rabu dani,!" Da gaske wai ranshi ya ba'ci dan haka ya kwashe min kafa, ya shiga zane ni, ban yi kuka ba. Amma tabbas na hasala. Inda nayi ta gaya mishi magana masu zafi, abinda ya janyo hankula mutanen gidan kenan, har Nawwas yazo ya amshi bulalar hannun shi. "Nawwas taya zan saye ta, tana min abinda ya gadama, Ni sa'an tane? Da zata na min rashin kunya?" "Nayi maka rashin kunyar ni Baiwarka ce da zaka mai dani kamar Matarka, ina son ahalina aka raba ni dasu. Kanwata fyade maka mata, domin jinyar ta na yarda a sayar dani, ta sami lafiya kasan abinda na gani? Akan. Idanuna mahaifina ya koma ga Allah, akan idanuna naga gawarwakin mutane babu iya a jirgin ruwa. Sai kace na lankwasa kai na nayi maka da'a bayan kai ma ba d'aga kafa kake ba. Zunzurutun son kai da rashin adalci.dauko ni kayi domin biyan bashin Kanwar ka, ka tab'a sanin yadda rabuwa da d'an uwa yake da zafi? Kanwata barin ta nayi cikin jini bata ko takawa. Amma dake ka kai kaloluwar rashin adalci kana gaya min ina da taurin kai. Toh gaya min, tun daga ranar da mahaifina ya auri matar shi muka fara halin rayuwa, sai me dan zuciyata ta kangare, wallahi babu wanda ya isa ya gaya min magana na kyale shi kowa shi koda kuwa zan bar duniyar ce baki daya." Daga haka na juya zan bar dakin ya dawo dani. Fincike hannuna nayi tare da fita daga gidan baki daya. Can dajin bayan gidan na nufa, ji nayi an riko hannuna a hankali na juya, Nawwas ne. Kwace hannuna nayi tare da dauke kai na daga gare shi sabida ina jin zafin abinda Abrad yayi min. #Mai_Dambu... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: https://www.wattpad.com/1035082730?utm_source=android&utm_medium=link&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=Mai_Dambu&wp_originator=yUmz6Z0cBGRcg47Bgvv2ZD%2FSnDgR%2BVPsyMIvVrjo9GUw8D7lOFwC63elHnxRFmQIkdBL0Bia2oMxA%2BBjsxRPkdkT3Kn32SHlitYTOtxqCvX28M64v01jxsXY8xxzoCbs 🐾ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜🐾 Book 1 Mai_Dambu BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM Page 19. "Me yasa baki da hakuri ne? Me yasa kike nuna taurin kanki da yawa ne?" A fusace na kwace hannuna ina kallon shi, "Kana da d'an uwan?" Lashe bakin shi yayi yana kallona, gyada min kai yayi sannan yace min. "Koma dai" "Kasan ciwon da yake cikin rabuwa da d'an uwan ka? Kasan yadda nake ji akan kanwata? Ban ki na sami duniya da abin cikin ta toh wallahi zan sadaukar mata koda kuwa abinda nafi so yana cikin sa dan haka ka kyale ni!" Zuba mata ido, yayi tare da kallon yadda take fada, tayi Mishi wani irin zarra da kwarjini. Ji yaƙe kamar ya janyo ta jikin shi, amma yadda ta tsuke fusakarta yasa shi jin ina bai isa ba, wani kaya sai amale. Haka yayi ta bata hakuri ta hakura, zama suka suna hira, wanda duk rabi labarin masoyinta Noman ne, Da zata fahimci yadda ya tsani Sunan Noman da bata cika shi da bashi labarin jarumtar shi. Ji yaƙe kamar yayi ta kwarara ihu. Har ta fahimci itace kawar Zuciyar shi. Bamu bar gurin ba sai magarib, muna fitowa muka nufi cikin gidan, Abrad yana tsaye. Ko kallon shi banyi ba. Ina sallah na fito zan koma gurin Bayi yan uwana. Suna zaune su uku a falon, gani na zan wuce ya kasa hakuri. "Karki yarda ki!" Juyawa nayi tare da matsowa kusa da shi. "Sake nanata abinda ka fada?" Na tambaye shi, "Nace karki yarda ki fita" Dafe goshina nayi sannan nace. "Wallahi nasan gamo nayi, zan cigaba da addu'a kawai!" Na juya na koma dakin na kwanta, tuni barci yayi gaba dani har aka kawo abiinci ina barci, can naji ana lallube ni, bude idanuna nayi ina kallon Abrad, a raina nace. *Ni kam na shiga uku! Wannan mutumin bai da aiki sai ta Iskanci* Akan fuskana kuwa tsuke fuskar nayi domin na nuna mishi ni ba haka bace, da zai dake ni kuma ya biyo dare ya lallube ni. Sauka nayi daga gadon tare da zabga mishi harara, sannan na koma saman kilishin da yake kishingida na kwanta. Duk yadda Abrad yaso ya rage dare dani naki, karshe ma da ya ishe ni tashi nayi na nufi ban daki tare da yin tsarki da alola nazo na fara sallah, Tun yana daukar sallah wasa nake har ya gaji ya kwanta, ban tashi a gurin ba sai da sanyin asuba ya ratsa ni, sannan na gabatar da sallar asuba, na koma na kwanta,.ina kwanciya yana hayewa ruwan ciki na. Kirjina da basu da wadataccen girma ya shiga murza, sosai yake murzani tare da daura min nauyin jarabar shi, dauke kai nayi dan abinda nasani bana son abun babu amfanin na cigaba da biye Mishi haka ya gama ko alamar motsi banyi ba, domin nayi alqawarin duk abinda zai min wallahi ba zan motsa ba. Abinda ya bashi mamaki kenan, ya sauka kai na, a raina nace. *Allah ya raka taki gona* Haushi ya kama shi..haka ya juya min baya, yana jin har lokacin da barci ya dauke ni, ban kuma bin ta kanshi ba, * Kwance yake cikin ruwan zafi tun kusan yamma da ya shiga dakin wankar bai fito ba, yana kwance cikin ruwan zafi. Wato dakin wankar shi kamar za ace wata irin dutse ne aka faffe cikin shi, sannan aka tara mishi wani irin kasa a karkashin dutsen , a duk lokacin da zai yi wankar akan zo a kunna wuta a jikin ƙasar, ita zata samar da zafin da zai yi wanka dashi. Idan ruwan yayi yadda ake bukata sai a kashe wutar, TOH wannan zafin da dutsen ya dauka shi zai taimaka mishi har ya gama da zafi ko awa nawa zai yi a cikin ruwan kuwa. Kallon halittar shi na d'a namiji yayi, rabon shi da yayi motsi tun ranar da ya rabu da makauniyar nan, tun jiya yake fahimtar tana bukatar mahadinta, sake narkewa yayi cikin damuwa. Kafin ya bude idanun shi. Yana juya kafar shi cikin ruwan, wasa da gashin kirjin shi yayi sai lokacin ya kalli tafin hannun shi. Wanda suka yi jajjur, ya mike daga kwanciyar da yayi yana kallon yadda gurin yayi. Yana wanke ciwon yana kallon yadda Hajiyar shi take zillo. Kamar tana niman hanyar arcewa. Murmushi yayi sannan ya shafa kanta, tare da matseta a tsakanin cinyar shi ya cigaba da abinda yake yi. Yana gamawa ya mike zai fita. Idanun shi ne ya dauka akan wani abun shi. Kallon abun yayi yana kuma tare da fatan sake, share tunanin yayi tare da ficewa daga ban dakin. Yana fitowa ya zauna tare da kallon kayan shi da aka zab'a mishi. Bai saka ba haka ya cigaba da kula da ciwon shi. Shigowar Fudail da wata kyakyawan budurwa ya sashi d'aga kai yana kallon su. "Sultan Mehran! indelah inji Sultanah Hoyam wai tazo." Dauke kai yayi tare da kallon inda man shafawan shi yake, wanda ake haɗawa tun daga kasar roma ake kawo mishi tun yana yaro. Fita Fudail yayi tare da bar musu d'akin. Takowa tayi gaban shi ta rasa me zata yi, bai ce mata kome ba. Amma kuma bai yi na'am da ita ba, asalima baya son ta tab'a shi ne. Yana lura itama tsoron shi take. Haka suka dauki lokaci suna wannan yanayin kafin, ya mike da kanshi ya dauki man ya shafa a jikin shi. Tana tsaye, kuma abinda ya hanata yin wani abu yadda ya tamke fuskar shi yasata jikin mugun shakkar shi. Yana gamawa ya dauki kayan shi a hankali yake saka kome na shi. Zaka sha mamakin idan kaga yana yin abu da kanshi wanda kuma zunzurutun zafin nama zai iya dukar kartin maza talatin bai gaji ba, amma hidimar rayuwar shi kuma sai ya shafe awa biyu yana Abu daya. Tun garin da haske har garin ya fara duhu. Sannan ya kammala. Ajiyar zuciya ya sauke tare da juyawa ya duba gadon shi, fita yayi bayan ya kalleta da wutsiyar idanun shi. Yaga bata ko motsin Arziki. Tunda ya fito, ya kalli Fudail tare da mishi alamar ya fito mishi da wancan abinda ya kai mishi dakin. Da sauri ya shiga cikin dakin ya fito da ita, bai yi wata wata ba. Yasa a zane ta kuma ba a inda Sultan zai ji ihunta ba. Dan yana bukatar nutsuwa da hutu. Bayan fitar shi can ya dawo tare da cewa. "Sultan Mehran naga bata yi kome ba, sai yanzun ne take gyaran dakin." Lumshe shanyayyun idanun shi yayi tare da kara shigewa jikin kujeran kamar wani zuma, shigowar Rakshan da wasu bayi dauke da katon tire na abinci. Tunda suka shigo aka shiga jerawa, domin abincin ma daga gurin Sultanah Hoyam yaƙe. Bayan ya gama shiryawa da wasu bayi guda biyu, sune suka shirya na Sultan Mehran, sanan suka koma gefe tare da cewa Rakshan sun kammala. Shi kuma ya gayawa Mehran, anan ma sai da ya b'ata lokaci kafin ya mike kamar ba zai tafi ba, kuma yunwar ce take addabar shi. Koda ya zauna a hankali ya shiga juya abincin. Kallon Rakshan yayi sannan ya kalli matan guda biyu, kafin ya d'age hannun shi akan abincin bayan ya saka cokalin azurfa a cikin tasar abincin. Can zuwa wani lokaci ya zare, haka yayi ta duba abincin. Aka'idar azurfa ko guba mutum yaci ana sakawa a cikin abinci ko bakin shi zai nuna alama ta hanyar dafe jikin cokalin. A hankali ya shiga cin abincin bai wani ci sosai ba. Dan ma gasheshen nama yaci da Madara, sannan ya mike daga gurin, idan yana tafiya langwai langwai, duk da yana da jiki da kira me kyau ba zai hana ka hango lalacin shi ƙarara ba. Takobi ya dukka tare da nufar cikin ɗakin horo, ya shiga bawa kanshi horo, yana da yi yana nazarin wasu abubuwan, yana gamawa ya fito. Hannun shi harde a kirjin shi, kafin yace musu. "Taswirar kasar nan!" Da sauri suka fita, ya cigaba da zaga dakin yana nazarin abinda ya faru. Bayan kamar minti goma sai gasu da taswirar suka zuba a gaban shi. "Ai Sultan Mehran Allah yaso mu da mun sha wuyar niman shi." "Allah! Waye shi?" Kallon juna suka yi Rakshan da Fudail. Duk sai sukayi tsuru tsuru. Tab'e baki yayi sannan ya shiga zagaye makeken tabirin da suka shigo dashi aka baza tasweran. Murmushi yayi sannan ya shiga duba iyakokin kasar shi. A hankali ya nuna wasu iyaka guda biyu, ta b'angaren gabas, take Fudail yayi zane a saman gurin. Ya nuna yammacin kasar ma, da kusancin kasar sai arewacin kasar. "Nawa ake amsar harajin?" Gyara zama suka yi sannan Rakshan yace. "Muna amsar haraji mafi girma daga fataken da suke shigowa kasar nan da kimanin kashi sha biyar cikin dari. Yan kasuwa suna bada kashi talatin cikin dari. Idan aka hada ya tashi arba'in da biyar." "Dame masarautan ta dogara?" Ya kuma tambayar shi, kasancewar shi mara ilimin addini, haka bai hana shi fahimtar rayuwar shi ba, kuma ya fahimci girman nauyin da aka daura shi akan shi. "Masarautan ta dogara da hanyoyin uku. Tana fitar da zinari! Tana fitar da rakumai tare da sarrafa karafuna zuwa kasashen duniya." Shiru yayi sannan ya kuma kallon su. "55% yana shigowa ta wannan hanyar kenan?" Ta watsa musu tambaya. "Eh SULTAN Mehran!" "Ina kuke kai kuɗin?" Ya tambaya tare da wasa da takobin shi, "Baitul Mali! Tare da ajiyewa ana!" Daga hakan ya juya tare da mai da hankalin shi kan taswirar, rike wuyar shi yayi kafin ya isa gurin ya fara magana dan yasan cewa dole zai magantu. "A cikin ku waye ya iya Rubutu da karatu?" "Ni ne Sultan! Inji Fudail." "Toh!" A hankali ya zauna akan wani kujeran hutu, ya shiga musu bayani da sauya hanyoyin saman da kudi na cikin masarautan, tare da gaya musu abinda yake bukata, dokoki yake sakawa tare da kafa mugayen sharadodi. Yana yi yana tsotsar bakin shi. A cikin shi aka saka dokar hana raba wasu manyan mutanen fadar, tare da sauke su wa'adin su bai yi ba. Sai dokar daukar sabin dakarun sojin. Tare da watsa wasu zuwa iyakokin kasar. Aka kawo maganin bayi, suma aka ce ganimar fada ce, kar a taba su. A kaiwa Ammun shi itace zata yi kome akan su. Take aka shigar da kome zuwa fadar shi. Kwanciya yayi jikin shi yana ciwo, juyi yake. A yanzun kan yana bukatar abokiyar rayuwa, yana bukatar macen da zata ɗebe mishi kewa, gyara kwanciyar shi yayi yana kara jinjina qarfin hakurin shi akan mace bayan yasan daɗin su. A tsarin shi yana don duk abinda zai taba ko zai ci yana son yaci gaba rabon shi na kanshi. Tsotsar bakin shi yake tare da jin tsigar jikin shi yana tashi. Lumshe idanun shi yayi, tare da jin wani yanayin da bai isa ya fassara ba. Dan yana kyauttata zaton mafarki yaƙe. A hankali yake jin halittar jikinsa ta mike sambal, sai tsirta da yawan jaraba take, rabon shi ya faɗa wannan yanayin tun lokacin da ya daina hulda da mata, asalima kyamar abin yake ji, amma idan bai yi karya ba, akwai wani dalilin da yasa shi fadawa wannan yanayin. Baya fatan haka ya zama hujja akan shi. Sai da yayi rub da ciki kafin ya samu atenal din shi ta bar harbo sabis. Dakyar wata irin barci me cike da mafarkin ban takaici, domin kafin gari ya waye ya juya bakin mai tas a jikin shi, kamar zai fasa ihu, dan koda ya shiga ban daki, ganin gaban wandon shi yayi jagwab, haka ya cire tare da sakawa a cikin ruwan wankan sai da yayi wanke wandon cike da matsanancin kunya, kafin yayi nashi wankar tare da jin ba dad'i. ** Karfe goma aka yi liyyafar da baayi ba jiya, bayan nan Abrad ya gabatar da bayin shi tare da nuna musu yan matan, matasa dasu. Har zuwa lokacin idnun shi suna kasa bai d'ago ta dube su ba. Rakshan da Fudail ne suka fitar da Bayin, sannan aka nufi shashin Sultanah dasu. Anan Abrad yayi musu sallama sabida dayawan sarakuna zasu bar kasar, haduwa suka yi da Wazeeriyar Sultanah Amrah. Suka gaisa kafin ta gabatar mishi da Yarta. Me suna Banafsha. Cikin shigar alfarma, kallon juna suka yi sannan yace mata. "Har yanzun babu labarin Almirah Joindah! Duk yadda Sariyah taso Allah ya bayyana ta haka bai samu ba, har ta rasu bata ga Mahaifiyar ta ba. Gaskiya abin da ciwo, mace daga haihuwa ace an nemi ta an rasa?" "Eh wallahi, har yanzu babu labarinta sai dai ai ko zuwa yanzun kasan ta mutu!" "Ba za a rasa sauran irinta ba, Insha Allah zata bayyana." Ya faɗa tare da wuce su. Kallon shi tayi ranta na b'aci, taya duk abinda yake faruwa yake mata mayafi da cikawa muradinta. Duk shekarun da ta diba tana bautawa Sultanah Amrah, ace tana ji tana gani sai dai tayi ta zama a Wazeeriyar Sultanah. Ba zai yiwu ba, dole ta dakile kome domin idan ta kuskura aka samo sauran irin Sultanah Amrah har abada burin ta na yarta ta zama Sultanah a cikin masarautan Askandariya ba zai sami dama ba..... Lalaci more⚔️🐾 Labarina na kuɗi ne! Dan haka saura Pages 21 na kammala FREE BOOK one 🙏🏼✊🏽🧗🤣 Alqur'an idan na sauko daga katanga 🤨😂 zaku ji a jikin ku.... #Mai_Dambu..... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 Book 1 Mai_Dambu BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM Page 20... "Matukar ina raye Babu wanda ya dace da Askandariya sai Banafsha." Ta faɗa a sanyayye. --- Muna shiga cikin gidan, aka wuce damu ban daki. Wanka muka yi tare da tsayawa a layi, saka mu aka yi muka zare mayafin da muka rufe jikin mu, sannan aka shiga duba mu sama da kasa. Tare da bincike jikin mu. Wato zunzurutun binciken har da bakin mu aka duba, ana ware mu. A hankali layin yazo kai na. D'ago kai nayi na kalli matar. Bayan ta duba kasa na. Gyada kai tayi sannan ta bude bakina tana kallon bakina zuwa daso rina, farcen hannuna ta kalla. Tare da kallon cikin idanuna. Siririn yatsar kafana da dunduniya ta, gyada kai tayi sannan ta koma gefe tana magana da yar uwarta, zani suka bamu muka daura. Sannan suka bawa kowa shedan shi da zai tsaya akan aikin shi. Ni kuma suka kalle ni tare da cewa. "Gaskiya ba zaki zauna a cikin mu ba, sai dai zamu kai ki gurin Sultanah Hoyam ta ganki." Gyada kai nayi sannan suka saka mu a gaba har zuwa shashin Sultanah, tunda muka doshi shsshin kamshi yake dukar mu, har muka shiga dakin. Muka tsaya kan mu a sunkuye, A hankali suke gabatar mata da mu, tare da kiran sunan mu. Yadda suka bata bayani akai na, ga kuma ciwon da yake fuskana sai yace musu. "Ku kaita haramtacciyar Fada, domin bana son Yarona na ga fuskarta mara kyan nan hankalin shi ya tashi. Jiya an kai mishi Husna ya korota, sabida baya yi abinda ya dace ba. Yau ku gaya musu su san abinda ya dace, idan yana wanka toh ku tuntube shi ko yana bukatar taimakonku gurin cude mishi bayan shi, idan kuma ya fito toh a kula da inda ya saka fuskar shi da idanun shi. Bana son ya kuma korafin ba a kula dashi ba." Tana gama fadar haka ta nuna mana kofa, muka fita. Duk sauran an nuna musu inda zasu yi aiki nice dai aka kai ni haramtacciyar Fada, a hankali na shiga cikin gidan. Babu kome sai tarkacen tsohon sarki, dan haka ina shiga suka kalle tare da tambayar ta. "Daga ina kike? Meye ya kawo ki nan?" Kallon shigar jikina nayi sannan nace musu. "Daga wancan gidan nake aka ce nazo nan nayi muku yan aikace aikace." "Toh bakar fata! Mun muna me konannen fuska, an tab'a gaya miki idanun ki sak yake da ya maje, Shairah fitar min da ita tsoro take bani!" Inji wata budurwa a cikin gidan, kallo daya nayi mata, na dauke kai, dan har gaba ta tsaya. Murmushi kawai nayi, zata kuma takawa na saka mata kafa, duk basu lura ba. Haka ta hantsila ta fadi. Mik'ewa tayi cikin fusata. Ta kawo min duka, na kauce ta daki iska. Sake kai min duka tayi, nayi maza na bata guri ta fadi, cikin jin haushi da takaici, ta kuma juyawa zata kai min duka na saka mata kafa, ta fad'i. Har sai da ta fasa hancinta. "Ni kika fasawa hanci?" Cikinin fushi ta dauki kwanon cin abinci na tangaran, ta kwada min na kauce tare da dukar hannun nata, sai da suka zube a kasa na koma gurin da nake tsaye na tsaya, sake mik'ewa tayi taja wuka tawo kai na. "Ya isa haka! Ke mafadaciya daga ina kike?" Sai lokacin na d'ago kai ina kallon matar da take fitowar, wacce mulki da izza suka taru akan fuskarta, kwayar idanun ta kuwa cike yake da fusata. Kwarjini tayi min, dan dole na sunkuyar da kaina. Tana isowa gabana, ta d'aga kai na tayi tare da kallon kwayar idanu. "Meye sunanki?" "Ikram!" "Hm! Me suka turo ki kiyi a cikin wannan gidan?" "Sun bukaci nayi aiki kawai!" Na bata amsa a takaice, "Yayi kyau! Shine kika aika abu mafi kuskure?" "Bana jure cikin mutunci bane" "Kenan idan aka tab'a ki zaki fusata?" Sake sunkuyar da kai nayi, sannan nace mata. "Eh toh ya danganta da irin tab'a ni da zaki yi!" Kallon wasu mata tayi sannan tace mata. "Ku nuna mata abinda ya dace Narjis" Gyada kai tayi sannan ta nuna min hanya. Muna barin gurin tayi murmushi. "Me ka Fahimta?" "Fusataciya ce!" Gyda kai tayi sannan tace mishi. "Baka fahimci abinda ka gani ba, amma dole ta zama iya tawa ce." Jinjina kai yayi sannan ya kuma shiru. ** Tunda suka yi faɗa yake jin babu dad'i, sai da ta kai barci Barawo yake ɗaukar shi, wani masifaffen kewar Ikram yake cika mishi zuciya. A hankali ya fito daga cikin jirgin ruwan, anan ya sami Nawwas a tsaye. "Kai ma kana cikin yanayin damuwa ko?" Juyawa Nawwas yayi tare da dauke kan shi yana kallon taurarin da suke sararin samaniya kafin yace. "Me zai sanya ni shiga damuwa?" Jingina yayi da jikin wani gwafa, sannan ya kurawa Nawwas ido, tare da sauke ajiyar zuciya yana lashe bakin shi cikin wani irin yanayi na daban. "Ina kaunar Ikram! Toh amma ka amince ta tafi a baiwa?" "A'a karka dauki haka a matsayin son kai!" "Nima ban ce kana da son kai ba, amma duk abinda kake kauna baka mishi rikon sakainar kashi!" Dan lasar bakin shi yayi tare da kallon ruwan. "Ban sadaukar da ita ba, dan son zuciya ta ba, sai dai haka da nayi zai sama min zaman lafiya da al'umma ta." Gabaki daya Nawwas ya gundura da surutun shi, ko yace soki burutsin shi, dan haka ya ki amsa mishi, asalima share shi yayi daga maganar baki daya, domin ya tsani renin hankali. Haka yayi ta gaya mishi yadda yake jin babu dadi rabuwa da Ikram, shi kuwa Nawwas ji yaƙe kamar ya rufe shi da duka, cikin mugun takaici ya juya tare da barin gurin, ya mishi sallama saboda barci da yake ji, kuma ba kome ya saka shi jin barcin ba sai sututun Sultan Abrad, Tunda ya shiga cikin dakin, ya kwanta ringingine, abubuwan da suka gabata ya shiga dawo mishi, tun daga ranar da ya daukota har zuwa lokacin da ya shiga cikin dakin Abrad yaga yadda gadon kwanciyar su, ya hautsine ranar Dakyar yayi barci, dan ranshi yayi mugun b'aci sosai.ga kishin da ya cika mishi zuciya. ... ~~~ Tunda na fahimci gidan da nake na shiga hankalina, domin sau dayawa ina fuskatar cin fuska da tozarci, daga masu kirana da me idanun mage, sai masu zagina da bakar fata. A hankali na fahimci larabawa suna da mugun kyamar bakin fata, domin ido da ido. Suke guduna, abu daya ya kwance ni shine ina daka yan banza. Sauri nake zan tafi gidan da nake aiki, yan matan bayi biyar suka tsare min hanya. "Ke me idanun mage mummunan dake mara fasali, kaskantacciyar baiwa. Sai munci ubanki." Kura musu ido nayi, sannan na dauke kai na zan wuce. Suka kuma dawo dani gaban su. Kallon su nayi sosai ina kara tuna ta yadda zanci Ubansu a tsanake. Hango mu da fadawar masarautar suka yi, take suka kore mu, na wuce gaba abuna, Ashe yan iska suna biye dani, har nayi nisa, suka sake tare ni, kasancewar gurin babu mutane, nad'e hannun rigana nayi, tare da falfalawa da mugun gudu, aukuwa jakuna suka biyo ni, a wani bayan lambu muka tsaya, nayi tsalle na karyo itaccen bishiya. Na fara gyarawa, tare da kallon su, dariya suka saka tare da nuna ni. "Ke bakar fata! Kina nufin Mu zaki daka da bulalar hannunki?" Murmushin Mugunta nayi musu, sannan na wullar da bulalar ina me durkusawa ina basu hakuri. Yan iska, sai ga shi suna dariya, zasu dake ni, Kamar yadda suke tsammanin zasu min, sai labarin ya sha banban, domin kuwa Hango Sultan Mehran suka yi da gudu suka bar gurin, tun kafin ya iso mutanen shi sun taso min, tare da korana kar na bari ya ganni. Barin gurin nayi ', dan sun nuna zasu iya dukana.... ~~~ khartum. Babban birnin Sudan, kallon Juna suka yi shida Sarwat. Ba kome yasa suka kalli Juna ba, sai.yadda suka ga ana sayar da mutane, d'ago kan da Noman zai yi ya hango wani mutum,. yana ƙoƙarin gudu, da gudu yabi bayan shi, tare da niman kama shi. Karshe dai garin gudu suka fada cikin ruwa, aikuwa Noman ya shake shi. "Me yasa kake gudu? Meye nufinka!" "Ko zaka zaga duniyar nan da niman Ikram ba zaka tab'a samun ta ba, domin tayi maka nisan da bazaka iya cimmata ba," Inji Mutumin, Sake shi Noman yayi cikin tashin hankali da kaduwa, kurawa juna ido suka yi. Idanun shi ya cika da kwalla, a hankali ya shiga fitowa daga cikin ruwan, tausayin shi Mutumin yaji, yace mishi. "Me yasa ba zaka bincike ni da karfin tsiya ba?" Cak Noman yayi tare da juyawa yace. "Akan me zan maka da karfi sai ka gaya min? A'a Allah yana sane da abinda kai min, dan haka wallahi babu kome." Ya juya zai fita, abin shi cikin wani irin yanayi mutumin yace mishi. "Ban san inda take ba, amma da alamu tana yankin larabawa ne!" "Nagode sosai!" Daga haka ya bar cikin ruwan, ya koma inda yaga ana cinikin bayin, inda shima ya nemi a saye su, dakyar aka sami mutanen da suka saye su. Sannan suka bar Gabbar tekun Sudan. ~~~ SAMAIND Wata uku A hankali nake ganin yadda ake koyar da Jasrah, ita ke koyawa nice nake dauka. A hankali suke daura mata litattafai akanta, sai sun gama shirya mata zai zube, Kallona Matar da nake mata kallon Mahaifiyar Jasrah tayi. A hankali ta yafato ni, na isa gabanta, "Shairah ka gwada shiryawa Ikram mu gani!" Babu musu ya shiga daura min littafan akai na, tare da kallona yace min. "Zaki saka hannunki a k'ugun ki, sannan d'ayan hannun ki cigaba da juyawa,tafiyar a sanyayye ake yinta, babu amfanin zafin nama." Lumshe idanuna nayi sannan na kalle shi, muka Cigaba da tafiya, suna kallona. Wasa wasa matar nan tayi bala'in janyo ni jikinta, tare da sakawa ana koya min, dab'iar masarautan, tare da nuna min wasu abubuwan da ya fara bani tsoro. Domin sai da ta fahimci abinda Abrad ya saka min fuskana, ta saka aka cire min, sannan ta nuna min rufe fuskar kawai ya wadattar, ~~~ A hankali ya farka daga barci, kallon wasu kyawawan yan mata yayi, tare da dauke kan shi. Gyara kwanciyar shi yayi, tare da lumshe idanun shi, idan yana kaunar ganin yan matan nan ya mutu a kwance, ya tsani ganinsu. Amma Ammuh ta dage mishi lallai sai ya mu'amalantu dasu. "Sultan Mehran! Ruwan wankan ka yana." Tab'a wani abu yayi a jikin gadon shi, sai Darakshan ya shigo har cikin ɗakin,kallon shi Mehran yayi tare da juya mishi baya, kad'a keyar yan mata yayi, suna fita ya mike zaune. Tashi yayi tare da nufar ban dakin, shiga wanka yayi ya jima yana fama da mulki a cikin ruwan, kafin ya fito. Ya shirya cikin kayan sarauta, sannan ya nufi shashin Sultanah, tun da ya shiga ya sami yan mata suna rawa a gabanta sanye da wasu kaya masu kama da tsirara, zama yayi tare da sunkuyar da kanshi kasa, murmushi tayi sannan tace mishi. "Barka da safiya, Mehran!" Bai tanka mata ba, sai ma kara sunkuyar da kan shi da yayi, zuba mishi abin karyawa tai sannan ta zuba mishi ido. "Mehran! Dama akan gwamnonin nahiyar nan nake son ko zaka dakatar da su,ka kwaso wasu." Bai kulata ba, amma kuma bai fasa cin abincin ba, shiru tayi kafin ta cigaba da mishi bayanin yadda zai tafi da mulkin shi. Cikin mugunta da zalinci, kar yaji tausayin kowa, ya hukunta duk wanda yake da hannun a kawo mishi harin bazata. Yana gamawa ya mike tare da goge hannun shi, zai fita yace mata. "Hmm!" Sannan ya fita, jimawa kadan Fudail ya shigo, tare da ce mata. "Sultanah Hoyam, Sultan Mehran yace kar a kuma tura mishi yan mata castle din shi, idan ba haka ba zai sanya mu sare kan su." "Amma akan me zai..?" "Umarnin da ya bamu kenan idan muka kuma ganin wata mace." *Allah ka jikan Iyayena😭😭😭😔🤲🏽* Book dina kudi ne #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 Book 1 Mai_Dambu BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM Page 21. Sake baki tayi tana kallon shi, kafin ta tattaro sauran kuzarinta tace mishi. "Akan wani dalili zai ce haka?" "Baya da ra'ayin mata ne, idan kika cigaba da turo su zasu mutum ne, dan haka ayi hakuri da turo su." Daga haka ya fita, shi kuwa Mehran yana fada, an kawo karshen binciken harin da aka kawo mishi lokacin da ake bikin bashi sarauta, wata uku da suka wuce. Kallon Magatakardan masarautan yayi, sannan ya cigaba da kallon hanyar waje. Ba kome yaja haka ba, sai yan mata guda shida da aka turo su, suyi rawa. Tunda suka shigo ya dauke kan shi, tare da kallon Darakshan. Dakatar da yan matan yayi tare da koran su. Ana ƙoƙarin gabatar da wanda suka kai mishi hari, kawai sai gani aka yi fadar ta cika da hayaki. Kafin kace kwabo an kwace takardan da aka kawo na bincike. Murmushi yayi sannan ya mike zai bar fadan, ya saka Darakshan ya nimo mishi mutanen da suka yi binciken. A sirrance bayan sun fita daga fadar. Cigaba da tafiya, yayin da abubuwan al'ajabi suka shiga faruwa, a kowani ɓangare na masarautun larabawa, musamman akan yaki da cinikin bayi. A cikin wata na shida da zuwa masarautar na sami horon zama daya daga cikin amirorin masarautan, musamman yadda Sultanah Fazilatul nisa take nuna min ni din kamar lu'ulu'u ce me daraja, dan haka kar nayi wasa da damata. Duk wannan Kawata min duniyata da take min sam baya burge ni, kawai gida nake son komawa. Na gaya mata kai na, a sunkuye. "Zaki koma gida, amma kafin nan so nake ki shiga cikin wancan gidan,idan kika shiga toh kin gama min kome, zaki iya tafiya gida." Gyada mata kai nayi, sannan wani abun da basu sani ba.tun da aka kawo ni, ba zan ce waye ba. Amma da zaran karfe goma sha biyu yayi na dare,za a tashe ni. Daga nan zan fita. Ban san waye ba, dai amma koya min yaki yake na fitan hankalin. Bai tab'a min magana ba, amma yana bani horo na fitan hankalin. Horon da yake bani irin horon da ake bawa maza ne, domin idan muka gama da takobi, horon dambe yake koya min. Karfe uku nayi zai juya yayi tafiyar shi,nima kuma na koma bangaren mu na bayi, dan haka na sami horo ta kowani fanni, Matsalata guda daya ce shine tsangwama ta da suke da baka, takai ko wanka muka shiga niman hanyar tozartani suke, dan haka na sami Sultanah da maganar abinda ake min. "Toh karki damu, zaki bar cikin su ma." Gyada mata kai nayi sannan na bar gurin na cigaba da abinda nake, ina halkance da abinda Jasrah take min, ban tab'a jin haushin ta ba, sai ma dauke kan da nake mata. Bayan na bar dakin mahaifiyarta, shiga tayi cikin damuwa tace mata. "Amih! Me yasa sai Ikram." Mika mata hannu tayi sannan ta karasa jikinta, tana faɗin. "Naka sai naka, dadin zama sai bare, barta tayi miki aikin da Bazaki iya ba, sauran kuma ki karasa. Akwai abin da na gani a tare da ita idan ta gama miki aikin zata bar miki sauran." Murmushi tayi sannan ta cigaba da gaya mata irin taimakawa da Ikram take mata. Dan haka karta d'aga hankalin ta. ~~~ Wato akwai abinda ake kira ƙaddara, idan Allah yaso haka sai ya faru bata tare da kowa ya fahimci haka ba. Sau dayawa mutane sukan iya shirya kome dan cikar Muradin su, amma sai kaga Allah ya shirya nashi tsarin sama da nasu. Haka ce ta faru, Sultan Mehran zai fita rangadi, dan haka suka shirya Dawakai kusan dubu goma tare da mahayan su, daga can gefe keken dokin shi ce me dauke da wasu irin Dawakai masu shegen kyau..farare kal kai, masu gashi har kafar su kamar an saka musu, dawakan manyan ne daga yankin turawa aka kawo mishi. Ana ƙoƙarin saka keken tsakiyar mutanen na, Dawakai suka fara ihu da bori, lokacin Ni na fito zan wuce haramtacciyar fada. Shi kuma yana ƙoƙarin shiga cikin keken, na hango wata irin maciciya, tana kokarin karasowa inda kafar shi take,abinda ya saka sauran dawakan ihu tare da gwara juna, Saura kiris ta sare shi, ban san lokacin da na iso tare da fisgo shi ya fado kai na ba. Haka muka zube kasa, dawakan suka. Shiga gudu. Kallona yake ido cikin ido, zuciyar shi tana wani irin bugawa har ina jin haka a kirjina, hannun shi dukka biyu suna kan dukiyar shanuna, a hankali na zare hannun shi, tare da ture shi na mike da gudu domin har zuwa lokacin Dawakai basu bada daman da mutanen shi zasu iso gare shi ba, da gudu nayi ta shiga tsakanin dawakan na bar gurin, bin gurin yayi da ido, yana jin wani abu yana mishi yawo a kwantar shi, kamar wanda aka saka mishi wani abu. Lumshe idanun shi yayi tare da cigaba da kwanciyar a gurin, dakyar Darakshan ya iso inda yake, suka mishi kawanya. Tashi yayi zaune tare da cusa hannun shi cikin tsakiyar kirjin shi, yana kuma jin sautin bugun zuciyar shi, tare da fitar numfashinta a kan fuskar shi. Mik'ewa yayi a sanyayye kamar wanda kai ya fashe mishi a cikin shi, tunda ya shiga cikin gidan ya kwanta bai ce musu cikanku ba, bai kuma ce ga abinda zasu mishi ba. Amma idanun shi a rufe suke. Jikin shi kuwa a mace take. Ba zai iya bada labarin abinda ya faru ba, amma tabbas yana da yakinin akwai abinda yake bibiyar shi, musamman lokacin da yaji ta ambaci wata kalma ya kasa fahimtar Meye haka yake nufi, *Ya Rabbi* Me ye haka? Sake shiga cikin damuwa yayi tare da kara shigewa jikin kilishin da aka shimfid'a mishi a falon yayi. --- Tunda na samu na bar gurin da gudu,.nake jin zuciyata tana wani irin bugawa, tsoro da firgici suka taro min a guri guda, fuskar shi tana cikin Sulken yaƙi, wato hular baka ganin kome sai hancin shi da yar bakin shi ruwan hoda. Ƙwayar idanun shi har wani ratsi_ratsi yake na alamar ja, "amma ai ba a kai na ya fadi ba, toh taya aka yi na ya juya kasa Ni kuma na koma saman shi,alamar nice na fadi akan shi?" Sake shiga rudani nayi sanin da nayi dai nice na taimaka mishi amma taya? damsshin da naji a wuyana ya sani shafa gurin, "jini?" Na fada da karfi ina me tsalle gefe guda, toh ta ina jinin yazo. Duba jiki na, na fara ina mamaki. Kafin kace me na sake shiga rudani. ..kai karshe da na Fahimci cutar da kai na nake sai, na manta da batun na nufi gurin aiki na, amma maganar gaskiya na wuni a ranar suku suku, ba dan kome ba, sai dan yawan jin sautin bugun zuciyar shi a dodon kunne na. Tunda na shiga cikin gidan suka fahimci, akwai abinda yake damu na, amma zunzurutun zurfin ciki na, babu wanda ya isa ya san me suka kyale ni, ina gama share musu ko ina na juya zan fito, Mamar Jasrah tace min. "Yau zamu yi darasi akan Budurwan Masarauta, amma manta kawai, zaki gane anan gaba" Nasan tana son koyar dani, amma Ni ban ga dalilin haka ba. Yadda take warware min sirrin cikin gidan sarautar ya bani tsoro da Mamaki, dan haka zunzurutun tsoron da yake cikin labarin ya sani ji kamar zan mutu na dawo, sai da muka kusan wuni tana bani labarin yadda aka kafa daular da yadda kowa yake kokarin sai ya kafa haramtacciyar ra'ayin shi a cikin daular. .... Sai bayan magarib na baro gidan, na gaji sosai. Dake ban tab'a fita cikin dare ba, ban san yadda masarautan yake ba, ashe suna sake wani katon kare me sufar kura, shafa gefen cikina nai,.tare da dauko sarewa na. Sam na sha'afa na saka a bakina kenan naji gurnannin abu a bayana. Da sauri na juya tare da kallon shi, haushi yayi min. Naja da baya, ya kuma min haushi naja da baya. Cikin wani irin zafin nama, muka kasa a guje, bina yake ina kaucewa yana bina ina kaucewa, sai da ya kusan kamo Ni na kwace. Yankar wata yar lungu nayi, kawai sai ji nayi kamar an d'ago ni sama,turus karen yayi, nima zunzurutun tashin hankali ban fahimci me ya faru ba, sai da na bude idanuna na kalle ni a tare da wani mutum,dake akwai duhu bana hango kome saboda fuskar shi tana lullube cikin duhu, nima nawa fuskar tana lullube. Hannun shi a k'uguna, a hankali ya hade jikin mu, wanda ya haifar mana da bugun zuciya lokaci guda, yana rungume ni ya sakewa karen nan, wani abu, wanda yasa karen faduwa, zunzurutun rashin mutunci sake ki yayi daga saman yayi tafiyar shi, haka na fado kusa da karen da ya suma, na tsallake zan wuce. Juyawa nayi tare da d'aga kai na. Shima yana tsaye amma bai juya bayan shi ba, tafiyar shi ma yake kokarin yi. A hankali na juya tare da barin gurin, da sauri na nufi shshin mu, tunda na shiga na Fahimci akwai sabin bayin da muka samu. Ban kula kowa ba kai na a sunkuyar zan wuce. Shan gabana aka yi, sake ratsa gefen ta nayi ta kuma shan gabana, daga can gefe ina hango Narmin tana kallon mu, kai hannun tayi.zata cire min mayafin fuskana, nayi maza na dake hannunta. "Mahlika karki tab'a ta, ki rabu da ita" "Narmin ba zan iya ba, duke min hannu tayi, bakar fata tana da izza har haka." Ta tako har gabana, tare da kai hancinta zata min isgilanci, sai kuma ta shako kamshin turaren da taji shi, bayan shigarta Falon Sultanah Hoyam, har take tambayar Narmin ko zata sato mata turaren Sultanah nan ne, dan kamshi yayi mata. Kwaɓe ta Narmin tayi tare da gaya mata wannan turaren SULTAN Mehran ne, ta kuskura tayi hauka sare kan ta zai yi. Dan haka ta shiga hankalin ta, amma kuma kamshin Turaren ya zauna cikin kwakwalwar ta, wanda ya haifar mata da daukacin kaunar shi. Kallona tayi kirjinta na wani irin bugawa, cikin fusata ta kai min duka dan ban zaci haka daga gare ta ba. Faduwa nayi can gefe, "Narmin wannan yar yarinyar naji kamshin turaren Sultan Mehran a Jikinta a gidan Uban waye ta samu?" "Sultan Mehran?" Kafin kace me, dama suna jin haushina tuni suka tara min fadawa, aka dauke ni zuwa shsshin Sultanah Hoyam, ita kanta taji kamshin dan haka ta tashi tare da sakawa a riko ni har shashin Mehran. Tunda muka shiga baya kusa, haka ta haura sama,can sai gasu tare yana sanye da wata rigar shan iska. Kallon mu yayi tare da mutanen da suka riko ni, sannan ya zubawa Sultanah Hoyam ido. "Mehran! Taya akayi yarinyar nan ta sami turaren ka? Abu yaja ana ta kanannan magana." Dauke kai yayi kamar bada shi take ba, tana kuma tambayar shi ya juya ya bar mu a gurin, cikin takaici da bakin ciki, tasaka a kai ni can wani gidan Horo me suna Darul Azab... . Bayan tafiyar mu ne tasaka aka kawo mata Mahlika. "Kinyi abinda ya dace, dan haka ina son ki saka ido akan kome na motsin yarinyar, dan in har ta sami kusanci dashi a bayan fage yake nan. Kema bana son kusancin ki da Mehran kasancewar ban yarda da kowa akan shi ba. Kinji Ni?" "Eh na ji ki Sultanah." "Zaki iya tafiya!" "Nagode Sultanah" Wannan littafin na kuɗi ne.. *Allah yajikan Iyayena 😭😭* #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 Book 1 Mai_Dambu BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM Page 22 Tana da fita ta sake murmushin mugunta tace. "Lokaci yana zuwa Sultanah Hoyam." A hankali take takawa, tana nazarin abinda Mahaifiyarta tace mata. "Narmin itace makamin mu, sabida itama tana da ciwon Sultanah Hoyam, idan muka rike ta zata bamu hadin kai. Burina ki sami kusanci da Sultan Aamaan Mehran, yadda zaki yi abinda babu wnada ya tab'a yi, amma karki sake Abban ki yasan cewa akwai cin Amana a cikin tafiyar domin ba zai yarda ba, kuma zai iya dakatar dake abinda zaki yi." Murmushi tayi a karo na biyu, sannan ta nufi hanyar shsshin su. ~~~ Tunda aka kai ni, darul Azab, wanda yake cike da zalinci karkashin kulawar wasu maradai mara imani da mutunci, ya sani shiga cikin tashin hankali, domin kuwa wani irin nau'in azaba suke bawa kowa. Suna da wata bulala me dauke da wasu irin allurai a jikin shi, dan haka suka shiga zane ni dashi. Har sai da nayi laushi, haka suka kyale ni, washi gari suka tashe ni da ruwan zafi, aka daura sabon azbtuwar. .. tunda gari ya waye FAZILATUL take saka idanun akan zuwan Ikram babu ita babu labarinta, har zuwa rana anan ta tura darda ya tafi niman ta, sai hangota yayi a tsakiyar masarautan an saka bayi suyi ta jifarta da d'anyen tumatiri, da sauri ya koma ya gaya mata. Bisa al'adar idan aka gama mata wannan uƙubar, zasu kuma yanke mata hannun sabida tai sata, dan haka ta rubuta wasika izuwa ga mutanen gari tare da gaya musu, irin nauyin Uƙubar da Sultan Aamaan Mehran yake ganawa mata da bayi, bayan kowa yasan halin shi dan luwadi ne. Kasancewar an cika ana kallon Ikram har aka watsa musu takardun, basu Fahimta ba, lokacin da suka fahimci sakon da yake jikin Takardan, aikuwa talakawa suka shiga bore, tare da kunce Ikram, sannan suka juya al'amarin satar izuwa cewa. Ya kamata zai yi luwadi da ita ne, ita kuma garin gudu ta shafe kamshin turaren. Dan haka lokaci guda, maganar ta zama wutar daji, tare da zama babban al'amari. Talakawa sun fusata ai nu, dan haka suka ce ko ya fito ya kare kanshi ko kuma ya sauka a kujeran mulkin. *Wani irin tashin hankali nake kuma fuskanta ne? Wani irin bala'i ne ya ke kuma tunkara na? Me yasa sai Ni? Innalillahi wa'inna ilaihi rajioun* Wadannan sune abinda yake yawo a raina, duk da sun kwance ni, na kasa tafiya. Sakamakon yagewar da tufafin jikina yayi. Ina durkushe a gurin. .... "Wannan wani irin rashin daraja ne? Idan kasan zaka yi kazamar rayuwar ka, sai ka..." Cikin zafin nama aka hango kan Mir Jazib, yana tsalle gangan jikin shi yana birgima jini yana ambaliya a cikin fadar. Takarkarewa Sultan Mehran yayi ya kwatsama musu ihu, sabida yadda yake jin zuciyarshi tana ci da wuta. Idanun shi Jajjur ya nuna su da yatsa yana huci. "Ku dauko min ita!" Ya juya tare da barin Fadar zuciyar shi tana ci bal-bal-bal. Ina sunkuye naji an dauke ni cak, tunda suka dauke ni basu ajiye ni ba, sai a katafaren shashin sa, wanda yake dauke da kamshin turaren da ake bala'i akai. Tunda suka ajiye ni, jikina ne yake rawa sakamakon hango shi da nayi tsaye tare da juya min baya, yana daure da kwarjalle. Dakin kuwa kwalbar turaren ne a fashe a ko ina. Juyawa yayi tare da kallona idanun shi da fuskar shi abin tsoro ne. Domin sunyi jajjur. Shiga ban dakin yayi tare da barina a gurin, dan haka ban yi karambanin kome ba, na kwanta sabida zazzaɓin da yake cin jikina. Tunda na kwanta a gurin nake gani dishi dishi, ba zan iya tantance abinda ya faru ba, sai dai na farka ne a wani daki karami a dai cikin castly ɗin. Tashi nayi a hankali na ga maganin tare da abinci. Tashi nayi na fara ci, sannan na lura da ban daki na shiga nayi alola da wanka na fito. Ina idarwa daya daga cikin mutanen shi ya shigo min, kallona yayi ina ƙoƙarin saka mayafin fuskana, takowa yayi gaba na, tare da kai hannun shi zai tab'a ni, na kaiwa hannun duka. "Me zaki boye a fuskar ki? Baki san har jikinki na gani ba." "Kayi kuskuren ganin jikina, amma yanzun zaka biya ladan ganin da kayi." Wani irin karar da muke kama gashin kaina na dauka, tare da suka Mishi yana kaucewa, wani irin azazzaben fada muka kama a cikin d'akin, tunda yaga jikina wallahi sai na fasa mishi idanun shi. Aikuwa Allah ya bani Sa'a na soka mishi tsinken, a saman idanun shi, tare da kai mishi wata irin duka, ihu Yasaka tare da kiran Fudail ya kawo mishi dauki, duk da na sha duka amma haka bai hana Ni jin dadi, na tsinka mishi jijjiyar saman idanun shi ba. Shigowa Fudail da Darakshan suka yi, suna kallon yadda gashi kaina ya lullube fuskana. "Ke wacce irin mutum ce da bata jin magana?" Inji daya daga cikin mutanen. "Rashin darajar ku ya janyo haka, idan baku kyale ni ba, wancan lusarin dan daudun sai na burma mishi wuka ta cikin shi ya bullo ta bayan shi. Ko kuma ta alkalamin shi ya fito ta duburar shi." Fitar da shi suka yi, sannan suka koma gurin Sultan Mehran suka gaya mishi. Da hannun yayi musu alama, su fitar da Ita, dan haka suka fita da sauri abun su, kai ta shsshin bayin suka kuma yi, tun daga ranar ban kuma samun rashin mutunci ba. Sai dai kuma an sauya min aikina daga can haramtacciyar Fada, zuwa cikin Fadar. Inda nake kawowa manyan fadar abin sha da naci, wannan shine aikina da kuma dalilina na zama cikin masarautar. Idan akwai Abinda yake min ciwo yadda suke kai min duka a ɗuwais dina,.duk da kuwa dattawa ne babu matashi sai shi da masu kula dashi. Bai tab'a kallon haka a matsayin cin mutuncin ba, kawai abinda ya sani ya zab'i a tozartani sama da abinda nayi mishi. Yau na kawo musu abin sha, watsarwa suka yi tare da finciko ni, Mir Rahil yana ƙoƙarin kai hannun shi cikin rigana, na daki makogaron shi, take numfashin sa ya tsaya cak. Caaaa dakaru suka min da takobin, zare na jikin Mir Rahil din nayi, tare da jan layi. Mamaki ne ya kama kowa a gurin. "Ke ki ajiye takobinki!" "Ba zan ajiye ba sai na kashe wancan kazamin me wanka cikin datti." Aikuwa yaki ya barke a tsakanin mu, me shegen tashin hankali. Kafin kace me na jikata mishi dakarun fadar, ina kallon shi dukda na gaji sosai, abinda ya kwace ni a hannun su zafin nama, a duniyar yaki zafin nama itace sama da kome, durkusawa nayi akan gwiwata, dogare da takobin ina huci. A hankali ya mike tare da zare takobin shi, ya tako gabana. Da ace nasan waye a gaba na, da har duniya ta tashi ba zan so na kuma hada karfin dantse da wannan basamuden ba. Mik'ewa nayi tare da tattara gashin kai na, na mai da baya, sannan naja kafana baya tare da jan layin. Na mishi alama ya taso idan ya shirya. Gyada kai yayi tare da sake murmushin takaici. Yau da mace zai yi fada. Bari yaga wani irin horo ta samu. Sai dai kashhhh Fudail shi ya sha gaban shi tare da kawo min mugun sara kamar zai rabani gida bi. Tunda muka fara gwabza yaki tsakanin mu, muke jin kamar zamu kashe junan mu, dukda wutsiyar raƙumi tayi nesa da kasa, sannan abin kunya ce a gare shi faɗa da mace, shi yasa Fudail ya amshi fadar tare da fadawa musu maganar da yayi matukar tasiri a ransu. "Ba zamu tab'a barin Sultan Mehran yayi fada da yar karamar kiyashi ba" Dan haka tunda muka fara, ko kwarzanin shi banyi ba, sai ma kare kai na da nake, domin Idan ya kawo min sara, ji nake kamar da mutane dari nake fadar, yarda takobin nayi tare da kallon shi. "Me kika taka?" "Idan ka shirya!" Da nasan cewa bala'in da zan tarowa kai na, haka ce da ban yi yunkurin juya fadar zuwa dambe ba. Domin lokaci guda nayi dana sanin yafi karfin kwando dubu, domin dukar kawo wuka Fudail yayi min. Koda ya juya, babu sultan Mehran a cikin fadar. Daukata yasa aka yi, suka kai ni can Shashin bayi. Sai da na kwana uku, kafin na warware kamar jaka. Ina zaune aka watsa min kaya. "Ki saka zaku je can babban majalisar Sultan zaku sanya su nishadi." "Ba zanje ba." "Zaki" "Toh naga mai kai ni!" "Idan baki kije dan Allah ba zaki dan azabar shi." Lashe bushashen lebbena nayi sannan na shirya ba daura wata mayafi kai, cirewa suka yi tare da daura min wata jigidan zinari wanda kana motsa zaka ji karan har cikin kanka. Kafana ma haka da ko ina, kayan da na saka yar karamar buje ce, me tsagu har tsakanin cinyoyina, sai dan karamin dan kamfe da yake makale da shi. Kirjin kuwa dama akwai wani yadin da muke daure nonuwar mu dashi, dashi na daure nawa, amma sauran basu daure nasu ba. Sun barshi yadda suna rawan yana zillo. Tunda muka gama suka shirya mu, tare da nufar shashin. Muna shiga aka fara mana kid'a, lumshe idanuna nayi tare da jin sautin kidar har cikin kai na. A hankali muka fara rawan, ana watsa mana wani irin ruwa, kafin kace me duk mun bugu, zan iya cewa ban san kome ba, amma tabbas naga lokacin da wanda muka yi fada dashi ya dauke ni, sama sama nake jin kamar ihu da hayaniyar muryan mutane. Tun daga nan ban kuma fahimtar kome ba, sai da safe. Na tsince kai na a wannan karamin dakin nan dai. Gyara kwanciya nayi zan cigaba da barci naji an sheka min ruwa, zubur na miki tare da kallon mutumin. "Banza kawai! Insha Allah akan wancan dan luwadin zan rama." A fusace ya shigo dakin tare da shake min wuya, dariya ya bani nace mishi. "Toh ba dan luwadi bane? Me yasa ya ajiye kartin maza irinku yana zaka takashin ku..." Marina yayi tare da ture ni, sannan ya fita. Tashi nayi na shiga ban daki nayi wanka da alwala, nafito tare da sallar ta sallolin da suke kai na, ina cikin addu'o'in ya kuma kawo min abincin. "Da fatan baka saka min guba ba?" "Da zaki ci ki mutu ai da ba haka ba" "Sai dai kai ka mutu domin duk abinda aka min sai na rama akan wancan mara mutuncin." Na shiga cikin abincina,.haka ya fita yana tsaki a ranshi. Yana gama shiryawa ya kalle su, sannan yasa kai ya fita.. abubuwan da suke faruwa yake dawo Mishi kan shi, tun daga haduwar shi da yarinyar har zuwa yanzun, takaddarirancin ta yayi yawa dole ya sauke mata shi, dole ya koya mata hankali. Dan haka ya tanadar mata da nau'o'in azaba. ..... Koda naji gidan babu hayaniya,shiryawa nayi tare da barin cikin gidan, na nufi haramtacciyar Fada. Kimanin sati biyu zuwa uku kenan bamu samu damar haduwa da juna ba. Ina shiga na karasa gurin Maman Jasrah. Zube gwiwata nayi cikin ladabi da biyayya. "Aikinki yana kyau? Amma yaushe kika koyi fada haka?" Sosa kai na nayi sannan nace mata. "Kasancewar munyi fama da hare hare da yaki yasa muka koya dan kare kanmu." "Kinyi aikin da ya dace saura mataki na gaba, dan banyi tsammanin lokaci guda Mehran zai barki a cikin fadar shi ba, dan haka ki nutsu kema ki koyi halin masarautan ki koyi dabi'ar su." Daga nan ta shiga daura min darasin mu na gaba. Tare da yadda zan kuma samun shiga cikin gidan sosai. Wannan littafin na kuɗi ne. *Allah ka jikan Iyayena 😭😭* #Mai_Dambu. [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 Book 1 Mai_Dambu BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM Page 23 Ina cikin sauraronta, sai ga dakaru. Suka shigo cikin gidan. Basu yi wata wata ba, suka saka Ni a gaba. Ban yi musu ba, tunda muka nufi cikin gidan na fahimci ran Mutumin nan ya ɓaci. Ban d'aga hankalina ba, sai da naga ya saka manyan kartin maza, dai dai fitowar Sultan Mehran, suka shiga zane ni. Tare da tambayana da Izinin waye na fita. Idan na basu amsa tabbas ina tsoron su, idan nayi shiru kuma zasu ji bakin ciki. Dan haka nayi banza dasu, ganin haka suka ci-gaba da zabgata, sai da suka ga kayan jikina yana yagewa, kai na kwance sabida zunzurutun dukar, wanda ya haifar da zubar jini daga bulalan. Yana zaune ya daura daya akan daya. Ba kome yake bashi mamaki ba, yadda taurin kai ya hanani ihu, jana suka yi zuwa dakin da nake, lokacin sallah azhar yayi da haka nayi ta bin bango na shiga ban daki, nayi alwala na fito. Sai da na fara sallah ne kuka ya zo min, tare da shashekar. Kumshe idanun shi yayi tare da kallon Abincin da yake gaban shi ya fara ci a hankali, yana iya jiyo kukanta amma bai da wani damuwa akan haka, sai ma takaici da haushin da take bashi. Ya gaji da sauraron ihunta. Ture abincin yayi tare da ɗaukar bulalan ya nufi d'akin. "Afwa Sultan Mehran! Ta tuba ba zata kuma ba." Inji Darakshan, banza yayi da su ya shige d'akin, ganinta yayi ta kai sujada, tana kuka tare da kirariwa Ubangiji, abun ba wai tana yi a fili bane a Zuciyarta ne har ya fito fili. Kalmar da ya tsaya mishi a rai ya cigaba da hautsina mishi lissafi, "Ya waduddu Ya Zul-arshin majid! Ya fa'alil limayuri" Ji yayi kan shi kamar zata fashe abinda yayi niyya ya tsinci kanshi ya kasa aiwatar wa, da sauri ya fito, domin ji yaƙe d'akin tana mishi zafi kamar an hura mishi wuta. Abinda zuciyar shi ta fara gaya mishi ba kome bane face. *Lallai yarinyar nan matsafiya ce, kuma zata iya halaka mutanen birnin ka, kayi gaggawan sawa a halakata* Cikin wani irin tsawa yaji wani shashin zuciyar shi tana cewa. *Ba matsafiya bace, kayi bincike kafin ka zarta da hukunci* Take zuciyar shi ta kasu bangare biyu, zama yayi cikin damuwa yana kallon su. Ganin yadda ya fito yana haki, a fusace suka nufi d'akin, suka tadda ita tana sallah. Cikin fushi Darakshan ya nufeta, kamar wanda aka tura shi dakin wuta, ne zunzurutun zafi dole suka fito basu shirya ba. Kallon juna suke dashi, bakin shi nason yin magana, amma kamar wanda aka rufe mishi bakin,dan dole yayi shiru yana kallon su. Amma zunzurutun mugunta dariya yake musu a ranshi, musamman yadda suke hada gumi. Tashi yayi ya wuce sama, daga nan ya hana kowa shigo mishi, ko masu kula dakin shi baya kaunar su shigo mishi. Gashi dakin shi yayi wani irin datti, abinci ma tsakanin shi da Allah ya kaurace musu, Fudail ne ya fahimci abinda yake nufi, dan haka da kan shi ya saka ni a gaba muka haura har dakin shi, na gyara kome na goge kome, tare da tattara kayan dattin shi ne fito dashi. Me wanke mishi kayan shi ya amsa, sannan Fudail yace min. "Akwai dakin girki kece zaki cigaba da mishi girka." "Akan me?" "Sabida haka yake bukata." Kamar zanyi magana sai kuma na fasa, tun daga ranar na koma Jakar Sultan Mehran, kamar zanyi kuka wani lokaci a dakin girkin nake kwana, sakamakon yadda kome dare zai Turo na daga mishi shayi, idan ina barci haka Fudail zai tashe ni. Kuma dan rashin mutunci, idan na gama abincin sai an sani na ci kafin yaci, ina tsaye zai gama mulkin shi kafin yaci, yana ci yana wulakanta ni, ta Hanyar watsa min ruwa, ko furza min abincin a fuskana, ko kuma ya kwala min kofi, iya wahala ina fuskanta da Mehran. Amma ban tab'a jin ko ganin wata rana zan sami yanci ba. Yau ma ina kwance, naji ana zungurina, bude ido nayi na kalle shi. Daga shi sai yar kwarjalle, da wata rigar shan iska, da sauri na mike, dan ban tab'a ganin shi ba, ido da ido babu alkyaba. Yau ma dai gashi ne yayi mishi rumfar da fuskar shi. Tsayawa nayi ina kallon fadaddar kirjin shi, me yalwacce da gashin a kwance luf. Yana rike da kofi a hannun shi, sai juya kofin yake. Banyi aune ba sai ji nayi an saka min kafa, na zube kasa. Wallahi idan ka gan shi ba zaka tab'a kawowa zai yi irin wannan muguntar ba, amma ina mugu, kamar bashi ba. Tashi nayi na shiga ƙoƙarin hura wutar, sai na kunna zai kashe, ajiye abin hura wutar nayi a fusace zan fita, make ni mutumin nan yayi, kai na ya bugu da bango. Anan na sume mishi. Bai damu ba, ya tsallaka ni. Ya fice Daga dakin girkin, dake ranshi yana kaunar shayin kafin ya kwanta, dole ya d'ago Fudail yazo ya watsa min ruwa, tare da taimaka min na hada mishi ruwan zafin, kai na kamar zai fashe, ina aikin ina kuka. Ina gamawa Na mika mishi zan fita sai gashi ya kuma shigowa, bai magana ba shi lallai sai dai nayi mishi girki, kallon shi nayi dan dare ya raba sosai, haka na shiga aiki babu ji babu gani, kuma yana tsaye. Dakyar na kammala aikin, ina gamawa ya kalle ni, na zauna jagwab. Saka hannun shi yayi tare da zuba abincin gabaki daya. A razane muka kalle shi, kwalla ce ta shiga cika min ido. "Yadda ka tozarta Abinci sai Allah ya tozarta ka." Buge min baƙi Fudail yayi tare da kwashe abincin. Ya mika min. "sake wani" "Ba zan girka ba!" Kallon Fudail yayi sannan ya kalli hanyar fita, yana isowa inda nake ya daki kafana da kafarshi, yadda kuka san an karya itacce haka ya b'alla min kafa sannan ya ficce abin shi. Ihun da nake yasanya Fudail da Darakshan suka kuma shigowa..ganin ina gurnani. Tare da rike kafar da ta lankwashe. "Kai Amma Sultan Mehran bai." Gyaran murya muka ji, daga bakin kofar koran su yayi daga kitchen ɗin, haka ya juya ya fita shima. Washi gari kafar ta kumbura sumtum, kuma dan bakin mugunta wai nayi abin karyawa, dole Fudail ya gaya mishi gaskiya. "Sultan Mehran, yarinyar nan.ba zata iya aiki ba, sabida zazzaɓi da karaya." Lallai shi zasu renawa hankali dan haka ya juya ban shi. "A fidda ita." Haka Fudail yazo ya fita dani, zuwa gidan Me magani Lingesa, suka daura min kafar, bayan nasha bakar azaba. Duk da ban wuce kwana ashirin a cikin shashin Sultan Mehran ba, amma kuma na sha azaba a cikin gidan. Dan haka na dauki wannan fitar nawa a matsayin abinda Allah ya bani. --- Ba a san munafukin da ya gayawa Sultanah Hoyam cewa Ai akwai mace a shsshin Sultan ba, sai gashi hankalinta yayi mugun tashi. Yana fada ta tura mishi sakon idan zai koma gida yazo tana son ganin shi. Kallon dan aikan yayi bai ce mishi kalla ba, sai bayan an tashi ya nufi gidan. Tunda ya zauna take magana, gashi ta zuba mishi abinci, loma daya ya kai bakin shi, furzawa yayi tare da kallon ta, a hankali ya mike zai fita tace mishi. "Mehran! Don Allah karka yarda da yarinyar domin kashe ka zata yi! Haka suk.." "Kenan kece kika kashe Abba na?" A zabure ta kalle shi jikinta yana rawa, murmushi yayi sannan ya fita daga d'akin, tana ganin ya fita ta kira Narmin, tasaka aka dauko ni, bayan ta min duka da bulala sannan tasaka aka mai dani gurin jinyar da nake tare da cewa za a kai ni. Shashin Amir Hood, a can zan zauna na cigaba da aiki. ~~ Noman. Sun isa Abu Dhabi, inda suka shiga nima na, babu ni babu labarina, karshe wani ne yace musu. "Wai kun anan zaku same ta? Tabbas naga me kama da ita a Andulus, dan haka ku tafi can zaku sami labarinta." Sabon tashin hankali, haka suka sake juyawa suka koma masaukin su, washi gari suka kuma ɗaukar hanya, ta jirgin ruwa. ~~ Wata na daya ina jinya, sannan aka tura ni shsshin Amir Hood, inda yake dauke da matasa maza kusan guda biyu. Yan biyu ne yaran Abdul Malik, Zuhair da Zunoon. Yaran matasane da suka haɗu iya haduwa, sai dai basu Mehran ba, Zunoon bai da matsala asalima bai da ra'ayin mata, domin a gefe guda yana da ilimin addini sosai, sakamakon dan uwan shi Zuhair da ya kasance kullum sai na ganshi da yan mata bayi sama da biyu. Bana sake mishi fuska, kullum na shiga shshsin sa, zan gyara mishi gado, da suka lalata zanyi duk abinda ya dace, idan zan fita ne yake tsare min hanya. Dauke kai na, nake yi abuna sannan na fita daga dakin, haka ko a Kitchen zai shigo min, sai dai naji duka a mazaunaina, wannan rashin darajar yana min ciwo. Dan haka na shiga tara shi, ranar da ya cikani zai sha mamaki. ..... Wasa wasa Mehran ya fara kin abincin da ake girka mishi, a hankali ya buɗe musu ido, lallai sai dai su dawo mishi dani, tsuru tsuru suka yi an rasa wanda zai gaya mishi ai Sultanah tasa an mai dani can Shashin Amir Hood. "Ina yarinyar take?" Ya tambaye su a tsawace, had'iye yawun suka yi, tare da cewa. "Sultanah Hoyam ta." Lumshe idanun shi yayi cikin wani irin b'acin rai, sannan ya bude akan su, yace. "Waye a cikin ku ya gaya mata akwai mace anan?" Tsoro da tashin hankali ya hana su magana. "Afwa Sultan!" Wani irin cira yake, dan haka ya mazge kamar bai damu ba, amma kasan ranshi yana jagule, sakamakon yadda bakin shi ya sakalkace da diban albarkan hannunta, sannan dan tsaya an sami munafukin da ya saka a ka raba shi da ita, duk sai ya zabga musu rashin mutunci. Yake ayanawa a ran shi. Share batun yayi dan karsu darsa wani abu a ransu, dan ya fara jin ƙishin ƙishin wai ya damu da bakar fatan da take kula da shi. A hankali kwanaki suka shiga tafiya sama da baya ma, tun yana iya dauke kanshi baya magana, har takai ya kasa hakuri. Gurin Sultanah Hoyam ya nufa, yadda ya zauna Fahimci abinda yake damun shi. "Mehran!" "Me yasa?" Ta tambaye ta, "Meke faruwa,?" "Yarinyar da kika dauka!" "Wacce?" Girgiza kai yayi tare da mik'ewa ya nufi hanyar waje, bai kuma mata magana. Tunda ya bar gurinta bai kuma magana akan Ikram ba, asalima tattara ta yayi ya saka a gefe, sabida rashin hankalin da iyakokin shi da kasar jordan suka sami wata b'araka, haka yasa aka fara shirin tattaunawa, karshe aka sami labarin suna shirin yaki. Dan haka ya shirya da shida zaratan jarumai su kimamin dari cif. Tafiyar bai da ra'ayin shi amma idan ya tuna matsalar da yake tukarar kasar shi, dan haka ya nufi yakin, dake an san Dakarun SAMAIND basa fitowa kad'an, dan haka suma suka shirya musu. Tafiyar kwana uku, suka yi tare da tura dan leken asirin su, ya duba musu yawan dakarun, anan suka sami labarin dakarun miliyan uku ne, murmushi Yayi sannan, ya fara musu zanen yadda zasu ci garin da yaki ba tare da sun tab'a talakawan kasar ba. Aikuwa haka ce ya faru, domin shigan dare suka musu, ana tsaka da shagali, suka farmake su. Inda suka kama Sarkin Jordan. Sultan Suhaib Salem. Tare da duk masu hannun akan a farmake su. "Ba ra'ayina zubda jinin kowa ba, amma ku da kuka ci amana ta, zaku fuskanci horo." Daga haka yasa aka sare kawunan su, aka kafa a tsakiyar birnin, bayan ya nimo mutanen da suka dace da masarautan, ya nad'a su a sarakunan kasar jordan. Sai dai wannan abun ya faru akan Idanun Yar Sarkin Sultan Suhaib Salem, wato Almirah Jennah. Wacce take kuka kamar ranta zai fita, bayan tafiyar Sultan Mehran itama ta.... *Allah ya jikan Iyayena 😭* Littafin nan na kuɗi ne. #Mai_Dambu. [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 Book 1 Mai_Dambu BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM 24 Tafiyar kwana bakwai kacal ya kai su Jordan ya kuma dawo dasu, koda aka ce an hango rakuman su. Wani irin murna mutanen gari suke, babu abinda ya kuma burge su kamar yadda ya shigo garin a basaja, aka kasa ta tantance shi a cikin jama'ar shi. Ya shige cikin Masarautan babu wanda ya gane shi. Tunda ya shigo Masarautan bai tsaya ko ina ba sai shshain Mahaifiyarshi, cikin murna da dauki ta rungume shi. "Albarka ya baibayi rayuwarka!" Sake ta yayi sannan ya nufi castle din shi. Tunda ya shiga ya sami gidan ko ina kal kai, amma babu wannan karsashin da ya d'andana na kwanaki ƙalilan kafin rabuwar shi da Yarinyar. Cogewa yayi daga bakin kofar, cikin takaici ya juya bai ce musu kome ba. Duk inda ya wuce binshi ake, dan ko takalmi babu a kafar shi. Ya gaji, wata biyu ana niman na uku rabon shi da ita, shi ko dan cikin shi yana niman ta, yana bukatar ta a matsayin baiwar shi da zata mishi abinci. Wannan abun da take karantawa ko take renawa yake son saurarra, yana son ganinta cikin kadaita lokaci tana goho da dungure iya haka ma ya wadatar dashi. Kai tsaye Shashin Amir Hood ya nufa. --- Tunda aka kawo ni, Zuhair yake bina da mugun nufi, sau biyu ina kwatar kaina da wuka, domin ya sha giya zai zo yayi ta niman lalata min rayuwa. Yanzun ma na idar da abincin sune na kai inda ake ajiyewa, na shiga wanka, shine ganin ina ban daki ya biyo Ni. Allah ya taimake ni na saka yar shimi na Kenan, ina saka rigar ya shigo ban dakin. "Ke bakar fata! Ke mayya ce? Idan ke mayya ce haka zan ratsa tsakanin hamada da tekun ki nayi likaya a cikin alkaryan ki, dan haka ki nutsu kar na ji miki ciwo." Cikin bakin ciki na saka rigar tare da kai mishi duka zan gudu,ya saka min kafa, na fadi. Da sauri na mike tsaye, muka shiga wani azazzaben fada kamar zamu kashe kan mu, matsalar da aka samu, ya kware a iya caskale, fiye da yadda baka tunani, dan haka idan ya naushe ni na fadi sai naji a jikina nake iya tashi. Kuma bana iya maida mishi martani sai dai kare kaina. Tunda ya dake ni a mukamiki na, na fadi can dakyar na mike zan zauna ya kuma kai min duka a cikina, tare da ɗauka ta cak. ya maka da kasa, mikewa nayi kamar na suma. Yana zuwa Allah ya taimake ni akwai karamar wukar da na yanka tuffa, samun wukar nayi na kwanta akan shi, yana zuwa ya saka hannun zai yaga min riga , na yanki fuskar shi. Ihu ya saka tare da kai min mugun duka, sannan ya yaga rigar har kasa, tare da kaiwa shimi na sura sai da ya rabata gida biyu. Nonuwa na ya chafka, na fasa ihun me mugun karfi, ina niman kwatar kai na, murza su yake da karfi tare da kai bakin shi yana cizon su cikin mugunta, ihun da nake har wajen kofar Shashin. ...... Jikin shine ya dauki rawa,bai tab'a jin sautin da ya hargitsa mishi lissafi irin na yarinyar ba, cikin wani irin sassanyar sarsarfe ya isa bakin kofar Shashin dakaru suka nemi hana shi shiga, zare yar gatarin shi yayi, tare da musu saran faskare tuni suka zube matattu a gurin. Sake nufar cikin gidan yayi yana bin hanyar da sautin muryan Ikram yake fitowa, haka kawai yake jin wani irin mutuwar jiki, dakyar yake iya d'aga kafar shi, zuciyar shi tana wani irin lugude, ji yaƙe kamar wanda ake buga mishi ganguna, yana isa kofar, dunkule hannun shi yayi cikin wani irin fisgar numfashi ya daki kofar sai da ya ɓalle katakon kofar. Wani irin abu yaji ya tsaya mishi a ranshi, tunda yake yasan ya kwanta da Yan mata, bai tab'a kawowa zai ga yadda ake, keta alfarmar mace ba sai yau. Goldrn eyes d'inshi masu matukar sheki suke wani tara oily a cikin su, jijjiyar idanun shi sun wani dauki ja suna tsattsafo da ruwan kwalla, yawun bakin shi ya kwafe.idan bai yi karya ba numfashin sa basa wuce kokofin huhun shi da har zasu bawa zuciyar shi. Yana tsaye kamar me tunani, ya kura musu ido. Mika mishi hannu take cikin walagigi da tashin hankali, tare da jin ina da mutuwa nayi, da wannan wulakancin da ake min, cikin wani irin kuka na mika mishi hannu. "Me....me....meh....ran." Cikin wani irin fitar numfashina, na mika mishi hannu, a hankali idanuna suka fara shirin kafewa, dai dai lokacin da Zuhair, yake kunce wandon shi tare da fitar da Crown prince din shi. Wani irin damka yayi mishi tare da sake wani irin huci kamar gamsheka, ya rike wuyar shi, ya wani gwara shi da bango. Kamar an watsa faten wake a tire haka ya watsar da dan banza. Cire fitar yakin shi yayi tare da cire asalin rigar cikin shi, ya juyar da kan shi, ya yafa mata. Domin baya tunanin tana raye. Shigowar Fudail da Darakshan, sai Zunnoon, da Amir Hood, suka shigo. Zama yayi yana karkade kafar shi. Yana matsa hannun shi suna bada wani irin sauti kass-kass. Motsin da Zuhair yayi Yasaka shi mikewa tare da cewa. "Rakshan, Dail ku kashe shi. Ku rufe tarihin shi. Karku barshi ya rayu dan zai iya hakewa matan mu." Zuɓewa Zunoon yayi tare da Amir Hood. "Don Allah kayi hakuri, ka hukunta shi ta wani shashin, hukuncin kisa wallahi zai tab'a rayuwata, don Allah kayi hakuri." Yadda yaga hawaye a idanun Zunnoon da Amir Hood, Yasaka shi dauke kanshi tare da mik'ewa, yana zuwa inda Zuhair yake ya wani saka kafar shi ya daki B din shi tare da y'ay'an gwaibar shi baki daya, wani irin razanannen ihu me dauke da nishi yayi sannan ya zube ragwajab. Murmushi yayi sannan ya fice tare da kallon Inda Ikram take kwance. Zuwa Fudail yayi ya dauke ta cak, yana mamakin yadda fuskarta ya kumbura, yana tafiya ana take mishi baya, har castle din shi, aka kai ta dakin ta, aka shiga duba ta, dan Darakshan ya tawo da Lingesa likita. ~~ Sultan Mehran na barin gidan, Amir Hood ya juya yana bin bayan shi da kallo me dauke da ma'anoni masu yawa. Haka shima aka dauko wani likitan su, ya fara duba shi. --- Sai da na kwana na wuni, sannan ya farka da Ihun tare da kiran sunan Noman. Yana zaune a falon shi, yau bai fita fada ba. Shi nan yayi fushi da abinda Zubair yayi, asalima bai san Zubair din ba, amma yake kokarin ganin ya sauke haushin sa akan kowa ma, Ihun da nake yayi masifar cika masa kunnen, amma ya share kamar bashi ba, idan ka ga yadda ya dauke kai sai ka rantse da Allah ba ihun ne ya dame shi ba. Shigowar Lingesa tare da Fudail yasa shi kallon su, na yan dakika kafin ya maida kan shi gaba. Haka suka shigo dakin ina ganin su na shiga Niman hanyar boya, watsa min wani abu Lingesa yayi tare da goga min wani farin abu,tuni barci yayi gaba dani. "Razana tai idan ta samu barci Insha Allah zata manta kome." Gyada kai yayi sannan suka fita yana nuna mishi wasu abubuwan da zan sha. ~~ Oman. Duk da yana sane da Ikram tayi mishi nisa, amma baya jin koda da rana daya kaunar ta ya ragu a ranshi, asalima bakin ciki da damuwa yake damun shi, shi yasa idan dare yayi yake fita daga Masarautan ya nufi bakin kogi ya zauna. Nawwas kenan, wanda ya mutu a kaunar Ikram, idan akwai abinda ya tsana ya bude idanun yaga Abrad yana gaya mishi wasu sirrin Ikram, duk da bayi tarayya da ita ba, sai dai yana ji a bakin cikin kusancin da ta samu da Abrad. Shi yasa yake shiri na musamman akan ta, da kuma Abrad, da duk wanda zai kawo mishi tsaiko akanta tabbas zai aika shi garin da ba a dawowa, kai koda kuwa Abrad ne da kan shi. ~~ Andulus Yau kwana tara kenan, suna walagigin niman shi. Kafin suka sami labarin inda Me safara da yan matan yake, cikin dare suka mishi diran mikiya. Yana barci da yan mata a saman jikin shi. Toshe mishi baki suka yi, tare da daure shi. Kafin suka tashe shi. "Ina yarinyar da aka kawo maka daga kasar Suda?" Girgiza kai yayi tare da nuna bai sani ba, kuma da gaske ne dan bayan su Ikram an kawo mishi yan mata dayawa. Yarfa mishi mari Sarwat yayi tare da shake wuyar shi, yace. "Baka gane yarinya me tsadar idanu ba, zaka ga idanunta irinta mage." Da sauri ya musu alamar ya gane ta. "Dan kaniyar ka tana ina?" Suka tambaye shi bayan sun cire mishi abun baƙin shi, "Kasar Oman suka saye ta!" "Dan matar gidan ku, zamu tafi can mu daukota da kai kuma zamu tafi." Haka suka saka shi a gaba suka bar gidan shi da shi. ~~~ SAMAIND Yau kwana uku kenan da dawowa ta, shsshin Sultan Mehran, tsakanin mu kamar wuta da auduga, domin duk gwanintar da nayi mishi bawan Allah nan sai ya make ni. Wasa wasa ya cigaba da azabtar dani, ta hanyar amfani da make ni, nima kuma bani da hakuri,.yana tab'a ni zan rarumi abu nayi kanshi. Karshe dai haka zai min shegen duka, ta hanyar saka min kafa, ko kuma bayan hannun shi. Bayan ya karya zai bar gurin, kawai bawan Allah nan ya take min kafana, har cikin kokon raina naji takun, ban san lokacin da nayi wani tsalle na rungume shi ba. Faduwa muka yi dukkan mu, wanda hakan ya haifar mana da bugun zuciya lokaci guda, kallon fuskar shi nake, wanda yake sanye da hular sarauta. A hankali ya bude idanun shi, yana kallon mayafin fuskana. Yana jin wani abu yana harbawa a cikin jikin shi tare da saukar mishi da wata irin kasala, kamar wanda yayi dogon tafiya haka yake fitar da numfashin sa, har yana dukar fuskana. Hannun shi ya kai zai d'aga abun fuskana, nayi maza na mike akan shi, tare da barin gurin. Ji yayi kamar wani abu yana yawo akan shi, a Sannun yake jin zuciyar shi tana budewa haka duk wani ƙafan sadarwan jikin shi yana bude kan shi. Kamar wanda ya sha giya haka yake jin kanshi a buge, dakyar da sidin goshi ya tattara sauran kuzarin shi ya mike, Yana hada hanya. Fadar da bai fita ba kenan, tunda ya shiga dakin shi ya kwanta rub da ciki. ..... "Ki daina kuka!" "Amma meye nayi mishi da yake kaunar dukana?" Na tambayi Rakshan da yake rarrashina, "Ba duka bane, ki nutsu zaki Fahimci abinda yake nufi dake." Gyada mishi kai nayi, tare da share kwallar da ta zubo min. A hankali nake rayuwar kunci,.duk da ina da yakinin wata rana zan sami yanci amma bana hango yancin nan kusa, lokaci yana tafiya a hankali har muka shiga watan azumi. A lokacin na Fahimci waye nake zaune a kasan shi. Domin duk masu kula dashi suna Ibada,shine kadai baya azumi baya sallah. Ranar da aka ɗauki azumi na fahimci hakan nayi kuka n zubda kwalla, tausayin shi da tausayin rayuwar shi ya sani zuba mishi ido yana cin abinci. "Me yasa baka azumi?" Na tambaye shi kasancewar na kasa hakuri da yanayin shi. "MEHRAN!" Har cikin kanshi yaji tsigar jikin shi yana mik'ewa, bai tab'a jin wanda yake kiran shi da sunan shi kai tsaye bayan Mahaifiyarshi ba. Da wutsiyar idanun shi ya kalle ta, sannan ya cigaba da cin abincin shi. Zai kuma kaiwa bakin shi, na rike hannun shi, Kai min mangari yayi na fadi can, kafin na mike cikin fusata ba ture teburin abincin. Takobin shi da yake makale a falon ya zaro, shi zan zubdawa abinci. Kamar sa'ar ta. A fusace yayo kai na, Allah ya bani Sa'a na dauki mayafin teburin na wurga mishi ya lullube shi, takobin shi ya fadi na dauka da sauri na saka a kan wuyar shi.... *Littafin nan na kuɗi ne* Allah yajikan Iyayena 😭 #Mai_Dambu[5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 Book 1 Mai_Dambu BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM Page 25 Zare mayafin yayi, tare da kura min ido, cire hular kan shi yayi tare da mai da gashin kan shi baya. A karon farko da muka kalli cikin idanun juna, tare da dauke kan shi kamar bai damu ba, kawai sai ji nayi ya buge hannu na, tare da kaiwa kafana duka, zai kwashe ni, mayafin da ya wular nayi maza na fada kai tare da dukar kujeran da yake zama ya shura mishi. Tarewa yayi da kafar shi, sannan ya tako gabana, Allah ya taimake ni na dauki karamin wukar yanka tuffa, kamar yadda ya kawo min sara, a dokin wuya na, haka na kai mishi wukar wukar a kirjin shi, sai da ta huda Sulken jikin shi tare da tab'a fatar shi ta ratsa har zuwa tsokar kirjin shi, rike hannu na yayi tare da sake takobin shi. Yana kallon fuskana. Jinin da yake zuba akan farin jallabiyar. Wani irin tsoro ne ya kamani, na kasa cire hannun kuma na kasa daina tura mishi wukar. "Zaki kashe ni!" Ya faɗa a sanyayye, wani irin rawa jikina ya dauka lokaci guda nayi baya da wukar tare da zare shi a kirjin shi, zuɓewa yayi a jikina, jini na zuba kamar an bude kofar ruwa. A hankali ya shiga zamewa daga jikina, wani irin rawa cikina ya dauka tare da bin shi da ido, wancan lokacin da na hadu da mutumin dajin nan ya dawo min, jin shi nake kamar a lokacin ne muka hadu da mutumin da nake son na kuma gani. *NOMAN!!!* Zuciyata ta ambata, da sauri na ture shi ya fadi kasa, nima jikina ya dauki rawa, a karo na babu adadi. Wani irin kuka ne yazo min lokaci guda na mikewar nayi zan fita da gudu naji ya fisgo ni. Mutumin nan dan duniya ne. Idanun shi a rufe, rike Ni yayi gam kuma yana kwance babu alamar numfashin sa. "Innalillahi wa'inna ilaihi rajioun, Ubangiji ka cece ni kar nayi kisan kai wallahi kashe ni zasu yi,Wayyo Allah Kanwata Airan." Bai sake ni ba duk da kokuwar da nake yi, dashi fisgo ni yayi kan shi tare da, kifani akan shi. "Wayy..." Hannun shi ya saka tare da d'anne min bakina, sai da ya nace. "Wash" Daidai shigowar Fudail da Darakshan, sai Mahaifiyar shi, sake matsa bakin yayi nace. "Ashhhh!" Da sauri suka juya, sannan ya kuma make min bakin fashe da wani shakakken kuka nace. "Wayyo Allah na, na tuba ka bar ni haka." "Uhmmmm!" Da sauri Mahaifiyar shi ta bar gidan, tare da jadadda musu cewa su tabbatar idan ya gama tana niman shi. A cikin kuwa kamar yadda na ji mishi ciwo haka Mehran yayi ta lugude da bakina, sai da yaga jini na diga sannan ya ture ni, na bugu da jikin pillar dakin, dif na dauke wuta. Sakamakon buguwar da nayi, wanda ya haifar da suma na, bai damu ba, tashi yayi tare da nufar dakin shi, ya isa har cikin ban dakin shi ya cire kayan shi, tare kallon inda wukar ta lume, sai da ya wanke ciwon tass sannan ya dauki magani ya shafa tare da rufe gurin, ya saka wata riga, ya fito dakin shi ya kwanta. *Me yasa ta shigo rayuwar shi? Me yasa yake jin kome irin na wancan yarinyar da ya hadu da ita a dokan daji? Me yasa take mishi kallon abubuwa dayawa? Toh waye Allah nan da ta damu dashi ne haka? Me yasa take ce mishi bai sallah bai azumi? Toh su din Sallah da Azumin me yasa ake yin su?* Duk wannan tambayar da yake bai da amsar su don itace zata bashi su. Lumshe idanun shi yayi yana zane hoton fuskar wancan da ya hadu da ita cikin daren nan, wancan Yarinyar tana da fuska me dan tsawo, sannan a tsaye ba zata wuce wannan ta cikin gidan shi ba. Gyada kai yake yana kuma tuno kusancin da ya shiga tsakanin su d'azun nan,ji yayi wandon shi yana harbib iska, ba tare da ya sani ba, sai jin yayi tsinkekken ruwa daga jikin shi tana zuba daga gurin, lumshe idanun shi yayi, a yanzun ya aci ace yana da iyalin kan shi, koda bai yi aure ba ace yana da matar da zata dauke bukatar shi a matsayin shi na namijin duniya. Da wannan tunanin ya shiga barci. ~ A can fada kuwa, ba tare da sanin shi ba aka shiga kara haraji tare da cutar da talakawa babu ji babu gani,. Ana ladsbtar da kai dan dole, sannan ana bin mutane gida ana amso kayan da suka noma karfi da yaji. Wani abin da ya kuma d'aga hankalin mutane, yadda dakarun suke daukar yan mata da sunan Sultan Mehran, daga nan ana shiga dasu sai dai a dawo musu da gawar yar su. Ga azumi yazo ana fuskarta matsala ga rashin abincin kome ya tadda furashi. Duk abinda dakarun zasu yi da sunan Sultan Mehran suke yi. Sanadin haka ya fita akan mutane suka fara tsanar shi. Tare da kai kukan su ga Allah. Ana cikin haka wani abin takaici ya kuma bazuwa inda aka shiga yawo da Sultan Mehran akan idan ya kama mace ta dubura yake kwanciya da ita dama kuma an mishi wannan shedan. Cikin kankanin lokaci aka fara mishi bore da Zanga Zanga, wanda ya saka asalin dakarun masarautan tarwatsa Yan zanga zangan. ..... "Toh ina Mehran yake? Yasan ba zai iya zama haka ba, sai ya saka ana kwaso musu ɗiyoyin talakawan shi yana lalata dasu " Shiru duk suka yi suna sauraron Amir Hood, wanda ya zakalkale yana masifa, zaka rantse da Allah ya kama Sultan Mehran da aikata laifukan da ake zargin shi da su. Dalilin da yasa mahaifiyar shi da makusanta shi suka zo niman shi kenan, suka ji muryan shi da Ikram suna cikin wannan yanayin. .... Zirga zirga take a cikin babban falonta, abu biyu ya tsaya mata a rai, na farko abinda yake faruwa a gari na biyu, samun shi da suka yi yana masha'a da Baiwar shi. Abinda ya girgiza ta, kenan duk gudun da take na tsawon shekaru ya rushe?, duk wannan hakilon da take na tsawon shekaru ya tashi a banza? Wabi irin zufa yake karyo mata tare da tsinewa Ikram yafi kwando dubu. Da alƙawarin idan ta same ta, tabbas sai ta saka an mata mafi girman uƙubar da har ta koma ga mahaliccin ta ba zata manta dashi ba. Gyada kai take kawai gashi ta hana kowa shiga gurinta, saboda kar bakinta ya fadi abinda bata shirya gyara shi ba. --- Gyaran murya Fudail yayi lokacin da ya shigo babban falon ya tsince Ni kwance, munyi kaca-kaca da gurin, alamar babu sauki, kirjin shine yayi mishi nauyi sam bai so wannan alaƙar ta shiga tsakanin Mehran da Ikram ba, dan Allah ya gani yana jinta a ranshi. Amma ya zai yi da ƙaddara ta riga fata, daukarta yayi zuwa dakinta. Gyara mata kwanciya yayi tare da shiga ban dakin ya dauko tsumma da ruwan zafi, yayi ta saka mata a goshinta har ta farka, sannan ya mike tare da kallon ta. "Nagode!" Na fada a hankali, girgiza min kai yayi tare da daure fuskar shi yace. "Allah ya gani bana son alaƙar ki da Mehran!" Da sauri na kalle shi na wasu dakikai, sannan na lumshe idanuna, tare da yada kai ina jin bayana yana ciwo. A hankali ya tako tare da sunkuyar da kanshi, yana kallon fuskana. "Ki taya masoyinki kanki kare kanki!" Lumshe idanuna nayi a karo na biyu, tare da maida kai na saman matashina ina sauke wani irin ajiyar zuciya. Kewar Noman da kaunar shi yana kara samun matsuguni a raina, Juyawa yayi ya fita, bai jira me zance ba, sai dai kuma yana cike da ɓacin rai, koda ya isa bakin kofar da zata sada shi da dakin Mehran. Wani irin abu yaji ya takore mishi kirjin shi, dan dole ya juya tare da barin shashin, dan yana shan alwashin duk abinda Mehran zai yi sai dai yayi dan sai ya raba shi da Ikram. Da wannan alwashin ta fita daga gidan. Sallah azhar ya d'agani na nufi ban daki nayi wanka tare da alwala, sannan na fito nayi sallah. Tare da saka kaya na fito, ina tafiya a hankali, sannan na nufi madafin, abinci nayi har da na bude bakina, ina gamawa na fito na ajiye mishi na shi, sannan na gabatar da sallah a falon. Ina cikin sallah naji motsin shi, ban fasa ba har ya shigo. Kura mata ido yayi cikin nutsuwa, yadda take da kokarin yin sallah da Ibadar ta yayi masifar tab'a zuciyar shi, bai san akwai ranar da zai ganta bata sallah ba. Har mamaki yake idan yaji muryanta tana karatu ko waka ne oho, duk da shi Balarabe ne baya fahimtar karatun da take, sai dai abinda yake yawan ganewa shine idan tana karantawa tana mugun jin dadi dan har akan fuskarta yake ganin nutsuwa da kwanciyar hankali. Zama yayi tare da kallon yadda take addu'a, dukda yana jin haushinta na wani lokaci, amma yawan ibadarta yakan sashi jin dadin zama kusa da ita. Bai san ya jima a tsaye ba, har sai da Rakshan ya shigo falon yayi mishi magana tare da gaya mishi halin da gari yake ciki. Ko takan abincin bai duba ba, ya fita daga gidan, kayan jikin shi daga farar jallabiya babu kome. Ganin dattawan fadan sun fusata kamar zasu cinye shi, yana kallon shi, tare da jin su dan baya fahimtar abinda suke fada sai da can. Ya gaji da hayaniyar su ya daka musu wani uban tsawa wanda Yasaka suka shiga cikin nutsuwar su, zama yayi yana kallon su, sannan ya kura musu ido, ya kalli Fudail da magatakardan masarautan, yana sauraron shi. Yadda yake bayani cikin nutsuwa da zargin shi da ake, ya sashi gyara zaman shi cikin nutsuwa, ya daura daya akan daya yana wani girgiza kafar shi, tare da kallon su daya bayan daya. Murmushi yayi sannan yace musu. "Idan kuma ba Ni bane fa?" Shiru suka yi tare da kallon shi, mik'ewa yayi sannan ya kalli wata agogon karfe wanda wani mutumin rum ya kerawa masarautan, da zallar karfen azurfa sai dutsun jauhari, wanda aka yi adon madubin agogon dashi. "Karfe nawa?" Sunkuyar da kansu suka yi, "Karfe uku Sultan!" Shiru yayi kamar ruwa ya cinye shi, kamar baya cikin fadan. "Uku na asuban gobe!" Daga haka ya mike, zai bar fadan. "Wai kai wani irin mutum ne mara mutunci!" "Ku kama shi!" Haka suka kama Mir Rahil, aka fita dashi yana jan Bala'i wa Sultan Mehran. --- Tunda ya koma yake zirga zirga, tare da zurfaffa tunanin shi, koda baya mu'amala da mutane tabbas yasan ana bin shi da sharri amma yadda ake gudanar da mugun nufin ne bai tab'a tsammanin haka zai faru ba, dan haka ya dauke kan shi kamar bata sane da abinda yake faruwa, a kowane lokaci yana kara fahimtar mutanen da suke zaune dashi musamn dattawan da suke fadar shi, yana kuma kara gane meye matsalar shi dasu. Na farko dai yasan mulkin da yake kai ne basu so, na biyu basu tab'a tsammanin shi din ba kanwan lasa bane sai da aka bashi mulkin, dan haka yana sane da wannan abun sha yayi sanadin da suke kin shi kamar zasu kashe shi. Muryan ta yaji tana karatun Suratu baqara, bai san lokacin da ya taka har kofar dakin ba, yana tsaye a gurin har ta tsayar da karatun sauke ajiyar zuciya yayi sakamakon yadda na sami nutsuwa da sauraron muryanta, da karatunta, a sanyayye yake kuma jin yana Samun sauki daga cikin damuwar da yake fama dashi. Kan shi yana kuma budewa daga cikin duhun da yake fama dashi, a karon farko da yaji yana son ya sami wanda zai taya shi fahimtar rayuwar da yake ciki, sai dai bai san yadda zai fada halin da yake ciki ba, dan dole ya juya baya tare da komawa dakin shi amma tabbas yana cikin damuwar da yake niman abokin hira da raba damuwar shi. Littafin nan na kuɗi ne Allah ka jikan Iyayena. #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 Book 1 Mai_Dambu BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM Page 26 Shiru yayi yana kuma nazarin halin da yake ciki. Ga shi nakiya sun sako shi a gaba, gashi yana kuma son sanin waye yake tab'a shi ta hanyar da bai sani ba. Dan haka ya dawo gurin cikin abincin shi ya zauna tare da kura mishi ido, kamar yana son gano wani abu a cikin gurin, amma a zahiri ba haka bane tsabar damuwa da tayi mishi yawa ce da tashin hankali. Ya rasa ta inda ya rage da mutane suke tab'a shi haka, dan haka ya shiga dakin shi tare da tsayawa yana kallon madubi, kallon kirjin shi yayi wanda yake dauke da ciwon wancar yarinyar, ya jima yana kallon yadda gurin yake sannan ya cire rigar shi ya dubi ciwon ba wani babba bane. Amma kuma yana d'an jin zafin shi a jikin shi kad'an kad'an, wanka yayi tare da sake gyara ciwon,kafin ya koma dakin shi ya shirya,tsaf. ---ina karatu naji kamshin turaren shi,dan haka sai na kasa fahimtar abinda nake karantawa,dan ina jin kaifin idanun shi a kaina, nutsuwa nayi na cigaba da karatuna har ya gaji ya bar gurin, yana barin gurin ina sauke ajiyar zuciya, sannan na cigaba da karatun kusan karfe shida na rufe karatun, sannan na fito niman abinda zanyi buda baki dashi, tashi nayi tare da shiga kitchen ɗin na shiga girki ina gamawa na juye tare da jerawa a tire, na shiga dakina dashi. Sannan na fita daga dakin na nufi babban maajiyin abinci na duba ajiyayyen ya'yan itacce, na hauro sama, ina kallon shi ya harde cikin bakakken kaya, kallon inda yake banyi ba, sannan na shige d'akina, na zauna har lokacin shan ruwa yayi, nasha ruwa. Bayan na idar na nufi ban daki nayi alola, gabatar da sallah nayi sannan na zauna ina azkar har lokacin isha yayi na gabatar tare da sallar tarawee, ina idarwa na kwanta a hankali. Ina kwance naji an rufe kofar dakina ta baya, nasan wulakancin Mehran ne, sai ban damu ba. ~~ Babu wanda ya san kudirin shi, sai dai kuma bayan ya gama sauraron karatunta,yaji bata motsi a cikin dakin, shine ya rufe ta,sannan ya fita daga gidan, ta baya, wato ta tagar dakin shi ta zura igiya ya sauka. Tare da daukar makamai na balai ya shirya a bayan shi, sannan ya nufi cikin dokar dajin da take bayan gidan shi, wato idan ana maganar farauta toh abinda Mehran yayi kenan, domin abinda yake zargi ne ya faru,mutanen da baya tsammanin zai same su a kusa su ya samu. Cikin ban mamaki ya dira musu, suna tsaka da masha'a da yan matan da suka ce shi ya turo du dauke su. Razane suka mike tare da kallon shi.kowannen su ya dauki makami. Bai shirya musu ba dan haka ya sunkuyar da kan shi tare da raba kafar shi d'aya da kasa, yayi wata irin tsayuwa me mugun daukar hankali, irin ta sarakuna, cikin ihu da karaji suka nufe su. Nan suka falle da wani irin azabben yaki tare da kaiwa juna sara da suka, takobin shi ce ta fadi ya kuma saka hannun shi ya zaro Gatari hannun biyu, yake kai musu sara da ita. Idan ran shi ya b'aci ko gaban shi baya gani, d'an batalikin nan cikin rashin mutunci yayi ta girbe halittun Allah, yana gamawa ya jibge su ya zauna akan su. Kadawar Bishiya da saukar ganyayyeki yasa shi fahimtar akwai wani gumurzun a gaban shi,mahayi ya gani tare da dokin shi, dan haka bai shirya ba. Dan ya rena mahayin, cikin Sa'a kuwa mahayin ya dauki kwari da bakar shi ya saita daidai kirjin shi, ya sake mishi kwarin cikin wani irin zafin nama, ya shiga kare kanshi, yana falfalawa da gudu, wato yana tun karar mahayin tare da kare kan shi da gatarin hannun shi, cikin Sa'a kuwa aka same shi a gefen cikin shi,da sauri ya kabe amma ina bakin kwarin ya shiga, dan haka yabi mahayin tare da wurga mishi gatarin hannun shi, aikuwa suka fadi can da dokin, sosai, ji yayi kamar wani abu yana yawo a jikin shi, dan haka ya juya da wani irin azabben sauri ya koma gurin da aka yi yakin, ya hango wani akan doki yana gudu. Dan haka ya xari wani karamin wukar shi ya wurgawa mutumin, rigib ya zube daga kan dokin, sannan ya isa gurin Mutumin ya d'aga shi tare da jan linzamin dokin ya daure shi tam, sannan ya nufi tantin dakarun bokin yaga yan mata birjin an gama lalata musu rayuwa, A hankali ya fito daga dakin tare da zama, yana jin jikin shi yana kuma ɗaukar bakon yanayin da yake ji kamar daga ciwon da aka harba shi ne. Dan haƙa ya mike tare da umartan yaran su tashi su gyara jikin su, shi Ceton su yazo yi. A hankali suka gyara kan su, shi kuma ya haura doki, bai ce musu kala ba suka shiga gaba bin bayan su, dan baya son wani abu ya kuma samun al'ummar shi bayan haka. Mutumin da ya kama yana jan shi, wanda ya harbe shi ne dai bai samu nasarar kama shi ba, har bakin kofar masarautan suka isa, bugawa yayi Dakarun da suke tsaron kofar suka ce. "Waye?" "Sultan Aamaan Abdus Samad Aamaan, Mehran!" Jikin su na rawa suka bude kofar, da sauri suka bude kofar, kallon su yayi yana ganin su biyu biyu, bai ce musu kala ba ya wuce. Cikin karfin hali yayi ta taka Yan matan kofar gidajen su, sannan ya juya dakyar ya nufi cikin gidan sarautar, yana jan mutumin nan. A lokacin karfe uku saura da karfi ya kai shi har cikin fadar, ya daure shi da wata makata idan aka tab'a tabbas mutumin nan ya fado mutuwa zai yi dan haka ya shirya mugunta kala kala, sanan ya nufi castle din shi da sauri, dakyar yake bubuga kofar gidan, Rakshan da Fudail suka zo suka bude mishi kofar, a hankali ya shige yana rike cikin shi. Bai tsaya ba, sai kofar dakin Ikram. Jingina yayi tare da bude kofar d'akin. Ina tsaye dan tunda suka shigo wajen karfe ɗaya suka duba baya nan hankalin su yaso tashi sanin cewa yana fitar dare yasa Rakshan share shi, ganin har karfe biyu bai dawo bane yasa su shiga damuwa dan duk suna kofar babban falon kasa. Bude kofar yayi tare da faduwa a jikina, muka zube tare, cikin wani irin fisgar numfashin sa, yace min. "Sun harbe Ni!" Ya kai hannun shi saman cikin shi, tare da riko hannuna ya kai kan ciwon, wani irin tsoro ne ya kamani, ban san lokacin da na fasa ihu ba, tare da kiran su Darakshan da Fudail, sune suka kawo mishi dauki tare da ɗaukar shi zasu fitar dashi. "Karku kai ni ko ina? Anan zanyi jinya." Ya nuna musu saman gadon da nake kwana. "Mehran!" "Nace anan!" Ya daka musu tsawa, a sanyayye suka kwantar dashi tare da kallo na. "Ikram! Ko zaki fita ki koma falon da." "Ita zata yi jinya na!" Ya faɗa musu kai tsaye, "Amma Mehran idan Sultanah Hoyam tazo." Tari ya fara me dauke da wani irin koren amai,da sauri muka zuba mishi ido, d'aga rigan shi Fudail yayi sai ga tsinin kwarin, bai tab'a ba, suka fita shi da Rakshan, bayan fitar su, ne kiran Lingesa, kawai sai ganin wani mutum da bakakken kaya muka yi a bakin kofar dakina. Tashi yayi dukda yana ganin dishi dishi, bai hana. Shi daukar gatarin da yake k'ugun shi, da gudu mutumin yayo kan shi, fisge gatarin hannun shi nayi na tari mutumin, muka fada wani azazzaben yaki a cikin dakin, ban tab'a sanin wahalar da yake bani koya min yaki yake ba, sai yanzun da abin ya kama nayi.har kamar zan fada kan shi, a hankali ya mike tare da tsayawa a bayana,. Lokacin da mutumin ya kai min wani gawurtaccen sara, na tafi zan fad'i. Hannun shi ya kai tare da dafe cikina, da sauri na juya ina kallon shi. "Kuyi irin abinda nake yi!" A hankali ya maida ni kirjin shi, tare da rike daya hannun nawa tare da nuna mutumin da takobi, kafin yayi mata alamar ta matso, cikin kwarewa da iyawa yake koya min fada tare dashi, dan ya fahimci mutumin da muke yaki dashi.tsohon kashi ne, shi yasa ya hada karfin shi kwarewa ta, muka shiga wani irin fada me mugun cin rai. Tunda muka fara, yake cije wa, idan abin ya ciyo shi sai dai naji kanshi a kan wuyana, tare da matse ni a jikin shi, idan ya sake shi kuma mu Cigaba da bagwaza fadan. Cikin hukuncin Allah ya daura yakin zuwa wani na daban,wato ana amfani da makami ana amfani da hannun ko kafa, kafin kace kwabo mun.hada mata zafi jin ana shigowa yasa ta buga wani abu abu dakin yayi mugun duhu. Tari muke har suka shigo mana, zuɓewa yayi a bayana, tare da sauke wata irin numfashi, da sauri suka kwantar dashi, aka fara bashi kulawar gaggawa. Ni kuma na shiga kwashe duk abinda aka fasa ina gyara dakin. Ina gamawa, na fita a daren dai dakina ban rintsa ba, har gari ya waye dan masu kula da lafiyar shi basu tafi ba, haka ma Lingesa bai fita ba. Haka suka kwana suna fama dashi, kasa sahoor har lokaci ya wuce, ina zaune shigowar Sultanah Hoyame ne ya sani mukewa yana kallon ta, bata bi ta kai na ba, ta shige dakin. Tana ihu fitar da ita aka yi, shi kuwa yana kwance kamar gawa. Sun sami nasarar cire kan bakar, sai dai matsalar an yi amfani da mugun guba ne a jikin bakar, wanda a lokaci guda ya canja mishi halittar shi, jikin shi yayi kore shar. Hatta idanun shi kore yayi, dan haka Sultanah Hoyame tace a daga shi daga dakin a maida shi dakin shi, ko kuma shsshin ta. "Kiyi hakuri yace ko mutuwa zai kar a fitar da shi daga dakin nan!" Cikin faduwar gaba take kallon shi, Zuciyarta yana zullumi. "Akan wani dalili?" "Haka kawai!" Da sauri ta bar dakin tare isowa inda nake sallah, dukda tasan cewa babu kyau tayi yada zata katse mata sallah da tayi, cikin jin haushi, take kallon ta. Ina idarwa Naji an rufe ni da duka tana tsine min. "Makira Tsinanniyar yarinya, meye kika mishi yace a wancan kaskantacciyar dakin zai zauna, meye kika mishi da ya zab'e ki sama da sauran matan da nake tallata miki!" Janya ake tana ihu tare da cewa sai ta kashe ni, babu digon kwalla a idanuna Asalima kallon ta nake, murmushi nayi mata, Fudail yace mata. "Sultanah babu abinda yake tsakanin su fa, kawai yafi son zama a dakin ne." Fisge rikon da suka mata tayi,sannan tace. "Ki gaggauta warware abinda kika mishi, idan ba haka ba zan kashe ki. Kuma na haramta miki sallah a cikin wannan gidan." Da sauri na d'ago kai ina kallonta, anan ne nace mata. "Koda kuka fanshe ni a baiwa baku gaya min bazan yi ibada ta ba, dan haka rayuwata fansa ce ga addina." "Ku fita da ita! Ku azabtar da ita sama da furucin bakinta." Haka suka kasa koda motsi ne, suna kallonta. "Sultanah babu wanda ya isa hukunta Ikram dan tana karkashin Kulawar Sultan Mehran ce!" Aikuwa ta birkice musu da fada, akan me zasu ki amincewa a fita dani. Haka ta Karachi masifarta tare da fita daga gidan baki daya,.tun jiya ake abu daya ba a sami makarin karya gubar ba, haka aka shiga niman masu maganin gargajiya. A lokacin gubar ta fara fadar da jikin shi, dan haka suka yi ta fama dashi. Wunin ranar an shigo da masu maganin gargajiya sun kai hamsin, gashi an sanar da masarautar da garin baki daya, haka ma iyayen yan matan da aka kwashe sun gayawa Iyayen su ba Sultan Mehran bane, wasu ne da wani dan cikin masarautan, dan hakan iyayen su suka shiga addu'a Allah ya tashi kafad'ar shi, domin kuwa a gurin ceton su ne aka harbe shi.. Littafin nan na kuɗi ne. Allah ya jikan Iyayena #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 Book 1 Mai_Dambu BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM Page 27 Daga cikin mutanen da aka tafi da yaran su, sunyi kokarin taimakawa da gudummawar su, na magani amma babu nasara, asalima sai muke ga babu wani canji, Dan haka na kalli Lingesa nace Mishi. "Zan sami Hulba da habbatul saudat! Sai y'ay'an zaitun!" "Zaki samu!" Muka juya zamu fita, finciko Ni, Sultanah Hoyame tayi tare da cewa. "Idan Sultan MEHRAN ya mutu gawarki ba za'a same ta bama balle ke din." Ban kulata ba, muka fita, cikin gaggawa nasa aka nika min hulbar, sannan na zuba mata ruwan zafi na sannan na kuma dafa wani hulban da Habbatul saudat tare da garin zaitun, na zuba a wani ƙaramin buta, sannan muka nufi dakin shi, muna zuwa. Ka bude min cikin shi na zuba kwab'abben hulban sannan na saka suka d'aga shi yasha. Sannan muka koma gefe muna jiran abinda Allah zai yi, kasa nutsuwa nayi na nufi waje nayi Alola tare da gabatar da sallah, sannan na dawo bakina dauke da kirariwa Ubangiji na. Sun bani damar nan da kwana biyu idan babu canji zasu nimo wani taimakon. Dake ana ta jaraba masu maganin, muna gurin Sai ga Narmin da wata matashiyar budurwa, cikin wani irin shiga tazo duba shi. Kus-kus suka yi da Sultanah da Narmin sannan ta kalle mu, kafin tace mana. "Zaku iya bata guri zata yi aikinta." Kallon ta nayi haka kawai naji raina bai kwanta da ita ba, juyawa muka yi zamu fita sannan na juya na kalle ta, sam bata da gaskiya ko na miskala zarra, haka muka fita ban san me suka yi da Sultanah Hoyam ba itama ta fito. Tunda suka kawo me maganin nan bana ce ba, amma jikin Mehran babu yadda yake, kullum zata zo da safe, zata zo da dare. Wai tana bashi magani. Haka kawai na shiga dakin tare da d'aga ciwon amadadin gurin ya kame sai ma ya kama ci kamar ana tab'a shi, dan haka bayan tafiyar da dare, kawai na fita har shsshin bayi na samo lalle da kashin shanu, sai Hulba da Habbatul saudat da zaitun. Na saka na hada tare da zuba Mishi ruwan zam-zam wanda na samu a gurin Narmin, sannan nazo na kwab'a na zuba a gurin ciwon. Idan akwai bakin sihiri sanadin kashin shanuwan nan zai nuna, idan kuma guba ce zata motar gurin, idan kuma dajine ma zai nuna alamar shi, dan haka ina sakawa na tsaya a dakin har asuba na tashi nayi sahoor, sannan na duba ciwon, wasu irin tsutsa suka cika saman maganin, fita nayi na kira Fudail yazo muka kwashe tass, sannan yace min. "Me ya faru?" "Kwashe maganin wancan matar nayi, sannan na saka mishi wanda nagada a gurin mahaifina, Insha Allah zuwa gobe da yamma ciwon zai kame, sai dai ina son son Allah a hanata shigowa domin kuwa." "Baki da lafiya! Ba zai yiwu ba, kawai ki kyale ta tayi abinda taga zata iya! Kema kiyi wanda zaki iya. Bana son kusancin ku yana." Rike k'uguna nayi tare da sauke gwaron numfashi sannan nace mata. "Baka da lissafi! Taya ina ganin tana cutar shi zan." Fisgo ni yayi tare da Hadani da bangon dakin, yana huci duk kowani dakika ji nake kamar zuciyata zata buga idan na fahimci yadda kike kai Gwauro ki kai mari, a gaban Mehran ji nake kamar na kashe kowa na hana shi ganin ki. Me yasa ba zaki Fahimci yadda zuciyata take kaunark..." Girgiza kai nayi wani irin kuka yason taso min, na shiga cewa. "Zuciyarka bata maka adalci ba, bata maka adalci ba, bata maka adalci ba, tuntuni ina da wanda nake kare kaina domin shi, kabawa zuciyarka hakuri akwai wanda yayi dashe a cikin tawa, bana jin har abada zan iya samun sama dashi don Allah ka rabu dani." Na kwace hannuna tare da juyawa na fita daga d'akin, wani lungu na shiga tare da tsugunawa na fashe da kuka, sama da yadda nake jin zuciyata take min, me yasa nake fuskarta wannan matsalar?,shi me yasa maza suke kowa min farmaki da tallar kaunar su? Shin Ni daya ce mace ko kuma akwai wasu matan da su ba zasu je gare su ba? Sai da nayi kuka na koshi sannan na fito, zuwa dakin. Na shiga hada ruwan zafi ina goge mishi jiki tare da shafa mishi mai, da turaren bakhoor, sannan na samu na tura shi gefe tare da gyara inda yake kwance, na shiga gyara d'akin. Ina gamawa matar nan tana sammakon shigowa. Wani irin kallon kallo muk'ewa juna, ido cikin ido. Zata wuce na tsare hanyar ta. "Ina da abinyi baiwa!" Takowa nayi gabanta tare da kallon cikin idanun ta, sannan nace mata. "Ki kirani koma meye! Ban damu ba, sabida bani da ciwo a raina da rayuwata sai d'an kalilin, kawai ba zan iya baki damar ki cigaba da illata lafiyar shi bane, Ni mace ce haka bazan tab'a son ganin an wulakanta ki ba, amma kika sake dakarun Samaind suka san kina zuba mishi guda da matsatsaku a jikin shi domin ya mutu." Wani irin murmushi nayi mata irin na gefen bakin nan, sanan na nuna mata hanya,alamar ta fita tun muna sheda junan mu. Zare takobin ta tayi, nayi maza na kai karamin wukar da yake kwaibinta da na zare wuyarta. "Wani irin halacci yayi miki da kike kaunar kare lafiyar shi?" Ta tambaye ni tana kallon idanuna. Murmushi nayi mata sannan nace. "Iya tsare kimata ya ishe ni na tsare lafiyar shi!" Murmushi tayi sannan tace min. "Ina jiye miki tausayin rayuwar da zaki fuskanta, ba zan kyale shi ba. Amma hango halaccin dake kwayar idanun ki yasa ni zan d'aga mishi kafa, sai na kuma dawowa." Ta juya bata kuma cewa kome ba, tun daga ranar na cigaba da kula da lafiyar shi. Ina kuma bashi maganin da nake hada mishi. A hankali jikin shi ya fara washewa. Sai da muka shafe kwanaki goma sha biyar, yana kwace amma kuma ana ganin canji, mahaifiyar shi ma ba laifi, jikin shi yana motsawa. Sai dai rashin mutunci yana nan babu abinda ya sauya. Sai dai wani Iskancin da yake min. Idan ina goge jikin shi. Wato alkalamin shi mik'ewa take tsaye, ban tab'a lura da haka ba, sai wani rana da nazo goge mishi maran shi, dake da ruwan zafi nake goge mishi jikin, ina matse farin tsumar a saman ruwan na saka a kan cikin shi tare da gogawa tare da kaiwa saman maran shi, cin karo nayi da abu a tsaye ta rigar shi. Da sauri na kalle shi. Idanun shi lumshe, yana sauke wata boyayyen ajiyar zuciya. Ina ganin yadda jikin shi yake d'an daukar rawa. Da sauri na cire hannun daga gurin, harbib iska kawai abin yake. Tsalle nayi na koma gefe, ina kallon shi tare da sunkuyar da kaina kasa, na rasa abinda zan mishi. Kamar yadda nake mishi. A hankali abin ya koma ya kwanta, na cigaba da goge mishi jikin shi. Haka na cigaba da kula dashi har ya fara tashi zaune lokacin ciwon ya warke, idan na kawo mishi abinci yana ci, kallona yake idan yaji ina motsa baki na,ina karatu. Idan nayi shiru kuma sai yayi kwarewar karya. Haka zan taso na kawo mishi ruwa, idan zai karb'a zai hada da hannuna, da sauri nake sake mishi kofin, tare da kallon shi. Mara kirki sai ya wani b'ata rai, kamar ba shi ba, haka zan zare hannuna kai na a sunkuye, baya kaunar yaga bana kusa dashi yanzun zai fara gyaran murya. Har sai na leka d'akin. ~~ Oman Kallon shi take daga nesa, gyara tsayuwa tayi tana kallon shi, gyara gashinta da yake gaban goshinta. "Unaiza wancan waye ne? Yau kwana uku ina kallon shi!" "Almirah Azizatul Nissah, ai yazo niman Baiwa Ikram ce, har sun hadu da Sultan Abrad. Yanzun ya fara aiki a masarautan nan ne domin ya cika wa'adin da zata cika shekara daya." Fuskarta ne ya nuna rashin jin dadi akan labarin da Unaiza ta bata, ta juya a hankali sannan ta kuma kallon shi tace. "Ki shirya mana zama dashi." ---- Waiwaye... Kwanan su Noman tara suka iso Oman, Dakyar suka sami ganin Nawwas, sannan Ya Ra'ess ya gabatar da Noman ga Nawwas da kuma abinda ya kawo shi, kallon shi Noman yayi sannan ya dauke kan shi. "Kace kazo anan niman Ikram? Meye alakarka da ita?"" "Kanwata ce" ya bashi amsa a takaice fuskar shi babu walwala ko alamar wasa. Gyada kai yayi sannan ya dauke kanshi daga Noman yace. "Toh zan kai ka ga Abrad, idan ya amince sai ku tattauna." Daga haka suka juya suka fita tare, har fadar Sultan Abrad, nan suka tattauna har da dalilin da yasa aka fito da ita, da kuma Mutuwar Airan. Jikin su yayi masifar sanyi, asalima dukkan su uku sun ji tausayin ta da kumar kaunarta a ransu, gefe guda Nawwas har da kishin Abrad, sabida yana da yakinin yana kaunarta har yau. Sun tattauna tare da bawa Noman daman ya zauna nan da wata hudu masu zuwa Insha Allah zasu dawo da ita. Ga kuma Almirah Azizatul Nissah tana kokarin sako kai cikin rayuwa shi. ~~ SAMAIND Masu iya magana suka ce lafiya uwar jiki babu me fushi dake, haka ta kasance akan Sultan Mehran, yau dai da wani irin yanayi ya tashi, dake ana mishi wanka Fudail, tsakanin shi da Allah ya b'ata rai baya son wankar su, sai dai nice zan tashi na shiga na mishi. "Idan nice zan maka wanka kana balagagge kace na maka wanka toh karka yi ka zauna da dattin ka waye zai damu kai ne zaka damu." Idanun shi lumshe kamar baya d'akin asalima gyara kwanciyar shi nayi, ina kallon shi abinshi tana ta Iskanci, a raina nace. *_Wannan mutumin bai da kunya! Sam tirr_* "Idan kin gama zagina sai mu shiga ki min" kallon shi nayi bakina a sake, cike da al'ajabi. Shiga ban dakin nayi tare da hada wani ruwan, juyawa da zan yi na same shi a tsaye da wani asuwaki yana goge bakin shi, a hankali nayi kasa da kai na, ina kallon kasa. Takowa yayi gaba na, tare da d'aga min hannun shi, wayyo Allah na. Shi wannan bai da kunya sam, kauda kai nayi na fara kokarin cire mishi, amma na kasa sabida ya fini tsayi, kallon shi, ina haki. Duk da yau na tashi bana azumi amma kuma bana jin dadin jikina sabida ciwon maran da nake fama dashi. Tawowa yayi gabana kafar zai fada kai na, na tare shi muka jingina da bango. "Me...h...ran. ka cire ka..ya.n ma..na!" Nayi maganar ararrabe muryana yana rawa, a hankali ya zare rigar, fuskar shi a murtuke. Kallon kirjin shi nayi wanda yake cike da gargasa, wani irin kyamar shi naji kamar zan yi amai, sororo yayi yana kallona tare da dauke idanun shi a kaina, gashi dai alamar karfafan namiji ne dan yafi Abrad da Noman cikar halitta, hannun shi yakai keyar shi bayan ya haɗa su ya miko min kwarjallen shi na warware mishi. Kamar wacce aka watsawa ruwan sanyi kalau, jikina ya fara karkarwa. Komawa yayi ya jingina da Kofar. "Yanzun don Allah ba zaka iya taimakawa kanka ba sai na tab'a ka, bayan haramun ne tunda ki ba muharamman ka bace" Na fada mishi haka ina kuka kamar wacce yace min zai min wani abu, jikin shine yayi sanyi musamman yadda ya ga jikina yana rawa, alamar dai na gama firgita da shi. A hankali ya juya min baya tare da cire kwarjallen shi, nima juya mishi baya nayi, gashi na tsare mishi inda zai wuce dan haka ya tsaya a bayana, shi dayan shi yana jiran na matsa mishi. Jin haka jin motsin shi, ashe zanyi mugun gani ne na juya, kawai sai ganin abu nayi. "Innalillahi wa'inna ilaihi rajioun!" Na fada da karfi tare da juyawa da baya zan fada cikin ruwan wankan yayi maza ya riko wuyar rigana. Take ya haɗa da tausassan mangwaron kirjina, da sauri muka kalli...... 🤔😏Irin naka salon kenan.... Allah kajikan iyayena Littafin nan na kuɗi ne #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 Book 1 Mai_Dambu BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM Page 28 A hankali na sauke idanuna daga cikin nashi cikin matsanancin kunya, jikina yana kuma rawa. Dake Allah ya taimake ni muna daura wani fallen yadi a kirjin mu, yadda babu abinda zai sami nonuwar, a Sannun yake saussauta rikon har Allah ya taimaka ya sake ni, kawai na kuma tafiya zan fadi Yasaka hannun shi ta k'uguna. Hannu na duk biyu suna kirjin shi a dunkule na rufe idanuna, ina sauke ajiyar zuciya. Cikin mutuwar jiki ya janye Ni daga jikin shi ya shiga wankar shi. Kin yin kome yayi ya tsaya yana jirana na mishi. A Sannun na ja kafana zuwa gare shi ina me shafa wata ruwan sabulun wanka na, na fara goga mishi da wata soso irin auduga nan, ina mishi ina me dauke kai na, har na kammala mishi tare da ajiye sosan na shigo dakin na dauki Mayafi sabuwa kal na koma na kai mishi, sai da ya gama b'ata min rai da lokaci sannan ya amsa daga hannuna. Wato ina ga Mehran so yake na dauke shi ko ya koma jinjiri ina ina ina dashi, haka Ni daya nayi ta masifa a rai na, kamar zan dake shi. Yana gama mulkin shi ya fito, dan har na riga shi fitowa, ina zan iya rayuwa da mutumin da yake abu kamar kwai ya fashe mishi a cikin shi. Bayan na gama na fita sami baki suna jiran shi, dawowa nayi ba gaya mishi. Takowa yayi gaba na, yana zuwa ina matsawa har muka kure bangon d'akin. Hannun shi naji a kwaib'ina, da sauri na kai mishi bugu yayi maza ya tare, na kuma buge hannun ya tare, kallon kwayar idanuna yayi, wani irin budewa kwayar idanun shi yake, ban tab'a sanin cewa akwai abinda zai haifar min da nutsuwa ba sai da na kalli cikin idanun shi, har wani irin budewa dan bakin tsakiyar idanun shi yake tare da fitar da wani shegen maiko, ji nayi kafaffuna basu iya daukata, kirjina kuwa kamar ana buga min wani abu, ji nayi numfashina ina kokawa dashi, dan haka ban san lokacin da na zube a kirjin shi ba, mayafin da yake daure ne a k'ugun shi suka nemi zuɓewa kasa, cizon lebbena shi yayi cikin wani irin yanayi da bai san yana tare da shi ba, sai da na fada jikin shi, dan tsabar mugunta, janye jikin shi yayi na zube a gurin, sannan ya duba dakin babu wani abu sai alkyabar shi da Fudail ya dauko mishi, yafawa yayi sannan ya fito. Mik'ewa suka yi tare da kallon shi. "Sultan Mehran ya jikinka?" Niman guri yayi tare da zama yana kallon gefen shi wanda yake dauke da kayan ciye ciye, a hankali ya motsa bakin shi kamar me fama da ciwon baki yace. "Da sauki!" Kallon shi suka yi, sannan suka sunkuyar da kansu. Gyaran murya Amir Hood da Mir Umdatuddawla yace. "Sultan Aamaan Abdus Samad, mun tawo baki daya ne mu baka hakuri da!" D'aga musu hannu yayi sannan ya kalle su daya bayan daya sannan nuna musu kofar fita, kan shi kwance saman matashin kujeran. A hankali suka yi ta mik'ewa daya bayan daya, suna fita, karshe dai ya rage shi daya a falon, fitowa nayi ina ƙoƙarin shiga kitchen, bin bayana yayi da ido, ganin yadda na b'ata kayana da jini ya sashi dauke kai, bai ce min kome ba, har na gama abinda zan yi na fito na koma dakin, tasowa yayi tare da shigowa, wai zai gaya min abinda ya faru da jikina shine ya tako har inda nake tsaye, sai ji nayi an wurgani gado, na tashi da sauri. Ya kuma mai dani tare da zama a bakin gadon ya janyo kafana, a hankali ya ture ni ta daya gefen kyakyawan zanin gadon ne ya b'aci da jini, yana ganin na Fahimci haka ya mike tare da barin d'akin. Saka kai na nayi a tsakanin cinyoyina, na rufe idanuna sa karfin tsiya. Ina sauke ajiyar zuciya. Tashi nayi na shiga wanka nayi sosai sannan na gyara jikina, ina gamawa na taso tare da nufar kitchen na daura mishi gasheshen nama sai madara da nayi gyaran shi. Na kawo mishi. Tunda na kai dakin yana zaune tare da kallon yadda na gyara gadon tsaf, zama yayi ya fara cin abincin a hankali. Tunda na gama ya nutsu na fita daga dakin. ~~ Tunda Sultanah Hoyam taga ya sami sauki, ta shiga aiko mishi yan mata tsalla-tsalla. Wai suzo su dauke mishi kewa, sai dai abinda ka kasa Fahimta akan shi yan matan baya barin su, su shiga min dakin, sai dai kuma zai fito falo dasu ya zare kayan shi ya kwanta suna mishi tausa, dake Allah ya taimaka bana jimawa a cikin hailata, kwana hudu ne, lokacin ana sallah saura kwanaki ƙalilan za ayi. Bana son kwanakin tahajjun ya wuce ni ne, ranar da nayi tsarki ranar na fara sallah tahajju, idan ina karatu bawan Allah nan dawowa yake falon ya zauna har sai na idar sannan yake komawa dakin shi, sake kwanakin azumi zanyi dan haka yana ganin ina sahoor, bai ce min kome ba, sai gyara kwanciyar shi da yayi tare da lumshe idanun shi, yana son kyawawan dabi'unta. Ibadarta ya zarta tunanin shi, tana da kokari akan kome, sai dai matsoraciya ce na kin karawa, yana son mace me kokarin irin na Ikram. Kaf kwanakin da nayi ina ibadana, tare dashi muka yi domin tsakkanin shi da Allah ya saka idanun shi akan ibada na, kasa hakuri yayi tare da kiran Fudail. Shiru yayi tare da kasa cewa kome, sannan.yace mishi. "Kasan wani irin abu yarinyar nan take yi? Shi ba waka ba shi ba hira ba, meye shi? Sannan idan karfe sha biyu da rabi yayi tana wani abu, da d'aga bayanta dama. Haka idan karfe uku da rabi yayi toh ba zata kuma kula Ni ba sai tayi abin, Fudail ina cikin damuwa?" Kasa yayi da kan shi tare da cewa. "Mehran ba kome take ba sai ibada." "IBADA?" Ya tambaye shi tare da kura mishi ido, sannan yace mishi. "Kai kana yi ne?" Gyada mishi kai yayi alamar eh, "Me yasa Ni bana yi?" A dimauce Fudail ya zuba mishi ido, shi kanshi ya hangi firgici da tambayar da yayiwa Fudail din. Shiru yayi a gajiye sannan ya juyawa Fudail baya, yana sauke ajiyar zuciya. "Mehran!" Dakatar dashi yayi, bai kuma magana ba, haka Fudail ya fita, ---- Ina gyaran kifin da Darakshan ya shigo min dashi, akan zan dafawa Mehran, na nutsu bakina yana ambaton sunan Allah, shigowa yayi cikin madafin ya tsaya a kaina, ban d'ago ba amma kuma hakan bai min dadi ba, kasa jurewa nayi ina kallon shi. Kafin nace mishi. "Ko wadanda ba musulmai ba, idan zasu shiga gurin musulmai suna faɗin, Amincin Allah ya tabbata a gare ku. Wai me yasa kake haka ne?" Haka kura min ido yayi, sannan yayi kasa da kanshi, jikin shi a sanyayye ya fita daga cikin madafin, bai zame ko ina ba, sai shsshin Mahaifiyar shi. Kura mata ido yayi cikin wani irin rauni yace mata. "Waye Ni?" "Mehran ban gane ba?" Ta tambaye shi akan tambayar da yayi mata. "Waye Ni?" Ya kuma tambayar ta, "Ka nutsu ka min bayani me kake nufi da haka?" Hawaye ne ya shiga sauka daga cikin idanun shi yana kallonta, bakin shi na rawa, yace mata. "Me yasa bana sallah?" Wani irin bugu zuciyarta yayi cikin tashin hankali a zuciyarta tace. *Kai Na shiga Uku na lalace! Wannan shaidaniyar Yarinyar sai ta t lalata min rayuwa Ya zanyi?* "Yanzun Mehran akan sallah ne kazo ka tsitsiye Ni?" Ta faɗa fuskarta a daure, tare da niman guri ta zauna, sannan tace mishi. "Zauna muyi tsayayyen magana." Ba musu ya zauna, cikin hikima da dabara ta shiga kawo mishi abinda ba shi bane, tare da gaya mishi, wacece Ikram sannan ta gaya mishi ai surkulle take. Dake Uwa ce, kuma tana da hangen nesa dan haka tayi ta b'ata Ikram a hankali cikin dabara sai da ta cusa mishi rashin yarda akan Ikram kuma ta zauna ta gaya mishi abinda yasa take jin ba dad'i akan zamanta a shashin sa, dan haka ya kore ta, idan ba haka ba zata kawo mishi rudani. Sai dai kuma kasa yarda yayi daga abinda ya faɗa yana kallonta cikin nauyin harshe yace mata. "Fudail yana yi" "Toh munafukai ne, kuma suna son ganin bayan ka ne, idan baka manta ba, lokacin da baka da lafiya haka suka yi ta cin Amanar ka, idan kuma karya ne ka tambayi Darakshan Fudail da Ikram suna mummunar alaƙa. Yanzun ma idan da zaka shiga gidan a bazata zaka same su." Ita lallai dole so take ta raba shi da Ikram, musamman da Darakshan ya kawo mata tsegumin Fudail yana son Ikram kuma yayi alwashin ko za a kashe shi ba zai tab'a barinta ba. Kurawa Mahaifiyar shi ido yayi wanda ya zaro su kamar zasu diro kasa,ji yaƙe kan shi yana wani irin yatsuna kamar an zuba mishi tsutsa akan shi. Sunkuyar da kai yayi bai ce kome ba. Amma hatta gashin jikin shi a mike suke. Dan haka ya tashi daga inda yake zaune ya saka kai zai fita, tace mishi. "Mehran kayi ƙoƙarin karkade munafukan da suke jikin ka, idan har Fudail yanayin sallah tabbas shi da Ikram bayan ka suke son gani, idan kuma kaki toh ba makawa." "Ina ruwa na?" Ya tambaye ta, cike da mamaki take kallon shi, yadda lokaci guda ya gwaleta, ya sa kai ya fice, idan ka kalle shi sai ya baka mugun tausayi, domin yayi laushi sosai, kuma a iya kan fuskar shi zaka karanci yana cikin tashin hankali da damuwa, duk inda ya gifta gaishe shi ake dakaru na bin bayan shi, cikin nutsuwa. Fuskar shi ma'abociyar kwarjini da haiba ta fito fess, kana ganin shi kaga wanda yake ji da mulki da izza, amma yau jin amintattun shi. Suna ha'intar shi yasa shi jin babu dad'i, ba zai iya kashe Fudail ba haka ba zai iya kashe yarinyar da yake jin dadin sauraron muryan ta ba. Amma tabbas zai iya raba su, cikin sauki zai haramtawa Fudail shiga shashin sa har abada, har ya iso kofar da zata sada shi da falon sama yaji Muryan Ikram. "Kai jinka ina zaune ne anan abisa jin dadin rayuwa ta? Toh ina nan ne dan babu yadda na iya, ina nan ne sabida fansar rayuwar kanwata, ina nan ne domin kanwata. Iya adadin lokacin da na diba ya cika tabbas ko bai zo min ba zan koma mahaifata, Idan masoyina yazo Tabbas ba zaka kuma gani na nan ba." "Amma kuwa wannan masoyin naki sunan shi gawa! Domin wallahi na rantse miki da wanda rayuwata da mutuwata take hanun shi sai na kashe duk wanda ya kuskura ya keta Alfarmar Mehran! Duk wanda ya kuskura yazo nan da sunan yazo daukar ki, bayan kina kasar mulkin Mehran sai na raba kan shi da gangan jikin shi. Dan haka ke mallakin Sultan Aamaan Mehran ce, babu wanda ya isa ya kusanci inda kike balle ya tafi dake k..." Gyaran murya yayi bayan ya shigo falon yana kallon mu, munyi cirko cirko,. Dauke kan shi yayi tare da wuccewa abin shi. Murmushi Fudail yayi tare da sauke wata Boyayyen ajiyar zuciya, tabbas yasan nadan Allah ya mishi baiwar iya fahimtar ana kusa dashi ba da ya tafka kuskuren da ba zai tab'a barin shi ba. Lokacin da Mehran ya iso bakin kofar, yaga alamar wani yana bakin kofar, dan haka bai dakatar da Ikram ba, sai dai shi ya sauya kalaman shi. Fita yayi daga gidan. Burin shi ya cika dama abinda yake son gani kenan Mehran yaji Ikram tana da wanda take so. Tunda ya shiga dakin shi ya kwanta, tashi yayi zubur. Tare da kaiwa da komowa, wato tana da yakinin akwai wanda ya isa ya keta Alfarmar shi yazo ya dauke, ya ga shegen da ya isa ya shigo har sansanin shi ya dauke ta.... Littafin nan na kuɗi ne. Allah ya jikan Iyayena #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 Book 1 Mai_Dambu BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM Yadda yake huci sai ka rantse da Allah, an zo daukarta ne nan kuwa zunzurutun rigima ce kawai yake damun shi. Kamar wanda aka mintsine shi ya fito daga dakin, kitchen ɗin ya nufa tare da kallon bayan ta, yadda yan k'ugun ta da mazaunanta suke juyawa a hankali. Ikram ba ta bata da cikakken halittar jiki, bata cikin jinsin sirarra ko irin lutayen nan. Sannan ba za a kirata ramammiya ba, daidaigwargwado tana da jiki me kyau, musamman k'ugun ta, kirjin ne dai sai a hankali, domin a shafe yake, yan nonuwan kamar na me kirgan dangi. Amma kuma kamar wanda aka dasa su daga kasa, a cike suke tam daga sama ne zaka dauka babu su. Sannan rashin kulawa da abinci me gina jiki ya taimaka matuka gurin boye cikar halittar jikinta, k'ugunta ne zuwa mazaunin ta, kamar wacce aka hura abu ko aka mata dashen shi. Domin idan ka nutsu zaka ga har wani motsawa suke, tunda yake bai tab'a kare mata kallo ba sai yau, bai tab'a ganin mace me diri irin ta ba, wannan halittar shi ya kad'a mishi hankali lokaci guda, had'iye yawu yayi cikin b'acin rai, ya juya tare da barin gurin. Ya ga shegen da ya isa ya shiga mishi iyakar kasar shi domin daukarta. Haka yayi ta aiyanawa a ranshi, dan haka a washi gari ya maida Fudail fada, sannan ita kuma ya zuba ido akanta, yana kallon iya gudun ruwanta. Gefe guda ya dawo da mugun halin shi, idan tayi mishi abu zai kai mata mangari ko ya tad'e ta, ta fadi, wani irin zazzafar k'iyayya ce ta Kuma haihuwar kanta a tsakanin su, wanda ta kai Itama Ikram din ta fara rama abinda yake mata, ai kuwa yace bai iya ji ba, azaba kuwa babu iya ka. Kuma babu halin ta fita ko ina, tana cikin gidan. ---- watan shi takwas da bashi mulki aka fara turo y'ay'an gwamnonin yankunan hudu nan, akan zasu yi zama dashi na tsawon wata hudu idan suka fahimci juna, sannan za ayi bikin su bayan wasu wata hudu masu zuwa, wato wata takwas zasu yi suyi suna nazartan tsarin mulkin ƙasar da yanayin cikin gidan. Dan haka aka shiga kwaskwarimar masarautan baki daya, tare da dawo dashi asalin tsohon shsshin Mahaifin shi. ---- Yau naji a raina ina son bisa sarewan Uwaisul Qarni, dan haka na tafi d'akina bayan na gama abinda zan yi na fara busawa, a hankali duk da bawai ina fahimtar abinda nake busawa ba, amma kuma ina jin wani irin kewa da son kasancewa da yar uwana, ina busawa hawaye na zuba daga idanuna. A hankali dakin ya fara wani irin sanyi da kad'a iska me dad'i,hade da sanyin kamar nadamina. Lumshe idanuna nayi ina kara bisa sarewar, ina kuma yi tare da hango Airan tana dariya tare da gudu da wani dan karamin rago suna gudu a tare. "Barka dai magajiyar sarauta" da sauri na bude idanuna, tare da zuba mishi. Murmushi yayi sannan ya kuma cigaba da tasbihin da yaƙe yi,. Kallon gurin nayi tabbas ina dajin nan ne. "Baba yaushe nazo nan?" Na tambaye shi bayan na koma kusa dashi, dariya yayi min sannan yace min. "Ai kin bisa sarewa kuma Insha Allah zata kawo ki har nan da yardan Ubangiji. Nasan kina cikin kaɗaici bayan kaɗaici, gashi kin fara aikin da ya dace amma kuma kina zubda ladar ki" Kallon shi nayi tare da sake baki sannan nace mishi. "Wani irin aiki na fara kuma na ke zubda la.." "Kin fara ai! Kuma kin gama gina kome a cikin aikin ki, saura ki jira lokacin da Cigaban shi zai zo miki, don Allah ki taimaka ki saka shi ya san waye shi ? Ki taimaka ya san halin da al'ummar kasar shi suke ciki, baki san wani abu ba. Aamaan na biyu sunan yana mulki ne amma ba shi yake mulkin ba wasu ne suke mulkin, Jikata ki taimaka ya san inda yake ya kuma san waye yakewa Hidima. Don Allah ki taimaka. Koda zaki na fuskarta wahala a tare dashi ki tabbatar yasan abinda yake yi, akwai mutumin da ya kama kafin ya kwanta ka jinya, amma an kubutar dashi bayan an fitar dashi sun nemi kashe shi dan kar ya tona musu asiri sai dai Allah bai basu Sa'a ba, guguwar ƙaddara tana zuwa gare ki, don Allah ki tsaya ki bashi kariya." "Baba ka sani a duhu wallahi, duk na rude na kasa fahimtar kome." "Da Sannun zaki fahimci abinda nake nufi, yanzun dai ki taimaka ya fahimci alkibla." Kura mishi ido nayi tare da cewa. "Me yasa sai Ni?" "A duk lokacin da tafiyar dare ta kama fatake, abu uku yake zuwa mishi! Na farko namun daji! Na biyu yan fashi! Uku ina zai saka kafar shi babu hasken farin wata babu fitilar da zata taimaka mishi. Toh dole ya hakura da tafiyar ko ya tsaya ya kwana a gurin ko kuma yayi taradda aradu da fadin kai! Bilqisul Ikram dole ki zame mishi fitilar makafi!" Wallahi duk sai na rud'e tare da zuba mishi ido, ga baki daya na rasa abinda yake nufi, kamar zanyi kuka nace mishi. "Baba don Allah me kake nufi? Don Allah ka min bayani" Dariya yayi sannan yace min. "Ko na miki filla filla ba zaki tab'a yarda ba, sabida rashin adalcin da zuciyarki take miki." --- "Sultanah, har yanzun babu wani abu daga Ikram!" Inji Shairah. Murmushi tayi sannan tace mishi. "Babu wani abu, aikin da na saka ta take min, kuma nasan zata dawo min da Alkhairi nima kuma zan mata kyautar alkhairi." "Mama, don Allah a kashe ta, bana kaunar ta. Bana son ganin ta, wallahi gani nake kamar ba zata." Wani irin kallo Sultanah Fazilatul nisa tayiwa Jasrah, cikin b'acin rai nuna mata hanyar dakin ta, babu musu ta nufi hanyar d'akinta. Babu wanda ya kuma magana, sai ma shiga hankalin su da suka yi, domin har yanzun babu wani sako daga Ikram sai suke ganin kamar zata ci amanar su. --- Jikina wani irin rawa ya dauka tare da jin sanyin ya lullube ni, "Don Allah karka bani abinda ba zan iya dauka ba, wallahi bani da yancin." "Zaki iya tafiya! Domin na gama abinda zan iya miki, taimako gkg yi tare da jahadi." Girgiza mishi kai nayi, zan yi magana na tsinci kai a dakina. Wani irin gumi ne yake karyo min, a hankali na koma na kwanta da baya, ina sauke ajiyar zuciya. Wannan wacce irin ƙaddara ce ta shigo min babu sani na. Bayan yan kwanaki, Mehran zunzurutun rashin yarda ya mai dani Jelar shi, eh toh dai yanzun haka dai tun jiya aka kawo min kaya daga kasar roma, kallon kayan nake wata irin doguwar riga ce, sai kallon kayan nake ina kuma kallon shi, a hankali. Buga min kofar dakina aka yi na mike tare da buɗewa, Rakshan na gani. "Kina b'ata lokaci fa" Gyada mishi kai nayi tare da cewa. "Toh." Sake kofar yayi tare da jirana. .... Ajiyar zuciya ya sauke tare da kurawa wani gurin ido, meke damun shi? Shi kansa bai san lokacin da ya yanke hukuncin bata wakiliyar shi ba. Ya san dai ba zai iya rabuwa da ita ba, shi yasa ya yanke shawarar bata wakiliyar shi, ko mahaifiyar shi bata san cewa zai bawa Ikram wannan muka min ba. Haka kawai yake ji Tabbas akwai matsala a tare da wannan hukuncin da ya zartas, dan haka ya mike a hankali tare da nufar hanyar fita bayan ya shirya tsaf sannan ya bude kofar shi. Hangota yayi tana ta gyara zaman mayafin kayan, tana son zata rufe jikinta, bai ce kome ba ya nufi kofar Darakshan ya bude mishi, yana fita mu ma muka bi bayan shi. Yadda yake tafiya a hankali haka muma muke tafiya a hankali, har muka isa fadar. Na koma bayan kujeran shi na tsaya. Darakshan ya mikawa Magatakardan masarautan wasikar da Sultan din yasa shi ya rubuta juya da dare. _Budaddiyar wasika! Zuwa gare ku. Abisa ka'idar daular nan Sultan yana da ikon sakawa kuma yana da ikon cirewa Dan haka Sultan Aamaan Mehran ya nad'a Bilqisul Ikram Mustapha a matsayin Wakiliyar shi daga yanzu zata fara aikin ta, sannan tana da ikon ta shiga cikin hurumin fada!" Cikin kafuwa suke kallona, tabbas duk yadda aka yi an tab'a kimar masarautan,mik'ewa Amir Hood yayi sannan yace mishi. "Sultan Mehran shin ka tuntubi mahaifiyar ka akan haka?" Kallon shi yayi sannan ya dukar da kan shi. " Toh gaskiya dole ta san wannan al'amarin idan ta kama ayi binciken" "Ita me muqami na biyu a cikin wannan Daular, sai bana nan zata zartas da hukunci idan ina nan bana bukatar kowa yayi min katsalandan akan abinda na saka raina da zuciyata zanyi." Tabbas gaskiya ya faɗa amma kuma tun shudadden zamani aka daina wannan al'adar ta wakiliya, sannan kuma a tsarin daular mahaifiyar shi ita keda ikon zab'a mishi wakiliya, idan kuwa har shi ya zab'o toh ba makawa sai an dakatar da wacce ya zab'a. Dan haka sai basu damu ba dan sun san babu yadda za ayi Ikram ta zauna a cikin su, kiri kiri suka suka ki rantsar da ita akan lallai sai Sultanah Hoyam. D'an aike aka tura ya kira Sultanah Hoyam, koda ta iso ta zauna a kujeran kusa da shi, nan magatakarda yayi mata bayani, kamar farko, juyawa tayi tana kallon shi, sam Mehran baya jin maganar ta, tuntuni taso ya rabu da Ikram amma yaki. Tana zaman lafiyarta zai janyo mata masifa. Ganin yadda ya b'ata rai ne ya saka ta dauke kai sannan tace mishi. "Ita wacce aka bawa muqamin wakiliya, ba jinin sarauta bane dan wakiliya Ni ke da ikon nuna maka ita, dan haka Akwai wacce tafi cancanta a bata muka min ba baiwar ka ba, Jasrah Abdul Mannan Hood, itace ta cancanci zama wakiliyar ka, yau kwana biyar kenan da Amir Hood ya kawo min batunta. Sannan ita kuma Ikram zata iya zama nakusa da wakiliyar ka, hakan na yanke." Kurawa kasa ido yayi, duk sai ya bani tausayi. Taya yana sarki za a ce sai yadda aka yi da shi, wato idan na fahimta mahaifiyar shi itace dai a mulkin. Bai ce kome ba, ya mike zai fita daga fadar, suka dakatar da shi. "Sultan!" Cak ya tsaya tare da lankwasa hannun shi, kallona yayi tare da nuna min hanyar da zata fitar dani, duk sai jikina ya mutu. Kallon Fudail yayi tare da mishi alama da ido, ya rufe kofar, sanan ya tsaya a gaban su. "Sultan Aamaan! Akan me zaka kawo mana bakar fata cikin tsarin mulkin mu? Taya zaka nemi lalata mana tubalin daular mu. Sannan kaskantacciyar baiwa a bata muqami dai dai da na yan majalisan mu?" Inji Mahaifiyar shi, Mir Rahil da yasan halin Mehran shiru yayi, yana jin sauran manyan fadan suna bin bayan Sultanah Hoyam. Shi dai baice ta tafasa ba balle ta kone, dan haka ya cigaba da sunkuyar da kanshi kasa, yana jiran zantuntukar su. Bai tab'a nad'a kowa ba, amma yau da yayi kowa yana jin haushin sa,asalima kamar dama suna cike dashi, gashi lokaci guda Mahaifiyarshi har da ita a cikin masu mishi wannan rashin darajar. Ya shafe awa daya yana sauraron su, idanun shi rufe, kuma yana tsaye akan kafar shi. Dan haka suna ganawa bai ce musu cikanku ba, ya juya tare da barin su nan suna luguden lebbe. Ina tsaye a gaban Madubi, ya shigo min dakina, har na manta rabon shi da ya shigo dan tun bayan azumi da yaji sauki ya koma dakin shi. Yana shigowa ya zauna sharaf tare da zuba min ido, muna kallon juna ta madubi. Janye idanu na nayi sakamakon yadda idanun shi suka fara min siddabarun shi nan dai, kasa Cigaba nayi da kallon shi ina me dauke kai na, a hankali. Tare da yin kasa da kaina. Shi kanshi sauke kan shi yayi tare da ajiyar zuciya, yana cikin damuwa sosai, ban matsa ba a gurin sai wani dabara ce tazo min na fice a hankali na dibo mishi ruwa, na kawo mishi. Kamar jira yake na mika mishi ruwan ya amsa ya kafa kai sai da ya shanye, sannan ya kuma shanyewa. Wurgi yayi sa kofin yana kallona idanun shi yayi jajjur yace min. "Waye Allah?" Littafin nan na kuɗi ne.... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 Book 1 Mai_Dambu BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM Page 30 Da sauri na mike ina kallon shi, sabida tambayar shi yazo min bazata, yadda yake min abu kamar wanda ya sha giya ya sani yin baya, biyo Ni yake fuskar shi tayi jajjur, dan bakin shi ruwan pink sai wani rawa yake, a hankali ya kai ni bango tare da dafe hannun shi daya da bangon, yana kallon fuskana wanda ya ke cike da mamaki. "Ki gaya min waye Allah?" Cikin rawan murya yake maganar. Jan hancin shi yayi tare da cewa. "Ba zaki gaya min bane?" Ya kuma tambaya na, kasa nayi da kaina, tare da cewa. "Allah shine wanda ya halicci samman da kassai, babu abin bautawa da gaskiya sai shi. Shine wanda ya halicci Annabi Adam ya samar da Nana Hauwa'u daga jikin shi. Ubangiji shi ya halarci kome a cikin kwana bakwai, wata rawaya suka ce a cikin kwana shida. Kuma shi yafi cancanta mu bauta mishi." Kai hannun shi yayi saman kai rigar jikina, yaja igiyar gaban rigar, rike hannun shi nayi. "Ubangiji ya halicci Annabawa, kusa dari da goma sha uku, sannan ya zare manzan guda ashirin da biyar, sannan ya basu addinin suyi da'awa shi." Sake fauce hannun shi yayi sannnan ya zare rigar zai fadi kasa na rike hannun shi. "Ubangiji ya aiko Manzon Allah, Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama,cikin kabilar larabawa sabida yawan damuwar da suke me yasa ba a aiko wani daga cikin su ba, domin Yahudawa sun fi yawa a cikin annabawan. Sai gashi ya aiko musu dan uwan su, bakuraishe! Bahshimi, Dattijon kwarai, kuma aminttacen ya zo mana da addinin musulunci. Kafin nan dole idan zaka yi imani da Allah sai ka isa sharudan musulinci. Ubangiji yayi mana gata da ni'ima." Zare igiyar yayi, cikin tashin hankali, na shiga mishi bayani tare da gaya mishi girman musulinci da abinda ya haramta, idanun shi sunyi jajjur, jijjiyar goshin sa sun mik'e. Uwa uba na jikin shi. Wani irin zazzaɓi ne ya rufe shi, kifi kanshi yayi bayan ya sunkuya goshina. Har ina jin zafin jikin shi, ga baki daya ya narke min, gashi ba kadan ba, duk sai na damu da kai na. Kasa mishi kome nayi. Shi a tunanin shi yana rayuwa ne cikin takura ashe akwai babban kalubale da yake ciki. Me yasa Mahaifiyar shi ta kashe mishi rayuwa? Me yasa ta hana shi fahimtar Meye rayuwa? Musamman da yake kuma jin tasirin addinin Musulunci. Kasa fadin kome yayi har na kai shi bakin gadon ya zauna, kasa rabuwa yayi dani, yana rike da hannuna.kanshi a jingine da cikin, wani irin ajiyar zuciya yake saukewa daga lokaci zuwa lokaci, ban san ya ban tausayi ba, sai da na shiga shafa kan shi ina yatsina gashin kanshi sannan na fahimci tausayin shi da yake raina. . A hankali na kawo mishi sharudan musulinci, tare da dokokin su, d'ago kai yayi tare da kallona sannan ya kuma mai da kan shi, ya rungume ni, nasan yana cikin damuwa ne, amma haka kawai Mehran ba zai tab'a rungume ni ba, fahimtar lokacin sallah yayi ne ya sani, janyewa daga jikin shi. Kallon na yayi tare da dauke kan shi, a hankali ya mike yana dafa bango, tab'e baki nayi a raina nace. "Miskilin banza kawai, ya wani kwaso jiki kamar wani abun Arziki akan azumi ranar kamar zai dake ni, yau kuma kaje sun kulla maka tsiya zaka sauke min. Mitseww!" Naja yi tsaki abuna, ban kuma jin zuriyar shi ba, domin iya abincin da na girka na rana yana nan na daren ma bai ci ba, ashe yana can kwance babu lafiya, shirun da nayi yayi yawa ne na tashi dake ban tab'a shiga dakin shi na wannan shashin ba, sai yau. Da sallama na shiga a hankali, kamshin turaren sandal ne ya daki hancina, wannan shashin Narmin ce take shigo da wasu bayi mata guda uku har da Mahlika suke gyara mishi, tunda na shiga na hango shi can tsakiyar gadon, ya dunkule cikin bargo, a hankali na isa ta gefen shi na haura gadon tare da jan bargon na dafa goshin sa. Tab'e baki nayi a raina nace. *Mazaje ana jin jiki* Taba goshin sa nayi tare da gyara mishi kwanciyar shi, a hankali na fita daga dakin na je na sirka ruwan zafi, nazo na taimaka mishi ya rage kayan jikin shi sannan na shiga goge mishi jikin shi tare da dafa goshin sa. Ina gamawa na gyara mishi kwanciyar shi, sannan na fita dama alkama nayi da madara, sau zuma da na saka kaɗan. Yayi kauri kamar me, bai tab'a sha ba, haka na shiga na taimaka mishi ya tashi, na fara bashi yana sha, tare da kallona, har ya kusan shanyewa sai ji muka yi an bankad'e kofar ko alamar sanarwar ana shigowa gurin shi ba yi ba, da sauri na mike zan bar d'akin, ya dawo dani na zauna tare da zuba mata ido ina bashi yana sha. "Ke zoki fita." Rike hannuna yayi tare da dauke kan shi daga gare ta, ina bashi yana kallona a fisge, ganin nima ina son na fitan don haka ya sake ni a sanyayye. Satar kallon shi nayi hankalin shi yana kan hannun shi, amma nuna a zahirin gaskiya Ni yake kallo. Kamar zai zun duma ihu yake bin bayana da ido. "Mehran! Meye alakarka da ita?" Shiru yayi tare da dauke kanshi yana Cigaba da abinda yake yi. "Kana Sonta ne?" Ta tambaye shi a tsawa ce. Nan ma bata samu amsar ba, jikinta a matukar macce ta zauna a kusa dashi tare da rike hannun shi, kwalla na zuba mata. "Mehran me ye tsakanin ku da har ka zabi ka bata matsayi dai dai da ahalin ka " murmushi yayi sannan ya gyara kwanciyar shi tare dauke kan shi daga gareta ta yana me juya mata baya. "Toh tunda babu yau zan watsar da ita wajen masarautan." Tashi yayi zaune yana kallon ta cike da al'ajabi yana hango son kai murarran a tare da ita suke fuska yayi tare da dauke kan shi, sannan yace mata. "Na rantse da Allah dan baki koya min bauta mishi ba, sai na zubda jinin wanda bai ji ba bai gani ba, karki sake wani abu ya same ta domin zan iya daukar kowani kasada amma ban da na tab'a Ikram, Bana sonta ban tab'a jin sonta ba, kawai dai ina mutuntta ne sabida yadda itama take sadaukar da nata rayuwar domin ni." Cike da mamaki tare da tsoron da ya bayyana akan fusakarta ƙarara mikewa tayi tare da gyada kanta, tana kallon shi girgiza kai tayi. Tare da hango iyakar gaskiyar shi a kwaryar idanun shi, tare da kaunar yarinyar da yace baya sonta. Mikewa tayi cikin iko tace mishi. "Toh zaka ajiye mana mulkin ƙasar nan kuwa?" Murmushi yayi cikin nutsuwa yana shafa kanshi sannan ya kwantar kanshi akan matashin sa, a fusace ta ficce daga d'akin. ...... Tana fita bata tsaya wata wata ba, tasaka aka kawo Ikram aka fita da ita, tare toshe mata baki. Tunda aka wuce da ita darul Azab, akayi ta manna mata wuta a jikinta. Duk karfin zuciya da taurin kai sai da nayi ihu tare da kiran shi ina niman dauki shi, sabida hannuna da kafaffuna duk sai da aka kona min su, sannan aka dauke ni zuwa dakin da yake dauke da wasu irin beraye, takowa tayi har cikin ɗakin. Ta saka takalmin ta tana taka min ciwon jikina. "Shekaru ashirin da bakwai ina shirya kome, yar iska a cikin wata bakwai kin lalata min kome! Kice zan zuba miki ido. Shima Mehran lallabashi nake sabida kar ya fahimci manufar da take raina, anan zaki tabbatar har karshen rayuwar ki, kuyi ta barbada mata gishiri kuna azabtar da ita har sai ta mutu. Sanan ku barta da berayen suci namar jikinta har sai ta kare." Haka matar nan tayi tafiyar ta tare da barina a cikin mugun yanayi, wanda ko fahimtar kai na bana yi. Ban san iya adadin lokacin da na dauka ina kwance ba, sai da naji kamar ana caccakar ciwon jikina yasa Ni motsawa, beraye ne suka cika kai na, suna gurguran jikina, ihun da nake yasa su guduwa, tare da niman mafaka, haka nayi ta ihu ina niman dauki. ~~~ Tun kusan rana yake jiran abincin shi babu Ikram babu labarin ta, haka ya sashi fitowa a hankali yana kallon yadda aka cika mishi babban falon shi da yan mata suna ta jiran shi. Ko kallon su bai yi ba ya wuce abin shi d'akinta, yana zuwa ya bude kofar, yaga kome a watse kuskuren da Sultanah tayi kenan, dan tabar mishi alamar cewa daukar Ikram tayi da karfi, da ace ta saka an gyara ko ina babu abinda zai bayyana mishi cewa daukarta aka yi. Juyawa yayi a fusace tare da shiga dakin shi ya shirya cikin kayan yaki, yasan tabbas zata iya sakawa a hana shi fita dan haka ya dauka har da makaman shi. Yana fitowa matan da suke falon suka razana, bai bi ta kansu ba ya fita abun shi. A kofar fita ne ya ga dakaru kusan hamsin. Saka kai yayi zai fita suka hada hanyar kallon su yayi tare da musu alama su bashi hanya suka dauke kansu, dan haka ya zare takobin shi. Babu tausayi a ranshi ko digon imani ya shiga musu wani irin kisar gilla, ko nace kisar kiyashi. Sai da ya karar dasu a cikin dakika dari uku da talatin, sannan ya share jinin da ta b'ata fuskar shi ya saka kai ya fita tare da isa bakin kofar shashin, kallon shi dakarun duka yi yadda jini yake diga daga jikin shi babu musu suka bashi damar wucewa. Nufar hanyar shsshin Sultanah, anan ya same wasu dakarun da ta saka. Murmushin mugunta yayi domin yana ganin kamar ta manta da waye shi. Yasa ta zuba mishi kananun dakaru, gyara tsayuwar shi yayi sannan yace musu. "Kuna da iyalan ku! Dan haka bana son ku rasa rayukan ku a banza" ya fadi haka tare da kallon su. Bashi hanya suka yi dan ya gaya musu gaskiya, yana saka kan shi falon ta ya samu suna ta shagali da mutanen fadar shi. Gyara tsayuwar shi yayi tare da rikon takobin shi ya nufe ta. Tana ganin shi ta mike tana kallon shi, gabanta ya isa tare da wurga mata takobin shi. Yana kallonta. Huci yake kawai amma a ranshi kadai yasan abinda yake ji. " Da na gaya miki cewa karki tab'a ta kin zata ba zan sani bane? Kin zata bazan Fahimci abinda kika aikata bane. Yarinyar da take kokarin akai na kike saka Ni magana akanta, ko? Yarinyar da tunda nake ban tab'a ganin tayi fashin sallah ba. Yarinyar da take kare kanta da addinin ta, kike so ki hallakata. Na rantse da Ubangijin da kika hanani bauta mishi, sai na sare kan duk wanda ya azabtar min da ita." Gaba daya ya haukace musu. Ya gigice musu fada yake tare da musu alƙawarin sai ya sare kawunan mutane, Allah yasa yaga ba daidai ba, kawai ya juya ya bar musu falon. " Dama yarinyar tana ibada har haka ne? Me yasa kuka kai mishi ita?" "Tambaya na kake Amir Hood? Toh Yarka zaka tambaya Fazilatul nissa, itace ta saka aka kawo ta shsshinsa." ...... Yana fita ya nimo Fudail suka nufi darul Azab, suka shiga har karkashin kasa, inda ake azabtar da mutane, ihunta yaji tana niman taimako, ji yaƙe kamar zuciyar shi zata fado haka ya isa bakin kofar, ya saka Gatari ya fasa kofar sannan ta shiga d'akin da yake dauke da mugun duhu. A hankali ya shiga jin yayi tuntube da ita, dan da taji an bude kofar bata kuma ihu ba, bata iya hango na waje haka kuma na waje bai iya hango ka. "Wayyo Allah na!" Na fada lokacin da ya taka min kafana. "Amahh!" Ya kira sunan da nasan dai ba nawa bane. "Amahh kiyi min magana mana." Yayi magana a raunane, "Ba zan kuma barin wani ya cutar da lafiyar ki ba" yadda yayi maganar zaka Fahimci har cikin ranshi yake jin zafin abinda ya faru. Littafin nan na kuɗi ne.. #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 Book 1 Mai_Dambu BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM Page 31 A yadda yake maganar zuciyar shi kamar zata buga, bai san dalilin da yasa yake jin tashin hankalin tun bai ganta ba, jin ana lallubar kafar shi ya sashi maza ya kai hannun shi tare da riko Ni. "Wayyo Mehran ciwo na!" "Amahhh!" Ya kuma kiran sunan da ya rad'a min yau, ban amsa mishi ba, d'aga ni yayi na sake mishi wani irin wahalalliyar kuka, gaba daya ya saka hannun shi ya d'ago Ni, muka fito waje. Jikina da yake kone da wuta babu inda beraye basu ci ba, haka ta riko Ni har waje sosai yana kallona da idanun shi wanda suke kokarin zubda kwallar da ta cika mishi ido yayi sannan ya cincibe ni muka fita daga gidan. Kallon Fudail yayi tare da cewa. "Ina zamu kai ta?" "Madinatul Mah, akwai shugaban su yana jinyar konar wuta." Furza da iskar bakin shi yayi tare da kallon fuskar ta, yace. "Muje!" Keken dokin shi aka kawo mishi ya shigar dani bayan ya taka matakailai din keken, sannan ya badda Umarni a tara mishi dakaru kimananin dubu daya su bi bayan shi shi, kuma tawaga biyu yake bukata. Sannan su tsaya a gaban shi. Sultanah Hoyam da tawagar Fada suka tawo mishi. Yana tsaye, har aka gama tattaro dakarun. "Mehran!" "Fudail ka hado min kayan mu!" "Sultan Aamaan mune sama da kai fa!" "Darakshan da Zunnoon su rike al'amuran har na dawo!" Cike da mamaki suke kallon shi Zunnoon da basu tab'a haduwa ba, asalima baya shiga al'amuran mulkin daular yau shi aka bawa damar ya rike daular baki daya. "Mehran ina magana kana." "Darakshan kar na dawo na sami ba daidai ba, Ka nuna mishi kome." Duk yadda suka so ya saurare su, bai d'aga kai ya kalle su ba. Asalima Fudail yana isowa suka ya shiga keken shi, shi kuma Fudail ya shiga jagorancin bataliyan dakarun baki daya. Suna barin masarautan Amir Hood da Sultanah Hoyam suka nufi haramtacciyar fada, tana sane da duk abinda yake faruwa, dan haka zaune take tana bawa wasu kifaye abinci, suka shigo mata a fusace. "Me kika aikata? Meye alakarki da Yarinyar da kika tura ta?" D'ago kai tayi fuskarta shanye da toka, tace musu. "Maraba da zuwan Munafukan sarari Aminan Boye ga guri ku zauna!" Cike da al'ajabi suke kallonta, a lokaci guda, murmushi tayi sannan tace. "Shairah basu ruwa!" Haka ka kawo musu ruwa da butar shayi, tana Cigaba da watsawa kifi abincin. Tare da kallon su, "Fazilatul nisa meye nufinki? Duk wannan faffutikar da nake sabida ku nake, amma baki gani ba." D'ago kai tayi ta zuba mishi ido, na wani lokaci kafin tace mishi. "Lallai Abba kaso kanka dayawa, koda yake ban ga laifinka ba." "Akan me zaki tura wata runduna jikin D'ana? Meye yayi miki da ba zaki kyale shi ba, nice nayi miki laifi ba Mehran ba." Murmushi Sultanah Fazilatul nisa tayi tare da zubda kwalla. Ta kalli Narjis kwalla na zuba mata. Sunkuyar da kan su, suka yi suna jinjina qarfin hakurin ta,. Karfin sadaukarwanta. Irin abinda tayi ba kowacce mace bace za tayi. Mik'ewa tayi a hankali tare da nufar gaban zanen hoton Sultan Abdus Samad. "Me yasa ka sani aikata abinda ba zan iya dauka ba, me yasa?" Kamar yana jinta take tambayar shi. Goge kwallar kan Fuskar. Juyawa tayi tare da nad'e hannunta a kirjinta. "Kace kana faffutikar ganin ka inganta mana rayuwa? Kace kana yi ne sabida mu? Toh meye ka ke nufi?" Murmushi Hoyam tayi sannan tace mata. "Zama bawa Jasrah wakiliyar Sultan Mehran, sannan Yanzun hakan Zunnoon shine magajin garin nan kafin Mehran ya dawo, don Allah ki bamu hadin kai yarinyar nan ta fita a rayuwar shi." Kallon son kai take musu kiri kiri sun hanata farin cikin ta, sun hanata jin dadin da kowani mutum yake ji, sun tauye mata farin cikin ta, murmushi tayi sannan tace musu. "Bana da ra'ayin kome daga gare ku, Ita kanta Jasrah ku dauke ta, ku tafi da ita, Ikram itace makamina, itace zata bani abinda nake buƙata. Ku kashe ni da rai na ku zata zan zauna a haramtacciyar fada ce, ku binne ki da rayuwata ta ku zata bazan iya tono kai na bane. Har abada babu wannan a tsakanin mu, ku tsimayi jiran wutar fansa wanda zai narka da kowa." "Amma me yasa kika tura mishi mace me addini?" Inji Amir Hood, wato mahaifinta ta, Cak taja ta tsaya, juyawa tayi tana kallon su, kafin ta fashe da dariya, sannan tace musu. "Haka nake son ganin Zakina ya farka daga mummunan barci da aka saka shi, haka nake son ganin Jinin Abdus Samad ya farka daga kawayan da Miyagu suka mishi, da ace kinyi abinda ya dace da har abada ba zan iya shiga tsakanin ba, amma son zuciya yayi miki katuttu, sannan ina sane da abinda yake tafiya kin kama ta kin saka an azabtar da ita,toh kin kyauta ki ji tsoron ranar da zan ficce daga nan, wallahi ki fara gudu kiyi gudu karki tsaya nan kusa. Kai ma ka kiyayye abinda zan zo maka dashi..ba iya kai ba har da sauran mutanen da kuke kula kome dan lalata mishi mulkin shi. Kin koya mishi mugun aiki, Allah ya kawo wacce ta koya mishi aiki na gari, zaki yi danasanin laifin da kika aikata. Kina ji kina gani wannan matsayin da kike na Sultanah zai sauka daga kanki zai koma kan wata.." Tana gama gaya musu haka ta juya abinda ta barsu a gurin, tun da ta shiga dakinta take kuka, wiwi sabida biyan buƙatar wasu ta sadaukar da rayuwar ta,ta kuntattawa kanta da abinda take so. Ta lalata farin cikin ta, da hannunta. Wani irin kuka take lokaci guda, Allah ya kawo mata mai ceto sai dai bata son ta zama butulu, bata son ta butulcewa Ikram bata son ta cutar da ita, idan ta dawo zata sallame ta kawai, ba zai yiwu saboda biyan buƙatar ta yar mutane ta rasa rayuwar ta, ba. Ita zata fuskanci GOBEN ta, zata kuma Cigaba da zama har ranar da zanen Qaddara ta zai goge, zata zama me yanci kamar yadda kowa yake dashi amma ba zata bari su salwantar mata da yarinyar ba, duk da wata shashi da zuciyar ta yana bata wasu abubuwa na daban. ~~~ Tafiyar wuni guda ne gashi basu fito ba, sai kusan la'asar suka fita dan haka basu shiga garin ba sai ana sallah magarib. Tun kafin su shiga garin aka sanar da shugaban su, ga mayakan SAMAIND nan sun tunkaro garin, cikin kaduwa da tashin hankalin ya kalli Alimah yana huci sannan yace. "Karki yarda na fahimci kina da hannun a zuwan su." Cikin tsananin Fargaba ta gyada Mishi kai, sai da suka yi sallah sannan Fudail ya gabatar da kanshi tare da abinda ya kawo su, "Subhanallahi tana ina mara lafiyan?" "Tana tare da Sultan Aamaan." Da sauri Suka fito daga cikin masalacin suka nufi wajen gari, kafin kace kwabo, sun iso cikin garin. Gidan shi suka nufa inda aka musu masauki shi kuma Mehran aka bashi wani bangare na saukar baki na garin. A daren aka taso mata suka shiga girki na musamman, za a kaiwa dakarun da suke wajen gari, Yana rike da hannun ta, kura mata ido yayi tare jin kamar ciwon a jikin shi yake, matse hannun yayi a hankali kamar me mata tausa. "Har tsawon kwanaki nawa zata dauka a hakan" Kasa yayi da kan shi sannan yace. "Allah ya taimake ka, Sultan zata samin kwanaki ashirin da daya zuwa kwana talatin!" "Hmm!" Ya fadi a kasan makoshinsa, yana kallon shi ya gama hada maganin, a gurin sakawa ne fa, mutumin yace bai san zancen ba shi zai shi ya saka mata maganin da kanshi, murmushi yayi sannan yace mishi. "Kayi hakuri, zan dauke ta kamar Y'ata zan kula da ita, don Allah karka ji." "Bani maganin" Babu musu ya mika mishi tare da fita a dakin, a hankali yake zare mata rigar jikinta, tare da shafa mata maganin a gurin ciwon ta, koda ya isa gurin kirjinta ne ya kura mata ido, sannan ya dauke kan shi, yayi ya shiga shafa mata har, zuwa kan cikinta, yatsar shi ne ya kai kan cibiyar ta, anan ne kome ya kunce mishi.da sauri ya gama shafa mata. Ya maida rigar ya saka mata. Haka suka kwana bayan an bata magani wanda bata ma san anayi ba, sabida doguwar suman da tayi. ~~ "Toh wallahi kasan abin yi, domin Fazilatul tana dab da lalata kome." Inji Sultanah Hoyam. Shiru yayi tare da jan gemun shi yana tuno abinda ya faru, shekaru talatin da bakwai baya. Sabida yasan idan yayi mata magana a lokacin ba zata tab'a yarda bukatar su ta biya ba, amma da yayi mata hikima, bai zata kome zai lalace haka ba, kuma bai tab'a kawowa har yau zata kai tana raye.. Yayi imani da Allah da bata raye da kome zai zo mishi da sauki, amma kasancewar ta a raye shine ya hana shi samun kan wancan d'an kusun uwar, d'an banza duk hanyar da aka bi sai ya kauce, Insha Allah da zaran ya cika shekara daya dole ya bawa Jasrah daman zama Sultanah ta gaba. Koda Mehran baya so sai haka ya faru, yaga shegen da ya isa ya hana faruwan Al'amarin. "Karki damu, zamu sami abin yi ba zamu tafi a hakan ba, domin itace tayi riba, domin ita ke da Kowani b'angare sabida sanin cewa zata iya samun karfin mulkin da zata iya hana mu walwala yasa barta a gurin. Babban shirin da zamu yi akan su ba karami bane, dan haka ki saka ido akan shi idan ya dawo, Ni kuma zan tinzira ta, tabar min Jasrah sai na san yadda zamu yi mu tura ta jikin Mehran, ta yadda zata cire mana Ikram a jikin shi." Murmushi suka yiwa juna tare da kowa ya kama hanyar shi, a hanyar komawa Fada, itama ta fara nata shirin. "Mahlika lokacin ki yayi, ba zan tab'a barin wani ya shigo min ba tare da na dakatar dashi ba, wato ga sakarya na tashi a biyu. Babu hmmm Amir Hood kenan dole ka fadi a kasa na." Da wannan tunanin ta na cikin gidan. Shima a nashi tunanin cewa yake. "Daga ke har Fazilatul nisa, dole na kawar da hankalin ku, na sami juya zaren azabarina na mulki kamar yadda naso haka tun baya, ba zan tab'a baku damar zama wannan yanayin ba. Har abada Ni zan cigaba da gwara kome, cikin tsarina. Shima Mehran zan kasance cikin tafin hannu na." Kamar yadda itama tayi murmushi, bayan ta gama shirya gadar zare, haka shima ya sake murmushin mugunta tare da aiyana abinda yake shiryawa nan da d'an wani lokaci. ~~~ Washi gari Da kan shi yayi ta bata madara har lokacin bata farka ba, tare da duk da haka yana jin a ranshi kome zai zo mata da sauki, kallon fuskarta yayi tare da dan bakin bakinta, hannun shi yakai kan bakin yana shafawa, tare da shafa kanta, a hankali yana me tausaya mata, tabbas uwa ba zata tab'a kuntatta d'a ko Y'a ba, wani irin zuciya ce a kirjin Maman shi? Wacce irin rashin imani ne a ranta, da har zata saka a yita azabtar da mutum babu tausayi ko jin kai. Idanun shine yayi jajjur, amma zai dauki mata ki akan wannan abun da tayi. Ba zai tab'a kyale ta ba. "Sultan Insha Allah zata sami sauki, ka rage damuwa kar kai ma ka." Inji Fudail, Mik'ewa yayi tare da fita daga dakin, ya nufi waje. Fudail yana biye dashi. Tare da jin Maman Mahlika suna tattauna akan wani abin da ya faru. "Eh wallahi ance zaki ne wasu sunce damisa ne, amma kuma bamu san me ba, sai dai ya kashe Marwan ya kwashe kayan cikin shi ya cinye." Kallon su yayi tare son jin meke faruwa. "Wallahi bamu san meye yake faruwa ba, kawai dai ya fara cinye mana dabbobi ne tun wancan watan, yau kuma ya tab'a dan gidan ladanin garin nan.." Saura Pages 9 na gama free book ```Book one free ne, book two da three na kudi ne 200₦ ta bank 0472282105 ki katin mtn ta wannan Number +2347035133148 ko ta wannan Number 08130269641``` #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 Book 1 Mai_Dambu BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM Page 32 Bai kai ga rufe baki ba wasu mutane uku daga cikin dakarun da suke wajen gari suka iso gurin a guje a bisa Dawaki suna haki. Sanan suka sauka a kan dawakan tare da kai hannun su gefen kirjina su bayan sun dunkule, suka Gaishe shi sannan biyu suka koma gefe. Babban cikin su ya fara magana. "Sultan an sami matsala a inda muke!" "Hmm!" Yace mishi tare da kafe shi da ido,yana sauraren shi, "Wani abu da bamu san meye shi ba, wa kashe mana dakaru guda bakwai, yau da asuba." Iskar bakin shi ya furza bayan ya sauke ajiyar zuciya, shafa kan shi yayi yana kallon cikin garin baki daya, sannan ya kalle su. Yace "Muje naga yadda garin yake." Babu musu suka shiga take mishi baya yana tafiya tare da kallon yana yin garin, har suka fara shiga dajin, basu yi nisa ba suka soma jin gurnannin abun, durkusawa yayi tare da kallon sawun abin. Sannan ya kalli Fudail yace. "Me kake tunanin yana yin wannan b'arnan?" "Ina ganin damisa ce!" "Anya zata iya wannan b'arnan a lokaci guda,?" Bai bar Fudail ya karasa magana ba, ya tari numfashin sa. "Toh Allah manasani." Juyawa yayi tare da kallon Fudail, sannan ya ce musu, su juya. Har sun fara tafiya ya fara jin takun abin, umartar su yayi tare da hawa bishiya, suka zubawa Sarautar Allah ido, can kamar minti goma sai ga abin ya fito, ƙatuwar damisa. Hauka take sosai a duk lokacin da ta juya gefe da gefen ta, tayi da duba kusurwan kowani bishiy tana noman abu, kallon daya badakaren yayi yaga akwai baka a hannun shi, makalewa yayi jikin bishiyar sosai ya amshi bakar tare da jan shi da karfi ya sake mata a gadon bayan ta, ihu tayi tare da niman wanda ya harbe ta, ta kuma jera kwarin a jikin bakar har uku ya harbe ta, ihu ta saka tare da nausawa daji. Basu kuma jin duriyar ta ba suka sauko. Kallon juna suka yi. "Akwai abinda suka taba mata." Da haka suka shigo gari tare da yiwa Baban Mahlika bayani, kiran mutanen garin yayi tare da tambayar su, waye ya tab'a damisan nan. Hango wani mutum suka yi ya juya da gudu, take Fudail yabi bayan shi da gudu, tare da saka mishi kafa, ya dauko shi suka dawo. Gaban Sultan Mehran. Mika mishi hannun Mehran yayi tare da kallon shi. Babu musu yace musu. "Tun wancan watan me muka shiga daji ni da yarana, shine muka ga yaran suna ta kiwo toh sun bani sha'awa, shine na kwaso su." Kura mishi ido Mehran yayi yana hangon rashin imani akan shi. Kallon Fudail yayi, take ya dauki wasu dakaru suka nufi gidan Mutumin. Sun sami Kanwar mutumin tana ta wasa da ya'yan Damisan, daukar su suka yi cikin Shegen tsiwa ta kalli Fudail tace. "Kai me zaku mana da abun wasa na?" Wani kallon banza yayi mata tare da sakawa a dauke yaran, ai kuwa ta sha gaban shi. " Bazasu dauka ba! Waye kai." Rikota yayan yayi cikin rarrashi yace mata. "Jiya mun yi baki ne, Sultan Aamaan na SAMAIND yana cikin garin nan ya kawo matar shi jinya dan haka kiyi hakuri, uwar su tana ta kashe mutane." Tasa keyar shi suka yi, ta rike hannun shi. Jan shi suka yi tare da tafiya dashi, bin bayan su tayi tana kuka. Har kofar gidan su mahlika, tunda ta isa kofar gidan ta ga kusan rabin yan garin suna gurfane, kallon yaran damisar yayi yana kallon mutumin. "Ku hukunta shi!" Da gudu ta shigo gurin, tare da rungume yayanta, tana ihu. "Wallahi ba shi bane ya saka aka dauko su,nice na dauko su. Don Allah ku bar min Yayana don Allah ba zai kuma ba." "Alhamdulillahi, Sultan mara lafiyan ta farka!" Kiran Fudail yayi tare da mishi magana a kunne, sannan ya koma cikin gidan. Yana shiga cikin gidan, yaga yadda nake kokarin tashi zaune. Tsayawa yayi a bakin kofar, tare da kura mata ido, gaba daya ji yaƙe kamar bashi ba, wani irin yanayi yake ji akanta, wanda ba zai iya daukar shi a karamin abu ba, shafa kan shi yayi sannan ya tako kamar mara gaskiya ya iso gaban ta,.ya ja kujera ya zauna yana kallon fuskarta. Hannun shi ya kai saman kumatunta yana shafawa tare da kallon cikin idanunta. Dukar da kai na, nayi ina wasa da hannuna ina kallon farcen hannuna, wanda suka samu nasu azabar, d'ago kai na yayi tare da cewa. "Meye nufinki?" Janye kai na nayi,.tare da kallon jikina yadda ya kama magani sosai, sake tambaya na yayi ban d'ago kai na kalle shi ba, asalima dauke kai nayi daga gare shi. A na uku ne ya fusata tare da mik'ewa yayi wurgi da kujeran tare da daka min tsawa. D'ago kai nayi a hankali ina kallon shi.. "Kin rena ni?" "Toh ka rabu dani mana, dole sai ka zauna da ni ne, ka tafi kayi rayuwar ka, ka bar ni na koma gurin ahalina na gaji da zama a kasan ka. Ka barni na tafi nayi rayuwa ta da wanda nake so. Yana gab da isowa inda nake. Don Allah ka kyale ni, ka barni na." Buge min baƙi yayi tare da shake min wuya, ilahirin jikin shi rawa yake, idanun shi sun firfito. "Kika kuma kira min sunan wani namiji, sai na cire mishi gaban shi na ajiye mishi yayi rayuwa babu gaban shi." " Na gaya maka ina da wanda nake so na kuma na gaya maka, Noman yana nan zuwa gare ni, sai dai ka kashe mu baki daya, mara imani da tausayi, ka rabu dani mana, dole ne sai na zauna a karkashin mulkin zalincin ka, mugu Azzalumi kawai. Kaje kai da Mahaifiyar ka sai Allah ya bi min hakkina. Ina fama da maraicina kuka rabani da farin ciki na, domin biyar bukatar kanku, baku san kome ba sai zalinci ko Allah madaukakin ya hana kan shi zalinci shi yasa baya zalinci dan shi adalin sarki ne. Ku kuma dake dabobbi ne bak..." Kifa min mari yayi tare da kara min, d'ago Ni tayi tare da hada ni da bango, ya shiga marin bakina, kamar zai watsar min da hakora na. "A iya kai na kake nuna jarumtar ka me yasa baka fita kasan meye a ke yi a cikin garin ba, kana kiran kanka da suna sarki kana kashe mutanen ka. Hakkin mu ba zai Barka ba." Cak ya tsaya yana kallon fuskana, a sanyayye wannan wacce irin rayuwa ce, watsar dani yayi a gurin tare da ficewa ya barni, Alimah tana jin su. Kasa hakuri tayi tare da shigowa dakin tana kallon yadda nake goge bakina, zama tayi tare da cewa. "Me yasa kike mishi haka? Ko baki san babban mutum bane?" Kallon ta nayi haka kawai naji a raina bata min ba, bakamar mijinta da yake da kirki ba, ita kuma fuskarta na kalla na Fahimci tana da fuska biyu, dauke kai nayi ban bata amsa ba, dan nima idan naji a raina ko Sultan da aka haifa a mulki sai haka, surutu tai ta min har ta gaji ta fita, Na bita da harara. Haka na zauna ina nazarin rabona da ibada na, dan haka bayan fitar ta mijinta ya shigo da Fudail. "Ina son yin sallah" "Me yasa kike b'ata mishi rai ne?" "Wa kenan?" "Sultan Mehran mana!" Ya faɗa a sanyayye. Yana kallon yadda nake kokarin yin alola. "Toh sai me dan na b'ata mishi rai? Ba namiji bane shi, ai anyi shi dan na gaya mishi mara dadi da me dad'i, dan haka kai ma ka kara gaba kafin na kalli cikin idanun ka na fesa maka rashin kunya." Na fada tare da dauke kai na, zuciya yayi shima ya fita. "Y'ata ki daina yin haka, Sultan Aamaan yana matukar girmama Al'amarin ki, karki saka shi ya fara jin tsanar wasu matan." "Baba! Na gaji da zama a kasan mutumin da babu Allah a cikin tsarin shi, Baba na gaji da ganin Mehran baya ibada, me yasa ba zai gane girman Ibada ba, yau da ace Ahlillu kitab ne zan mishi Uzuri, amma musulmi ya haife shi fa, daular da yake mulki a gurin Kawun Annabi ne ya kafata. Shi waye da zai barranta kan shi da rahamar Allah, dan haka Ai Cigaba da jin bakakken magana har sai ranar da ya fara sallah. Zan daina mishi wulakancin" "A'a babu dole a cikin addini karki tilasta shi bayan bai da niyya, ki bari dai idan shi ya bukaci hakan, kusan haramun ne tistalaw ayi addinin Musulunci dole. Karki yi haka, tunda yana jin maganar ki, kiyi kokarin ganin ya fahimci addinin kanta, Insha Allah zai yi yadda kike so." Nasiha yayi min a cikin hikima da dabara, sannan ya nuna min illar abinda nakewa Sultan Mehran, tunda a kasar shi nake bai dace na yi ta mishi hawan kawara. Ni kuma ina mishi haka ne da haushin Mahaifiyarshi. .... Daukar yaran damisar nan suka yi tare da kai mata dajin suna bin hanyar da tabi, can suka ganta a yashe, Allah sarki duk da harbin jikinta bai hanata yunkurin mikewa ba, ajiye mata yaran yayi tare da kallonta, cikin dabara da hikima, ya zaga bayanta ya cire mata, kwarin da ya harba mata, sannan suka bar gurin tare da hawa bishiya, suna kallon ta, yaran shiga jikinta suka yi tare da fara shan nono, girgiza jikinta tayi tana lashe kan yaran, har suka gama sha, suka mike tare da barin gurin. Abinda ya faru ya sanya shi kara tausayin Ikram, tabbas itama rabata aka yi da nata rayuwar, shi yasa ta zama wata irin baudaddiyar mutum mara dadin zama. A hankali suka sauko tare da barin dajin, tunda yazo garin jiya bai samu yayi wanka ba, dan haka suna isa gidan Yasaka Fudail ya hada mishi ruwan yayi wanka, sannan ya cire kayan marasa nauyi dai dai da shigar kowa ya saka, tare da ajiye na mulkin yana me jin shi sakayau. Yana son zuwa duba jikinta dukda abin da tayi mishi, amma zuciyar shi tana hana shi, dan haka ya share batun ta ya cigaba da abinda yake yi, har dare. Kunna wutar itacce aka yi suka zauna a waje kasancewar an fara tunkarar lokacin sanyi kuma suma suna fama da dusar ƙanƙara. Hira Fudail yake tare da Baban Mahlika, sosai ban da shi da yayi zurfi cikin damuwa, domin kuwa hiran da suke tayi mugun tab'a shi wanda kusan dukkan su akan addini ne, sai yake jin babu dadi. Dan haka ya mike tare da musu sallama, ya nufi gidan shi. "Sultan baka duba Ikram ba?" Girgiza musu kai yayi sannan ya wuce abin shi. "Suna son junan su, amma rashin fahimtar juna yasa suke azabtar da ruhin su!" Inji Baban Mahlika, "Babu kome a tsakanin su, kawai dai basa jituwa ne amma bana tunanin akwai soyayya a tsakanin su" Dariya yayi irinta manyan sannan yace mishi. "Akwai kauna a tsakanin su, me tsafta kuwa, dan haka karka yi mamaki suna kaunar junan su, kawai taran miskilai ne ba lallai kowannen su ya fahimci haka ba,sabida yadda suke mu'amalatar junan su, kamar zasu cinye kan su." Haka dai yayi shiru, bai ce kome ba, dan yana dab da fasa ihun mara amfani, taya yayi sake har suka fara kaunar junan su? Taya Ikram da Mehran zasu ci amanar shi. Dan haka ya mike tare da mishi sai da safe, daga yanayin hiran da suka yi ya fahimci yadda yake boye shaukin shi akan wani abu na daban. ---- A hankali lafiya ta fara samuwa dan mun kwashe kwana goma sha tara, ina jinya har na fara fita waje, ana hira dani, dan ma ana sanyi sosai, amma kuma haka bai hana ka fahimci bana shiri da Mehran ba, Fudail ne abokin hirana da Baba, shima sabida ina ƙoƙarin daukar takobi ina koyan fada ne, tunda jikina ya sami lafiya. Koyan yakin da nake a gurin Baba yasani fahimtar shima tsohon kashi ne, dan haka idan muka fara kamar ba zamu dai na ba, gashi wani lokaci har kuskuran shi nake da takobi. Yau na kamar kullum muna cikin haka na yanke shi a damtsan shi.yarda takobin nayi tare da zuwa kusa da shi, ina cewa.. "Don Allah kayi hakuri! Bada gayya bane." #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 Book 1 Mai_Dambu BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM Page 33 "Waye ya koya miki wannan zafin naman haka a fada." Juyawa nayi tare da kallon Mehran da yake zuwa, ya d'aga ni daga jikin ba yace min. "Baki da hankali!" Daga haka ya cire kayan shi ya daure hannun baban yana ce mishi yayi hakuri bani da hankali, amma zai koya min hankali. Daukar takobin yayi tare da nuna min na baban na ki dauka. Tsawa yayi min na dauke kai batare da yin banza dashi. Haka yayi ta cira karshe dai Baba ne yayi ta min dariya yana zuga shi wai. " Ai Sultan taji tsoro ba zata kula ka ba, dan haka ka kyaleta." Cikin jin haushi na dauki takobin, na tunkaro Mehran, yana kallona, ina zuwa ya saka min kafa na fadi kai na ya lume cikin dusar kankara,cikin jin haushi na mike muka cigaba da azabben faɗa. Fudail yana kallon mu, abin haushi yake bashi, dan haka bai damu ba, sai da yaji na kwala ihu tare da kiran sunan Allah. Ya juya da sauri yana kallon yadda jini yake zuba daga gefen cikina. Sam ko a jikin Mehran, asalima gurin baba ya nufa ya riko hannun shi zasu wuce. "Fudail dauko min ita, yau tayi karo da Maza!" Wani abu yaji ya tsaya mishi a ranshi, juyawa yayi a hankali ya kalle ni. Cikin idanun shi kuwa sakon gargadi nake gani, kar na sake Fudail ya dauke ni, idan ba haka ba! Take idanun shi suka shiga budewa da rufewa alamar zunzurutun masifa da yake tanadar min. Koda Fudail ya zo ya dauke ni, kasa amincewa nayi dan wallahi Ni kadai nasan abinda nake gani a cikin kwayar idanun Mehran, da kaina na safe cikin, muna shiga gidan, dai dai ya fito zai duba ko an dauke ni ya hango ni ina jan numfashina, sabida jiran da yake dauka na, kamar ba gurina zai zo ba, ganin zan zube yayi maza ya tare ni. Lokaci guda numfashina yana wani irin fita tare da bugun zuciyata. Dauka na yayi zuwa dakin yana tsaye Baba ya samin magani, sannan ya fito. Wani b'ata rai yayi yaki kula Fudail dan kishin Fudail yake, duk da bai san lokacin da ya fara jin ƙishin sama da haka. --- bayan kwana biyu, muna hira a waje da dare. Baba da Fudail har dashi kan shi Mehran, hira muke. Can Baba yake cewa.. "Akwai lokacin da Sarki Abdus Samad mahaifin Sultan Mehran ya aike ni Askandariya, kusan shekaru ashirin baya, naga Yar sarauniya Amrah Joindatullah kamar ku da ita har ya b'aci, a lokacin ana batun auren ta da Sultan Zahil na kasan Yeman. Tun daga nan ban kuma ganin mace me irin halittar kwayar idanun irinta ba sai ke, dukda ance min Amirah Sariyah itama tana da irin idanun ta, amma ban tab'a ganinta ba." Kura mishi ido nayi, ban ce kome ba. "Amma Ikram daga wani yanki kike?" "Sudan!" "Toh taya aka yi kika tsinci kanki a Samaind?" D'ago kai nayi idanu na jajjur ba kalli Mehran, wanda shima Ni yake kallo. "Sai da safe ku" Nace musu, Boyayyen ajiyar zuciya, mutane biyu suke sauke, lokaci guda. Fudail da Mehran, murmushi baba yayi, sannan yana kallon yadda kowannen su yake kokarin ganin ya kafa kan shi, lallai akwai aiki babba. Washi gari. Na taso da wuri, dan haka nida Fudail muka nufi daji saro itacce, lokacin da ya fito yayi ta raba idanu yana jiran yaga ta inda zata fito, yana son tambaya amma baya son abinda zai sanya kimar shi ya ragu akan idanun mutanen, dan haka yayi shiru har aka gabatar mishi da abin karyawa, daidai lokacin muka dawo muna dariya da hira, kan shi a sunkuye bai d'ago ba balle ya kalle mu, cin abincin yake a zuciye kamar wanda ake tura mishi. "Sultan Mehran!" Dakatar da cin abincin yayi. "Ina son zan fita wajen gari muga halin da jama'ar mu take ciki." "Zan bika muje!" Tari ne ya sarkafe shi sosai fa, kamar zai shiɗe, haka suka yi ta bashi ruwa, ina zuwa na fara shafa bayan shi, cikin jin zafina ya juya tare da ture ni na fadi. Kallon shi muka yi, tashi nayi a hankali ina kallon shi. "Kazo muje Fudail" Ran shi ne ya kuma b'aci bai ce kome ba, ya juya tare da cigaba da cin abincin shi, ko a jikina Ni kuma na fice tare da nufar waje, koda Fudail ya fito muka yi tafiyar mu. Tashi yayi ya koma dakin shi, ya zauna yana jinjina qarfin rashin mutuncin da suka Mishi. Amma yana ji yana gani bai iya dakatar da ita ba, kasa hakuri yayi shima ya shirya ya fita ta baya, Baba yana kallon shi ya ratsa daji. Haka yayi ta bin su ta daji, da hirarrakin su, tare da tsayawa suyi yan magana, tare da fahimtar kaunar da Fudail yake mata, suna cikin tafiya suka haɗu da kura, dan haka Fudail yace mata. "Kinga wannan lutayen basu fitowa su daya, dole akwai yan uwan su a can gefe shiga tacan naji da wannan." Kad'a linzamin dokin tayi tare da shiga cikin dajin da Mehran yake ciki, yana kallonta.. aikuwa sauran kurayrn suka farmata, shi kuma yana fama da wasu, tun daga nesa ake harbin su da kibiya, har suka shiga tsakiyar dajin, jin saukar abu dimmmm daga sama yasa ta juyawa, tana kallon shi ya zare gatarin shi ya juya da karfi ya shiga saran su, har dai da ya kashe su tass. Sannan ya juya yana kallon ta, Kallon juna suke, dan tana mamaki yadda ya iya kashe dabbobi babu rangwame, fisgota yayi daga saman dokin, ya had'ata da bango, yau kan sai ya cire mayafin da take manne da fuskar ta, ya gaji da ganin kwayar idanun ta masu ban tsoron nan. Kai hannun shi yayi tayi maza ta rike, dan haka ya kalli yadda take zare. "Don Allah karka tab'a min kimata." Fuskar shi ya kai saman nata, tare da kai hannun shi bayan wuyarta ya tab'a a hankali take ta zube mishi a jikin shi, ajiyar zuciya ya sauke. Tare da rungume ta. Tsam yana ji kamar su dawwama a hakan. Kallon gefen fuskarta wanda yake baki kiririn. Gefe guda kuma me kyau, dukda da baya jin dadin zama da ita amma haka ba yana nufin baya jinta bane. Matsalar shi da ita bata iya fahimtar lamarin shi bane, shi kuma ba Sakarai bane da zai ta bude baki yana ihu, dan aji halin da yake ciki, kuma idan duniya da gaskiya ita tafi dacewa ta fahimci waye shi, "Ikrammmmmm!" Fudail ya kwala mata kira, juyawa yayi ya hango shi daga nesa, ajiye ta yayi a hankali, sannan ya ya dauki gatarin shi da gudun Bala'i ya bar gurin, jin motsin ana gudu yasa shi nufar gurin, koda ya isa ya samu babu kowa sai gawarwakin kurayen, gata can a gefe tana sume, da sauri ya isa gurinta, tare da sab'ata a kafada. Dokin ta ya kama ya daura ta akai, sannan ya hau nashi ya kad'a dawakan suka koma Madinatul Mah. ..... Yana kallon shi ya dawo, tare da shiga ya sauya kayan shi. Sannan ya fito tare da zama kusa da Baban Mahlika, duk da zaman kurame ne, amma bai hana shi gaya mishi gaskiya ba. " Me yasa kake boye abinda zuciyarka take so? Sultan" Cike da al'ajabi ya kalle shi sannan ya dauke kan shi yana lissafin lokacin da ya dace. "Sultan kana son Baiwar ka?" "Bana sonta, ban tab'a kaunarta ba, har abada ba zan kaunace ta ba. Kawai tana karkashin kulawata ce. Kabar wannan abin a tsakanin mu." Yana kai aya, Fudail yana isowa da azabebben gudu, tare da ita. "Malam Fudail lafiya kuwa?" "Wallahi kuraye ne suka kai mana farmaki, toh ban san me ya faru ba, amma garin ta tsira da lafiyarta ne ban san me ya faru ba, ina ganin fadowa tayi daga saman....." "Innalillahi wa'inna ilaihi rajioun, ba dai ta sami rauni ba?" Inji Baban Mahlika, "Wallahi ban sani ba, domin sai gata nan a sume!" Kamar bai san kome ba, ya cigaba da feke bakin takobin shi, kallon shi Baban Mahlika yayi yasan shi ya kai mata dauki, amma da za ayi.magana yace bai damu ba. Dan kar a Cigaba da harbo jirgin shi. Ko damuwa bai yi ba, da Fudail ya dauke ta. Akan fuskar shi zaka Fahimci ai damu ba, amma a cikin ran shi kuwa bakin ciki ne da kishi kamar ya rufe Fudail da duka, amma ya matse. Bayan sun gama shiga da ita cikin gidan, "Na shiga uku! Wannan yarinya zata kashe ni." Ya faɗa a sanyayye, kamar me rad'a. Sunyi kokarin ta farka amma barci ya dauke ta, dan haka suka fito, dan dole Fudail yayi musu sallama ya bar kauyen zuwa wajen garin. Yana tafiya amma gabaki daya nazarin abinda ya faru yake, anya Mehran bashi ya kawo mata dauki ba, toh amma me yasa bai damu ba? Kawai ya share batun baki daya. ..... Bayan tafiyar shi ne Baban Mahlika yace mishi. "Sultan zaka iya shiga ka duba ta" Tabe baki yayi tare da share batun kamar baya gurin, har yamma lokacin da aka yi sallah isha Fudail ya dawo, suka kafa hira. Duk da yana lura da yadda take mishi kallon kurilla ba. Ganin kallon yaki karewa ne ya d'aga mata gira daya, "Ahhh" na fada duk suka zuba min ido, "Lafiya!" Idanun yana kan shi baki sake nace musu. "Babu!" Cigaba aka yi da hira, aka Cigaba da hira, can idanun mu ya kuma sarkafewa da juna, kyafta min idanu yayi. Da sauri na juya baya, ina juyawa ya d'aga min giran shi dukka biyu. "Wayyo Allah na!" "Lafiya suka tambaye ni a razane tare leka inda nake zaune. "Wani abu ne da yake yawo a kafana!" Nan aka shiga dubawa, muna hada ido ya sake min murmushi, Haka suka gama niman basu samu ba. Tsakanin shi da Allah yayi ta manna min hauka, kafin kace kwabo kasa nutsuwa. Baba ne ya fahimci abinda Mehran yake min dan haka ya mike tare da mana sai da safe. Fudail ne yaki mik'ewa dan bai san meke faruwa ba, sai da Baba ya kira shi tare da bashi Shawaran ya bawa Sultan guri. Yana ganin babu kowa daga Ni sai shi. Lumshe idanun shi yayi tare da kurawa wutar idanu. Ganin babu abokan hira yasa nima na mike zan bar gurin, dole ta gaban shi zan wuce. Ina zuwa gaban shi ya saka min kafa, zuɓewa nayi a jikin shi. Fuskar mu tana kallon juna. Da sauri na fara kokarin sauka daga jikin shi. Kara matse ni yayi yana kallon cikin idanuna. Ganin zai azabtar dani da wannan idanun shi ruwan zaiba, ya sani dukar da kaina tare da dunkule hannuna a kirjin shi. "Mehran!" "Hmm!" "Sake ni kar wani ya ganmu" "Ahmm" "Don Allah ka sake ni kar wani ya ganmu naji kunya" "Kunya?!" Ya tambaye ni, d'ago kai nayi tare da kallon shi, aikuwa abinda nake gudu ne ya faru, domin idanun mu yana haduwa da juna, take naji kamar an daki gabobbina, ya sake lokaci guda na ji kamar bani da wata kuzari a jikina, kwanciya nayi a jikin shi, tare da sauke wata irin ajiyar zuciya. "Karfe biyar, na asuba ina jiranki!" Yayi maganar kamar me rad'a. "Humm! Ina zamu je!" Matse ni yayi. Nace. "Ouch!" Bakin shi ya kai kunne na, tare da sake min wani irin numfashi. Cusa kai na nayi kirjin shi ina shaƙar kamshin turaren shi. "Meehraan!" "Amaaahhhh!" Yaja sunan kamar yadda na ja nashi. "Don Allah ka daina haramun ne, mace baliga da namiji baligi suka haɗu, na ukun su shaidan ne!" "Hmm!" Ƙoƙarin mik'ewa nake amma kamar wacce a ke manna ni da jikin shi na kasa koda motsawa, a hankali ya mike tare da ɗaukata, bai zame ko ina ba, sai masaukin shi dani. " Meehhh" Kallona yayi tare da isa bakin kofar Masu kula da kofar suka bude, shiga yayi dani a falon me dauke da kilishi ya..... *Ya dai dan kurma🤔☹️😏* ```Book one free ne, book two da three na kudi ne 200₦ ta bank 0472282105 ki katin mtn ta wannan Number +2347035133148 ko ta wannan Number 08130269641``` #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 Book 1 Mai_Dambu BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM Page 34 A hankali ya shimfida ni a saman kilishin sannan ya koma gefe yana me cire takalmin kafana, d'gowa nayi ina kallon shi. Lumshe idanun shi yayi tare da Cigaba da cire min, sannan ya mike ya nufi inda wutar itaccen yake ci, yana me zare kayan jikin shi. Tagwayen ajiyar zuciya nake saukewa, gyara wutar yayi sannan ya dawo kusa dani ya zauna. Tare da kurawa tagar dakin ido, tashi yayi tare da sake labulayen, sannan yayi irin kwanciyar sarakuna, yana wasa da gashin kai na. Kallon shi nayi bai kalle ni ba,. A hankali barci yayi gaba dani. Kusan har tsakiyar dare yana zaune a gurin, juyawan da nayi ne ya sashi kallon yadda na farka, mik'ewa nayi tare da tattara mayafina, na nufi ban dakin dake cikin dakin shi nayi alola sannan nazo na fara sallah nafilla. Har kusan karfe uku ina sallah. Ina idarwa na kwanta, sai lokacin na lura da shima yayi barci, a dan takure. Shiga dakin nayi da lallubar na dauko bargon shi. Juyawar da zanyi naga mutum a duhu, ihu na ware zanyi ya rufe min bakina, tare da cewa. "Tafi can!" Ajiyar zuciya na sauke sannan nace. "Wallahi ka bani tsoro daga yau kayi sallama kafin ka shiga guri." Share ni yayi ya koma bakin gadon shi ya shiga cire kayan shi, da sauri na juya mishi baya, ban daki ya nufa, ya kwara ruwan sanyi. Dakyar ya fito, yana rawan sanyi, ina tsaye sake da baki lokacin da naji yana watsa ruwan sanyi a jikin shi, kamar wani gungumen dutse ya jibgu a gadon shi, lokaci guda. Girgiza kai nayi tare da cewa. "Toh kashi nayi wallahi bazan iya wanka ba, balle kai." Rufa mishi bargon na fara yi, ya fisgo hannuna na fada kirjin shi. "Sanyi!" Ya fada tare da kaduwar sanyi hakoran shi suna dukar juna, janyo Ni yayi sosai, har cikin bargon, niman yadda zai rabu da sanyin yake. "Meehhh!" Hancin shi ya shiga gogawa da nawa, lokaci guda ya fara ƙoƙarin shigewa jikina yake, wani irin azzabbrn tsoro ne ya shige ni. Sabida yadda yake wurgi da kayan jikina zaka rantse da Allah, wani abu yake son yi dani, nan kuwa rage sanyin shi yake son yi, a hankali ya rabani da kayan jikina, sai dan abinda nake daure kirjina( wato kamar yadine kamar towel, shine madadin bra.) Shigewa jikina yayi tare da boye fuskar shi a wuyana zuwa kirjina, goga fuskar shi yake kamar zai shiɗe. Tausayi ya bani, ban san lokacin da na rungumo shi ba, tare da kifa kan shi a tsakanin kirjina da wuyata. Dakyar barci ya dauke shi, kamar yaro karami haka ya shige min, kasa barci nayi ina kallon shi, tare da tunawa da Noman da Airan, hawaye ne ya shiga zuba min daga cikin idanuna, sakamakon tuna kanwata da masoyina. ina gurin har aka kira sallah farko, tashi nayi a hankali na zare shi daga jikina. Na nufi ban daki nayi tsarki da alola, sannan na tsince kayana na saka, kafin na gabatar da rakatul firj. Ina idarwa na gabatar da sallah asuba, na jima ina addu'o'in. Kafin ya motsa tare da kallon yadda haske yake shigowa dakin. Ji nayi a jikina yana kallona, dan haka ban juya ba ne Cigaba da Addu'a, ina idarwa na mike tare da dauke sauran kayana da suke kasa na fara saka, sannan na janyo matashin dake gefen shi zan d'an kwanta, zubur ya mike zaune, Jan kwarjallen shi yayi tare da gyara zaman shi ya sauka daga gadon, ya nufi ban daki can ya fito tare da kallona yana jiran na nuna mishi kayan shi, ban kula shi ba sai dai nasan ana sanyi dan haka na duba mishi wata ƙatuwar rigarshi,.tare da sauran kayan shi takalmi da hula. Kallona yake ina ajiye mishi, ban san ya taho har inda nake ba, sai da na d'ago kai na, kawai Naji bakin shi a goshina. Da sauri na d'aga kaina ina kallon shi. B'ata rai yayi kamar bashi ba tare da, daukar kayan shi zai saka na fita na bashi guri. ~~ Tunda Baba yace ya basu guri ya nufi makwancin shi, bai iya kwanciya ba, kawai dai yana tsaye a jikin taga, yana kallon su. Bai taba sanin so zai mishi illa har haka ba sai yau, hawaye yaji yana sauko mishi daki daki. Yana tsaye har Mehran ya dauki Ikram, suka shige basu yana tsaye a gurin har asuba, sannan ya tafi sallah. Yana masallaci a zaune Baba yace mishi. "Kayi hakuri da zanen ƙaddara, ta zana ka a cikin su. Amma ba yana nufin zaka sami hakan ba, dashi ta dace." "Baba baya sonta! Ni nafi dacewa da ita, bana son na rasa ta." Ya faɗa a raunane. "Zaka rasa ta ai! Kuma mafi girman rashin ma kuwa, kayi hakuri gaskiya." Daga haka bai kuma magana ba, har garin ya fara haske. Yana fitowa masalaci ya hango su, zasu shiga daji. Kirjin shi ne yayi nauyi, yana kallon su har suka kulewa ganin shi. Kasa hakuri yayi yabi bayan sun, sai da suka yi tafiya me nisa sannan suka tsaya a bakin wani guri me kamar tsuni (Mountain) Gatarin shi ya dauka tare da shiga daji ya saro itaccen da zasu zauna, sannan yazo ya hura musu wuta, tunda suka zauna a bakin tsunin yake cikin yanayin farin ciki, ba zaka tab'a fahimtar haka ba, dan fuskar tana nan a turnike, kallon yadda take kallon wutar bakinta yana motsi yayi. Yanayin bakin burge shi yake, dauke kai yayi tare da d'aga kan shi yana shaƙar iska, kallon hanyar da suna biyo yayi, bai ga alamar kowa ba, sai dai kuma lokaci zuwa lokaci yana jin alamar kamar ana kusanto su. "Ke dawo nan!" Ya faɗa mata haka, da sauri na dawo kusa dashi, kallon yadda ganyayyekin bishiyar da muke zaune yake saukowa ne, can kuma ya lafa, zaman mu a tare ya haifar mana da wani irin kusancin sosai domin muna gogan juna. Mun jima a haka babu wanda yake iya ko motsi, d'an gogan kafadana yayi na d'ago kai da sauri zan lalle shi, fuskar mu ya haɗu da juna, idanun shi cikin nawa, da sauri na rufe idanuna, murmushi yayi tare da shafa fuskar na. Janye daga jikin shi nayi tare da mik'ewa, sai ji nayi kamar an wurgo dutse daga sama, dib ya sauka a tsakanin mu. Baya nayi tare da kallon katon halittar birin da ya diro gaban mu, juyawa yayi yana kallona, tare da wangale baki ya fasa ihun da dajin sai da ya amsa baki daya, a razane na toshe kunne na. Tab'a shi Mehran yayi. A fusace ya juya yana huci, kallon juna suka yi tare da juyawa dukkan sun, suka kalle ni. Sabida ba fara ƙoƙarin juyawa da gudu, gatarin shi ta zare a cikin rigar sanyin shi, yayi kan birin suka kaure da azzabbrn fada. "Karki yarda ki gudu!" Tabbas rayuwar duniyar nan cike yake da al'ajabi, domin kuwa Mehran ya kafe ya nace, yana fada da biri ne sabida ya nufi kan Ikram, dan haka cikin hauka da fusata birin ya juya ga Ikram wacce take kokarin boya a bayan bishiya.naushi daya yayiwa bishiyar ya zube. Nan kuwa Mehran ya kuntatta rayuwar shi da sara, ihu yayi tare da dukar kirjin shi, duk yadda yaso guduwa tare da niman tsira da rayuwar shi Mehran ya hana, sai da ta kai birin nan ya fadi akan gwiwata shi ya zube a gurin, sannan Mehran ya kyale shi, kallo yayi lokacin da ya haura saman birin ya tsaya, tare da goge jinin da yake diga daga goshinsa zuwa kan hancin shi. Ni wallahi tsoro ma ya bani, na fara ja da baya, yarda gatarin yayi tare da mika min hannun, sai ji nayi anyi sama dani.. "Aamahhhhh!" Ya kwala min kira, yana kallon yadda biri suke wasan kura ni, ihu nake ina niman daukin amma ina juyawa yayi da mugun gudu, ya koma gurin kayan mu. Yana zuwa ya dauki kwari da baka, ya kuma shigowa dajin da gudu, daga nesa ya daidaici birin da yake rike da ni ya sake mishi kwari har uku, timmmm ya fado daga sama. Aikuwa suka kuma fusata gashi nan dai suna ganin shi dan mitsitsi sai tarin bala'i ya kuntatta rayuwar su, ya hana su sake, haka yana harbin su yana binsu da takobi, bai cika son fada da takobi ba. Amma matukar ya dauki takobin toh kuwa zai raba mutum biyu ne. Duk wannan fadar da ake akan Idanun Fudail yana son yaga gazawar Mehran, amma abu ya ci tura asalima kara tunzura shi hakan da suke yi yayi. Birai dai ganin Mehran yayi musu mugun barna yasa suka fara gudun ceton ran su, tare da barin gurin, dakyar Allah ya kwace su, bayan sun kai Ni karshe tsunin. Wanda kasan shi yake dauke da wata irin ruwa me gudana, (spring water) ko nace korama. Ganin haka yasa shi zuwa da gudu, tare da wutsar da kayan fadan yana mika min hannun. "Zo nan! Karki damu ina tare dake, da dad'i ko ba dad'i." "Baka da tausayi, ji yadda kake ta kashe dabobbi, haka idan da mutane ne suka kawo min farmaki haka zaka kashe su. Mehran ka kyale Ni nayi." "Karki sake ki fada domin kankara ne a cikin ruwan." "Ka tafi bana son ganin ka!" Ban san ya aka yi tsantsi ya akwashe Ni ba. "Meehraan!!!!!!" Da gudu ya biyo bayana, tare da kara kaifin gudun shi, har ya kasance yaci mani, kafin ya riko ni, mun fasa ƙanƙarar da ta rufe saman ruwan baki daya. Muka fada cikin ruwan, me masifar sanyin, riko hannuna yayi tare da kamo ni mika fada kokuwar fitowa, dakyar muka fasa wani gurin, sannan muna fito waje, kallon yadda nake numfashi yayi, ya fitar dani wajen baki daya, daukana yayi tare da sakani a kan kafadar shi, yaga zan takura mishi dan haka goyani yayi. Ya nufi kauyen dan yabi bakin gaɓar kogin ne har cikin kauyen, da azabar gudu. Koda ya isa dani na suma, karb'a na Baba yayi. Tare da bashi wani ruwan magani da zafi, yana sha shina ya yanki jiki ya fad'i. Murmushi Baba yayi yana mamakin wannan kurman Kaunar. D'aga shi yayi zai kwantar dashi Fudail ya shigo fuskar shi a turnike, yana kallon Mehran. Tsana da kishi ne suka cika mishi zuciya, tare da kallon yadda muke yi wani irin Fayau. "Ina suka shiga ne? Dajin mun nan akwai hatsari fa" "Fada yayi da birai domin yayi musu barna, sosai domin ya kashe babban su, sannan ya kashe su bilhaki." "Alhamdulillahi! Biran nan sun dame mu, bamu isa muyi noma ba zasu lalata mana, matan mu suka tafi korama diban ruwa, suyi lalata dasu, yaran mu maza idan suka tafi kiwo su kwakule musu idanu su kashe dabobbin mu Sultan Mehran rahama ne a gare mu Allah ya turo shi. Domin tun zuwan shi yake bata kashi da duk wani abun da zai cutar da al'ummar Musulmi. Allah ya bashi tsawon rai yadda zai mulki SAMAIND cikin adalci." Dakyar ya iya furta "Amin" tare da zuba makaman Mehran, tunda ya kawo ni, nake sume. Shi yayi farka, kuma ya damu sosai. Amma Ikram babu alamar farkawa, tana kwance sai yadda aka yi da ita, shafa kanta yayi cikin tashin hankali ya kalli Maman Mahlika. "Zata kai Yaushe bata farka ba?" "Iya wa'adin da Allah ya nufa zata farka." Kura Ikram idanun yayi cikin damuwa, a hankali ya nufi kanta yana shafa fuskarta. A ranshi kuwa tambayar ta yaƙe. *Me yasa ba zaki farka haka ba! Me yasa ba zaki takaita barcin nan haka ba? Ina tare dake! Ina kuma tsaye a tare dake! Zan tsaya miki a zahiri da bad'ili. Bilqisul Ikram* Ya faɗa tare da sumbatar goshinta, yana me jin kamar zuciyar shi zata buga. Motsi kafarta yayi a hankali ta kuma motsawa, ya zata gizo take mishi dan haka ya dauke kan shi, ganin da gaske tashi za tayi ya sashi dauke kai kamar bai ganta ba.... #Mai_Dambu ```Book one free ne, book two da three na kudi ne 200₦ ta bank 0472282105 ki katin mtn ta wannan Number +2347035133148 ko ta wannan Number 08130269641``` [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 Book 1 Mai_Dambu BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM *Wannan shafin naku ne Aunty Mamieh Mom Imam, da MOM Sayyid and Noor 😒😏 Me za ayi da basamuden kun nan* Page 35 Tarin da nake hade da aman ruwa ya sashi fita daga dakin ma, Baba ne ya shigo yana mamakin halin shi kamar bai damu ba, sai da ya gama bani kulawa sannan yace min. "Kina jina?" "Eh!" "Yawwa sannun taso muje!" Haka na taso jikina a sanyayye ga ɗan karen sanyin da nake ji, bayan ya nuna min yadda zanyi amfani da ruwan wanka da yadda zan sha, ya fita. Cire kayana nayi, sannan nayi wanka tare da wanke kayan tass, ina gamawa na nufi dakin na shafa mai sannan na same su, suna cin abincin ranar zama nayi na fara ƙoƙarin ci. Ruwan zafi aka mika min, na sha sannan na fara cin abincin. ---- wato Mehran tsakanin shi da Allah ya hana Ikram da Fudail haduwa, wai gudun kar su keb'e zai ce taje gidan shi, tayi mishi aiki kuma babu aikin, karshe zuwa yake ya sakata a gaba tana mishi karatun Alkur'ani. Har yayi barci tana ganin haka zata mike ta rufe shi da abu sannan ta juya zata fita zai ce mata. "Banyi barci ba tukuna!" Haka zata cigaba da zama har itama barcin ya dauke ta,yana ganin ta fara barcin zai zuba mata ido. Har sai yaga ta fara kokarin faruwa zai rufe nashi. Idan kuwa sallah take, yana kallon duk yadda take, har ta idar, sai ka lura zaka Fahimci haka, idan baka lura ba, sai ka zata barci yaƙe. A hankali suka cika wata daya cif, wanda ya kai watanin shi goma da zama sarki,. Zaman wata daya nan. Wani irin amayar da SO Mehran yayi a aikace amma a zahiran ce ya kasa furta kalmomin yabo ko burgewa, amma duk me hankali da tunani ya ga yadda yake ririta alamarin ta, sai ya fahimci yadda yake kaunarta. Ana gobe zasu bar garin, mutanen garin suka shirya musu biki da dare, anata shagali da raye raye, haka yan mata suka jata bata so, amma haka ta shiga. Kura mata ido yayi tana rawa. Tare da dariya. A karon farko da yaji tana tafiya a tsakanin zuciyar shi, kura mata ido yayi yana fadin a ranshi. *Sirrintacciya na! Kinga yadda dariya yake kara Kawata fuskarki! Kin san girma da darajar farin cikin ki kuwa? Sirrintacciya na! Kin fahimci yadda kike haska dukkan Ni manta gurin? Idan da kin san da haka da murmushin ki sai tafi hasken farin wata kawa! Dariyar ki sai tafi iska kad'awa! Farin cikin ki sai tafi sanyin damina! Sirrintacciya na! Tayu wasu sun gaya miki sirrin kyanki! Amma Ni da nake tare dake zan iya gaya miki shi yasa.* "Sultan ko zaka shiga cikin rawan ne?" Girgiza kai yayi tare da nuna alamun a'a, hango Fudail yana ƙoƙarin shiga filin. Ya sashi b'ata rai, ya mike babu shiri, haka ya shiga cikin rawan. Kamar wani mashiya ko sikago, yana tsaye yana kallon yadda take dariya da juyi, hannun shi ya kai zai riko ta, ta zille mishi. Sake kaiwa yayi ta kuma zillewa. Saka mata kafa yayi ta tafi luuuuuu zata zube ya tare ta, suka d'an rankwafa, yana kallon cikin idanun ta, itama tana kallon na shi. *Kai kan ban san wani irin mayye bane?* Murmushi me sauti ya sake mata, tunda take bata tab'a ganin murmushin da tayi mata kyau, har kumatun shi yana lubewa ba sai yau, hannun ta takai gurin, tare da kallon shi, tsintar kanta tayi da sake mishi murmushin tare da lumshe idanun shi. *Sirrintacciya na!!!* *Heydar!!!* Ta faɗa a ranta, can kuwa kasan ranta wani tunani ne yazo mata, lokaci guda ta kwace kanta zata fadi ya d'agata cak, ya dire ta da kafarta, dai dai lokacin da aka gama kid'ar haka sai ya bawa mutanen gurin damar tafa musu. Wannan yanayin ya haifar mishi da farin cikin da ba zai tab'a Mantawa ba, a hankali na zare hannun daga gare shi na fita daga filin da gudu, bai damu ba, shi dai ya fito abin shi yana me zama a gurin shi. Baya son ya cika zakewa akan al'amarin Yarinyar nan, duk da zuciyar shi ta zab'e mata suna da sirrintacciyar shi. Ya jima yana nazarin abubuwan da ya rasa na farin ciki, shigowar ta rayuwar shi ta bashi kome, d'agowan da zai yi ya duba yaga babu Fudail. Da sauri ya mike tare da niman shi, zuciyar shi tana raya mishi suna can suka cin amanar shi, har hango su yake a idanun shi, yadda Fudail yake sumbatar ta, haka ya ficce a cikin mutanen ya shiga niman su. Can bayan gidan shi ya juyo muryan su, kamar fada suke ma ko meye yana zuwa kawai ya same shi kusa da juna, kallon su yayi bai san lokacin da zuciya ta kwashe su ba, ya tako tare da kifawa Fudail duka. Sosai fa, sai da ya fadi. Cikin fushi Fudail ya mike tare da kallon shi, sunkuyar da kai yayi cikin nutsuwa yace. "Sultan yarinyar nan bata sonka kabarta tayi rayuwar yancin." Cakume wuyar shi yayi cikin fushi yana faɗin. "Ka dube ni, ka dube ta meye zanyi da kaskantacciyar baiwa ta? Meye zanyi da mace mara daraja a gare ni? Mace me daraja ma ban jin tayi min ma ba, sai baiwar da kowani kare da doki yake ƙiyasta surar ta. Ko matan duniya zasu kare ba zan tab'a kaunar wannan abun ba, domin bana kaunar mace irinta kazama mara tsafta." Sannan ya sake wuyar shi tare da kallona, idanuna suna kan shi. Ban tab'a ganin cin mutuncin irin wanda Mehran yayi min ba, had'iye yawun nayi sannan na bar gurin, ina barin gurin, ya kuma shure kafar Fudail yana fadin. "Idan na kuma ganin ka da ita zai na kashe ka! Ita din mallakata ce. Babu wanda ya isa ratsa tsakanin mu." Ya wuce abin shi, wannan abinda da yayi ya saka Fudail cikin takaici da bakin cikin mara iyaka, bayan tafiyar shi Baba da yake labe yazo ya d'aga Fudail yana faɗin. "Na gaya maka ka fita harkan su, suna son junan su!" "Baka ji abinda yace ba?" "Kishi ne, idan ya nutsu ka saka ido ka ga yadda zai koma." Tunda na bar gurin, kuka ne yake son zuwa min amma zunzurutun taurin kai naki barin shi ya saukar min, ina shiga dakin da aka bani na kwanta, tare da kara hasken fitilar dake gefen gadon akwai wani littafin dauka nayi tare da dubawa anyi rubutun da zallar bakin larabci. *Zafin hawayen Uwa cike take da tartsatsin fansa! Kamar yadda Sultanah Fazilatul nisa ta cutar dake haka nima zan daukar miki fansa akan duk wani ahalin sultan Abdus Samad* jikina ne ya dauki rawa, a hankali na fara ƙoƙarin gano dalilin da Yasa Matar gidan bata cika sake min ba. Shafi zuwa shafi nake karantawa, tare da yadda aka daurata zata je daukar fansa, daukar Littafin nayi na b'oye shi, sannan na kwanta, ina mamakin yadda aka yi babu wanda ya fahimci gidan da muke, wato mahaifiyarta tayi alaka da Sultan Abdus Samad, shine itama kuma suka zo da zummar alaka da Mehran domin daukar fansa mahaifiyarta. "Ina ruwanki? Shi ta shafa, can da yawar su." Na fada da sauri, duk yadda naso cusa rashin mutuncin da wancan me kama da karas din yayi min na kasa,kuma na kasa barci, har asuba ina zaune kuma abun haushin dan b'atar basira ko sallah nafilla ban yi ba, haka na gama cika da batsewa na, na tashi nayi sallah asuba, ina zaune sai hararar gefe da gefe nake irin sune suka min laifi. Koda gari yayi haske na shirya tsaf, na fito wai Mehran bai fito ba, Fudail yaje gidan wai kar a bude mishi kofa, dan haka muka zauna da Fudail muka yi ta hira, har da kyalkyalewa da dariya, sosai muka bude karamar dandalin nishadi, ashe mutumin yana kallon mu, wato shine ake mishi fatan mutuwa shi yasa babu wanda ya damu da lafiyar shi. Ko a jikina, har sai da Baba yace min. "Y'ata ki duba mana Sultan mana!" Ina ganin girman mutumin dan haka na tashi tare da nufar gidan, ina bude kofar yana zaune abun shi ko a jikin shi irin baku damu da rayiwa ta ba, A hankali na tura tare da sallama, ko d'ago kai bai yi ba. Haka ya cigaba da b'ata rai. Ni ya gayawa magana, amma yau shi yake fushin da banyi ba, d'an dukawa nayi sannan nace mishi. "Mu shirya ka fito ka karya sai mu." "Na soke tafiyar!" "Toh Allah ya kyauta." Na fada tare da juyawa zan fita, cike da mamaki nake kallon shi, kafin ya sunkuyar kan shi. *Sirrintacciya Ni kika wulakanta! Sirrintacciya!!!* A hankali na juya tare da kallon shi, sai kuma na fahimci yana cikin kaɗaici yana bukatar wani a gefen shi koda ba zai mishi magana ba, yana bukatar nutsuwa ko da kulawa ce, kasa fita nayi na tsaya a bakin kofar, da wutsiyar ido yake satar kallonta. *Sirrintacciya!!! Kizo na sami nutsuwa!* _Wato kai babu me gane alkiblan Heydar!_ Wani irin bugun zuciya naji dan dole naso juyawa amma na kasa, jan numfashi nayi da dan karfi sakamakon jin shi a bayana, ya sakala hannun shi a k'uguna ya bude kofar. A hankali nake sauke numfashin kamar wacce tayi mugun gudu. _Heydar yaushe!_ *Sirrintacciya na!* Juyar dani yayi tare da kallon yadda nake kifi kifi da idanuna, jikina yana kara sakewa sabida wani irin kasala da nake ji, d'ago kai na nayi, tare da bude baki zanyi magana, shima maganar yake son yi, amma baki na shi yana rawa. So yake yace wani abu. Amma ya kasa fahimtar kome akan haka, hannun shi ya saka a gefen kirjin shi. Kallon juna muke a sanyayye, kamar me rad'a yace min. "Baki ji" Tsintar kai na nayi da gyada mishi kai babu musu. Daga haka muka fito a tare, yana kallon yadda mutanen garin suka fito domin mana rakiya, yar karamar jawabi yayi musu, sannan yayi musu sallama. Ya shiga keken dokin shi, Ni kuma aka baki doki, ina kallon Fudail muka shiga hira, muka dariya. Sosai muke hira, dukda hiran sama sama ne, bai hana Mehran yin magana aka dakatar da tafiyar ba. "Shigo nan!" Yabi Fudail da mugun kallo, tun da na shiga ya murɗe min hannu. Nake kokarin kwace kai na, sakani barcin dole yayi. ~~~ Bayan barin mu SAMAIND. Sunso kwarai su juya kan Zunnoon, amma yaki basu fuska dan Allah yayi shi mutum ne mai addini, shi yasa suka kasa tabuka kome. Dan haka kamar yadda suka shirya sai ya dawo haka kome yake tafiya. Yau tun safe aka turo zai dawo dan haka kowa na garin murna yake, tare da gyara mishi fadar shi da turakar shi, idan ka gani zaka Fahimci akwai baki. Ana kiran sallah la'asar muka shiga garin, kallon shi nayi nace mishi. "Sultan kasan dayawa basu sanka ba,me zai hana ka hakura da keken nan, muyi badda kama kaji wani hali mutanen ka suke ciki." Kallona yayi dan haka aka tsayar da Dawakai muka sake shiga duk da bawai shiga bane, cire kayan sarautan shi tayi ya dauko wata tsohuwar rigar Fudail ya saka, dan ya mika mishi, Ni kuma na gyara shiga jikina, muka sauka daga keken, suka yi gaba. Ni dashi da Fudail muka shiga garin da kafa, muna tafiyar kurame, kai Mehran mugu ne, hana Ni magana yayi ina ji ina gani, wasu manoma muka fara samu, daga kan su muka fara cin karo, tare da tambayar su halin da suke ciki. Nan suka yi ta fade fade, wasu su fadi Alkhairi wasu su fadi sharri har da abinda aka musu, Musamman yadda ake matsa musu da haraji tare da kwace musu amfanin gona su, kamar yayi kuka yadda suke bayanin, dan haka lokaci zuwa lokaci yana kallona, tare da dauke kai, har muka iso kasuwa, anan ne naga abinda ya kusan sani suma. Domin idanun ya sauka akan.... Wannan littafin na kuɗi ne..... #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 Book 1 Mai_Dambu BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM Page 37 A raunane ta kalle su, kafin ta juya ta bar falon, can lambu ta koma ta zauna, kallon juna Sultan Abrad yayi da Nawwas, sannan ya sauke ajiyar zuciya yace mishi. "Wai da gaske kana son Ikram?" Da mamaki yake kallon shi, abinda zuciyar shi take raya mishi ba kome bane kace Eh kome ta famjama famjam, amma ya kore tunanin haka ta hanyar amfani da hikima yace mishi. "Haba ina babban kaya sai amale ai Ikram sai irinku saraki ba irin mu yardaddun ku ba, ai tafi karfina." Nawwas ya faɗa cikin girmamawa. Gyada kai yayi tare da kallon shi, sannan ya fashe da dariya yace mishi. "Haba ai nasan kai ma wasa kake, manta da batun ta, muna zuba ido muga abinda ai faru". ~~~ SAMAIND Yau kwana biyu da fara bawa Yan matan da suka zo gurin Mehran horo, a cikin su har da Jasrah da Mahlika. Yaran Gwamnonin Yankunan shi. Sosai suke daukar abinda ake musu. Dan haka na maida hankali akan kaiwa da komowa duk abinda ake bukata daga gare shi, nice akan gaba. "Ikram! Ana son magana dake a lambun tarihi" "Ke Inam waye?" Na tambaye ta kasa kasa, "Wani ne wai Sarwat." Da sauri na juya baya na, tare da duba ko dakaru na biye dani. Ajiyar zuciya na sauke tare da nufar Lambun tarihi. Da sauri. Ina shiga na hango shi tsaye, yana me juya min baya. "Sarwat! Kasan kasadar da ka kawo kanka kuwa? Ina Noman din yake?" Juyawa yayi ya zuba min ido, hautsina kayan cikina yayi ban san lokacin da amai yazo min ba, na toshe baki na. "Meehhh! meehhh!! meehraan!!!" Rufe baki na, nayi da sauri tare da fashewa da kuka, na zube akan gwiwata. Durkusawa yayi tare da d'ago kai na, "Sabida bani da amfani shine kika manta da suna na! Noman Anwarulkharim! Shine cikekken sunan. Wakiliyar SULTAN Mehran. Nagode sosai, hakan ma Arziki ne. Ina kuma baki hakuri da abinda zan gaya miki, nazo ne mu koma gida.". Jan fasali yayi tare da kallona. "Kiyi hakuri! Idan kin shirya ranar da zasu zab'e mishi matan shi, ranar zamu bar garin nan, sannan bazan miki dole ki bani ba, amma mahaifanki zan mai dake, dan kina da damar zama da Sultan Aamaan Mehran, ko zab'an zama da mutanen Gezira. Idan kuma na matsa miki, Kuma kiyi hakuri, nagode." Rike hannun shi nayi tare da cewa. "Ka rufa min asiri meye yasa kake bani hakuri, zan bika zan bika naga Airan. Zan bika naga gidan mu. Zan bika sabida kai ne kawai a zuciyata, wallahi babu ranar da rana zata fito ta fadi banyi kukan rashin ku ba, Noman ina kaunar ka, ko yau ka tashi mu tafi." Girgiza kai yayi tare da cewa. "Kiyi hakuri! Airan ta rasu." Kukan ne ya tsaya min cak, baki na sake, wasu irin kwalla ne suke zuba min wannan bai sauka ba, wannan ya sauka, ban san lokacin da ya bar gurin ba, ina zaune baki a bude, na dimauce. D'ago ni aka yi, tare da juyar dani, baki na a sake. Ina kallon shi tare da dakarun da aka baza ana niman Noman, saka kai na yayi a kirjin shi tare da rungume ni, sai lokacin na sami damar sake ajiyar zuciya, me tafe da kuka. Sosai nake yi. Tunda nayi wannan kukan har mukan shiga cikin gidan, ban kuma kuka ba, hawaye na ne ya kafe tare da saukar min da zazzaɓi, sosai na kwanta babu lafiya. Tsawon kwana uku bana ko magana abin duniya Dame shi..idan na kalle shi tausayi yake bani, dan haka ranar da na fara magana abinda nace mishi. "Karka ajiye ni a cikin abubuwa masu kyau, Ni bakar kaddara ce! Ba lallai bane na zame maka farar aniya. Ina baka hakuri domin Ni ba mazauniya bace. Zanen Qaddara ta ce ta kawo ni daular ka, ko ina nan ko bani nan ka rike al'ummar ka, domin suna bukatar ka. Mehran mulki yana bukatar nutsuwa da fahimtar al'umma bai daya, sai kuma ina rokon ka, ka amshi addinin Musulunci kai ma zaka ji dadin a ranka. Amma babu dole domin mulkin adalci koda ba musulmi bane Allah yana mishi jagora, mulki musulmi idan babu adalci Allah yana rusata!" Matsawa nayi jikin shi tare da riko hannun shi na saka a saman fuskana, tare da cewa. "Mehran! Ina farin cikin zama da kai babu cuta babu cutarwa, Mehran kayi hakuri gaskiya ba ayi Ni domin nan ba, rayuwa ta da farin cikina suna wata duniyar na daban." Kasa magana nayi sannan a hankali nake gaya mishi rasuwar kanwata, tare da kasa gaya mishi gaskiyar guduwa zanyin, domin har ga Allah yana bani tausayi,. Sannan na dauko wasu takardu da na hada bayanan da na samu a cikin fadar shi da almuddaha da ake a cikin masarautan shi na mika shi. Sannan na mishi bayanin halin da Masarautan shi yake ciki, tare da saka hannun na jikin shi, ake zaluntar al'ummar shi. Zubawa juna ido muka yi sannan na fara dawo mishi da kalaman shi da muka yi lokacin da muka je madinatul Mah. "Ni mace ce mara daraja, Ni kowani kare da doki yake bina, Mehran gashi kuma zan yi nisan zango, Mehran ka koya min yadda zan kare kai na, da lafiya ta. Sultan nagode sosai. Sultan nagode sosai." Kafe ni yayi da ido, tare da riko hannu na, cikin madaukaciyar damuwa yake karanta sakon cikin idanuna. "Karki fara abinda kike shirin aikatawa? Karki fara abinda zai kai mu ga biyan bashin a tsakanin mu, karki yarda kishi ya zama a tsakanin zubda jini. Zan baki farin ciki mafi daraja da kima. Ki zauna anan zan baki mamaki tare da saka ki farin ciki." Hannun shi ya kai kan cikina, tare da cewa. "Zan baki kome har da ajiyata ki ajiye min Airan ki ajiye min Abbinki da Abbina, Mehran zai baki .." "Idan ta kama ma rayuwata Zan baki kinji sannan indai akan musulinci ne na yarda zan yi shi karki ji kome, zan amshi musulinci karki yarda ki matsa daga cikin wannan daular, wato da nace naga wanda zai tsalleke sansani na yazo daukar ki shine ke zaki tsallaka ki tafi. Don me yasa kike da taurin kai. Me yasa ba zaki Fahimci abinda. " Kura min ido yayi yana son yayi magana amma babu wata kalma da zai yi amfani da ita sai kame kame, sai kuma kallona da yake yi, bana son wannan yanayin na shi, jana yayi gadon shi, tare da zaunar dani muna kallon juna, kasa magana yayi yana kallon cikin idanuna, na kasa cewa kome shima haka. Sai kallon juna muke.. da ace zai bude kirjin shi tabbas abinda yake rubuce ba kome bane sai sunanta. Shine a manne a bangon zuciyar shi, rike hannunta yayi yana murzawa a hankali, yana kallon yadda ta lumshe idanunta, hawaye na zuba, tsintar kansa yayi da sumbatar gefen kuncinta, yana share mata kwalla da hannun shi. Janyo ta yayi zuwa kirjin shi, suna kwance tare da shafa bayanta. "Me yasa ba zaki hakuri ba? Kaddarar mu daya ce" ya faɗa a sanyayye, d'ago kai nayi ina kallon shi tare da girgiza mishi kai, alamun a'a, dafa bayana yayi tare da kai hannun shi dukkan biyu ya dafe daidai inda kai na yake a kirjin shi yana me danne gurin, wanda nake jin bugun shi har cikin rai na. "Kirjina yana min ciwo!" Yadda yayi maganar a raunane sai da ya bani tausayi, tare da saka hannuna dukkan biyu, na rungume shi ina kara jin sautin bugun zuciyar shi. "Ki zauna da Ni mana" ya faɗa a hankali, sama da koda yaushe, "Mehran zanen ƙaddarata tana wani gurin kayi hakuri." "Ki bar bani hakuri, na shirya mana farin ciki, kinji nan dina bugawa yake sama da yadda yake bugawa a baya." Na kasa rike kuka na, haka na kasa fahimtar kome nake ji akan shi, amma duk da hakan zan tafi ba zan zauna da shi ba, zan. Juya Ni yayi daga kan shi, na koma saman shi, zuba min idanun shi yayi tare da kallon cikin idanuna. "Sirrintacciya" Ya fadi sunan kasar makoshinsa, tare. "Heydar" Na fada can kasa kasa, hada hancin mu yayi tare da gogan juna, hannuna na kai wuyar shi tare da cusa wa cikin gashin kan shi, ina kallon yadda shima yake cikin damuwa. "Mehran! Kanwata da nake faffutikar ganin ta sami rayuwa me kyau ta rasu, bani da kowa sai Allah, bani da gata sai na shi. Me yasa ba zaka cika mana kudirin mu ba, alkawari muka yiwa Junan mu, me yasa zaka yi amfani da karfin mulki ka dakatar da masoyan juna. A matsayin ka na adali karka cusa son Zuciya a cikin wannan yanayin." Daga hakan na janye jikina daga gare shi na sauka baki daya daga gadon, fita nayi daga gidan baki daya. Na nufi wajen gari. A hankali nake tafiya har na isa inda nake tsammanin. Zama nayi a kasar wata bishiya, na fashe da kuka, rana zafi inuwa kunna, haka nake ji kirjina zafi, ashe shi yaji dadin da ya fadi kirjin shi ka ciwo ni kuwa bani da bakin magana,. "Baba Uwaisul Qarni!" Shafa jikina nayi naji ashe babu sarewan, wani irin kuka ne ya kuma kwace min, tare da kiran sunan shi a hankali. Sanyin da na fara ji ne nayi maza na lumshe idanuna. Ina sauke wasu irin kwalla. "Barka da zuwa jikata, zo nan" da sauri na bude idanuna akan shi, tare da matsawa kusa dashi na daura kaina, akan kafadar shi. Kukan da nake yi ne, tare da shasheka. "Toh kiyi hakuri! Kuka me kike yi? Kinawa Sultan Mehran kuke ne ko kinawa Noman Anwarulkharim kuka?" Kasa magana nayi tare da d'ago kai na,.ina kallon shi. "Idanun ki suna fadan min gaskiya me yasa ba zaki fahimci muradin ki ba? Me yasa kike son saka kowa kuka? Karki bawa kowa samar sakaki kuka domin wata rana da hakan za a sakaki kuka. Sannan kiyi hakuri tare da rungumar ƙaddararki saura kiris kici nasarar farko amma kuma kome zai lalace. Ki duba girman haka mana." Kukan da nake ne ya kara yawaita, tare da kallon shi. A hankali ya mike tare da sauko ruwa a cikin wani akushin azurfa ya bani. Na amsa a hankali tare da kafa kai na na sha ruwan me mugun sanyi ga dad'i, yace min. "Ki duba girman dalilin da ya gaya miki wasu kalaman ai abin a bayyane take, ki sallame NOMAN ya koma haka Allah ya nufa, kaddarar ki tana tare da Mehran." "A'a baba wannan ba halacci bane, wannan son kai ne, taya zan rabu da mutumin da tun kuruciya make tare dashi" "Toh shi kenan, Allah ya tabbata da Alkhairi." Daga hakan bai kuma ce min kome ba, sai ma dauke ni da yayi na dawo inda nake, rike da akushin nan. Mik'ewa nayi tare da nufar cikin gidan sarautar, anan naga an bazama nima na. Yana tsaye hannun shi goye a bayan shi, ya zuba min ido, tsintar kai na nayi da kasa tafiya kafaffuna sun min nauyi, sakamakon irin kallon tuhumar da yake min, ina isa inda yake, ya juya min baya tare da cewa. "Rakshan ku kai ta kebantaccen shashi." Babu musu suka wuce dani haramtacciyar fada, inda aka watsa ni a cikin gidan, tasowa tayi tare da d'ago ni. "Sannun Ikram! Kinyi namijin kokarin da babu wanda zai iya, gashi nan dai saura kiris kuma kin fado daga tafiyar mu.". "Wai meye yasa kika sani wannan aikin ne?" Rike hannu na tayi. Sannan ta kalle ni. "Da farko naso yaudarar ki ne, kamar yadda ya zama dabi'u ga duk wani ahalin gidan sarauta, dan haka na saka ki a cikin kaddarar Aamaan, daga baya sai na Fahimci kece kika iya razana min mutanen da ban razana su ba, Ranar da ya nime baki wakiliyar shi na Fahimci ya isa matakin da ya dace na dakatar dake haka kin gama min kome, amma sai na. #Mai_Dambu ```Book one free ne, book two da three na kudi ne 200₦ ta bank 0472282105 ki katin mtn ta wannan Number +2347035133148 ko ta wannan Number 08130269641``` #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 Book 1 Mai_Dambu BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM Page 36 Kidime na fara bin hanyar da naga ya bulla, da gudu gudu, sauri sauri. Har na kusan cimma shi tare da kiran sunan shi. "NOMAN!!!!" Na kwala mishi kira, fisgo ni aka yi da sauri na juya ina kallon shi, tare da juyawa nayi tare da kiran shi da cewa. "NOMAN! Don Allah kazo." Kiran shi nake Mehran yana ja na, har yaga dai zan tara mishi jama'a, sakani barci yayi ta hanyar tab'a wuyana, sannan ya sabani a kafad'ar shi, muka shiga masarautan wanda babu nisa da kasuwan. "Ka tabbatar ka nima shi, karka sake ya rayu!" Yana nufar kofar da zata kaika cikin farfajiyar dakaru ne a ko ina, suna ganin shi dauke da mace, suka shiga zuɓewa a gaban shi, har cikin gidan ya nufa da Ikram, ran shi na kara b'aci, tabbas lokaci yayi da zai dakatar da ita ga shiga harkan kowani namiji, tunda ya fahimci yanzun ta haɗu da wancan banzan. Haka ya ajiye ta, yayi ta yawo a turakar shi zuwa cikin falon shi, yana jiran Fudail. Kamar ya tafi yayi aikin da kanshi, amma babu halin haka yayi ta zuba mishi ido. --- Haka Fudail ya gama niman me kama da Noman bai samu ba, karshe dai ya dawo babu wani labari. ~~ Waiwaye. Oman. Zuba mishi ido Azizatul Nissah tayi tare da cewa. "Kazo da al'amari me girma, amma zan taimaka maka, domin inda Ikram take ba sauki shiga gurin amma zan maka lamani daya, shine zan fita da kai ka gudu, ka tafi SAMAIND tana cikin fadar kasar, a matsayin baiwa. Amma maganar gaskiya Yayana da Nawwas cutarka zasu yi ba wai zasu bar maka ita bane. Yayana yana sonta, Ni kuma ina son Nawwas, shi kuma yana sonta, amma idan suka rasata zasu zauna lafiya sannan kai ma zaka same ta a cikin salama, idan kuma ka sake suka fahimci hakan tabbas zasu yi yunkurin kashe ka ne." Ajiyar zuciya ya sauke tare da kallon Sarwat sannan yace mata. "Na amince." Haka kuwa suka shirya tare da fita bayan gari, karshe dai Noman da Sarwat suka gudu abin su..tafiyar da zasu yi a jirgin ruwa kwana biyu, sai gashi sunyi shi a cikin kwana ɗaya rak da wuni guda, ranar da suka shiga garin ranar Mehran ya dauki Ikram zuwa Madinatul Mah. Yaso ya bisu, amma babu halin haka. Domin Sarwat ya hana shi. "Akan me zaka hanani bin bayanta?" "Ikram tana tare da Sultan Aamaan! Idan ka sake ka bisu wallahi yagalgala namar ka zai yi, sannan kuma ya hanaka ita, d'azun naji wasu dakaru suna maganar cewa, ai dan ya bata Wakiliyar shi ce, Mahaifiyar shi ta azabtar da ita, dan haka baka san yadda aka yi har ya zame ta a matakin wakiliya ba, don Allah karka manta ni Maraya ne, daga kai sai ita nake dasu. Idan ka sake wani abu ya same ku, zan iya mutuwa." Kurawa Sarwat idanun yayi cikin tausayi, haka ya danne damuwar shi, har ya shiga fadar Sultan a matsayin me kula da dabobbin da ake ci, duk yana jin kome akan Mehran da Ikram, yanayin da yaji labarin ne ya kashe mishi jiki, anya zata yarda ta dawo gare shi kuwa? Yadda kowa yake fadan albarkacin bakinsa. Lokacin da leken Mehran ya wuce a tunanin shi da ita suka wuce, sai daga baya ya lura babu kome a keken, shine ya juya tare da bin bayan inda keken ya fito, ya hango irin kallon da sukewa juna ita da Mehran, yaji zafin haka da kishinta, wato har ta manta dashi ta faɗa rayuwar wanin shi, yana nan yana dakin soyayyarta. Ko lokacin da ta hango shi kallon tsana da k'iyayyar yake mata, bawai kallon nazo gare ki mu koma bane. Shi yasa daga ta gan shi yayi maza ya b'acewa ganin ta, abin tausayi. Yana tafe hawaye na zuba daga idanun shi tare da danasanin akan zuwan shi da yabar ta kawai yasan Allah zai bashi wacce ta fita, amma haka ya dibo jiki ya tawo ba tare da sanin abin da take cikin shi ba. Muryanta da ihunta yana dankare a cikin ƙwaƙwalwar shi. "Noman kayi hakuri mu koma daga inda muka fito." Share kwalla yake tare da cewa, "Bazan iya komawa ba, zan tsaya har sai itace tace min na koma zan koma, amma zan tsaya mata. Don Allah koda ina da rai ko bani da rai ka tsaya mata. Kalabi ce a tsakanin rawuna. Don Allah ka bata kariya." "Me yasa kake fadan haka? Me yasa kake niman kashe min zuciya ta, don Allah karka sare da wuri hakan" "KISHI a tsakanin zubda jini! Ba zan iya dauke kai na akan abinda Zuciyata ta rayu da son shi ba, koda zan iya rasa rayuwata sai na dauke ta mun bar yankin nan. Daga nan zuwa ranar da za'a fara zab'en matan sarki kasaka ido zan nimo ta" Ya faɗa tare da juyawa ya nausa cikin dajin. ~~~ "Noman! Noman karka tafi kabar ni, Ina sonka" na fada tare da ware idanuna akan Mehran da yake kallona, idanun shi tayi jajjajur, huci yake kawai cikin shi ya kama da wuta, shi daya san halin da yake ciki. Kofin ruwa da aka ajiye mishi ya dauka ya shanye tass, sannan yayi wurgi da kofin. Ya taso yana hada hanya, tare da kallon ta. "Ni zaki yagawa mutunci a cikin al'umma ta, Ni zaki ketawa haddi? Lallai kuwa zaki kan Karen da kike kira da Noman akan farantin karanunakan SAMAIND anyi gunduwa gunduwa da namar shi." "Lallai da kayi kuskuren da har karshen rayuwarka kana dana sani, Aamaan Kace zaka kashe min Masoyina? Kace zaka saka kan shi a saman tire karannuka suci naman shi? Ubangiji ya baka sa'a, kai Izza da mulggki haihuwar ka aka yi dashi, Ni kuma na rantse da Allah sai na nuna maka mafi girman izza da takama, ka tab'a min Masoyina!" Shiru nayi ina kallon shi, kafin na zube gwiwata biyu, na hada hannu na tare da cewa. "Ka saka Ni duk abinda zaka saka Ni, ka min duk abinda zaka yi dan daraja Soyayyar da kakewa Iyayen ka, na zama fansa ga rayuwar Noman. Idan akwai abinda kake bukata ka" bakin shi rawa yake tare da kallo na, jikin shi babu inda baya rawa, zama yayi a gaban ta yana kallon yadda take kuka, tabbas yayi kuskuren ajiye ta, a matsayin sirrintacciyar shi. Me yasa zuciyar shi bata mishi adalci ba, me yasa ba zata iya hakura da zama da ita ba, kuka take sabida wani? Ba dan shi ba. Kura mata ido yayi yaga da gaske dai sabida Noman take kuka sai yaji zuciyar shi kamar zata fado, magana yake son yi amma kamar an cika mishi iska a kirjin shi zuwa wuyar shi, kura mata ido yayi. Dakyar Allah ya bashi ikon furta mata. "Sabida shi kike kuka?" D'ago jajjayen Idanu ta tayi tare da saukewa, sannan na ce mishi. "Taya bazan yi kuka ba, watanin goma sha ina wata duniya yana wata duniya, Aamaan me yasa ba zan mishi kuka ba! Don Allah." Girgiza zai yayi tare da mik'ewa yana faɗin. "Na haramtawa kowani namiji ke har abada." "Wani irin son kai ne haka? Idan dan budurci na nake faffutikar ganin bayan shi, zoka amsa. Ka kyale mana rayuwar mu" Na fada da karfi, sake kofin ruwan hannun shi yayi tare da juyawa yana kallona, ina tsaye tare da yaga rigar jikina, har kasa. Warware daurin kirjin na fara yana kallona, cike da al'ajabi, har na ware ya fadi kasa. Cire komai nayi ina kallon shi. Tare da zuba gwiwata a kasa, ina warware gashin kai na, sannan na d'ago mishi maganar da yayi jiya. "Duk da bani da daraja, na kuma zubda wani darajar, ka barni ka rayu da shi. Ko kuma sakamakon da zai biyo baya ba zai maka kyau ba." Tab'e baki yayi tare da barin d'akin ranshi a b'ace, ya nufi shashin Mahaifiyarshi, tunda ya isa ta mika mishi wani tulu da ruwan giya, ya jima rabon shi da sha, amma yau da yake cikin damuwa, yana sha'awan sha ko zai yi barci, dan haka ya shiga tultula shi a cikin shi sai da ya shanye tass, sannan ya lumshe idanun shi, so yake yayi magana amma ya kasa, baya son tarwatsa mata damuwar shi tunda bata koya mishi yadda zai fadi na shi damuwar ba. Abinda ya sani ya ginu akan kaɗaici kuma yana da yakinin kadaicin ce ajalin shi haka yayi ta nazarin abinda ya faru, gefe daya surar ta yake mishi gizo, duk da ba wata shahara tayi ba, ko wani abu da zai nuna a cike take ba, amma kuma hakan yana da matukar muhimmanci ya bashi aji na musamman, dan haka ya lumshe idanun shi, kana ya kuma buɗe shi, kamar yanzun yake hango tsayayyen kirjinta tare da d'an karamin cibiyarta wanda yake dige a shafaffen maran ta zai ce ko ciki ne oho, idan bai kaucewa gani ba, bayan da cikin a hade suke, juya mishi ita akayi yana kallon tudun cinyoyin ta tare da hango bayanta wanda ya fidda wani fadi gashi kamar dasa mata akayi. Lumshe idanun shi yayi tare da sake murmushin jin dadi, yana kallon inda take mishi gizo, kuma dago kai yayi yana kallon yadda take juya mishi, tsintar kan shi yayi da wani irin yanayi, ya mike a hankali. "Ina zaka Mehran?" Girgiza mata kai yayi sannan ya ficce daga cikin shashinta, ya nufi nashi. Tunda ya shiga ya same ta ta saka kayan, b'ata fuska yayi sannan ya koma saman kilishi ya zube daga nan dai barci. Wanda yake cike da mafarkai, akan Noman ya gudu da ita, haka yayi ta walagigi da niman ta, har ya gaji, mafarki daya yake nanata kan shi, har giyar ta sake shi ya farka, tana kwance. Tun daga lokacin ya saka idanu akan Ikram, wacce ta kuma lalacewa, bata cin kome idan zata yi sallah tayi ta faduwa kenan, sabida rashin abincin da bata ci, amma taurin kai irin nata, ya hanata hakura da burinta, ita kawai ta fita daga gidan. Bayan kwana biyu, aka bata wakiliyar shi, sosai bayi mata suka sami yanci a cikin su har da Inam, wacce take hannun Sultanah Hoyam. Tunda ta zama wakiliyar shi baya barinta sakat, duk wani abinda zai rubuta ko zai kafa doka itace ke rubutawa, wani lokacin idan aka turo sako ita ke karanta mishi, tunda ya fahimci haka kawai sai ya tsiro mata karatun dare, wato tsofin Littafin masarautan shi take karanta mishi yasa a kwaso. Gashi babu halin ta gaji zai tsiro da masifa da tsaki tare da mita, har dai ta dawo kusa dashi wai dan karta yi tunanin Noman ne, haka bai ishe shi ba, dai da ya tabbatar ya saka mata dokar bata fita wajen masarautan. Lokacin da aka turo yaran Gwamnonin Yankunan SAMAIND, itace tayi mishi hira yana zaune tayi ta zance dashi, gaba daya ya dauke kan shi kamar shi ya rako ta, ba ita bace ta raka shi lambun ba, haka yayi ta juyata son ran shi kuma ba zaka tab'a jin ya rarrashi ta ba, asalima nuna mata yake duk abinda zata yi dolen tane. Kuma dokar shi ce. ~~~ Oman. "Matukar Noman ya ci amanar mu, toh tabbas zamu kashe shi har lahira, Sannun kanwata kinyi aikin da muke bukata, idan da mune muka saka shi yaje can ba zai yarda ba, amma da kika kawo hikimar hakan kome ya tafi yadda ya dace.... Washi na gaji. ```Book one free ne, book two da three na kudi ne 200₦ ta bank 0472282105 ki katin mtn ta wannan Number +2347035133148 ko ta wannan Number 08130269641``` [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 Book 1 Mai_Dambu BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM Page 38 "Sai na Fahimci ashe bazan iya wannan b'arnan ba, domin Mehran ya d'aga muryan shi sabida ke? Ya kuma ragewa Hoyam matsayinta tare da rage na mahaifina. Ikram na Fahimci kin yin min abinda ban ma saka ki ba, Nagode sosai. Amma ki sani baki gama aikinki ba, domin akwai mutanen da sun shigo domin daukar fansa da laifin da nayi akan Mehran." Hawaye ne ya zubo min tare da rike hannunta, bakina ya gaza furta kome kallon ta nake a hankali ta cigaba da cewa. "Sun dauke Jasrah na kawo ta ne domin tayi min aikin da kika yi sai na fahimci bata da bushewar zuciya irin naki. Bata da kome bata da kwarjini da kamala, bata da nutsuwar zuciya da ruhi, na san nayi laifi masu girma, tun daga ganin ki na fahimci kece zaki share min kuka na, amma ban tab'a sanin cewa kina da naki rayuwar ba, na zata idan kika zama makusanciya da shi zai sanya ki manta kome da kome ki fuskanci wata rayuwa, sai na Fahimci ba haka ba. Mehran yana rayuwa ne ba tare da yasan me yake yi ba, Mehran yana rayuwa ne ba tare da ya gane halin rayuwa ba, amma haduwar shi dake ya sanya fahimtar darajar da Allah yayi mishi. Shairah, zo ka mata bayanin yadda zata fahimta." "Ba zan fahimci sakon da zata shiga bayan wanda zuciyata take ciki, don Allah karki kara labta min azabar da nake ciki. Me yasa sai ni? Me yasa ba zaki zabi wata tayi miji aikin ba sai ni? Wato mareniya wacce bata da gata da galihu na shigo tsakanin ku kuna gwara kai na, meye nayi muka haka ne? Me yasa na fito karamar ahali, shin kuskure na ne ko Kuskuren kaddarata ce, me yasa kowa yake son cillani wata rayuwa na daban, meye laifin rayuwata?" Na fada da karfi ina kuka, tare da shasheka, na rasa Uwa na rasa Uba, na rasa kome nawa, sai yau kalaman Ummina yake dawo min da tace. ```Bilqusul Ikram! Duniya tana da fadi da yawa, ƙaddara mace ce da ba a san me zata haifar ba, ina ji a jikina bai zama dole na amfanar da gaba ba, amma tabbas rahamar Ubangiji yana bibiye da rayuwar wanda yayi imani dashi Karki manta! Halayyar da dabi'u suna tafiya ne kunnen doki, gashi ba zan kai ba balle nace zan so ki rayu kamar sarauniya! Zan so naga yadda zaki amshi karfin mulkin``` Ajiyar zuciya na sauke tare da kallon kasa, hawaye na zuba min, abinci ta ajiye min da kanta tare da zama a gabana, wanke hannun tayi sannan ta fara diban abincin wanda aka dafa shi da nikekken nama, tana bani a baki hawaye na zuba min, itama haka. Tare da kallon yadda idanuna suke zubda kwalla. "Ya kamata na cire wannan abun ki huta kema, ki rayu kamar sarauniya! Kinsan me ake kira da mulki? Ki zama sarauniya yana nufin ki adana darajar ki da budurcin ki ga sarki ne! Ina son ranar da ya amshi budurcin ki ya zama itace ranar da za a kiraki Sultanah Bilqisul Ikram Mustapha, ina son wacce ta iya fitowa daga yankin gabashin sahara ta mulke fararren fatan wannan yankin. Ina son izzar da nake hangowa da ikon nan ya tabbata akan ki, zama Magajiyar sarauta ba abu ne me sauki ba, idan har zai zo da sauki toh ina rokon Arzikin kar a tab'a kimar yaron can! Kar wani namijin ya kusanci nahiyar shi, ba dan Ni ba, ba dan na isa ba, ina rokon a kare budurcin shi domin cikar muradin mu, so nake ki wargaza." "Hmm!" Na fara dariya ina kallon ta, tare da cewa. "Na wargaza rayuwar su, ki wargaza nawa. Bayan nasan kome akan ku ahalin Abbasiyyah, cin amana yafi yankan takobi kaifi a cikin zuciyar ku, cin amana yafi kome faruwa a cikin gidan nan.. Wata goma sha daya nayi ina zaune daga nan zuwa nan har na isa shashin Sultan Mehran, yau kice zaki min farar dabara." "Akul Ikram! Kamar yadda zuciyar ki take cikin kauna da bege haka itama nata zuciyar take kwana da begen shi, taya hakan zai kawo karshen rikicin masarautan nan? Sultanah Fazilatul nisa ce a gaban ki kike gaya mata maganar da tafito bakin ki?" "Toh d'an daudu idan ban gaya mata ba, bari na tashi nayi rawa saboda ina murnan kun kashe min rayuwa? Jinka dan an haife ni a karamar ahali zai hana na kasa kwatar kai na ne? Tab kayi kad'an ka kasa," na faɗa. A madadin naga fusace ko fushi sai murmushi nake gani me hada da zubar hawaye, tana me mika min abincin. Kallon ta nayi sannan nace mata. "Kuka kike?" "Hmm! Eh" "Ni ne da kuka bake ce da kuka ba." Murmushi tayi bata kuma ce min kome ba. Har ta gama bani abincin sannan tace min. "Tun ranar da aka kawo ki na sami labarin irin halittar ki! Koda suka mika ki ga Hoyam nayi fatan ta dawo dake waje har akawo min ke? Idan har irin halittar jikinki Mehran zai samu. Cikin rayuwar shi tabbas sauran tarkacen da ake shirin zab'a mishi su. Sunyi asarar babba. Ni nan zan shawo kanki yadda zaki rike duniyar shi, ki zama kece a ranshi ko a ina ne!" Daga haka ta bar falon, tare da kallona. "Ni budurci na da Ni kaina, na Noman ne" Cak ta tsaya sannan ta juyo ta sake min murmushi, kafin ta wuce abinta. Ihu da bori nayi ta musu, tare da ture kome, babu wanda ya kuma bi ta kai na, wato ga mahaukaciya. ~~~ Duk wanda yake tare dashi sai ya fahimci, halin da yake ciki, duk wannan kuzarin da mulkin babu, sai dai ya koma musu wani irin masifaffen mutum, d'an kuskure idan aka aka mishi zai saka a kai mutum gidan horo, Mutumin da yabar giya, sai gashi ya dawo da shan giya sama da ruwan shan shi, a hankali Sultanah Hoyam ta shiga turo mishi yan mata, a duk lokacin da yake buge zata saka a kawo mishi mace, amma dake har cikin ranshi bayan son haka bai tab'a afka musu ba, haka zai gama shaye shayen shi, har ya yayi barci babu abinda yake hada shi da mace. A duk lokacin da ya farka zai zauna yayi ta kallon kanshi a madubi, Sabida tashin hankalin da yake zuciyarshi. Kasawa ne ace macen da take karkashin kulawar shi wani namijin ya zo ya dauke ta, Zubewar mutuncin shi ne da na daular shi, sannan kamar watsawa kanshi kasa yayi a ido, me zai cewa Mahaifiyar shi, idan ta mishi gorin wani namijin ya kwace mishi macen da take karkashin kulawar shi? Me zai cewa mutanen fada da kowa ya gama sanin ya kawo tane dan tayi goggaya dasu, me zai cewa Fudail da ya raba tsakanin su, lallai akwai tashin hankali a gaba kadan. Tunda ya saka aka kai ta kebantaccen shashi, da kanshi ya shiga fita niman Noman. Baya tashi fita sai dare, haka yake bin gidan baki, kullum sai ya fita, a irin haka, har ya isa wani gidan baki dake wajen gari. Suna cikin hira, ya shigo gidan. Kallon shi suka yi tare da cewa. "Waye kai?" "NOMAN nake nima?" Mik'ewa yayi sannan yace mishi. "Gani nan" "Ko za muje waje?" "Toh!" Fita suka yi Sarwat zai bisu Noman ya hana shi. "Ka zauna babu wani abinda zai faru." Yana fadar haka ya bi bayan Mehran, har waje..yana tsaye, a hankali ya nufa gaban shi.. "Gani nan!" Shiru yayi yana kallon shi, meye noman ya fishi da har Ikram ta zabe shi akan shi? Tab'e baki yayi sannan ya cigaba da abinda yake, kan shi a kasa yana wasa da gashin kan shi, cire mayafin fuskar shi yayi tare da d'ago kan shi, yana kallon Noman. Maza irin gurjiya, ba gaba da gaba ba, ko ta bayan sai an shirya, ja da baya yayi, cikin nutsuwa da mamaki tare da sauke kan shi ƙasa. "Kana bukatar gabatarwa ne?" "A'a Sultan Aamaan Mehran! Bana bukatar gabatarwa, Abinda yake gurin ka nazo amsa." "Ko?" Ya faɗa a sanyayye, yana kallon Noman. D'ago kai Noman yayi yana kallon shi, yana girmama al'amarin mulki, yana ji a bakin mutane yana da Izza, yau gashi ya gani da idon shi, domin kuwa maganar ma ya kasa bashi lokacin shi yayi magana. "A bisa adalcin da zan maiay, shine zan saka gobe a kawo maka kyauta na musamman, daga dangin zinari, lu'ulu'u, da wasu abubuwan bukata, ka bar min ita! Kayi tafiyar ka duniyarka, idan ta nutsu zan kawo ta taganku. Ita din muradina ce." "Gaskiya wannan adalci bane, ba zan iya fansar da soyayyar mu akan kananun abun duniya ba. Kabani ita na koma da ita, kamar yadda tazo." Inji NOMAN, .ware idanun shi yayi tare da kurawa noman, a hankali ya dage takobin shi. Tare da zare ta daga kubenta, a hankali yace. "Da alamu zan aika ka inda ba zaka dawo ba." . "Idan har akan Ikram ce tabbas sai da na rasa rayuwata." Cikin fushi da fusata tare da d'aga takobin, aikuwa aka fara iska, me ƙarfi tare da alamar garin zai iya samun ruwan kankara ko kuma dusar ƙanƙara. Azzabbrn yaki ne ya sarkafe a tsakanin su, kamar zasu hallaka juna. --- A firgice na farka sakamakon mafarkin da nayi Noman yana yaki da Mehran, ina tashi ban Nime izni ba, nayi ficewa ta tagar gidan. Gudu nake sakamakon iskar da take kad'awa, shashin Mehran na nufa, da Fudail na hadu. "Ina Mehran?" "Ya fita niman Noman?" Hannuna dukka biyu na saka a bakina, tare da kallon shi. Na kasa magana, da gudu na juya ya rufa min baya, haka muka yi ta zaga gidajen baki har Allah ya nufa muka isa wajen gari. A jikin wata itacce na tsaya ina maida numfashin da ya taso min, fada suke na tare da jima junan su ciwo. Walkiyar da aka yi ne ya sakani ganin yankar da Noman yayi mishi a hannun shi, shi kuma Noman a gefen kirjin shi, jini na zuba musu, duk da shi Mehran yana tsaye ba tare da ko layi kamar Noman da yayi taurin kai yana son kare martabar SOYAYYAR SHI. Shiga tsakiyar su nayi bayan sun kawowa juna mummunan sara. "Ya isa! Noman karka manta ina tare da kai, ina sonka amma bayana nufin zan Barka ka hada dantse da Sultan MEHRAN ba, shi din kamar Yaya ne a gare ni, kuma Uban gidana ne." Juyawa nayi tare da kallon Mehran, na sunkuyar da kaina ba. "Kayi hakuri! Yayi laifi da ya tako har sansanin ka domin farauta. Sai dai kuma kasan cewa, idan me guri yazo dole me taburma ya nad'e, kayi hakuri." "Ba zan yi hakuri ba, sai dai ki sallame shi, idan ba haka ba ajalin shine ya kawo shi daulata." Yana gama fadar haka ya juya tare da barin gurin, kallon Mehran nayi tare da juyawa na isa gurin da Noman yake kokarin faduwa, na rungumo shi, tare da sake kuka me cin rai ina cewa. "Me yasa ka fara tinkarar shi da yaki? Waye ya gaya maka cewa shi din gama garin mayaki ne? A cikin wannan lardin Noman don Allah karka kuma wannan kasadar." "Ba zan tab'a bar mishi ke ba ba, wallahi ba zan Barki ba, wallahi ko mutuwa zanyi sai na tafi dake, dan haka ki koma ki shirya akan idon shi zan tafi dake, wannan shine magana ta" *Toh fa 🤔☹️ inda ba kasa nan ake gardaman kokuwa* ```Book one free ne, book two da three na kudi ne 200₦ ta bank 0472282105 ki katin mtn ta wannan Number +2347035133148 ko ta wannan Number 08130269641``` #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 Book 1 Mai_Dambu BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM Page 39 _Daga wannan Pagen din insha Allah wanda zai zo shine karshe!_ Taimaka mishi nayi ya mike tare da kai shi dakin shi, muka shiga bashi taimakon gaggawa, saboda yankan da aka mishi, har jinin ya tsaya, sannan na lalle shi tare da Mik'ewa zan fita yace min. "Me yasa min fuskar ki?" Shafawa nayi sannan na ce mishi. "Babu kome!" Gyada kai yayi sannan ya koma tare da kwanciya da kanshi yana fadin. "Kar ki manta da tafiyar mu," "Insha Allah! Sai da safe!" Na juya tare da ficewa daga dakin, ina fitowa waje na hango Fudail. A hankali na karasa gare shi, sannan muka nufi cikin garin. "Me yasa ba zaki iya tafiya ba, ga damar tafiya amma ba zaki tafi ba! Ko kina tsoron Mehran ne kar ya saka a kashe ku?" Kallon shi nayi na wasu dakikai, sannan na cigaba da tafiya na, tare da kallon gabana. "Haba Wakiliyar Mehran, me yasa ba zaki amsa min ba?" Ya faɗa cikin raha da Tsokana, "Tausayin MEHRAN nake ji! Shi ya hana ni tafiya, da tun tuni nayi tafiya ta." "Ko kema kina son shi ne?" "Ko kana kishin shine?" Na fada ina murmushi tare da tsare shi da ido, fisgo ni yayi tare da hadani da jikin wata bishiya, yana kallon fuskana da nake kallon shi babu tsoro. Kan shi ya sunkuyar zai hada da fuskana nayi maza na kare hakan tare da kai mishi duka. "Ni ba kazama bace! Na haɗa jiki da shugaban ka, kuma na hada da kai wannan shine kolokuwar cin fuska da mutuncin Aamaan." Na fisge kai na, tare da mai da hankali na akan tafiyar da muke. Duk yadda yaso su fahimci juna taki asalima kamar bada ita yake ba, ga shegen kwarjinin da tayi mishi. .... Koda na shiga keb'entaccen shashi, na sami Sultanah Fazilatul nisa a zaune tana kallona, bata ce min kome ba, har zan wuce tace min. " Me yasa kike rusa shi daga kasa? Abinda kike aikatawa zai ja a dakatar dashi na tsawon shekaru uku zuwa goma. Abinda kike bukata ba zai samu ba, idan har kika sake kika bar masarautan nan, tabbas Aamaan zai iya fuskarta tsigewa daga muqaminsa. Tare da mai dashi daya daga cikin masu jiran gado. Don Allah Karki janyo min abin kunya da tashin hankali, sannan zai fita daga cikin gidan sarautar har sai ranar ya dawo da martabar shi. Duk da ba laifi bane hukunci ne laifin da ya aikata, na girmama Baiwar shi sama da dattawan Fada. Don Allah Karki saka ni asarar duk faffutikar da nayi, domin zasu mai dashi wancan fadar da yake wancan dajin ne. Gashi bai da goyan bayan gwamnatocin shi. Bai da goyan bayan mahaifina bai da goyan bayan Hoyam, kuma ba lallai bane sauran mutanen fada su taimaka mishi, don Allah Karki ja min asara biyu." Kura mata ido nayi tare da kallon yadda take cikin tashin hankali, sannan nace mata. "Wai ke meye Matsalarki da Shine? Ina ruwanki dashi ne? Meye nufinki akan shi Ni kam ma zargin ki nake, Wacece mishi ke?" Wani irin rugugi garin yayi tare da sake wata irin tsawa, wanda ya haifar da walkiya me shegen haske, tare da haska ko ina,cikin d'aga murya tare da izza me hade da iko tace min. "Nice Mahaifiyar shi!" Wani irin tsawa aka kuma bugawa me shegen ƙarfi wanda ya saukar da wani irin ruwan sama babu kakkautawa, ta tako gabana tare da kallona. "Tun daga lokacin da kika iya dukar Jasrah a cikin gidan nan, maganar Uwaisul Qarni ya tabbata zaki zo taimakona!" Da sauri na kalle ta tare da sake baki na. "Kinyi mamaki ne? Bayan na tabbatar dake ma kin san shi? Ba abin mamaki bane, haka bai wadatar dake ba, sai da kika yi mata duka ta kasa koda amsar kanta. Sannan Ni nasan cewa ke ba daga karamar ahali kika fito ba, amma bansa daga wani ajalin kike ba. Ba zan miki dole ba, sai dai ki sani kece kika kunna fitilar Mehran! Kuma kece kika kashe fitilar Mehran, nasan koda na hanaki ba zaki hanu ba, amma bana cire rai da rahamar Ubangiji, zaki dawo gare mu." Har ta isa bakin kofar ta, tace min. "Ki tuna uwar da aka rabata da D'anta, aka kuma saubanta rayuwar shi domin Muradin rai! Ki tuna irin kukan da uwa take a duk lokacin da aka ce mata D'anta Ya faɗa matsala, ki tuna uwar da take faffutikar rayuwar D'anta ya inganta. Nasan nayi laifi mafi girma a rayuwa ta, iya haka idan Ubangiji ya barshi a matsayin hukuncina yayi min gata, Ban tab'a kisan kai ba duk kuwa son mulkina, amma ina ji ina gani aka daura min Sharri yau kimanin shekaru talatin da takwas ina nan! Nagode Ikram!" A hankali na duba a azurfan da ya bani, tare da kallon shi a raina ina cewa. *Ina son ganinka!* Sanyin da ya kuma dawowa cikin falon ya sani zuɓewa a gurin ina sauke numfashin wahala. "Jikata!" Da sauri na mike tare da kallon shi. Murmushi nayi sannan na bude baki zanyi magana yace min. "Nasan ba zaki tab'a fadan Alkhairi ba, abinda ya kawo ko nan min zo ne ki gaya min wato hada miki baki muka yi ko?" Yayi murmushi sannan yace. "Ko daya! Sai dai idan kika bar daular nan a cikin kwanakin nan,. Zaki yi ta fadawa hatsari har sai kin dawo gare shi. Zaki fuskanci meye asalin rayuwa! Zaki yi kokarin ganin kin dawo amma ina daular tayi miki nisa kafin ki cin mishi. Ina miki murnan sabuwar rayuwar da kika zab'e fatan Alkhairi, a duk lokacin da kika Fahimci tazarar da take tsakanin ku zaki iya nima na, kai ki ambaton Allah kika yi sau uku sannan kika yi tawwasali da fiyayyen halittar Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama, zaki ganni amma kafin nan. Kamar yadda rubutu baya dama a saman Teku haka zaki ji kome ya tafi. Kina zarra da kika gada a gurin Almustapha! Kina da Izza da kika gada a gurin Joindatullah! Jinin Amratu yana yawo a cikin jininki, ki shiga duniya niman nasabarki, nan zaki gane falalar da Allah yayi miki ya ajiye ki a cikn wannan daular." Daga hana ya juyar da hannun shi, tsintar kai na ayi a falon, tab'e baki nayi a raina nace. *Daka hanani magana sai me?ba zan zauna ba* Gyara kwanciya nayi a gurin ina cewa. "Yau nasan bani da arzikin kwanan daki" dan haka na yi kwanciya ta. ~~~ Tunda ya shigo gidan ya zauna tare da tari, jini ne ya shiga fita ta hancin shi da bakin shi, kafin ya sami damar dafe kahon zuciyar shi da take mishi zafi kamar an kunna wuta. Shigowar da Sultanah Hoyam tayi tare da ganin shi a cikin wannan yanayin, da sauri ta kira Darakshan ya kira mata likitan fadar. Ba a bata lokaci ba, aka tawo dashi. A hankali ya shiga duba lafiyar shi,. Ya jima sosai akan shi kafin ya koma kasa tare da saka hannun shi a cikin jinin da yake kasa, murzawa yayi sannan a hankali ya juya tare da kallon Sultanah Hoyam, yace mata. "Ranki shi dad'e! Ai matsalar da ake samu zuciyar shi ce take ciwo! Akwai abinda yake b'oyewa a ran shi wanda ya haifar mishi da ciwon zuciya. Ku tabbatar ya gaya muku, idan ba haka ba tabbas zaku iya rasa Sultan Mehran har abada, domin ciwon tayi mishi mugun kamu." A hankali ya gama musu bayani sannan ya dauki yar jakar shi bayan ya basu maganin da zasu bashi, bayan tafiyar shi itama Sultanah Hoyam ta koma b'angaren ta, aka bar Fudail da Rakshan, suka zauna dashi bai farka na, sai tsakiyar dare. Ruwa suka bashi ya sha sannan ya koma zai kwanta ya kalli Fudail. "Ina take?" "Baka da lafiya Mehran, ka kwanta ka huta." Lumshe idanun shi yayi sannan ya kwanta tare da Cigaba da barcin shi. ...... "Me yasa ba zaki zauna dani ba." Bai tab'a zaton zata iya daukar wani abu ta illata shi ba, sai yanzun da ya gani da idanun shi. "Me yasa Qurratulain? Mutuwa ta itace fansar ki?" Ya faɗa dai-dai hawaye na zuba daga idanun shi. Jini yana zuba daga kahon zuciyar shi. Gashin kanta ya rufe fuskarta, kayan jikinta ya jike da jini jagab. "Kin san iya adadin lokacin da nayi ina dankon ki? Me yasa Qurratulain bata bincike Ni ba?" Shigowar wasu mutane da jajjayen kaya, hannun su rike da takuba, suka mata zasu yi cikin sani irin zafin nama, ya juyar da ita tare da cillata saman kujeran mulkin shi, sannan suka soka mishi takuban su, dukkan su bakwai har sai da takuban ya fito ta kowani kusurwa, zare wukar da ta soka mishi a kirjin shi yayi tare da tasa wani irin ihu. Sannan ya watsar da takuban da suka soka mishi, ya juya da wukar yayi ta kashe su, yana gamawa ya isa gaban ta, tare da zuɓewa a gaban. Ya daura kan shi akan cinyarta. Garin yayi wani irin Ja, tare da zubar jini ta ko ina, kamar ruwa, hayaki yana tashi a wajen garin, kukan al'umma da na dabobbi ya yawaita, kamar zasu fasawa mutane dodon kunne. "Ki sosa min kai na." Hawaye ke zuba daga idanun shi, yana jika cinyar ta, itama kuma hawaye ke zuba mata, tare da fashewa da dariya. Ta ture kanshi, tare da fasa ihun da sai da tagar da suke cikin fadar na glass suka yi ta fashewa, tare da zuɓewa akan gwiwar ta. ..... A firgice ya farka tare da dafe goshinsa,. Yana mamakin wannan mafarkin me matukar girma da muni. Sanyin asuba ne yake ratsa jikinsa. Ya lumshe idanun shi, tare da jin kiran Sallah daga can nesa, murmushi yayi sannan yana hango yadda take sallah. --- A firgice ta farka tare da sauka a gadon ta fito falon da Ikram take zaune itama zufa take,cike da tashin hankali,kallon juna suka yi sannan Sultanah Fazilatul nisa tace mata. "Kema mafarkin kika yi?" A tsoro ce tayi tambayar, Cikin fitar numfashina na kalle ta, sannan nace mata. "A'a!" "Eh shi kika yi! Idanun ki basu boye karya, sabida baki iya ba, kin iya boye damuwa ban da karya, mafarkin rushewar daular kika yi ko?" Ta faɗa cikin kuka tare da kallona. "Eh!" Na bata amsa a takaice, ina shakkar abinda zai biyo baya. Juyawa tayi tare da rufe kofar, alola tayi sannan ta gabatar da sallah nafilla, tare da kiran Uwaisul Qarni. "Sultanah! Ku barta ta tafi! Karki kuma dakatar da ita, Insha Allah, Allah zai sauya kaddarar shi, amma babu makawa kaddarar su a haɗe take, ƙaddarar shi ya shiga nata, haka kuma na nata ya shiga nashi. Zata dawo amma ban san lokacin ba, ban san me zata dawo yi ba, Allah ya sani. Shi zai kawo mana karshen rikicin masarautan nan. Rabo me tsannanin zai dawo da kome a kuma Cigaba da abinda aka dakatar. Shi kuma kiyi hakuri Insha Allah zaki sha mamakin yadda kome zai sauya. Zai baki damar samun D'anki a hankali kuma a hannunki. Karki manta Addu'o'in da kika yi ta mishi a baya shine zaki Cigaba da mishi har zuwa lokacin da rayuwar shi zata yi kyau mafarkin ku da kuka yi Allah ya fahimtar dani wani abu kan shi. Ki barta ta tafi, idan kuka sake ta zauna ba mamaki hakan ya faru ,na barki Lafiya." Gyada kai tayi tare da sauke ajiyar zuciya, abu biyu lokaci guda, farin ciki da bakin ciki, bata kuma zazzafa tunani ba ta cigaba da ibadarta kamar yadda ta saba. ~~~ Bayan wasu kwanaki abubuwa sun faru, a cikin shi har da mai dani shashin sa, zai sakani a gaba yana kallona, ina juyawa zai dauke kan shi fuskar shi a nanike, tab'e baki nake na cigaba da abinda nake, tunda dan bakin mulki dawo dani Office din cikin gidan yayi tare muke zuwa kuma muke kome, yayi ta wani cin magani kenan. Yau saura kwana uku a fara hidimar zab'ar matan da zasu zauna kafin su saba ayi maganar auren shi.... ---- *Wayyo Allah na! Labarin nan bai zama dole ya kare 40 ba maybe mu kara koda page 2 ne akan Free Pages din* ```Book one free ne, book two da three na kudi ne 200₦ ta bank 0472282105 GTBNK Ramlat Abdulrahman Manga ki katin mtn ta wannan Number +2347035133148 ko ta wannan Number 08130269641``` #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: ᎠᎪႮᏞᎪᎻ 𝘉𝘐𝘠𝘜 Book 1 Mai_Dambu BISMILLAH RAHAMANI RAHEEM Page 40 *Last free Page" Wato tun da na dawo nake lura dashi bai da lafiya, sai dai yaki bani damar fahimtar haka, zan ga wani lokaci yana amai, ina zuwa zai dauke kan shi tare da k'in juyawa ya kalle ni. Yau ma da ake ta kawo mishi kayan da zai saka na zab'en tsaye yake tare da wani farin tsuma, juyawa yayi tare da kallon inda nake tsaye, nima na juya bayana tare da jin ba dad'i. "Sultan wannan zai yi kyau! Sosai sannan zai dace da rana irin ta jibi ko Ikram?" Darakshan ya tambaye ni. Murmushi nayi sannan nace mishi. "Zaifi dacewa da wancan itace kalar maza, sannan wannan kuma shigar mutanen Sham ce." D'aga kayan aka yi tare da nuna mishi. "Bana bukata!" Ya faɗa fuskar shi a haɗe, dole zai min haka, amma kuma bai dame ni ba, haka na wuni suku suku, da magariba ina zaune na saka abinci a gaba, ina kallon shi ya shigo abin shi bai kalle ni ba, sai dai naji yana tari. Koda na isa tare da bashi ruwa buge hannuna yayi sannan yace min. "Bana bukata!" "Wai meye nayi maka ne?" "Baki san me kika yi ba? Toh tashi daga nan" "Amma Aamaan me nayi da zafi ne rayuwa kowa na da nashi ra'ayin da kuma abinda ya zab'e me yasa kake son tilasta min na zab'i abinda ba zai amfane Ni ba?" Idan dutse zai magana Mehran zai yi magana, shan giya yake hankali kwance, har ya fara buguwa kallona yayi tare da nuna ni da yatsar shi. Mik'ewa yayi tare da nufo ni. Mikewa nayi zan gudu ya saka min kafa, na fadi zai juye min ruwan na buge hannun shi tare da mik'ewa. Wani irin fada ne ya shiga tsakanin mu, duk da Ni kare kai na nake shi kuma so yake sai ya kai ni bango, take min kafa yayi na maza na sake shi. Ya hada ni da bango. Tare da d'ago kai na. Kokari yake mu hada idanu amma naki kan shi ya kai wuyana tare da kai baki shi yana sumbatar wuyar.. rike rigar shi nayi tare da ji kamar zan zube ƙasa, Matse ni yayi tare da d'ago haɓɓa na, kai fuskar shi yayi nayi saurin rufe idanuna, jin saukar numfashin sa akan fuskana ya sani bude ido na, a hankali. Sai cikin nashi Idanun. Kasa janyewa nayi ina kallon shi da kyau, tare da karanta sakon shi a sanyayye. A hankali zaka Fahimci inda ya dosa, tare da duk wani abinda yake tattare cikin idanun shi. "Mehran! Me kake SO?" "SO! Ban tab'a son abu na daban ba, dan haka ba zan tab'a yarda naso abinda ba zai kai ni labari ba, kina da damar tafiya duk inda yayi miki. Sai dai alqawari na tabbatacce ne, domin zan kashe shi!" "Akan me? Nice na dace da mutuwa ba shi ba, karka tab'a min shi. Domin ba zan tab'a yafe maka ba idan jinin shi ya zuba a banza!" Na fada mishi tare da kwace kai na, daga gare shi. Ina jin kwalla na zubo min. ..... Washi gari. Ana gobe zasu yi zaben shima kuma yana na shi shirin, a baya an sa taron sai dare ne, amma ya maida abun yamma, dan haka an Kawata fadar da ko ina gwanin ban sha'awa, tare da gyara ko ina, murmushi nayi ina jin wani irin yanayi yana shiga na, daga nesa yake hangota, yau tafi mishi koda yaushe kyau da kamala, kallon yadda take murmushi iska yana kad'a rigar jikinta tare da baza gashinta dake baya a zube cikin nutsuwa. Lumshe idanun shi yayi tare da tuno sunan da ya kirata da shi a mafarkin shi, dafa kirjin shi yayi tare da sauke ajiyar zuciya yace. "Qurratulain!!!" Ya kira sunan a hankali, kamar wanda yayi kiran da karfi sai da ta d'ago kanta tana kallon inda yake, tsuke fuskar shi yayi alamar baya kaunar tana kallon shi ma, Table baki nayi sannan na dauke kai na, tare da kallon kasa indai wannan mutumin bai daina min tijara ba, zai ga tsiya iya ganin idanun shi. Murguda baki nayi tare da dauke kai na, daga kan shi. ..... "Ku saka idanu akanta, ku nutsu ku duba ta inda zai shigo, idan kuka ganshi, ku kashe shi!" Yana gama fadar haka ya juya abin shi. Bin bayan shi da ido Fudail yayi shi kadai yasan meye yake ranshi. Ya kuma kara sanin cewa dole ya dauki mataki kan duk wanda zai kawo mishi cikas. Tun tasowar shi yake bauta mishi ba tare Ya tab'a bijire mishi ba, sai dai wannan karon sunyi tarayya akan Abu daya suke so! Kuma ba zai iya hakura da ita ba sabida shi ba, sai dai a rasa kowa wannan shine kudirin shi akan Mehran, ba zai tab'a bari a cutar da shi ba. Amma kuma ba zai taba barin shi da Ikram ba, itama ta sami abinda take so shine adalci. Ya kwana da sanin akwai masu son kashe Mehran amma basu sami damar idda nufin su ba, saboda kwarjininsa da kaifin shi. Ya sani ko a cikin taron su na masu kula da lafiyar shi, akwai mutanen da yake zargi, yazo jikin Mehran ne saboda Sultanah Fazilatul nisa,. Daukar fansa mahaifin shi Rizwan, Darakshan kuma ɗan Amir Fujai, Yasan cewa dukkan su Abu daya suka zo yi, amma baya fatan su sami galaba akan Mehran, duk da yasan ba lallai bane su fahimci cewa Mehran bai san kome akan Mutuwar Iyayen su ba, akwai wasu suna nan zuwa kuma yasan fansa zasu zo dauka. Matukar basu so a gobe ba zasu cigaba da tanadin fansa har zuwa lokacin da hakan ya zo musu. Duk da yasan mahaifin shi babban mashawarcin Sultan Abdus Samad ne, bai tab'a kawowa har zasu zubda jininshi sabida rashin imani ba, sannan yadda ya kasa fahimtar kome, ance Fazilatul nisa ce ta kashe Sultan Abdus Samad,. Toh meye mahaifin shi yayi aka kashe shi? Babu makawa yasan abinda aka shirya ne, kasancewar shi ma shawarci a cikin gidan. Kuma babban Aminin Sultan Abdus Samad. Akwai abinda ya kasa fahimta sam,.sai yanzun ne yake ganin beken shi na zama har na tsawon shekaru kusan ashirin babu wani abinda ya karu dashi. Ajiyar zuciya ya dauke tare da sunkuyar da kanshi, yana kallon ƙasa. --- A shashin Sultanah Hoyam, kuwa rutsa Darakshan tayi tare da gyara zamanta tana kallon shi cikin nutsuwa sannan tace mishi. " Har yaushe zaka Cigaba da had'iye fansar ka?" Ta d'aga kafa daya ta daura akan daya cikin wani irin yanayi take kallon shi, sunkuyar da kanshi yayi sannan yace mata. "Sultanah, ke Mahaifiyarshi ce kuma ban san me yasa kike son lallai sai munyi mummunar alaƙa ba, zai fi kyau ki sare kai na, da cin amanar da kike son nayi." Tasowa tayi tare da nufar shi tana shafa fuskar shi, tare da zagaye hannun ta, akan fuskar shi har ta sami damar tab'a mishi agogon karfen shi, zillo yayi mata sannan ta sake murmushi. "Zaka iya daukar fansan mahaifinka?" "Zan iya!" Ya faɗa jikin shi yana rawa sakamakon rike shi da tayi, kamar zai fasa ihu, sannan tayi kokarin dai da suka fada gadon, tare da kallon shi. Sannan yace mata. "Sultanah Hoyam, ki rufa min asiri." "Zan kara maka matsayi! Sannan kai ma zan fitar da kai na nuna musu kai jinin sune d'a ga Fujai. Idan kuma kaki yarda tabbas sakamakon ba zai mana kyau ba!" Jikin shi yana rawa, tare da rintsa idanun shi, haka tayi ta aiki da tsarin shi tare da bawa ranta da zuciyarta abinda take kwadayin samun shi, tunda yake ko bayi bai tab'a jin yayi wani abu dasu ba, amma yau ga Sultanah Hoyam tana amshi mishi samartakan shi, tare da sarrafa shi yadda ranta yake so. Gaji sosai, dan akan ta ya fara sanin mace, amma bai tab'a sanin zata iya sarrafa shi har haka ba, idan ya duba yadda ta manyanta. Kwanciya tayi a jikin shi tana fidda numfashin wahala, ta kalle shi sannan tace mishi. "Kana da dadin mu'amala, ban yarda ka ajiye ko baiwa ba, dan yin haka zai iya haifar mana da tarzoma, Ni daya ce a ranka kuma zaka Cigaba da ajiye ni " Ta fadi haka tana me mik'ewa daga jikin shi, ta nufi ban dakinta tana me gyara jikinta. --- tashi yayi tare da barin d'akin, ya saka kayan shi. Sannan ya nufi gidan shi, ya kwanta, kuka ne ya kwace mishi yazo ne daukar fansa mahaifin shi da taimakon Sultanah Fazilatul nisa, ya shigo fadar amma ita bai gaya mata fansa yazo dauka ba, bai san ta yadda zai gayawa mutane abinda ya kawo shi ba, dan bai yarda da kowa ba, sai dai kash wannan tsuhuwar mayyan ta lashe mishi tanadin shi akan matar shi da zai aura. Babu wanda yasan cewa yana cikin Amirai na cikin masarautan sai ita,.tabbas akwai dan leken asirin a cikin daular baki daya. Dan haka dole ya sake lalle, kuma zai sake jiki da Sultanah Hoyam domin ya samu daukar fansa mahaifin shi akan D'anta. ~~~ Yau tun safe ya kasa yin kome kasancewar yau za ayi zaben yan matan da zasu zama matan shi da wanda zasu zama Kwarkwarorin shi, had'iye yawu yayi lokacin da ta shigo sanye da doguwar riga, kanta yane da mayafi, tana ta murtsika hannun ta, duk sai yaji duniyar tai mishi fadi da kankanta, kallonta yake yadda ta sunkuyar da kanta, hawayen da yake son ya zuba daga idanun shi ya mai da, bai Cigaba da kallon ta ba, amma kuma yana kallonta da wutsiyar ido. "Har ila yau kina nan akan bakarki?" Mutsuke hannuna nayi tare da d'ago kai, ina kallon shi. "Mehran!" Ajiyar zuciya ya sauke tare da nad'e takardun hannun shi. Ya watsar a kasa, sannan yace. "Hmm" Ya mike tare da nufar kofar fita daga ofishinsa na cikin gida. "Har yanzun kina da damar, sauya tsarin ki?" "Aamaan Mehran! Kai adalin shugaba ne, kuma nasan zaka min adalci, Aamaan ba zan hana ka ɗaukar matakan da suka dace a kai na ba. Amma matakin da zaka dauka ya tsaya akai na. Wallahi na rantse tsarkin mulkin Allah, zan kashe ka. Zan tawo na soka maka wuka anan din da ake dafewa kullum Noman shine zab'ina karka sake mu hadu a matsayin Fure cikin Ƙaya!" Ina gaya mishi haka na juya abuna tare da barin gurin shi, so yayi mishi illa da ba zai iya hukunta ta ba, ya gaza fahimtar me yasa baya iya mata hukunci yanzun idan tayi mishi laifi. Lallai ta cancanci kyautar da ta dace, dan haka ya cigaba da tsayuwar shi a gurin har zuwa lokacin da aka fara kokarin fara taruwa, Lokacin da aka fara gabatar da zab'en ne, Noman suka fito daga cikin gidan sarautar shi da Ikram dai-dai lokacin da ake gabatar da sunan ta a matsayin shugaban Kwarkwarorin shi, tana rike da hannun Noman. Kallon kallo suka yi da Mehran, tare da Abrad da yake tsaye, sai Nawwas da Fudail shima yana kallon su. Sai Zuhair wanda shima ya gama kaduwa. Dafe kirjin shi yayi tare da kallon lokacin da Noman ya rike hannun ta, bayan ya haura doki ta haura bayan shi. Sannan ya sukwane dokin da mugun gudu, mik'ewa yayi a hankali, shi kanshi bai san yana zubda jini ta hanci ba, sai da Fudail ya rike shi. "Idan kuka kama su, ku sare min kanshi da hannun shi da ya rike ta, sannan ku kawo min ita. Nan." Gefe Abrad yaja Nawwas ya mishi magana, sannan suka fita da gudu tare da bin bayan su. Tafiyar minti ashirin ya kai su gabbar ruwa, suna zuwa suka sami Sarwat da jirgi yana jiran su, babu b'ata lokaci suka bazama. Suna yin nisa suma Dakarun SAMAIND da na Oman suna isowa. ~~~ "Abisa fifita baiwar ka sama da sauran danginka, Hukumar masarautan nan su shaida an dakatar da Aamaan Abdus Samad Mehran na biyu,na tsawon shekaru goma." Dafe kirjin yayi tare da mik'ewa dakyar kamar zai fadi, aka tare shi. Cikin gidan aka nufa dashi, murmushi Sultanah Hoyam tayi tare da kallon Amir Hood, da sauran gwamnatin kasar. `~` Tafiyar awa shida muka yi akan teku muka b'acewa ganin su, sai da muka isa gabar Asakandariya Noman yacewa Sarwat. "Kai juya akalar zuwa Istanbul." "A'a nidai nan yayi min!" "Kika ce yayi miki?" Gyada mishi kai nayi tare da murmushi. Shiru nayi ina kallon shi, _MEHRAN!!!_ zuciyata ta ambace shi. "Tunanin me kike?" Murmushi nayi sannan nace mishi. "Babu!" A takaice. "Na zata ko na wancan wawan ne" kallon shi nayi tare da jin zafin kalaman shi. " A'a ba wawa bane, don Allah mu mutuntta juna nan mu!" Daga haka na sauka a jirgin, domin naji zafin abinda ya faɗa akan Mehran, sai da nayi nisa dashi ne nake tunanin shi, duk ya ban tausayi, duk da bai fito ya ban hakuri ba, amma tabbas ya roke ni na zauna dashi, ta hanyar saukakka muryan shi akan barina gurin shi. A takaice dai haka muka shiga cikin garin, tare da niman gidan wani limami, ana sallar isha aka daura aurena da Noman Anwarulkharim, auren da ya biya sadakina da silallan zinari, ...... Bayan sun sama mana gidan da zamu zauna, nan da kwanaki kafin mu wuce Istanbul, shigowa yayi tare da kallona yana murmushi. Bana jin dadin rayuwa kawai na amshi auren ne matsayin abinda zanyi na faranta mishi. Dan haka bayan ya kawo mana abin Musa baki muka ci, nan yaja mu Sallah, kasancewar shi mutum masanin addinin Musulunci. Ya jima yana mana addu'a, sannan muka shiga hira tare tuno alkawarin mu. Mun shagala ainun, mun yi nisan da Bama jin kira, ihun jama'an gari tare da sauke nishin da yake yi ne ya hanani fahimtar kome, Buga mana kofar aka yi tare da cewa. "Noman Dakarun SAMAIND sun iso!" Da sauri ya katse abinda yake shirin kai ni lahira ban shirya ba, domin ban san yadda zan kira azabar da nake ji a tare dshi ba, sai dai bai kai ga isa inda ya dace ba Sarwat ya dakatar da shi. Da sauri muka mai da kayan mu, sannan muka fito da gudu muka yanki daji. Ashe sun mana kofar ragone, kasancewar shine a gaba suna ganin shi suka shiga saran shi, dan haka muka yi sauran sauya hanyar mu, shi kuma ya sami damar kwace takobin hannun mutumin suka shiga yaki, domin mu gudu, ihun shi da naji ne ya sani tsayawa can, zan dawo da gudu Sarwat ya kuma damke hannuna. Ya kuma nausawa dani dajin. Allah sarki duk da hakan bai Barsu ba, yaki faduwa haka ya cigaba da yaki dasu har ya daina iya yakin, sannan ya juya dajin da gudu, sabida yaga wasu sun bin bayan su. Haka yana binsu suka saran shi. Bakin wani rami muka tsaya Ni da Sarwat. Juyawa nayi tare da jin Ihun NOMAN. "Kabar ni na tafi gurin shi." Dakarun ne suka iso gare mu, tare da noman din da ya gana galabaita da zuban jini, soka mishi takobin suka yi. Ya zube akan gwiwar shi, "Sarwat ku fada ruwan" "Kizo nan mu mai daki SAMAIND Kyautar da Sultan Aamaan MEHRAN ne ya aiko ni!" "Wayyo Allah na, Wallahi sai na sare kan Mehran!" Na fada da karfi, fisgo ni Sarwat yayi tare da tafiya da baya. Famjaaaam muka fada cikin ruwa. A lokaci guda muka nutse cikin ruwan daga nan ban kuma tuna kome ba.... ```Alhamdulillahi anan na kawo karshen Book one Book one free ne, book two da three na kudi ne 200₦ ta bank 0472282105 GTBNK Ramlat Abdulrahman Manga ki katin mtn ta wannan Number +2347035133148 ko ta wannan Number 08130269641``` #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: TWO DYNASTY'S BOOK TWO _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 01 ......... A hankali nayi ta nitsewa karka shin ruwa, idanuna a buɗe ina kallon lokacin da dakarun Samaind suka soka mishi takobi, daga nan ban iya tuna kome ba, wani abu ne ya gifta akan idanuna. Koda Sarwat ya d'aga daga cikin ruwan ya shiga niman ta bai ganta ba, haka yayi ta lallumen ta, har ya gama bai ganta ba, dan haka ya fito bakin gab'a, tare da fashewa da kuka, ya zauna a gurin har ya fara hango dakarun suna zuwa gurin shi.. cikin ruwan ya koma, tare da tsallakawa daya gaɓɓar yana kallon su, suka gama niman ta, har suka gaji sannan suka bar gurin baki daya. Komawa gurin, da shugaban su yake suka yi, bai zare mayafin fuskar shi ba sannan ya kalli Noman da yake durkushe. Zuwa gaban Noman yayi tare da jan iska, sannan ya kalli NOMAN. "Ka gane Ni?" Cikin wani irin yanayi me wahalar fadi ya kalli ya kalle shi kasancewar akwai mayafi akan fuskar shi sannan ya sunkuyar da kan shi yana murmushi. "Nasan mutuwa zan yi, sai dai ban san me nayi maka ba? Yarinyar nan dai mata ta ce! Kuma a cikin daren amarcin mu, kuka ci amanar mu! Ni nasan mutuwata, kai kuma taka mutuwar ba zata yi kyau ba!" Dariya yayi sannan ya d'ago kan Noman yana fadin. "Kaunar da nake mata ko da Sultan MEHRAN ne da Abrad ba zan bar su ba, kaunar Ikram ne ya janyo haka! Sauka lafiya, amma kuma na rufe kofar da za a zarge ni" Cikin zafin nama ya yanke makogaron Noman sannan ya juya yana kallon dajin, kafin yace. "Ku jefa shi cikin ruwa kifi su sami kalace, ina mutanen da na tura su, nimo Ikram!" Da gudu suka tawo, tare da durkusawa sannan suka ce. "Ranka shi dad'e, Bamu same ta ba, gaskiya" Wani uban ihu ya buga sannan yace. "Maza ku koma cikin ruwan ku duba min ita ki na kashe kowa" ~~ SAMAIND BAYAN KWANA UKU A hankali yake bude idanun shi, Fudail ne da Darakshan, zaune a kusa dashi. "Ina yarinyar take?" "Sultan yau! Kwanan ka uku kana sume don Allah kayi hakuri ka sami lafiya." Kallon Fudail yayi cikin nutsuwa, tare da lumshe idanun shi. "Ta tafi kenan?" Gyada mishi kai suka yi, shigowar dattawan fada ne ya sashi lumshe idanun shi. "Mehran ya jikinka?" "Jikin shi da sauki." Kallon juna dattawan suka yi tare da kallon shi. "Ka ji hukuncin da aka yanke maka?" Lashe bakin shi yayi, tare da dauke kan shi akan su. "Toh daga yau zaka koma, Darul harami, ka zauna har sai ka cika wa'adinka sai musan abunyi! Kana da damar shiga duk wani abinda ya shafi masarautar, zaka iya bada gudunmawarka ta hanyar shiga yaki ko kawo daidato, mulkin ce baka da hurumin shi, idan kuma muka sami labarin zaka dawo da karfin tsiya zamu iya yanke maka hukunci." "Mulki na Allah ne, shi yake bawa wanda yaso ya kuma karb'a a hannun wanda yaso, ba isata bace tasani samun mulki Allah ya nufa ta hanyar mulkin zan san waye shi. Sannan damar da kuka bani na zama anan shi zai kuma tabbatar min da Ni din d'an gatan Allah ne." Ya fada a hankali sannan ya dauki rigar shi yasaka, kafin ya nufi gurin da kayan shi yaƙe, zai dauka Fudail ya riga shi. Tare da hada kome na cikin gida wanda yake mallakar shi ne. "Sannan zaka iya zab'en yan matan lokacin bai kure maka ba." Murmushi yayi sannan yace musu. "Mace da dukiyarta basa gaba na!" A hankali yake hango ta ana gobe abin zai faru, iska yana kadawa tana kokarin rufe gashin kanta, wanda iska ya janye mayafin ta akan ta, yatsina fuska tayi iyaka, ana ya fahimci lafiyar gefen fuskarta, domin yaga yadda take tab'a gurin kar ya fita. Amma kuma hakan bai zo mishi ba. Bai san lokacin da ya b'ata yana gurin ba, har sai da Fudail yace mishi. "Mehran mun gama!" Sunkuyar da kai yayi tare da juyawa sannan ya gyara rigar shi, suka fito daga cikin gidan, ana tafiya da kan shi. Juyawa yayi yana kallon dakarun shi, wanda suka cire hular su. Zunzurutun girmamawa. Tunda ake sarakuna a cikin daular shine kadai yaki ayi yaki dukda kuwa members na emiraters councilors din shi suna bukatar hakan, amma bai tab'a jin a ran shi a zubda jinin mutanen shi ba. Lumshe idanun shi yayi tare da kallon hanyar da aka nufa dashi. Da farko sai kun wuce wani forests me tsayi da duhuwa, a hankali ya tsaya cak. Sannan ya kalli Darakshan yace mishi. "Gurin nan akwai macizai!" Gyada kai yayi tare da cewa. "Eh Sultan Mehran!" A hankali suka ci-gaba da tafiya har zuwa lokacin gidan me dauke da manyan katon get da tutar musulunci, murmushi yayi sannan ya kalli tsarin gidan, kamar wani Villa haka gidan yaƙe, duk da yasan akeken doki ya dace yazo amma ya zabi zuwa da kafa,.sabida yasan meye rayuwa. Dakarun sama da dari suka kwaso kayan shi, sannan aka bawa wasu dakaru kimananin dari biyar damar gadin shi, Amma an turo da wasikar cewa. Ana bukatar Darakshan a fada, kasancewar shi d'a ga Amir Fujai. Bayan tafiyar shine ya kalli Fudail da yake ta kokarin ganin ya gyara ko ina shida wasu dakarun. Bayan kamar minti goma sai ga Mahlika da wasu yan mata bayi suka shigo villar. "Ina mika gaisuwa Sultan Mehran, Sultanah Hoyam ta turo ni nazo nan na zauna da kai." Kallon shi Fudail yayi sannan ya kalle ta, yace mata. "Zaki zauna amma wa dakaru zaki kula da cin su." Gyada kai tayi sannan tace mishi. "Ina niman Alfarmar ko Aminttacen bawan Sultan zai bani damar mu kintsa gidan? Kallon Sultan Fudail yayi sannan yace mata. "An baku damar haka" Cikin abinda bai fi awa biyu ba, suka gyara gidan tare jera kome inda yake bukata, sannan ya kalli Fudail yace mishi. "Ina son nayi rayuwa kamar kowa, amma bani da alkibla, ko zaka sama min Malamin da zai na koyar dani?" Gyada mishi kai yayi, sannan ya zauna tare da kallon kasa kafin yace mishi. "Gidan nan yana bukatar maganin macizai dan naji kamshin su a ko ina" "Insha Allah Sultan zan tawo dasu yanzun," Haka ya fita daga cikin gidan, tare da nufar wajen gari, daga nan gidan limamin garin ya nufa, nan yazo mishi da batun akan abinda Sultan yake bukata. Gyada kai yayi sannan yace mishi. "Zan baka almajiri na, ka kai mishi, Insha Allah zai zauna dashi iya adadin yadda yayi muku, sannan kace gidan akwai macizai. Toh bani da wani abun da na sani akan haka ku nemi masu kama macizai, sai na kara muku da cewa kuna kona Habbatul saudat, a gidan da izinin Ubangiji kome zai bar gurin." Haka suka rabu tare da Almajirin malam, sannan suka shiga niman masu kama macizai, ana suka sami wani dattijo ya basu wani abu kamar alkama, sannan yace musu. "Ku watsa Insha Allah babu macizan da zasu dame ku" "Mun gode dattijo!" Ya faɗa tare da bashi silalar zinari. Tunda suka nufi cikin Darul Alharami, suke watsa abu me kama da alkama, har suka gama zagaye villar baki daya. Lokacin da ya shigo da alamjirin malam, bai ga Sultan Mehran ba, duba ko ina yake amma babu shi babu alamar shi. "Ke ina Sultan Mehran yake?" D'ago kai tayi tare da kallon saman villar, ajiyar zuciya ya sauke sannan ya nufi villar, anan ya same shi tsaye, ya juya yana kallon dajin da yake cikin masarautan, wasu shudadden yanayi yake ji. "Sultan" "Baka ce min.kome akan Yarinayr nan ba?" Sunkuyar da kanshi yayi kasa, sannan yace mishi. "Sun mutu!" Sake yadin hannun shi yayi, tare da ji kamar zai fadi, Fudail ya rike shi. Haki yake tare da kallon gefen shi, yadda wasu tsuntsaye suke tsalle, tare da taimakon junan su. Hawaye ne ya zubo daga cikin kwayar idanun shi daya, ya sauka akan hannun shi da yake dafe da kirjin shi. "Sultan! Kayi hakuri, ban tab'a sanin cewa kayi nisa a kaunar da kake mata ba, sai yau da ba zan taimaka musu ba, ban zama bawan kirki ba, na zama kamar sauran al'ummar da suke tawowa domin daukar fansa, sai dai nayi haka ne domin naga farin cikin akan fuskarta, banyi dan na tozartaka ba. Sultan zaka iya hukunta Ni akan laifin da na aikata." Goge kwallar shi yayi tare da cewa. "Waye ya gaya maka ina Kaunarta? Har yanzun bana kaunarta, banyi kuka dan ina kaunar ta ba, nayi kuka ne dan duniyar ta juya min baya, me yasa ta tafi bayan ta gama zagaye Ni da kome?" "Kayi maka Addu'a." Mikewa yayi dakyar yarinyar ta gama da rayuwar shi, ta buga mishi katon tambarin a zuciyar shi kuma ta tafi ta barshi da ciwon zuciya. "Zaka iya dukar bayana? Sannan a cikin dakika sittin ka daki kirjina?" "A'a Sultan ba zan iya ba?" "Zaka iya mana, karka damu kayi akwai abinda nake son ya fita ne" A karon farko da Fudail yayi tur Da rayuwar shi, tare da nuna son kai da son zuciya ƙarar akan Mutumin da bai damu da kome nasu ba, cikin zafin nama, yayi ya juya da tsananin sauri ya daki bayan Mehran, sai da ya fadi akan gwiwar shi, tare da aman bakin jini, lumshe idanun shi yayi sannan ya kuma mik'ewa, ya gyara tsayuwar shi, da sauri ya kuma dukar kirjin shi, sai da ya fadi da baya. Lumshe idanun shi yayi tare da bude shi a hankali. Iska ne ke kad'awa da wani irin saib'i, kamshin turaren miski da take sakawa ya cigaba da kad'a wa a iskar, lumshe idanun shi yayi tare da juyawa gefen shi da ake mishi magana, Fudail ne yake mishi magana amma idanun shi nuna mishi Ikram yayi tana dariya tare da mika mishi hannun ya mik'a mata kenan Fudail ya d'ago shi yana faɗin. "Sultan!" Kamar wanda ya tashi barci haka yake kallon Fudail, tare da kallon gefe da gefen shi, tayi ta fara har ya samu yayi aman gudan jinin, rike shi Fudail yayi suka koma cikin gidan, ya zauna a wani kujera me kyau irin na sarakai. "Sultan wannan shine Almajirin da Malam ya bani na kawo maka shi!" "Meye sunan ka?" Fudail ya tambaye shi. "Abul Bashar!" Shiru suka yi dukkansu, sannan Mehran yayi gyaran murya, "Ban san yadda zan bautawa Allah ba" ya faɗa irin in sound tone, kallon shi suka har da Fudail da yasan kome, sai da ya sunkuyar da kai. Zufa ne ya shiga karyowa Abul Bashar, sannan ya kalle shi a sanye cikin wani irin slow Voice yace mishi. "Da farko zan tambaye ka, kai zaka bani amsa, shin baka tab'a jin sunan Allah bane?" Girgiza kai yayi sannan ya shiga warware shi abinda ya sani, da yadda ya san sunan Allah, kallon shi Abul Bashar yayi sannan yace mishi. "Me ka sani a zaman ka da Yarinyar? Misali dangane da addini?" Lumshe idanun shi yayi tare da kawo mishi bayani tare da ayoyin da surorin da take karantawa. Musamman sura shida da ya haddace Suratul Yasin, Baqara, da Rahaman sai falaki da nass tare da fatiha. Sai iklas itace ma take bashi wahala, jinjina mishi Abul Bashar yayi tare da daura mishi cikaccikar musulunci, tare da koyar dashi wasu abubuwan, sannan ya gaya mishi dole ya shiga musulunci tukun. --- Shiru suka yi tare da kallon juna, sannan suka kara sunkuyar da kansu. Tabbas dole subi sharuddan da Sultanah Hoyam ta gindaya musu, amma ba zasu sake ayi musu wasa da rayuwar Yaran su ba, koda kuwa hakan zai zama fansa ga rayuwar su baki daya. " Dole idan zaku bashi yaran ku, kamar yadda muka shirya. Domin yin haka shi zai hana talakawa fahimtar an tsige shi. Idan kuma kuka k'i toh ba makawa abinda ake gudu zai faru." *Toh fa 🤔☹️ inda ba kasa nan ake gardaman kokuwa ```BOOK one free ne, book two da three na kudi ne 200₦ ta bank 0472282105 ki katin mtn ta wannan Number +2347035133148 ko ta wannan Number 08130269641``` #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: *FURE cikin ƘAYA* _CIGABAN DAULA BIYU_ BOOK TWO _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 02 Shiru suka yi tare da zubawa d'an wadan da yake musu bayani, cikin takaici da bakin ciki suke kallon shi. Gyada kai suka yi sannan suka ce. "Dunna mun Amince! Zamu bashi yaran mu." "Sai dai kuma! Akwai guguwa tana zuwa me ƙarfi daga yankin duniya! Wannan guguwar zata iya lashe kowa da kome! Hatta Ni ban tsira ba, zata iya shafa na" ya faɗa yana kallon su. "Toh me zamu iya yi domin mu kare kanku?" Murmushi yayi sannan yace. "Kaddarar da ta raba! Itace zata kuma had'awa, kar muyi fatan ya kuma faruwa, domin yin haka shine mafi kololuwar tashin hankali mu. Kusan yadda zaku yi ya karbi matan da zaku bashi, yin hakan shine zai karya alkadarin wancan al'amarin." Duk sun amince da abinda ya fada dan haka su bakwai suka yi fatan ya amshi yaran su. Koda kuwa yarka zata zo a kwarkwarah Toh fatan su bai wuce ta haifi D'a namiji ba, dan haka suka amince suna fitowa nan suka shiga musu, wannan nace shi yarshi ba zata zo a kwarkwarah ba, wannan yace shima haka. Take dai Amir Hood ya musu bayani da cewa. "Jasrah jikata zata zo a Matar shi, sauran kuma zasu zo a Kwarkwarorin shi. Idan yayi muku bismillah idan bai muku ba, toh zamu mika sakon gayyata ga sauran ƙasashen da makotan su, zasu iya amsa tayin mu." Yana fadan haka yana jan gemun shi, kuri suka mishi tare da dauke kan su, tare da cewa. "Shi kenan, mun Amince." Sun amince ne kawai amma bawai dan ransu yo so ba, kuma bawai dan zasu iya bijire mishi bane. .... Oman Idan bai yi karya ba, Hawaye ya gani a idanun Abrad. Kuka yake riris kamar yaro karami. "Waye ya kashe min Hoorulain? Me yasa baku kama wanda ya kashe min ita ba? Me nayi da zafi zaku kashe min Hoorulain?" Shake wuyar Nawwas yayi cikin tashin hankali, yana fadin. "Meye kai mata? Ban yarda da kai na, waye ya kashe min ita." "Sultan la Fahimce ni, babu wanda zai kashe ta da gayya. Mun isa inda aka yi abu babu alamar su sai jini da dakarun Samaind." "Mehran!!! Lallai ka dibo da zafi, wallahi sai na maka kisan da har ka mutu ba zaka daina jin zafin kisar da na ma ba." Kuka yake tare da dafe kirjin shi hawaye na zuba. Shi yasa maza azancin magana suka ce idan zaka gina ramin mugunta ka gina shi iya tsayin ka, domin baka san ta inda zaka fada ba. Kallon Nawwas yayi sannan yace mishi. "A shirya Azizatul Nissah! Zan aikata ta kashe Mehran! A matsayin matar shi, idan ta kama ma ta zo a kwarkwarah na amince tasan yadda zata kashe min shi, shine fansan ran Hoorulain!" Ya faɗa tare da kwanciya a kasa, yana zubda hawayen. Fita Nawwas yayi cikin takaici da bakin cikin mutuwar Ikram. Lokacin da ya isa da sakon Abrad, na mutuwar Noman da Ikram,kuka tayi ta yi, domin bayan taci amanar Noman, ya tafi sai ta fahimci Allah ya daura mata son shi. Kuma lokacin yayi mata nisa. A yanzun da taji labarin mutuwar shi kuma aka tinzira ta da cewa, Mehran ne ya kashe shi sai taji ta tsani Mehran, dan haka suna gaya mata abinda zata yi ta amince, tare da yarda. Dan haka suka shirya lokacin tafiya domin daukar fansa. ~~~ "Ta tafi! Ta tafi ta bar baya da kura! Uwaisul Qarni, Ikram ta tafi. Babu wanda zai iya fidda ni a cikin wannan kuncin rayuwar sai Allah, wallahi ban tab'a jin na cutar da ita ba, har yau ina sonta a cikin raina. Itace matar da zata iya tsaya mishi, amma ta tafi ta bar min shi a cikin kuraye, ta tafi ta bar shi a cikin muguyen mutane. Waye zai kawo karshen wannan al'amarin?" "Allah! Kin san da zata zo ne? Dan haka kamar yadda ta farkar dashi daga barcin da yaƙe, mu Cigaba da zuba mishi ido har zuwa lokacin da Allah zai dawo mana dashi! Karki zubda kwallan ki, Zata dawo kamar yadda ta tafi! Zata juyo kamar yadda ta juya, sai dai Allah ya yayyafa mana ruwan sanyi a cikin zuciyarta ya kuma bamu ikon iyawa da ita, shine abinda xan iya gaya miki!" D'ago kai tayi sannan tace mishi. "Ubangiji ya nufa, amma ina sonta har cikin zuciyata!" "Na yarda da haka" ~~~ Garin Gulsana. Gari ne da yake bakin kogi, me dauke da kananun mutane, irin gajajjerun nan, masu shegen kyau. Idan ka ga matan su, kyawawa ne gasu da manyan nonuwa, idan suna tafiya har wani rawa nonon su yake. Halittar duwawun su, ma kasa kasa Idan suka gyara gashin su, sukan saka shi can gefen kansu ne sai su dauki furen gulsana, su makala a jikin shi. Shigar su d'an kamfe ne da wani yadi da suke tare manyan nonuwar su, idan ka gansu suna tafiya har wani daukar hankali suke. Gasu mazan su jarababbun mutane ne, idan suka ga mace danne ta kawai ake a hake mata, amma kuma suna da dadin zama, da mu'amalar juna, sannan ana yawan kawo musu hari, har a kame wasun su. Duk bayan shekara biyu. Suna zaune ne a bakin teku, sabida basu da sana'ar da tafi su. Da shi suke shiga cikin gari su sayi kayan masarufi. Akwai wani matashi me suna firoz, yaron shi yafi kowa tsayi. A cikin kauyen baki daya. Baya magana da kowa sai yar me gari me suna. Izmah yau ma a tare suke, d'ago kai tayi tare da kallon shi zai watsa kimar kama kifin shi tace mishi. "Firoz! Wai baka da sha'awar mace ne? Ko baka da lafiya ne irin na sauran mutane?" "Lafiyata lau, kawai ba zan iya hakewa macen da nake so bane? Shi yasa kika ga na kyale ki d idan na miki damka daya zaki kwashi labari a gaba!" Tabe baki tayi daidai ya watsa komar, jin ya rike abu ya saka shi cewa. "Yau dai da Sa'a na watsa komata domin naji na kamo hanyar Arziki" dariya tayi mishi sannan tace mishi. "Ka manta daren jiya anyi ruwa dama, tayu Giwa ce ta faɗa ruwa, shine igiyar ruwa ya tawo dashi." Dangware goshinta yayi sannan ya cigaba da jan kimar shi, har Allah ya nufa suka janyo komar baki daya. A tsora ce suka dube cikin komar, mace ce cikin komar tana mace. Ihun da Izmah tayi shi ya farga da sauran mutanen kauyen, da gudu mutanen kauyen suka taso, aka janyo komar sannan aka shiga taimaka mata na gaggawan, tab'a wuyarta aka yi suka gyada kai. A lokaci guda suka sauke ajiyar zuciya, sannan aka dauke ta zuwa cikin kauyen. Cikin sauri aka nufi gidan Mawla da ita shine me maganin garin baki daya, dan haka ya shiga taimaka mata cikin sauri yana sakawa na cire mata kayan jikinta, dai dai shigowar, keyaan. Kurawa halittar jikin Ikram idanu yayi tare da had'iye yawu, cikin zunzurutun kwadayin shi. Yana kallon yadda take kwance babu numfashi. "Toh Mawla idan an gama kula da ita, a kawo min ita gidana domin nan yafi dacewa da ita ba gurin ka ba, bana son ana ganin ta kamar wata ganimar da aka tsinta." Ya wani bone fuska zaka zata da gaske shi ya cirota cikin ruwan da aka tsamo ta, " Abba yanxun Abinda kake yi dace? Duba halin da matar nan take ciki sannan kana cewa a gama a baka ita, Toh naga dan farka da zai baka ita idan ban kashe shi har Buzun sa ba," Yasan halin Izmah zata aikata dan bata da tsoro ko kad'an, dan haka ya koma gefe yana shafa kirjina shi zuwa wuyan shi, musamman ganin cinyoyin Ikram, wanda suka yi wani irin haske. Sambala sambala, had'iye yawu yayi cikin wani irin yanayi. Matse cikin Ikram mutumin yayi tare tare da marin wuyar da fuskarta, ruwa yake fita ta hanci da baki. Sai ta bayanta, ta xubda ruwa me yawa, sannan ta fara numfashi kunnen ta kuwa dama ruwa ne ya toshe shi. Muryan take ji kamar daga can can, ana kiran sunan ta bude idanu nayi naga Noman da Ummina sai Airan da Abba na. Murmushi suke min suna kallon yadda nake kwance. "Ku tafi dani!" Na fada cikin kasa da murya. Dafa goshina Ummina tayi sannan tace min. "Rayuwarku tana amfani a duniya! Idan muka tafi meye amfanin haka? Ki zauna domin karasa sauran aikin da kika fara." "Noman!" "Karki damu! Ki karasa aikin da kika fara." .mika musu hannu nayi sai gani nayi sun bi iska kamar yadda ake watsa gari a iska, haka suka Baje, a iska zabura nayi tare da tari me ƙarfi ina aman ruwa, rirrike Ni suka yi, na fara ihu ina kiran sunan Noman. Ban san me suka saka min ba daga nan barci yayi gaba dani. "Da alamu akwai abinda ya faru da ita,. Kuma idan ta farka da abun toh ba ta manta kome ba, idan kuma ta farka bata kuma tuna kome ba, tabbas wannan shine abinda ake kira kaddara." Inji Mawla, yana shafa kan Ikram da wani farin magani. "Toh Mawla meye Illar haka?" "Illar shi kuke son sani? Dubi tafin hannun ta, Kinga alamun zaman takobi, idan har ta farka da shi zamu iya sanin wacece ita, duk da saura kwanaki ƙalilan yan sumamme su kawo mana hari. Ku duba sararin samaniya, kunga taurarin zubda jini bai fito ba, amma kunga can tauraron taimako ne yake washewa, idan na Fahimta, abin bauta. Kunzu ne ya turo mana ita domin ceton rayuwar al'umma." Da wannan zancen kowa ya koma gidan shi, ban da Sarkin garin ya share guri ya zauna, shi yaga mace. Karku ganshi kamar an kira kwarya, amma dan bakar jaraba yana fadar cewa shi Ikram yake dakon yayi tarayya da ita, ai ance dogayen mata suna da dadin dandano.(🤔🤣D'an hegiya wannan bom ce ta kwashe maka kayan wasan yaranka anan) ~~~ Bayan awa goma sha biyu, a hankali na bude idanuna tare da kallon d'an bukkar da nake, mik'ewa nayi sakamakon jin kamar wani yaro ya tukwaikuye ki, dubawa nayi naga dan abu kamar d'an shekara bakwai, babu kome a jikin shi. "Innalillahi wa'inna ilaihi rajioun, wata duniya na fado kuma wannan yaron karami dashi." Gwartin da naji yana yi irin ta tsofin mutane, ya sani kallon shi da kyau. Ture shi nayi naga ya farka tare sake min murmushi, fuskar shi kamar kashin saniya, dan haka na dauke kai na, tunkaro ni yayi babu kaya a jikin shi, wani shegen duka na kai mishi tare da kwashe kafarshi na rike a hannuna, ina kallon shi gaba daya kayan aikin shi wato alkalamin shi basu fi ta yara yan shekara tara ba. Amma ya tsaya min zai min feleke, daukar wani igiyar nayi a dakin na kama shi tare da daure shi tam, sannan na zabga mishi naushi na fito dashi waje na rataye shi. Sannan na koma dakin na shiga niman kayan da zan saka, dakyar na sami wata irin riga kamar ta yaki, na saka tare da kwanciya, ina son tuna wasu abubuwan masu muhimmanci amma na manta dan dole na rintsa idanuna. Har kai na ya fara ciwo, sannan barci ya kwashe ni. Kamar wacce aka tashe ni na farka, sai nake jin kamar kunne na yana min gizo ana kiran sallah a can da nisa, a hankali na fito gidan tare da niman ruwa, sannan na shiga, zaga gidan har na hango kogi da sarsarfa na isa bakin Kogin na nayi alwala sannan na juya zan koma naga yan wadanin share su nayi, aikuwa suka ji haushi, suka hayayyako min, kwallon nayi tayi da su, tare da watsar dasu na wuce abuna, sai bin keyana suke da ido, ko ajikina. Ina isa gidan nan ne kuma na rasa yadda zanyi sallah, dan haka nayi dikakke, na fara sallah. ```BOOK one free ne, book two da three na kudi ne 200₦ ta bank 0472282105 ki katin mtn ta wannan Number +2347035133148 ko ta wannan Number 08130269641'``` #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: *FURE cikin ƘAYA* _CIGABAN DAULA BIYU_ BOOK TWO _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 03 A hankali na gabatar da sallah, ina idarwa na kwanta a gurin, barci ne ya dauke ni, hasken rana da hayaniyar mutane ya sani bude idanuna. Hango wata matashiyar Wada nayi tana zare min ido, tare da saka min wani mashi a wuya. Lashe bakina nayi tare da kallon ta, magana suke cikin harshen swahili ya sani kallon su kur sannan na juya musu harshen. "Kema kin iya Yaren swahili ne?" "Kwarai!" "Toh me yasa kika daure mana Sarkin mu, kuma mahaifina?" Murmushi nayi mata sannan nace mata. "Ku godewa Allah daure shi nayi, da ba kwashe mishi gaban shi nayi ba, kar ya fita harkata sai na shafe mishi gaban shi" "Dame kike takama ne?" Inji Firoz. "Jarumta!" Na bashi amsa, "Ku sunce ta?" Kunce Ni suka yi tare da saka min mashi a wuyana, ban kalle su ba, na nufi bakin kogi zan sha ruwa. "Ke mafadaciya?" Kirjina ne yayi wani irin bugawa, tabbas an tab'a gaya min sunan. Lumshe idanun nayi tare da son tuna inda aka tab'a kiran na da sunan ganin zan bawa kai na ciwo ya sani share zancen sannan na nufi cikin ruwan na sha kafin na fito. Ina gamawa na juya tare da kallon su, budurwan wadan ce tazo ta tsaya a kusadani. "Kiyi hakuri! Duk da daman. Ance zaki iya manta kome naki, amma muna nan da kike ganin mu,muna cikin damuwa domin kuwa saura nan da kwanaki a kawo mana farmaki,daga masu safarar mutane. izuwa kasashen duniya. Kizo ki ci abinci sai ki bar garin nan,dan zasu iya dirowa koda yaushe suna kama mana, mutane tare da kashe mana iyayen mu, bayan sun musu fyade. Don haka ki nutsu ki bar garin nan." "Iya taimakon da kuka min ba zai iya sani na tafi na barku cikin wannan halin ba, dan haka mu shiga gari." Haka muka yi ta zaga garin ina kallon yadda yake kawwace da manyan bishiyoyi, dan haka na ce mata. "Suna Ikram! Iya shi zan iya tunawa, sauran kuma ba san inda na saka su ba, zamu iya zama aminai ko?" "Eh Izmah zaki iya kirana!" Jan iskar garin nayi me dauke da kamshin furen gulsana, nace mata. "Wannan furen yana da guba me sakawa mutane suma, sannan kuma da bishiyoyi, yanzun abinda zamu yi Kinga wancan kogon muje!" Juyawa tayi ta kira Firoz, sannan muka nufi kogon babu koma. Kallon cikin kogon nayi sannan nace mata. "Zaku iya niman maganin kwari masu cutarwa a saka, sannan kuma zamu tattaro mutanen garin mu kawo su nan, Matasan gari da yan mata kuma zaku iya zama mu fahimci yadda zamu tunkare su." Koda muka dawo cikin garin nan muka hadu aka fara tattaunawa, tunda suke basu tab'a yaki ba, dan haka a cikin abinda zamu yi shine aka fara sarrafa kwari da baka. Da yadda ake amfani dashi kafin kace kwabo, har sun gane a cikin kwana uku, ana gobe mutanen zasu shigo aka maida Yan kauyen baki daya cikin kogon nan, matasan kuma suka haura bishiya, Cikin dare sosai, mutanen suka kawo hari, babu wanda ya kula su, sai da suka shigo cikin da'irar kauyen, muka sake musu ruwan kibau ta sama, garin gudu suka yi ya fadawa cikin ramin da muka hakka musu, ganin haka. Ni da Izmah muka nufe su, tana sake bakar ina tunkarar su da takobi. Ashe kofar rago suka min, domin ganin sun rubta a tarkon mu,, sai na fada a nasu. Ina zuwa gurin suna watsa min raga, ganin haka Izma ta saka a Cigaba da sake musu Kibau, haka dai suka yi ta jana, ana kashe su amma basu hakura ba, sai da suka ga dab zasu rasa kansu. Suka fisge Ni. Ganin haka Itama Izmah ta sauko tare da biyo bayan mu, haka suka hada da ita, da ni. A cikin wani abu me kama da keji, firoz ne yake Ihun kiran mu, nace Mishi. "Ka koma! Zan kare rayuwar ta insha Allah, ka koma ka kare garin ka, zan dawo maka da masoyan ka." Haka yan uwan shi suka rike shi, har muka b'ace. Firfitowa mutanen garin suka yi, tare da kallon hanyar da aka bi damu. "Daga karshe dai ta koya mana yadda zamu kare kanmu, sannan Izmah ta sadaukar da kanta domin ta, duk da bamu san wacece ita ba, amma ina da yakinin ƙaddara ce ta kawo ta." Inji Mawla, "Yarinya na ta fansan da kanta sabida yadda ta fansan da rayuwarta domin mu, iya haka ma ya ishe ni, amma na rike alkawarinta na cewa zata dawo min da ita, na rike wannan amanar!" Ya fada tare da fashewa da kuka, su kansu tausayin shi suke sabida yaran shi dukka hudu mata, duk mutanen sun tafi da su, sai Izmah ce ta rage. Dan haka koda gari yayi haske suka kwashe kayan yakin mutanen, suka kuma binne su. Sannan suka, koma gidajen su. Firoz yana zaune a gurin. _Masoyina! Kayi hakuri koda bana nan zan dawo wata rana, domin Ikram tayi mana kome! Ga mahaifina nan ka kula min dashi, ba zan iya ganin a tafi da ita ba_ Ta fadi haka tare da rungumo shi, hawaye ne ya zubo mishi. Shi kenan. Abinda alkalamina ƙaddara ya zana musu kenan, yayi musu rubutu a zanen ƙaddarar su lokaci guda, sun tafi. Kuka ne ya kwace mishi me ƙarfi sannan ya kalli garin da shawarar da Ikram ta badda, tace mishi. "Yanzun don Allah kuna da wannan fure kuke kallon mutanen nan a haka suke cin zarafin ku, da farko tunda kuna da duwatsu dole ku dawo nan da zama, sannan ku koyi sarrafa makami musamman da kuka kasance Kananun mutane, sannan daga can zaku iya karar da mutane ba iya kan bishiya ba. Amma kun zauna sai anzo an tozarta matan ku, meye haka? Don Allah koda bana nan ku taimakawa kanku." Ta fadi haka, yana juyawa ya gaya musu abinda zasu aikata, tare da yadda suka yi da Ikram. ---- "Sarwat! Dauke ta ku fada cikin ruwan! Ku tsira da ranku! Ikram ki gudu." "Sultan Aamaan Mehran ya turo mu!" Bude idanu nayi ina kallon cikin kejin me dauke da mata da yara, rike hannuna Izmah tai tare da daura kanta a kafadana. "Insha Allah! Zan mai daki gurin ahalinki." "Bana jin tsoron kome ko fargaba, sabida ina tare da Jarumar jarumai, akan me zan tuna abinda ya wuce min." "Iyaye nada muhimmanci, masoyi yana da daraja, karki sake ki manta da Firoz, kamar haka na tafi, ban koma mishi ba sai da kyautar mutuwar shi, Babban burina A duniya nasan waye Sultan Aamaan Mehran! Shi nake nima. Idanu rufe" Hawaye ne ya zubo min, ina kallon yadda itama take kuka. Tace min. "Ikram! Kiyi hakuri ya kashe miki masoyi ko?" Goge kwallar nayi sannan nayi wani irin murmushi, ta gefen baki sannan na maida hankali na, kan abinda nake yi. "Lallai jinin shi ya tabbata ga fansanki Ikram ba zan tab'a komawa ga mahaifinta ba, har sai na taimaka miki da kin dauki fansar jinin masoyinki." Gyada kai nayi, har muka isa wani gari me suna. Sira. Anan ake cinikin bayi kamar yadda ake cinikin dabobbi, kowa ya ganmu da Izmah, hari yake kawo mana. Dan haka muna tsaye aka ja gefe tare da yin kuskus, aka ce mana. "Ke me idanun mage! Kubi wancan mutumin." Ba musu na riko Izmah muka nufi inda mutumin yake, sannan ya kai mu gidan da wasu mutane suke, muna shiga cikin gidan. Suka yi ta kallon mu, har suka gama sannan d'aya daga cikin su yace masa. "Doguwar tayi min, wadar ce bana bukata." Kai hannu suka yi zasu juya da Izmah, nayi maza na juya hannun su, cikin zafin nama. Komawa da baya mutumin yayi. Ita kuma ta k'amk'ame ni. "Mafadaciya! Ya da saurin fusata haka? Ke nake bukata ba ita ba." Kallon shi nayi sannan na kalli yadda yake kallon Izmah, "Tare suka kawo mu, tare zaka saye mu! Idan bamu maka ba, zaka iya." Da gudu me tsaron lafiyan su ya kawo min sara,. Tsalle nayi tare da lankwashe kafaffuna, sannan na dira a kirjin shi, dayan na zuwa na zari wani abinda Izmah ta kama gashin ta dashi na soka mishi a wuya. "Ikram!" Juyawa nayi naga sun rike wuyar ta da takobi. Murmushi nayi irinta kayi kuskuren tab'a min ita, juyawa nayi tare da daura wukar da suke yanka tufa na wurga mishi sai da ta huda kirjin shi. Sannan na kalli mutumin wanda yake zaune ko a jikin shi. Sauran na gefen shi da suka sunkuya tare da yin kuskus, suka kalle ni. "Daga wani yanki na duniya kika fito?" "Wannan ba matsalar ka bane, yar Uwata tayi ciwon kai, Allah ya bani baiwar gintse numfashin kowa." Tasowa mutumin yayi, tare da cire babban rigar shi sannan ya kura min ido, yana faɗin. "Zan dauke ta, amma ki fara gwada kwanjinki dani, sai na san abin yi." _A duniyar fadar kareti, zafin nama itace nasarar ki, karki sake makiyinki yasan abinda zai sakaki kuka a fadar ku, karki dake kibawa makiyi daman kai ki kasa, zafin namar ki shine nasarar ki! Kinji ko Mafadaciya_ Ba zan iya tuna muryan waye shi ba, amma tabbas ya gaya min abinda ya dace, Alama mutumin yayi min sannan ya koma baya, haka kawai naji raina ya b'aci sosai da mutumin tsanar da ban san daga inda na fara shi ba, na tattara na tsane shi, dan haka koda muka fara fadar cikin zafin nama. Muke kaiwa juna mugun nufin. Sai dai yadda yake sauya salon shi, nake kuma iya bin shi har na kai mishi duka Yasaka shi fahimtar nafi shi zafin nama, sosai na hargitsa mishi lissafi, sai da takai bai iya kare kan shi, kafin na kyale shi. "Waye ya koya miki fada haka?" Juyawa nayi abu na, zuwa gurin Izmah, na durkusa tare da rungume ta, ina cewa. "Ba zan tab'a barin wani ya cutar dake ba, koda kuwa hakan sadaukarwa ce a gare ni. Duk wanda yake da bukatar mu, kofa a bude take babu wanda ya isa ya raba mu." Na fada da karfi, sannan na juya gare su, ina rike da hannunta, "Kunyi min! Kuma zan saye ku a haka. Sai dai kuma inda zan kai ku yana da matukar hatsari, dan wasa da rayuwar ku zaku je yi." "An haife ni ne dan nayi wasa da rayuwata, ba a haife ni dan na bautawa kowa ba, sai Allah."na fada ina kallon shi. Kura min ido yayi tare da kallon yan uwan shi. Gyada kai yayi sannan yace min. "Zaki iya tafiya!" Juyawa nayi tare da barin d'akin, aka nuna mana hanyar da zamu bi. "Me kuka fahimta a kalaman ta?" "Wallahi nima tsoro ne ya kama ni, don haka shima yayi wannan furucin lokacin da muka nemi hadin kan shi domin mu kashe Abban mu! Yau ga wata me kama da shi da muryan shi ta bamu amsar shi." "Kai murya ce kawai amma babu wani kama da suke yi, sai dai kuma zan cigaba da Binciken ta, har sai na gano gaskiya amma tana da zafin nama sosai, kuma bata wuce sha takwas ba, amma ta iya wannan b'arnan, idan ta gawurta za a shiga uku da ita a duniya." --- Ana kai mu dakin abinci aka kawo mana me shegen kyau da dad'i, sallah dake kai na na sauke sannan na zauna tare da kallon Abincin da Izmah take kallon shi itama, dan bamu yarda da abincin ba. Kallon kunnenta nayi naga azurfa ne. "Bani azurfan kunnenki!" Tana bani na soka cikin abincin sannan na rufe abincin, can na bude tare da cirewa, dan kunnen yayi bakikkirin. Murmushin gefen baki nai, sannan na dauki abincin na koma wannan babban falon na watsa musu a gaban su. "Lallai na sami abinda nake buƙata har kin fahimci da.... ```BOOK one free ne, book two da three na kudi ne 200₦ ta bank 0472282105 ki katin mtn ta wannan Number +2347035133148 ko ta wannan Number 08130269641``` #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: FURE cikin ƘAYA* _CIGABAN DAULA BIYU_ BOOK TWO _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 04 "Har kin Fahimci akwai guba a cikin abincin?" Watsa mishi kallon banza nayi sannan na ce mishi. "Waye ya gaya maka Ni jahila ce irinka, lokacin da muka shigo na daki wadancan kartin, ina kallon ka gyadawa matar da zata shiga damu cikin gidan kai, tare da kallon mu, a duk inda zan shiga nakan bawa ƙwaƙwalwata muhimmancin lissafi sama da zuciyata, dan haka ka kawo min abinda zamu ci ko kuma nayi maka wankan da kurbataccen abincin da ka bamu." "Me yasa baki da hankali?" Ya daka min tsawa cikin izza da fushi. "Ba a haife ni a cikin babban gida ba, dan haka sauke muryan ka k'asa yanzun kace ka sami abinda kake nima, ce maka akayi Ni karamar haja ce da zaka same ni a ruwan sanyi, Izzar da take cikin zuciyata ta wuce wanda yake zuciyarka. Ni haihuwata aka yi dashi kai kuma ba mamaki tsintar ta kayi, karka kara min tsawa dan zan iya tafiya babu wanda ya isa ya dakatar dani." Ina fadar haka na juya tare da barin gurin, har zan kulle nace mishi. "Yanzun zaka kawo min! Kuma da kanka, idan ka wuce dakika dari uku da sittin sai dai wata ba dai Ni ba." "Anya ba jinin shi a jikin Yarinyar nan kuwa? Kalaman shine akan harshenta! Ina jin tsoro Sulaiman yarinyar nan tana da boyayyen al'amari a tare da ita, don Allah mu hakura da niman wanda zai mana aikin nan muje muyi ta saka bayi suna jarabawa" "Kayi min shiru Muntaz! Kayi min shiru nace, ni bauna ne saniyar sake, bazan kuma juyawa ba, dan haka zan tafi da ita. Kuma zan mata duk abinda tace, cin Amana a jinin mu yake dan haka zan." "Amir Sulaiman ga abincin nan!" Ta faɗa a hankali, juyawa yayi ya amsa, sannan ya juya ya nufi cikin gidan, koda ya shiga ya same mu a tsaye, ajiye abincin yayi tare da zama ya zuba kome ya fara ci, sannan na zauna nima na fara ci, nayiwa Izmah magana ta fara ci, bamu kula shi ba. Amma kuma na fahimci akwai magana a bakin shi. "Ina gayyatar ki turaka na!" Bugawa kirjina yayi tare da kura mishi ido, sannan na dauke kai na, wani irin murmushi nayi iya gefen bakina, sannan na dauki nama na karayawa Izmah. "Ina bukatar goran giya, abokiyar tafiya na tana sha!" "Toh ranki shi dad'e, Sultana" A hankali na d'aga idona na kalle shi, sannan na sunkuyar da kai na, domin wannan kalmar ba sabo bane a gare ni, na sha jin shi a wasu lokuta da Bazan iya tunawa ba. Fita yayi muka ci abincin, kawo mana goran giya yayi, sai da yasha sannan na barta tasha, domin Ni Bazan sha ba, idan na sha nasan haramun ne, dan haka na maida hankali na, kanta, tunda naga taji dadin giyar, har kusan lokacin sallah, tana sha kafin na lura ta fara bugar da ita, tashi nayi na gabatar da sallah, ina sallah isha naga ta tuntsara, gyara mata kwanciya nayi. Sannan na nufi hanyar waje inda na sami matar nan a tsaye da kayan sawa a hannun ta, mika min tayi na nufi ciki na saka, sannan na fito. Kallona take cikin murmushi tace min. "Kina da sirrintacciyar kyau!" Murmushin gefen baki nayi sannan ta mika min turare na shafa, tare da nufar hanyar da ta nufa. Ina tafiya ina kallon shigar jikina, haka na shiga babban falon yana zaune sai had'a lissafi yake tare da shirya kome, a hankali na tsaya tare da gyaran murya,. D'ago kai yayi cikin nutsuwa yace min. "Zauna zinariya!" "Bani da lokaci. Ina jinka." "Kizo ki zauna a cinya na, dauke kai nayi ina me kallon ko ina. Muryan shine ya katse min nazarin da nake, "Ba baiwa na dauke ki ba, aiki zaki min amma don Allah kizo nan ki zauna." Babu musu na nufi gurin da yake nuna min, wato kan cinyar shi na zauna, hannun shi ya kawo tsakanin cikina ya manna ni a jikin shi. Wani irin tartsatsi naji tare da hasko min hakan ya tab'a faru da komawa, amma kamar mafarki kamar a zahiri. Wasa yake tsakanin cikina zuwa kirjina, kanshi a kan wuyana, yake cewa. "Zan dauke ki, aikin sirrin na wata shida, a masarautan marocco, zaki min wani aiki ne na musamman. Sannan zaki gama kiyi tafiyarki. Kawai abu daya nake so ki rufe sheda." Juyawa nayi na kalle shi, sannan na dauke kai na,. Nace mishi. "Wani irin aiki kenan?" "Kin tab'a kisa?" Juyawa nayi cike da mamaki, ina kallon shi. Sannan nace mishi. "Ba zanyi aikin ba!" "Kiyi hakuri! Dole ce takawo haka, zaluntana suka yi, suka kwace mulkin daga hannun mahaifina suna kashe min kanina,!" Cikin alhini da tashin hankali yake gaya min yadda suka ci amanar shi, tare da kashe mishi mahaifi da yan uwan shi,kuma sun hana shi koda tsinke daya ne na masarautar wai ya haramta mishi. Babban mutum ne fa, sai gashi yana kuka sosai, dan haka na sauka a kan cinyar shi na mishi alkawarin zan.dawo mishi da mulkin shi idan ya kama har da kisan zanyi dan na cika mishi alqawarin shi. "Amma da sharadi, matuƙar na fahimci kunci amana na, toh wallahi zan sare kanka na ajiye a wajen gari." "Haba babu wannan alqawarin, babu cin amana" ya gaya min tare da rawan jiki, yana son jefani cikin tashin hankali, kallon shi nayi tare da cewa. "Kayi hakuri! Na manta na gaya maka ina cikin kwanakin rashin mijina ne, don Allah ka gafarce ni." "Taya kika yi aure da shekarun nan ai mure rayuwar ki zaki yi,gaki da kyau." Sunkuyar da kai nayi sannan na ce mishi. "Kayi hakuri, nima na manta kome akan auren nasan ina da dai mijina kuma ya rasu, dan haka ka gafarce ni." Gyada kai yayi sannan ya nuna min hanya na fita,bin k'ugun yayi da ido, yana kallon yadda yake kad'awa kamar ya kwace, ya boye shi. Murmushi jin dadi yayi test da sauke kanshi yana me shafa kan shi a hankali ..... Koda na dawo dakin na samu tana ta barci, dan haka na zauna ina nazarin abinda wancan mutumin ya gaya min, bawai dan amshi maganar shi lokaci guda bane nayi aiki dashi sai kuma nayi wani tunani ai ba matsala ta bace kawai na share batun na shiga na gaba na, har kusan asuba na tashi nayi ibada na yadda ya dace, sannan na kwanta, ina nazarin yadda rayuwata take garawa,. Barci ya dauke ni. ~~~ *SAMAIND* _Budaddiyar wasika!_ ``` Ba zan muku sallama ba. Sai dai izuwa yanzun kun yi kuskuren sauke Sultan Mehran! Kuma zaku biya bashin da kuka ci!``` Kallon juna suka yi sannan kuma suka kalle Sultanah. "Ranki shi dad'e! Wannan sakon daga ina yake?" Cikin wani irin mulki da yake bin jikinta ta kalle su, sannan tace musu. "Taya zan sani? Bayan kune kuka fini sanin suwaye makiyan masarautan nan!" Ta faɗi haka cikin rashin kulawa da abinda ya faru. Shiru suka yi, sannan ta bude baki zata yi magana aka ji ihun karkeji, tare da fashewan dutsen da yake cikin tekun SAMAIND. Da gudu aka yi ta nufar cikin gidaje, ana b'oya.. Kallon juna suka yi sannan suka ce. "Toh meye haka yake nufi?" "Jini! Za a zubda jinin mutane, al'umma zasu zubda kwalla! Kafin nan ya faru mu fara dakatar dashi. Domin wannan babu karya a cikin shi zamu iya rasa mutanen mu a filin yaki" Inji Mir Umdatuddawla, Shiru suka yi sannan suka ce,ku nimo mana kwararru akan wannan harkan." Dakarun bakwai suka fita can sai gasu nan da wani tsoho, kallon shi suka yi, sannan suka ce mishi "meke faruwa?" Watsa wani abu yayi tare da kallon shi,ya cigaba da abinda yake har ya kusan karewa, sannan yace musu. "Kunyi kuskuren babba, ba zaku daina tashin hankali ba sai ranar da ya dawo mazaunin shi. A duk lokacin da aka tara taron namun daji, ana niman zaki yayi jawabi ko yayi jagora ne, babu yadda za a saka biri ya jorancin namun daji, idan shi mashin yaki ne, itace kansakalin yakin shi, idanun shi zaki ne ita zakanya ce, kuyi fatan ya dawo matsuguninshi, koda ya dawo bai zama dole su cigaba da kasancewa ruwa biyu ba, amma tabbas zasu iya zama abu daya. Idan ya kasance, zuciyar su." "Kai boka! Ba tatsuniya muka tambaye ka baka halin da kasar mu take ciki muke son sani?" Mir Rahil ya daka mishi tsawa. "Kwantar da hankalinka! Kasar ka nan amma babu kwanciyar hankali ne,babu wanda ya isa dakatar da shi sai Allah. Kuyi addu'o'in kar zubda jinin yayi yawa." "Dalla kama na shiru ka cika mana kunne, sannan ka gaya mana ya zamu yi da wannan al'amarin, daga nan sai muga abinyi." Koran kare suka mishi tare da alƙawarin zasu kashe shi idan ya kuma zuwa. Dan haka suka shiga niman manyan malamai da bokaye, aka fara binciken su ana gaya musu abinda zasu aikata, ana haka har Allah ya kawo shi. Gaishe shi yayi sannan yace musu. "Dakarun SAMAIND da al'ummar da suke fita zasu mutu! Ina me baku hakuri, abin bai tab'a faruwa ba zai iya faruwa a wannan lokacin, kuma a wannan karnin kuka zai yawaita, tashin hankali da fargaba zai zame muku taburman ku. Ku dakatar da kuskure baya, Karku dake ƙasar ta shiga halin halu'i. Cikin sanyin jiki suke kallon bokan, Kafin Darakshan yace Mishi. "Jeka Bama bukatar ka, domin SAMAIND jarumai take nima, ba ragwaye ba, ka kwaso tsufarka zaka juye mana haukar a nan" Haka suka yi ta koran manyan malamai da bokayen da suke gayyatowa, karshe suka nufi gurin dan kankanin Mutum mutumin da Sultanah Hoyam ta ajiye a cikin gidan, shi ya gaya musu cewa. "Yakin ba wata shiryayya bace, amma kuma zaku yi asara dakarun ku, akwai dalilin da yasa aka shirya yakin, domin wasu manufarwa wasun ku, dan haka ku gano munafukin bai da muhimmanci kamar ku gano yadda zaku dakatar da yakin dan ko basu ci garin baki daya ba, tabbas zasu raunana sojojin ku. Kuma zasu durkusar da ku, zasu muku kisar mummunke, kuyi kokarin dakatar da yaƙin" Dan haka yana gama koro musu jawabi, aka fara shirin yaki, a hanyar Amir Hood na komawa gida ne aka saka mishi bugu aka kaiwa Sultanah Fazilatul nisa. Kamar yadda yake watsar da kayan wankin haka suke watsar da shi, sannan suka cire mishi mayafin, arba yayi da Yar shi. Tsoron ganinta ya saka shi ja da baya, yana zare idanu waje. "Nifa Mahaifinki ne! Kuma duk abinda nake saboda ke nake yi" "Sabida kanka kake yi dai ko? Ina kuka kai min gudan jini na?" A firgice yake kallonta sannan yace mata. "Fazilatul nisa, ai mun manta wannan maganar, sannan kika fito a halin yanzu kika ce MEHRAN D'anki ne kuwwar hauka zasu miki" Dukar tabirin gabanta tayi tare da cewa. "Babu wani shegen da zai min kuwwar hauka, idan baku bani d'ana ba, wallahi billahi azim zaku ga balbalin bala'in da zai tunkaro SAMAIND baki daya, ku bani D'ana domin shine Kusar Yaki na" Yadda tayi maganar har gidan na amo yasa Amir Hood ya kaskantar da kan shi, yana bata hakuri. "Zamu maida miki shi, amma maganar gaskiya, gurin da yake akwai hatsari, domin guri ne me dauke da macizai da mugayen kananun kwari masu cutarwa, don Allah" "Ce maka akayi zuciyata ta cika da bukukuwan duniya ce? Ko ce maka akayi ina da burin na zauna daga gefe guda ina kallon shi yana cikin damuwa? Bani da zab'i kuma bani da buri shi kawai nake bukata, idan ba zauna dashi duk wata sadaukarwa zata biyo baya, ba kun kai shi darul AlHarami bane? Sai aka ce maka zan iya barin shi ya zauna baya ga maraicin da ya taso cikin kaɗaici bai isheku ba, har sai nanu duniya ce sama dashi?" #Mai_Dambu.... ```BOOK one free ne, book two da three na kudi ne 200₦ ta bank 0472282105 ki katin mtn ta wannan Number +2347035133148 ko ta wannan Number 08130269641``` [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: Monday-March-2021 FURE cikin ƘAYA* _CIGABAN DAULA BIYU_ BOOK TWO _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 05 Yadda ta daka mishi tsawa da madaukakiyar murya sai da Yasaka shi razana, tare da ja da baya, sannan ta nuna mishi hanyar waje. "Tabbas zan je gare shi, sai dai idan kun so dakatar da hakan Ni kuma zan baku mamaki, kamar yadda ka rabani da Iyayena!" Ta faɗa tare da juya mishi ba, tana zubda kwalla, yanzun ta fahimci dalilin da yasa Uwaisul Qarni yace mata. "Ki godewa Allah, da Hood bai cutar da fahimtar ki ba, dan ya kashe mutane dayawa, dan haka kece ya kasa kashewa ya kawo ki nan ki zauna, a matsayin matar sarki, kuma kinyi nasarar zama matar sarkin sai dai Abdus Samad babu soyayya a cikin tsarin shi, ban sani ba ko zaki iya samun soyayyar shi. Kiyi hakuri nayiwa Mahaifinki alqawarin rike bayan shi, dan haka ina tare dake babu wanda ya isa ya cutar dake face abinda Allah ya zana miki a cikin littafinki?" "Waye ya gaya miki cewa ke ba yar cikina bane? Ni na haife ki, kuma." "Mir Khulaifa Alhashim. Bakuraishe daga yankin makka, mahaifiyata Hajna daga d'ayifa, gidan Amirai. Sun baka dukkan goyan bayan su, har kama waye kai. Amma daga baya ka tura har Makka aka kashe su, sannan ka saka aka sato ni, duk da Mahaifiya ta, ta fito daga cikin babban gida ne, haka bai maka ba, sai da ka amshe dukkan arzikin mahaifina, ka fara kuka tun kafin kukan yazo maka, dan wallahi sai na tsaya akan kafana na saka ka gudun ceton ranka!" Wani irin tsoro ne ya bayyana mishi, shekaru sama da hamsin yau a dawo da maganar, tabbas dole ya kashe ta. Domin kuwa tana sako wannan batun sunan shi, hallakakke, domin hallaka shi zasu yi har lahira. Ajiyar zuciya yayi tare da ficewa daga gidan, amma sai ya dauki matakin da har abada ba zata dashi ba. Dakinta ta shiga tare da yin alwala, tayi sallah sannan ta kira Uwaisul Qarni, ta gaya mishi. "Yanzun zaki bar gidan na, Insha Allah domin zasu turo a kona gidan, yin haka kuwa daidai yake da manta tarihinki, amma idan kina kusa da Mehran babu kwaron da ya isa cutar miki" Gyada kai tayi tare da sakawa a kashe kayanta kaf, sannan aka hada da na su Shairah da Narjis, suka bar gidan. Basu zame ko ina ba sai hanyar gidan Mehran, har suka isa kofar gidan, yana sama can yana kallon su, saukowa yayi tare da fita bakin kofar shiga gidan, yana isa yaji masu tsaron kofar suna cewa. "Ba zaku shigo ba, ku koma sai gobe da." "Barsu man!" Da sauri ya juya tare da gaishe da Mehran, sannan ya bude musu kofar shiga, bayansu shiga ne yayi gaba abinshi, tsayawa suka yi, suna kallon gidan a hankali. A kasar zuciyarta kuwa cewa take. *Ikram Allah ya albarkaci rayuwar ki a duk inda kike yau kin dawo min da abinda na rasa yau nice Mehran yabawa izinin zama kusa da shi! Kai Sultan Aamaan Abdus Samad Mehran ga mahaifiyarka nan* Kamar wanda yaji abinda ta faɗa ya juyo a hankali, ya zuba musu ido, sannan ya tako a hankali har gabanta yace mata. "Kuzo ku shiga cikin gidan, akwai sanyi sosai a wajen nan!" A hankali tayi gaba yana Binta a baya, har suka shiga gidan, ya nuna mata wani kofa, sannan ya kalli Darda yace. "Ka koma bakin kofar shiga gidan, kayi musu bayani!" "Toh Sultan Mehran!" Ya hade hannun shi alamar yaji, sannan ya juya tare da barin gidan. Sake kallon Shairah yayi shima ya nuna mishi hanyar fita babu musu, ya juya abinshi, sai Kayan hannun Fazilatul nisa ya amsa tare da wuccewa.suna bin bayan shi. Har dakin dake kusa da na Mahlika. Ya nunawa Narjis inda zata zauna a dakin Mahlika, ita kuma Sultanah ya bude mata dakin, ganin yadda yayi kura yasa shi kallonta, sannan ya juya ya rufe kofar, tare da nufar sama, tana bin shi a baya, har zuwa dakin shi da yake kwana. Ya saka kayanta a dakin sannan ya bar dakin tare da nufar daya dakin hutawar shi. Tunda ya shiga da ita hawayen da take dannewa ya digo mata, kallon shi tayi yadda yake tafiya a hankali, kamar mahaifin shi. Tana tuna daren da ta gama hailarta. Suna lissafin kwanakin daukar ciki da Narjis. "Sultanah Fazilatul, idan har Allah ya amsa mana, kika shiga cikin turakar Sultan a cikin wannan kwanakin da kika gama aladarki Insha Allah ciki zaki samu, dan haka da izinin Ubangiji kin kusan daukar dakin na kanki " "Toh Allah yasa, dan bana son wancan Yarinyar ta rigani daukar cikin yarima anan gidan." Dariya suka yi sannan Narjis tace mata. "Ai masarautan nan tab'awa mace ko namiji damar mulki, dan haka ko Mace ce muna bukatar ta,!" Ajiyar zuciya ta sauke sannan tace mata. "Haka ne, idan ma macen na samu alhamdulillahi zan iya rike abuna har ta zama shugaban wannan daular." Dariya suka saka tare da kawwata kome yadda mafarkin su zai tabbata. Bayan sun mata iso da sultan, ta shiga har turakar shi, a wannan kwanakin da ya hanata fita, sai da tayi sati sabida tun tana al'adar take gyara jikinta, har sai da tayi shar da ita, sannan ta gama toh wani irin dad'i tayi mishi, dan haka ya manta da wata Hoyam sai da suka barje amarcin su, sannan ta fito tare da bawa sauran Kwarkwarorin shi damar su karasa abinda ta bar musu. Sam ta manta da batun cikinta da take da burin samu, tunda ya shiga yayi ta ciyar da ita soyayyar shi, sai taji iya haka ma ya ishe ta, haka ma ya wadatar da ita ba sai ta nime wani abu daga gare shi ba, ya nuna mata har duniya ta tashi yana jinta yana kuma kaunar ta. Dan haka a duk lokacin da zata kasance dashi kamar zata zautar dashi take, a hankali kome yake tafiya har ta sami wata biyu, anan ne bata ga hailarta ba, shine ta saka a ka kira me magani a sirtacceen aka duba ta, ganin ciki ne ta tashi da kwarin gwiwar ta, ta gayawa mahaifinta, anan kuma aka sami Matsala. Domin yayi murnan cikin amma kuma bayan nan tana barin gurin. Kome ya sauya ƙaddara mara dadi suka sauya a rayuwarta. Ajiyar zuciya ta sauke tare da kallon kofar, alwala tayi sannan tayi sallah raka'a biyu, sannan ya kwanta a gurin. Can dare ya leko nan ya ganta kwance a kasa, a hankali ya shigo tare da jan bargo ya lullube ta, yana me jin sonta a ranshi, da tausayinta. Yana fita ya nufi wata kujera ya zauna tare da kallon kofar tagar dakin, yadda farin wata ya haska ko ina. _Ni ban zo nan dan karasa rayuwata ba! Dalilin ƙaddara ta kawo ni rayuwarka don Allah Sultan kayi min izini na bar gurin nan! Shi wancan shine mafarina_ *Ikram! Ni ba zan hanaki tafiya da shi ba, sai dai na miki alkawarin duk wanda ya kuskura yace zai rab'eki wallahi Sudan shi gawa!* Dafe goshinsa yayi cikin tashin hankali. "Toh waye ya tsaya a karkashin maganata nayi? Tabbas akwai wanda ya san nayi wannan furucin! Shi ya karasa aikin da na fara." Lumshe idanun shi yayi tare da tuno abubuwa masu yawa kanta, yarinya ta zuba mishi guba a zuciyar shi, da tasan yadda ta illata mishi zuciyar shi da har abada ba zata nesata kanta dashi ba,, da tasan yarda ya kashe rayuwar shi da bata bi wani namijin na,.yayi imani da Allah ciwon da ta bar shi da itace ajalin shi. Ikram zanen ƙaddarar shi ce, ita bai san yadda zai nunawa duniya halin da ta jefa shi ba, amma baya jin ko yaki ne zata iya cinye shi kamar yadda ta mishi. Babu yakin da yake Illata lafiyar d'an adam sama da irin yakin da Ikram tabar zuciyar shi da ruhin shi suke faffatawa, ta kashe mishi rayuwa tun daga lokacin da ta shigo gare shi. Ta mishi illa bata sani ba. Wannan yarinyar dub duniya babu mayakin da yayi nasarar huda Sulken yaƙin shi ba sai Ikram, ta huda mishi kirji da halayyarta ta tafi tabar shi da Ita, ta fasa mishi zuciyar shi da dabi'arta ta tafi ta barshi. Lumshe idanun shi yayi yana me jin ina ma da zata dawo gare shi, ina da zata Fahimci abinda yake faruwa a zuciyar shi da har duniya ta tashi, ba zata kuma nisanta kanta da shi ba, tazarar da ke tsakanin su ya zarce tazara da take yawo cikin shekaru a duniya. A cikin abinda bai wuce sati Daya ba, amma jin shi yake sakakke mutum. Ga baki daya duk wata izzar shi da mulkin shi ta tafi masa dashi, bai tab'a kawowa da bazatarta yake rawa ba sai da ta tafi da shi ta barshi a gurin. Mulkin shi bai mishi ciwo ba, kamar yadda Ikram tayi tafiyar ta, kuma har yau mahaifiyar shi bata zo gare shi ba, me yasa duniya ta cika da tsananin son kai? Me yasa mutanen da kake ganin suna kuka domin ka basu kukan sai dai su saka ka kuka? Wato shi yayi mata matashiya da cewa. _Karki sake abokin adawar ki ya fahimci shine silar kukanki!_ Yau kuma ta zame mishi silar kukanki shi, yau gashi yana ihu babu me jin sautin bugun zuciyar shi, yasha saka kanta domin taji halin da tasaka zuciyar shi amma, yarinyar nan ta juya baya tayi tafiyar ta. A daidai lokacin da ya dace ta tallafa mishi tayi tafuyarta, waye zai san halin da yake ciki? Waye zai gane firgicin da zuciyar shi take ciki? Shi nan an kashe su A banza, indai har haka da tayi mishi illa wata zata kuma shiga tarihin rayuwar shi toh har abada yayi katangar karfe ga zuciyar shi. Ba zai kuma yarda wata ya mishi kamun kazar kuku ba, kamar yadda Ikram tayi mishi. Ba zai kuma yarda a sake ratsa tsakanin zuciyarshi a mishi illa ba, tayi na farko kuma babu wanda ya isa yayi na karshe Ikram ke daya na bawai amanar kai na da zuciya ta. Ya fadi haka a kasar zuciyar shi. Sanyin asuba ne ya dawo dashi dogon lokacin da ya ɗauka yana karanta wasikar jaki, ya mike tare da fita yayi, a can yaje suka yi sallah asuba, sannan Malam Abul Bashar ya shiga musu karatun su, musamman shi da Allah ya mishi baiwar daukar abu, gashi a cikin sati guda kacal amma yana daukar hadda. A hankali yake sauke ajiyar zuciya, lokacin da ya shiga cikin gidan yaji ya dauki kamshin turaren da na girki, Ikram ce ta fado mishi. A hankali yake takawa cikin gidan, yana hango yadda bayi mata suke ta shige da fice, tare da gaishe shi. Tsayawa yayi sannan ya kalle su a cikin katon kitchen ɗin da yake kusan yakai girman dakuna uku. Murmushi tayi tare da cewa. "Shigo mana! Sultan MEHRAN!" "Hmm!" Yace kasan makoshinsa, fita suka yi sannan ya shiga, kitchen ɗin, kallon shi tayi sannan ta cigaba da cewa. "Wannan abincin shine Sultan Abdus Samad yake so! Naso da na rayu kusa da kai na koya maka cin shi!" Kallonta yayi sannan ya cigaba da kallon yadda take girkin, cikin kwarewa, idanun shine suka shiga ciko da kwalla, yana tuna Yarinyar da take hana idanunta barci sabida shi.yau ta tafi tabar shi! Ajiyar zuciya ya shiga saukewa akai akai, tare da dafe ginin Kitchen din wato inda suke ajiye kome na aikin. "Da zafi mutumin da muke kaunar kasancewa dashi yayi tafiyar bazata da rayuwar! Sultan kana son Baiwar ka ce?" Wani irin ajiyar zuciya yake saukewa tare da dafe kirjin shi yayi yana kallon.. ```BOOK one free ne, book two da three na kudi ne 200₦ ta bank 0472282105 ki katin mtn ta wannan Number +2347035133148 ko ta wannan Number 08130269641``` #Mai_Dambu... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: Monday-March-2021 FURE cikin ƘAYA* _CIGABAN DAULA BIYU_ BOOK TWO _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 06 Kallon shi tayi yadda yake kokarin sake kwallar da ta cika mishi idanu. "Karka sake naga kwallar Bahashimin ya sauka kasa, karka sake naga kwallar Jinin Abbasiyyah ya sauka kasa, idan har jinin dake yawo na Abdus Samad ne toh baka isa naga kuka akan so ba, karka yarda naji duniya ta kira min kai lusari! A koda yaushe buri daya gare ni, Duniya da mutanen Samaind su ambace ka da Shan Sultan Mehran, yau kukan akan so! Me akayi tukun. Idan Ikram rabon kace zata dawo domin Ina sonta har cikin jinin jikina. Idan ba rabonka bace zaka sami matar da zata so ka." "Ba zata dawo ba!" Ya faɗa kan shi a kasa, dan yanzun yake jin yana da wacce zata taya shi kuka da murna, kiran nasabar shi yasaka shi jin wani irin yanayi a ranshi. "Akan wani dalili ba zata dawo ba?" Ta tambaye shi, hankalin ta yana kan majuyin abincin, "Sabida sun kashe ta, ita da mijin da zata aura" Sake abincin tayi tare da kallon shi sannan ta kuma rike abincin, bakinta na rawa. "Ina Fudail?" "Baya nan na aike shi" Wani irin tausayin shi ne ya tsaya mata a ranta, dan haka ta dauke kanta tare da Cigaba da aikinta. "A gaban mutane dari uku da wani abu,. Suga Sultan Mehran yana kuka don kewar masoyiyar shi? Na taso inda ake boye so da jin dadi saboda girma da Darajar gidan da ka fito, Shan Sultan Mehran zai iya alaka da baiwa amma bai sama tilas sai ya zurfaffa tunanin shi akanta ba. Duk da nasan kai namiji ne, kuma zaka bukaci mace a gefenka bana son kayi kuka dan so! Kayi kuka dan suwaye suke tare da kai,kayi kuka dan al'ummar da suke kasar ka. Karka zurfaffa tunanin akan goben ka, sabida ita din na al'umma ce, kayi tunani da kyau. Ikram ka rasa ba kome ba, dan haka ka dauki haka a matsayin jarabawar ka, karka sake so ya illata lafiyar ka." "Ammyn ba so bane! Shak'uwa ce, shi yasa na." Wani irin murmushi tai sannan ta juya tana cire abin hannunta, tare da kallon shi. "Ni kamar uwace a gare ka, tunjiya nasan kana cikin yanayin damuwa, amma na kyale ka sabida ka samu nutsuwar zuciya." A hankali ya kalle ta a sadadde, sannan ya mai da kanshi kasa, kafin ya juya zai fita. "Kayi wanka, yanzun zaka karya." Tsayawa yayi kafin ya fice daga kitchen ɗin, kwalla ta goge kafin ta nufi, waje ta karasa aikin ta, tare da kiran bayi suka tattara, abincin kallon Mahlika tayi sannan tace mata. "Ya Alima take?" Sake bowl din hannun tayi tare da juyawa a tsorace, tana kallon ta. "Ki biyo ni d'akina " Tun da suka shiga dakin kanta a sunkuye, har Fazilatul nisa tayi wanka, ta fito tana shiryawa kanta yake sunkuye, tana gamawa tace mata. "Baki gaya min ya take ba?" Zuba gwiwar ta, tayi a kasa tare da sake kuka. "Don Allah Sultanah Fazilatul nisa kiyi min rai!" Murmushi tayi sannan tace mata. "Taya zan miki rai bayan duk wanda zai kusanci Mehran ina sane da fansa yazo dauka a rayuwar shi? Da yau na kashe Alimah bayan nasan da hadin bakinta aka so watsar dani waje, ai da ba a haife ki ba. Meye nufinku? Kunzo daukar fansa akan laifin da aka yi shi domin tsira da rayuwar ta, Hoyam ta sakata ture ta, domin kawai su kirkiro rigima a tsakanin su." Sake fashewa da kuka tayi tana me kara kallon Sultanah Fazilatul. "Sultanah wallahi duk abinda kika sani zanyi." Murmushi Sultanah Fazilatul tayi sannan tace mata. "Meye shirin ku anan gidan?" Jikinta ne ya dauki rawa, sama da can baya. "Ba zaki gaya min bane ko sai na saka an muku yankan rago dukkan ku!" Cikin kuka take fadan abinda aka saka su, tare da wulaknta darajar Mehran, mugun aikin da aka sasu ba karamin abu bane, lumshe idanun ta, Fazilatul tayi. Uwace kawai zata iya daukar nauyin tashin hankalin D'anta. Murmushi tayi sannan tace mata. "Idan na saka aka kashe ki, kamar na bawa makiya dama su kalubanci Mehran ne, idan na barki a raye su din da suka turo ki sune ajalinki. Itama Mahaifiyarki da take ta faffutikar, ganin ta turo ki hmm cutar dake zata yi domin amfanin dake za ayi idan bukata ta biya zaki sha mamaki." Nuna mata Hanyar fita tayi, jikinta a sake, sabida bakin cikin abinda take ji take gani, Alhamdulillahi tana tare dashi ko babu kome zata zame mishi garkuwa. Fita tayi ta nufi dakin da ya kwana, ta kira shi yana zaune ya kurawa guri guda ido, zama tayi sannan tace mishi. "Kayi hakuri!" Wani karamin murmushi yayi wanda bai kai Zuci ba, ya ce mata. "Nagode!" "Taso muje ka karya;" Babu musu ya mike suka fita dashi. --- "Innalillahi wa'inna ilaihi rajioun! Yanzun ta ya aka yi gobara ta cinye Y'ata da jama'ar ta?" Take ya fara wani irin girgiza, kafin ya fadi. Jasrah itama kuka take tare da ihu, Goggonta. Dakyar aka fitar dasu daga filin gidan da ya kone murus, ana kai shi gidan shi ya sake murmushi, tare da cewa. "Kome ya kammala min" Dariya suka saka shida Jasrah tare da kamanta abinda suka yi a gaban jama'a, suna dariya tare da cewa ai an yarda dasu. ~~~ Bude idanu nayi ma ganin a saman rumfa, da sauri na duba naga Izmah, ajiyar zuciya na sauke tare da shafa kanta, ina faɗin. "Duk wuya duk rintsi sai na baki garkuwa!" "Sarauniyar barci, kin farka?" D'aga labulen nayi sannan na ce mishi. "Eh amma yaushe aka dauko mu?" Dariya yayi sannan yace min. "Karki damu da haka? Zaki ji kome a hankali." Mika min abinci yayi na kalli abincin sannan naki dauka! "Kina tunanin ko na saka guba ne?" "Ai nasan ba zaka zuba guba dan ka kashe ni ba, aiko dan cikar Muradin ka zaka barni a raye." "Toh tunda kin yarda da haka kici mana!" "Zanci kai, Abokiyar tafiya ta nake tunanin bata cin abincin irin wannan" "Toh yayi kyau. Tunda haka ne bari akwai wani nama sai ki bata." Murmushi nayi sannan na cigaba da cin abincin. "Ban san sunan ka ba, lokacin sallah yayi?" "Taya kika san lokacin yayi." Murmushi nayi mara sauti sannan nace mishi. "Ka duba sararin samaniya, rana ta raba tsakiya." "Toh Malama! Haka muka yi ta musayan kalaman har muka iso garin, kallona yayi sannan yace min. "Daga yanzun zan miki aika kuma zai zo har inda kike, domin nayiwa Amir Rahil alkawarin zan kawo mishi sabuwar baiwa, kiyi amfani da wannan damar ki kashe min shi. A sanyayye yadda kowa ba zai kawo hakan ba a ranshi, ina son kiyi aikin nan da wata uku, ki shiga jikin shi yadda babu wanda zai iya fahimtar kome." Gyada mishi kai nayi, sannan muka shiga cikin birnin da ake kasuwanci, kamar ba gobe. Gaskiya garin yayi min kyau, dan haka ina kallon shi har aka nufi gidan sarautar kasar damu. "Karki manta kiyi abinda ya kawo ki karki yi tunanin fadawa wata damuwar da zata saka mu hadu a fada." Gyada mishi kai nayi, tare da jin son garin da yanayin garin yana shiga na, sai da muka ratsa wani gida, muka ci abinci, sannan muka nufi fadar kasar. An shiga damu, har cikin fadar musamman yadda muka yi shiga na tukurun bayi, muna zuwa muka zube a gaban wani dattijo, wanda yake buga mulki kamar me, "Amir Sulaiman, har ka dawo daga tafiyar da kayi?" Wani a gefen zubewa gaban Mutumin sannan ya ce mishi. "Sultan Mu'allim na dawo daga tafiyar da nayi, da fatan zaka saka amshe ni hannun biyu biyu" Ya faɗa cikin taushin murya. Kallon shi wasu daga cikin yan fadan suka san halin shi, kallona suke, sannan wasu suka dauke kansu. "Yarinya daga wani yanki na duniya kike?" .kallon shi nayi sannan na sunkuyar da kaina, domin ya bani damar magana. "Daga yankin Afirka ta Tsakiya." "Meye sunanki!" "Salwah!" Kallona suka yi kafin suka ce, min. "Ita kuma wannan wadar ba?" "Jasmin" Na fada a takaice, ina me sunkuyar da kaina. "Ku kaita shashin bayi kafin a kaita inda zata zauna. wato shashin Sultan Rahil" "Yanzun za ayi yadda kace" Haka suka tasa keyar mu, har shashin bayi, muna shiga suka shiga mana dariya, ban yi mamaki ba, sai dai ita Izmah sai ya zama kaman cin zarafin ta suka yi..dan haka na rike hannun ta. Nuna mana inda zamu zauna akayi sannan aka bamu abinci, na saka hannu zamu, fara ci wata cikin yan matan dakin, tana sanye da jan kaya. Ta kai min duka. Ban kulata ba,. Na turawa Izmah abincin cikin tsoro ta fara ci, sake kawo min dukka tayi na buge kafarta tare da kai mata duka, sai da kashin kafar yayi tsawa. "Wayyo Allah! Kafana!" "Ba rigima nazo nima ba, kowa dan haka ku shiga hankalin ku, nasan halin ku na bayi, dan haka kar wata ta kuma d'aga min murya. Dan zan karya kasusuwan ku!" "Toh mafadaciya! Sake mata kafarta, ki shirya a kaiki shashin Amir Rahil." "Toh!" Na sake kafar sannan muka fara cin abincin, muna gamawa na mike tare da nufar hanyar ban daki nayi wanka da alola, ganin na fito zan gabatar da sallah duk sai jikin su yayi masifar sanyi, suka shiga kallon juna ina idarwa nacewa Izmah. "Muje na taimaka miki kiyi wanka!" Haka na taimaka mata tana gamawa na fito, nuna mata gurin kwanciya nayi sannan nace mata. "Ke Yar masunta, duk wacce tayi miki shirme kiyi mata yadda kuke watsawa kifi koma a ruwa. " Da sauri matar ta leko tana kallona, cike da mamaki rabonta da taji murya irin na shi kusan shekarar ashirin da biyar kenan, ajiyar zuciya ta sauke sannan na fito ina tafiya tana waige na. Har muka fito shashin,.wato akwai wata dabi'a da Abba yake yi, a duk lokacin da ya shiga damuwa, zaka samu ya kai hannun shi baya, yana tafiya. Wannan dabi'ar nakanyi lokaci zuwa lokaci. Amma ban maida shi ya zama abin dogara na ba, kawai yau na tsinci kai na dayin haka ne, aikuwa ina yi naga abun mamaki, domin duk inda muka wuce Ni ake bi da ido. Da gudu wani mutum yazo ya janyo Ni bayan wani lungu. Zuɓewa yayi a gabana, tare da cewa. "Ban san ki ba, amma tabbas jinin Ahalin Mu'allim yana yawo a jikin ki, wacece ke?" Kallon rashin fahimta nayi nashi sannan na juya tare da nufar matar, har muka isa gidan da zata kai ni. Babban gidane me dauke da manyan dakaru, a hankali na shiga bin bayanta na sami dakarun gidan dukkan su a tsaye, wai ana wasa da Amir Rahil. Sai ihu suke suna tafa mishi. Shi kuma ya rufe fuskar shi da farin kyale yana niman su, ashe ita matar ta koma gefe, dan laifina a katse wannan haukar.ni kuma ban lura ba, sai ji nayi an kamani tare da sake wata zazzakar murya kamar ba namiji ba. "Ahah na kama waye?" Hmm, mara mutuncin kawai sai ji nayi ya kai hannun shi kan nonona ya matsa tare da dumbular shi. Har cikin raina naji zafin abin ban san lokacin da na murɗa hannun shi tare da buga shi da kasa sai da ya fasa wata irina kara, sake juya kan hannun nayi zan karya. Suka samun takobin akan wuyana. "Kin san waye kika daka?" Zubur ya mike tare da zare idanu, yana me cire kyallen a fuskar shi, sannan ya kura min ido. Gefen bakin shi yana fidda jini, sauke wata irin numfashi yayi, tare da kallon yadda nake fusace. "Durkusa! Ki bashi hakuri kafin a hukuntaki!" "A'a barta kawai, a gaban waye ta kayardani? Shin kun gani ne?" Girgiza mishi kai suka yi sannan ya fashe da dariya kafin ya kira su dukkan su duka koma baya tare da cewa. "Kunsan m.... Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: Monday-March-2021 FURE cikin ƘAYA* _CIGABAN DAULA BIYU_ BOOK TWO _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 07 "Toh tunda babu wanda yaga lokacin da ta makani da kasa a manta batun, kuganta sai kace wata namiji, dan haka muje muji meke tafe da ita." Ya basu hannu suka tafa, sannan ya zo inda nake tare da goge jinin bakin shi yana faɗin. "Hmm! Zan miki afuwa sai kin bani hakuri?" "Hakuri?" Na kuma tambayar shi, kallon masu tsaron shi yayi sannan ya kane musu ido, yace musu. "Ko ba haka ba?" "Eh ki bada hakuri sai mu kyale ki" Ganin suna b'ata min lokaci nacewa matar. "Ko zaki taimaka ki kai Ni shashin yarima Rahil!" Cikin wani irin jin dadi ya gyara kwalar rigar shi, tare da kallon na ya nuna min kanshi da hannun shi yana faɗin. "Gani nan" Kallon shi nayi cikin mamaki nace mishi. "Kai?" "Baki yarda bane?" Ya kuma dawo min da tambayar yana gyara hannun rigar shi, alamar shine fa, takaici ya sani cewa. "Toh yanzun naji nayi laifi kayi min afwa" "Na miki! Amma da sharadi!" Kallon shi nayi sannan nace mishi. "Name fa?" "Zaki nuna min wani abu ne me laushin da na tab'a." Suke fuskana nayi tare da kaiwa kafarshi wani mugun taku, sai da yayi ihu. Sannan na kyale shi. "Baka da da'a ne? Ina mace kana tambayana abinda ka tab'a a jikina ai sai a rena ka" na fada mishi kasa kasa. "Kuma haka ne fa," yana kallon mutanen shi. Sannan ya gyara muryan shi yana faɗin. "Wacece ke? Kuma waye ya turo ki?" Da sauri matar tazo sannan tace mishi. "Sunanta Salwah daga tsakiyar Afrika, Amir Sulaiman ne ya kawo maka ita" "Salsabila! Sunanta daga yau. Dan tafi dacewa da sunan. Sannan mu shiga daga cikin gidan." Ya faɗa tare da goya hannun shi a baya, abun sai ya bani mamaki da dariya, wato shima yana yi, share batun nayi har muka shiga cikin gidan, muna shiga muka sami ana ta aiki, haka yayi ta bin bayin yana make musu duwawun su, tare da zuba musu dundu a baya. Da zafi amma haka suke dariya, ya kai kan wani dattijo kenan na buge ganin shi sai da ya saka kara. "Toh kuma meye nayi miki?" Ya faɗa a shagwaɓe, har idanun shi yana kawo kwalla, "Wannan abun da kake babu kyau rashin da'a ce, Allah bai baka mulki dan ka wulakanta rayuwar wasu ba, Allah ya baka ne dan ka sama abun tausayawa a gare su ka Fahimta?" Fuuuu ya wuce abinshi yana kuka. Kallona suka yi dukkan su, tare da cewa. "Mun gode!" Share su nayi tare da nad'e hannuna a kirjina ina kallon gidan, yadda suke aiki. Babu juyawa ina tsaye har sai da yamma tayi sannan ya fito sanye da kananun kayan mutanen ketare. "Ke zo nan" ya kirani. Ba musu na isa gaban shi, kallon shi nayi sannan yace min. "Don Allah yaushe zan fita daga wannan yanayin? Ni ina son nayi rayuwa kamar kowa amma kullum Kaka rufe Ni yake yi! Kisan sabida me?" Kallon ko ina yayi sannan yace min. "Sabida yaran Kaka Uku maza kashe su ake yi, An kashe Kawuna Almustapha! Sannan an kashe Me bin shi Abubakar! Sai Abba na sa ake kashe shi a shekara goma da suka wuce. Kuma sabida mulki ne, don Allah dube ni fa, ina son nayi rayuwa kamar kowa amma an hanani, Kinga kisan yadda zaki yi mu fita cin kasuwan dare don Allah!" Ya faɗa a shagwaɓe, kamar zai min kuka. Kallon shi nayi tare da hango yar tusar jakin da yake kunnen shi sak da na Abba na. Murmushi nayi sannan nace mishi. "Ban san yadda zaka fita daga gidan nan ba, kayi hakuri Amir Rahil!" Kamar ya saka kuka haka ya kalle ni, sannan ya dauke kanshi kafin can ya sake min kuka. Har da ihu, share shi nayi tare da juyawa na fita daga gidan. Na nufi hanyar gidan da nafito. Ina juya labarin da ya bani. "Zaki iya tafiya da kome yadda kike so! Idan ma zaki iya shiga jikin shi duk ba laifi, amma maganar gaskiya bana son aikina ya wuce wata uku." Juyawa nayi na kalli mutumin sannan nace mishi. "Ba a min dole aiki tunda nice nace zanyi toh a zuba min ido." Kallona yayi sannan ya share tare da nufar hanyar shi na daban, nima nufi gidan nayi. Ina shiga na hango Izmah a kwance a tsakar dakin babu kaya, kowa yana harkan gaban shi. Da sauri na isa gaban ta, tare da cire mayafina na rufe ta dashi, sannan na kalle ta tana kuka. Irin wanda aka tozarta. Taune bakina nayi ina kallon matan da suke tsaye tare da rike bulala sannan daya daga cikin su tana faɗin. "Eh munga Wada ce kuma tana da kayan mamaki shine muka duba ko tana da budurcin ta har yanzu." Fashewa tayi da kuka tare da rungume ni. "Ki mai dani Gulsana, na hadaki da Ubangijin ki!" Matse kanta nayi a kirjina, ina tuna alkawarin da na dauka a raina. _Ya Allah kamar yadda ka Hadani ƙaddara da wannan Baiwarka Ya Allah ka bani ikon kare lafiyarta daga duk wani abin cutarwa daga nesa ko kusa_ "Ban san me yasa mutanen duniya suke da zalinci a ransu ba, hmm" nayi wani irin murmushi. Sannan na dauke ta tare da ajiyeta a saman gadon mu, duk da tana da zuri amma dake zuciyata tana zafi bana jin kome a raina. Rufeta nayi sannan na koma na rufe kofar d'akin, tare da kashe wutar dakin da gayya, ban tab'a sanin cewa zan iya wannan b'arnan ba, sai da aka kwashi awa daya da rabi, sannan na koma gurin kwanciya ta, lokacin sunyi ihu har sun godewa Allah, sabida na rufe tagogin dakin. Sannan na koma nayi kwanciya ta a gefen Izmah, raina a b'ace. Haka na kwana ina kallon duk wani motsinta, kiran sallah farko ya tadda Ni nayi alola da gabatar da sallar asuba, ina idarwa nayi mata wanka, sannan na nufi gurin amsar abincin. Anan me bada abincin take tambayar yan dakin mu. "Me ya faru daku ne haka?" Kallona suka yi tare da ganin yadda nake hada abincin mu. Sannan na dauki tire na jera. Nazo zan wuce wasu kartin mata suka sha gabana, sunkuyar da kai Masu bamu abincin suka yi. Ajiye abincin nayi sanan na mikar da hannuna kashin hannun suka yi kara. "Cikin girma da Arziki ku bani hanya na wuce, idan ba haka ba, al'adu zasu fiki daraja." Na fada ina murmushin mugunta. "Toh me zai hana karamar yarinya!" Dariya nayi sannan na kalle su, rufeni suka yi da dukka gabaki daya dakin yayi shiru, sai karan sautin duka kawai yake tashi, a hankali na mike tare da ture su na dauki abincin mu, na fashe da dariya. "Bana rena mutum, sabida ban san baiwar da Allah yayi mishi ba." Nayi tafiya ta, kamar danyen nama haka suke ta zuɓewa a kasa. "Kunga Yarinyar nan Shaidaniya ce! Idan kuka Cigaba da tab'a ta zaku fuskanci tashin hankali. Dan haka ku kyaleta horarriya ce, tasan me take yi." Inji wani me tsaron shashin bayin. Zama nayi na kalle ta, sannan na bata abinci. Kallon yan dakin mu nayi suna ta ficewa a hankali kamar munafukai, sannan na kalle Izmah, nace mata. "Meye ke damunki?" Cikin zubda kwalla tace min. "A cikin matan nan ne akwai wata me halitta biyu! Itace ta dauke min kimata, Ikram haka tayi ta saduwa dani tun bayan fitar ki, Don Allah ki nema min guba nasha na rantse da abin bauta gwara Firoz yaji labarin mutuwa ta akan yaji labarin abinda ya." "Mutuwa ba ita bace karshen wasu abubuwan, ita din mafarin wasu abubuwan ce, a cikin matan da na daka bata cikin sune!". Kuka take tare da rike Ni tace min. "Bata nan, daga wani daki take zuwa." "Lallai sun tab'a me tsada, kuma zasu biya a furashi me tsadar biya, dan haka zan fita idan nafita zan kai kamar minti goma, zan dawo." "Ina jin tsoro!" "Kina tare dani, Ni kuma ina tare da Allah,tsoron me zaki ji? Kwantar da hankalinki, zanyi kome cikin tsarina." Na gaya mata bayan na gama bata abinci sannan na gyara mata kwanciya, na kalle su babu kowa a dakin. Fitowa nayi sannan, na fita abuna. Tsayawa nayi a waje tare da jiran wani lokaci, ina nazarin abinda zan musu. Har na kwashe mintotin, sannan na kuma shiga cikin gidan, ina zuwa na sami kofar a rufe an bar mutum daya a waje, tun daga nan na fara cin ƙwallon Ubanta, har muka shiga cikin dakin. Sun bankare ta ita kuma Yar iskan tana tsaye da surar maza. Rufe dakin nayi tare da jan wani katako na karya. "Hmmmm!" Nace musu, sannan na nufe su. Da farko sun zata zan ji tsoron karka su rufa min ne, ya sani tsayawa, nan kuwa gyara zaman katakon nayi. Sai da na karya hannun da suka rike ta, ita kuma mata mazan nayi mata dukar kare dangi a gabanta, sannan na juya abuna, na kula da lafiyar Izmah, bude kofar aka yi. Masu kula da shsshin mu ne suka shigo, nan suka tambaye ni, murmushi nayi sannan na nad'e hannuna a kirjina. "Toh me zan ce muku? Kun barwa bayi damar suyi yadda suke so! Sannan a cikin gidan da mata suke kun bar mata maza tana rayuwa. Ku gyara ko na gyara kowa zama a cikin gidan nan." Murmushi nayi sannan na juya na cigaba da abinda nake, ina gamawa na juya tare da kallon Izmah, fita aka yi da matan sam na manta da Amir Rahil. ~~~ Kallon su yayi tare da cewa. "Hanyar yanzun Salsabila bata zo ba? Ku duba min ko tazo" "Ran shi dad'e! Bata zo ba." Kasa zama yayi ya kuma sake tuma tsalle can, zai kai musu duka. Kamar wanda ya tuna ya meda hannun sa baya. Tare da kallon su. "Yallabai kaci abincin ka." "Kaniyar Abincin! Da shegen kwalkwal dinka, maza wuce da fuskar shi kamar abinci. Yarinyar zaku." "Amir ga Almirah Laylah tana zuwa." "Kuce ta tafi bana son ganin ta." Haka kuwa suka hanata shiga cikin gidan, ya daura daya akan daya, yana jiran Ikram, har rana ya fadi bata zo ba, sai yaji babu dad'i kawai ya share ba tare da ya kuma nuna damuwar shi ba. Washi gari Haka na tashi tare da kammala kome, sannan na rike hannun ta, muka nufi gidan Amir, tun a hanya take tambaya. "Ina zamu?" "Inda aka kawo ni aiki." "Me yasa yau sai dani?" "Karki damu, hakkin kula da lafiyar ki yana wuyana ne!" Muna isa aka bude kofar, yana tsaye hannun shi goye a bayan shi. Kamar sakarai haka yazo ya tsaya min. "Yanzun don Allah abinda kika yi ya dace, ki ajiye mutum kama na baki zo ba, gaskiya baki kyaita min ba." Wallahi baya had'iye yawu, haka yake ta magana kamar na zubda kwalla, Izmah kuwa dariya ya bata. Hannun nakai bakin shi, tare da cewa. "Ya isa haka!" Lumshe idanun shi yayi tare da kallo na, gabaki daya ya tawo zai zube min a jiki tuni na kauce na bashi hanya ya zube a kasa. "Ke mahaukaciyar ina ce? Amir Rahil kika sake ya fadi." Mutumin ya faɗa da gudu rike da bulalar shi, sai da na bari ya tawo na mishi kwaf daya. Na gyara wuyana tare da cewa. "Duk wanda ya ce zai min hawan kawara Ni kuma zan shayar dashi nono uwarshi!" Mika mishi hannu nayi ya mike tare da kade jikin shi. "Waye yace muku itace ta sani na fadi? Salsabila babu ruwanta da kome ko?" Ya kalle ni yana murmushi, tare da wangale min baki, sha-sha-sha kawai. Na fada a raina, sam bai da wata Izza irinta me mulki, sakarai lamba daya shine wannan amma kuma son shi masu aikin shi suke, Ni kuma.... ```BOOK one free ne, book two da three na kudi ne 200₦ ta bank 0472282105 ki katin mtn ta wannan Number +2347035133148 ko ta wannan Number 08130269641``` #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: Monday-March-2021 *FURE cikin ƘAYA* _CIGABAN DAULA BIYU_ BOOK TWO _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 08 "Sakarai kawai" na fada da harshen swahili, juyawa wani dattijo yayi tare da cewa. "Kema kin iya swahili ne?" Kallon juna muka yi da Izmah sannan muka sake murmushi, muka ce mishi. "Eh!" Ai kuwa muka shiga hira dashi sama dama, duk da nikan ba sosai nake magana ba, amma Izmah kamar taga yan uwanta, haka suke hira. Kamar wani dolo ya tawo gurina ya tsaya. Wangale min baki yayi irin hee (😬) zunzurutun bakin ciki kamar zan mutu, dan har da kai hannun shi kafadana yana dariya, da gudu ya jani muna nufi bayan gidan shi, kamar babban mutum haka suka shirya mishi gurin lambune, muna zuwa ya ture ni na zauna sannan ya zauna tare da cewa. "Bani labarin garin ku" Ina ƙoƙarin mikewa ya daura min kanshi akan cinyata, yana faɗin. "Duk wanda kika ganshi anan yayi zama na amana da iyayena ne. Salsabila! Daga ganinki naji zuciyata ta kamu da kaunarki! Kuma naji ina kaunar na gaya miki halin da nake ciki. Duk da kowa da yadda zai dauki rayuwar shi, amma rayuwata ta tana da muhimmanci a gurin kakanina. A cikin dakin su mahaifina na, saura Autar su Abba ne yanzun Amirah Raziyana, babu kowa duk sun kare. Sultan Mu'allim Abdulkarim, shine cikakken sunan kakana, yana da mata biyu, da Kwarkwarah daya. Sultanah Balkisu Ikram itace uwargidan shi, sai Amaryan shi Ummu Kulsum, matar tsohon sarkin nan garin ne, me suna Ahmad. Yana da yara maza hudu, da mata biyu, Yaran Balkisu sun Hada da Almustapha shine babba, Abubakar me bi mishi sai Aliyu, Abbana kenan, sai Autar su Raziyana. Dakin Ummu Kulsum, akwai yara maza huɗu mata biyu, Sulaiman shine babban, sai Usman da Yahya, sai Isah. Khalilah itace ke bin Isah da Nana A'ishah, dakin kwarkwarah shi kuwa akwai. Kamaliyah a yaki aka kawowa Sultan Mu'allim, tana da yara Biyu Abdullahi da Abdul Rahman, , Sultanah Balkisu Ikram, yar kasar Habasha ce, daga garin Minalik, mahaifinta sarki ne a can. Dan haka..." Barci ya cigaba da yi, naji zafin barcin shi gaskiya dan naso jin karshen Labarin shi, amma haka na hakura tare da dauke kai na.. Sakarai barci yayi abin shi fa, haka na gama duba ko ina na gidan ban ga kome ba, ina tsaye a bakin kofar fakon aka yi sanarwar Sultan Mu'allim ya zamo ganin jikan shi. Durkusawa nayi tare da gaida shi. A hankali ya taka har gaban Amir Rahil, wanda yake barci saman kilishi, shafa kanshi yayi sannan ya kalle ni. Kai na a sunkuye. "Yar nan! Don Allah Karki cutar dashi. Bai da laifi ko daya, naji ance tunda kika zo kike dukar shi, don Allah karki kuma ɗan nasan ba zai bari a hukunta ki ba, tunda har ya iya gayawa mutane baki mishi kome ba. Toh dan Allah karki mishi kome, idan turo ki aka yi Ni na dace da hukuncin ki ba bashi ba." Cikin girmamawa na ce mishi. "Allah ya taimake ka, wallahi babu kome a raina, ina haka ne dan na tuna mishi nauyin da yake kan shi, kayi hakuri ba zan kuma ba." Mikewa kakan yayi sannan ya tawo gaba na,yana faɗin. "Jikana amana ne a gare ki, gashi nan yana kwance kuma barci yake yi don Allah." Sake matse hannun na nayi cikin wani irin yanayi, sannan nace mishi. "Insha Allah!" Sannan ya fita daga gidan, kallon Amir Rahil nayi kamar na rufe shi da duka. Haka nake ji, sabida ina zaman lafiya an kuma kara min nauyin shi. Lokacin Sallah yana yi na wuce nayi sannan nazo na amshi abinci na kira Izmah da ta sami Abokan hira sai hira suke abun su. Zama nayi muka fara cin abincin, muna hira nan take gaya min tana son zama da Iyalan tsohon nan dan taga da tafi sakewa dashi, a duk lokacin da suke Yaren swahili. Kallon shi nayi sannan nace mishi. "Kana jin me tace?" Murmushi yayi sannan yace min. Ai ba a wani waje bane a cikin gidan nan ne, Kinga wancan kofar gidan mu kenan, idan kema baki son zirga zirga zaki iya zama anan." Murmushi nayi sannan nace mishi. "BABU matsala, haka ma yayi." Koda muka taso kayan Izmah na dauko musu, sannan na bata hakuri Ni zan zauna a gurin mu. Alhamdulillahi, ki babu kome tana inda zata sami tsaro da kulawa, su kuma dakin mu, sabida ita nake d'aga musu kafa, domin ko jiya da ka rikice kuka ta fashe dashi tana ya da baya, alamar tana jin tsorona. Dan matuƙar raina ya b'aci Ni kaina har mamakin yadda nake juyewa nake. A hankali kwanaki suke tafiya, wani irin shakuwa ya shiga tsakanin mu da Amir Rahil, kuma kamar mayye, indai ban zo ba, zai damu kowa har sai an duba ni. Dan da gaske na Fahimci wawan sona yake, Ni kuma a duniya babu wanda na tsana irin shi. Dan haka muka yi ta shirya yadda zamu kashe shi, shakuwar da muka yi tasa shi matsawa lallai sai na kawo shi yawo. Dan haka cikin kasada, na dauke shi bayan na mishi kwalliya da shigar wata baiwa, muka fita. Kamar zautacce haka ya rungume ni tare da sumbatar goshina. "Ina son ki, domin ke daya kika bani farin cikin da nake bukata, don Allah ki taimake ni, kina dariya mana" (😬) ya wangale min baki. Tsuke fuska nayi, sannan na wuce abuna, yana bina a baya, har muka shiga kasuwar, nan yai ta sayan kayan ciye ciye, yana mika min, har muka gama, wani guri da babu mutane, ya nuna min muke zauna. "Salsabila! Me yasa baki dariya." "Hmm" nayi tare da murmushin gefen baki, sannan nace mishi. "Ban san me yasa fuskata ta wadattu da fusata ba, a koda yaushe ina jin ciwon abinda aka min. Na kashe min mijina, bayan nan dama bani da farin ciki ko bakin ciki sai rasa shi da nayi, babban burina na nufi SAMAIND na kashe wanda ya turo min aka kashe min Noman ranar auren mu." Kura min ido yayi tare da sake abin da zai kai bakin shi. Idanun shi sunyi jajjur. Tashi yayi tare da nufar hanyar da zai kai shi wani gurin. Bin shi nayi tare da fisgo shi. "Meye nufinka? Zaka janyo min magana ne? Ka tsaya na maida kai inda na dauko ka." Kwace kan shi yayi tare da kallona yana zubda hawayen. "Ki kyale ni, karki kuma tab'a ni" Karan sautin zuwan abu naji dan haka na kwashe shi ya zube ƙasa, kallona yayi ya ga ina raba idanuna, hango wasu mutane nayi cikin duhu, su uku. Da sauri na fisgo shi muka bar gurin da gudu, tare da shiga cikin Jama'a, kallona yake. "Kinga abinda kika ja min ko?" Marin wuyar shi nayi tare da juyawa na goye shi, muka shiga barin gurin da gudu kamar zamu tashi sama, ina saka kafana a kofar gidan shi, na sauke shi. Suka harbo min.wani karfe kamar ƙaya ya suke Ni ta baya sai da ya fito ta gaba. Haka na samu na shiga tare da rufe gidan, masu tsaro suka tawo da sauri. "Ku shiga dashi cikin gidan" na fada ina layi, juyawa nayi tare da ɗaukar takobin ghaddafi, na fita, jini na zuba a kafadana, amma haka bai sani jin na hakura ba, komawa nayi inda aka fara abin. Na zauna tare da ɗaukar abinda muka saya na fara ci a hankali, gani nayi sun kewaye Ni. "Wato ke me taurin kai ko? Kin dawo" "Waye ya harbe Ni da ƙwayar karfe?" "Ba zamu gaya miki ba." "Wannan shine mafi girman kuskuren da kuka aikata, daga kanku ya zama tarihi." A fusace na juya muka fara yakan juna, a rayuwata na tsani kayan takaici, dan haka cikin fushi da bakin ciki, nayi ta kashe yan iska, aladu kawai. Ina gamawa na juya na koma gidan Amir Rahil. Na ajiye takobin na koma gidan mu, ina zuwa. Ina isa na samu duk sun yi barci, dan haka na cire kayana, na dauki kayan kulawar gaggawa da yake dakin na wanke ciwona, ina fitowa na samu an sace kayan jinin. Ina kwance kawai sai ji nayi an watsa min ruwa, ina bude ido naga dakaru da manyan makamai, dan haka na mike a hankali. Haka suka tasa keya ta, zuwa gidan yari. Bude idanu nayi tare da kallon inda nake, ban damu ba amma kuma kasar raina ina jin tsoron halin da na kuma jefa kai na, amma kuma nasan wancan sakaran zai nime ne ni. Bayan an kawo ni sai ga wani mutum, yana nad'e da mayafi akan shi zuwa fuskar shi. "Wacece ke? Meye na kawo ki masarautan mu da zaki kashe min mutane haka babu tausayi." "Basu tausaya min bane, nima na shayar dasu nonan babar su." Na fada ina kallon shi. "Hmm! Ku azabtar da ita yadda sai ta tuna ranar da ta gaya min magana ina Amir guda." Bai bar gurin ba nace. "Ko dai d'an Kwarkwarah ne! Amir Abdullahi ko kuma Amir Abdul Rahman!?" Cikin fushi yazo ya shiga kwallo da Ni, ya na iya na zama kamar dole. Bayan yaga na suma ne ya kyale ni, Ni kuma ba suma bane. Kawai ina iya dauke numfashina na tsawon dakika dari uku da sittin, sabida kwanakin da nayi a cikin ruwa. Fita yayi abin shi, kai na a ya she, suka mai dani gurin da nake, "Amma kuma yarinya karama ce fa?" "Ba daga nan take ba, tana da horon yaki. Sannan ta iya kisa na fitan hankalin, kafin yau naji labarin ta a bakin bayi yan matan nan, wai an kawo mafadaciyar baiwa bata magana da kowa sai kawarta, idan kuma ka sake tayi maka magana sau daya toh na biyu zata karya maka wani guri ne." "Ni kuwa sai nake ganin kamar ba zata iya daukar kasadar haka ba, domin tun bayan shekaru ashirin da biyar, ba a kuma samun jarumi irin Amir Almustapha ba, domin ance shine yake iya kisa cikin abinda bai fi dakikai dari biyar ba." Kirjina ne ya shiga bugawa, musamman idan naji sun ambaci sunan mutumin sak da na Abba na, lumshe idanuna nayi. Sannan na kurawa ciwona ido. Bayan awa goma, sai ga Amir Sulaiman. Yana zuwa ya shigo min, har cikin dakin. "Ke wacce irin dakikiya ce?" "Irin na wanda yake kanka." Cikin jin haushi ya d'aga hannun shi, rikewa nayi sannan na kalle shi. "Sam tunanin ka baya baka lissafi, ka tambaye su waye ya shigo bayan an kawo ni, sai ka dawo na gaya maka dakikancin da yake damun ka." Kura mata ido yayi, musamman yadda tayi maganar alamar babu wani tsoro ko fargaba a ranta, asalima ranta sake tayi maganar, bayan ya tambaya aka tabbatar mishi da wanda ya shigo gidan, kallon Juna suka yi sannan cikin karfin hali nace mishi. "Kayi tafiyar ka, nan da jibi zan fita duk tsarina ne, sannan kayi taka tsantsan da kowa, sabida ba kai ɗaya bane kake niman ran D'an Aliyu ba, kuna dayawa. Amma abinda nake so da kai tukun mu fara rage abokan adawar ka, idan aka gama dasu zaka iya samun damar kashe Amir Rahil, tunda shi daya ya rage maka." "Wai Ni kam wani irin horo kika samu ne?"ya tambaye ni, Murmushi nayi sannan nace mishi kaje zan baka amsar wata rana. Na fadi haka,ba tare da na kalle shi ba, bayan tafiyar shine na kwanta a gurin, bana jin dadin jikina da rayuwata baki daya, ina jin kewar abubuwa dayawa, amma ban san meye su ba.. kawo mana hari jiya ya sani fara kokwanto akan meye dalilin da yasa ake kashe yaran Sultan Mu'allim, musamman y'ay'an Uwargidan shi Balkisu Ikram? Haka kawai ruwa bata tsami banza, haka kawai ana kashe yaran d'akinta yau ga kisar ya fado kan jikan ta. Shafa wuyana nayi.sannan na zubawa dakin ido, a sanyayye na sauke ajiyar zuciya. #Mai_Dambu. [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: Monday-March-2021 *FURE cikin ƘAYA* _CIGABAN DAULA BIYU_ BOOK TWO _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 09 ..... Washi gari. Ya farka yana kallon d'akin shi, murmushin takaici yayi tare da fashewa da kuka, yau shi ne wani ya dasawa Kaunar shi soyayya da ta kasa Mantawa dashi, dole yayi yaki da kaunar da takewa wancan mamacin. Bayan ya gama abinda yake yi, yayi ta zuba ido har rana babu Salsabila babu labarinta, fitowa yayi sannan ya kalle mutanen gidan, so yake ya tambaye su, ita amma kuma ya kasa, dan haka ya share batun, har zuwa yamma babu labarinta, anan suka ga ya birkice musu. "Amir kayi hakuri zuwa gobe zamu nimo maka ita " "Dalla ka min shi, wani irin gobe kasan yadda ta tsare rayuwata da lafiya ta kuwa, kuje ku nimo min ita" Haka yayi ta masifa, karshe dai suka fita babu wanda ya gaya musu abinda ya faru, har washi gari. Rahil bai yi barci ba, kamar yadda yaga rana haka ya ga dare, can gurin asuba barci ya dauke shi, bayan ya farka yayi Sallah sannan ya tashi tare da ɗaukar alkalami ya tura ga kakan shi yana niman Izini a barshi ya fito. Dakaru aka tura kusan guda dari biyu,suka saka shi a tsakiyar su, har fada, yana shiga cikin fadar ya gaida kowa sannan ya zuba gwiwar shi a kasa, yace. "Allah ya taimaki Sultan!" Hawaye ne ya shiga zuba daga idanun shi. Shiru fadar yayi sannan Amir Sulaiman yace. "Shalelen Sultan meke damun ka?" Cikin shasheka yace. "Yarinyar da ka kawo min bata nan! Shekaranjiya na tistata muka fita." Kallon Kakan shi yayi da ya kura mishi ido, yana hango yaranta Yaron dan shekara ashirin da biyar, amma gabaki daya ya sauya sabida rashin adalcin magauta. "Sultan! Yarinyar nan kare lafiya na tayi tayi har taga zan bata matsala ta dake ni anan! Kafin na fita hayacina, goyani tayi tana gudu kamar ba mace ba, Sultan don Allah idan baka son karasa ni a duba ko ina na cikin kasar nan, domin lokacin da zata mika Ni ga Ghaddafi ina jin yadda taja ajiyar zuciya, Sultan ba nauyi na bane, sai na shigar wani abu jikinta. Don Allah ku nima min ita. Na ganta, ko ita ce wacce Ummina take ce min zata zo wata rana." Duk da kowa yasan Mahaifiyarshi ta rasu da tsowon cikin kanin shi, sannan an kashe daya kanin shi. Shine kawai yake raye. Cikin fusata Amir Sulaiman yace mishi. "Akan Baiwa kake kuka? Yau duk inda ta shiga sai na nimo maka ita." Ya mike tare da dakaru aka fita zuwa gidan bayin anan suka samu labarin tana kurkuku, wani badakaren ne ya goye ta, har cikin fadar. Mikewa yayi miyafin da take bayan rigar shi tana ja, kamar wacce iska yake kad'ata, ya isa gabanta cikin tashin hankali. "Salsabila!" Dakyar na bude idanuna. *Amma Yarinayr nan makira ce! Irin wannan aka same su suka kai hudu a fada tabbas wuta ce zata kone kome* Tafiya nayi zan fadi ya tare ni, yana me rike hannu na. "Don Allah. Bude idanun ki, gani nan a gabanki, ba zan kuma barin wani ya cutar dake ba kinji Salsabila" Murmushi Sultan Mu'allim yayi sannan yace. "Dama Baiwarka mayakiya ce?" Cikina ne ya bani wata kululu. Amma dake na dauke numfashina, sai ake ganin kamar na suma. Amir Sulaiman yace. "Abba! Dole ta zama mayakiya domin kare rayuwar magajin masarauta gobe, kaga ai ba laifi bane dan ta kare shi ta hanyar yaki." "Yawwa Baba na, ka fahimci abinda nake nufi." Inji Amir Rahil. Ko ta kan kowa bai kuma bi ba, ya dauki Ikram yayi waje da ita, sabida gani yake kara zaman shi kara nisanta numfashin ta, dan haka ya nufi gidan shi da ita, da sauri aka nimo likita ya fara bata kulawa, har zuwa wani lokaci. ___ "Ya kamata a kuma saka ido akan mutanen da suke kawo mishi hari ta karkashin kasa" Lumshe idanun shi Sultan yayi sannan yace. "Wazir! Ina son ka bincika min Wannan yarinyar sam bana son na kamata da laifin da ban sani ba, domin ina jinta kamar Almustapha!" Dake su biyu ne a dakin sirrin, abokai ne na amana, kuma suna matukar kaunar juna, Mahaifiyar Amir Rahil yar waziri ce, me suna Abu Ayyub, Gyada kai yayi sannan yace mishi. "Binciken zai iya daukar lokaci, amma zamu yi Insha Allah, sannan ita kanta yarinyar ina zargin turota aka yi, yanzun kuma toh." A hankali suka gama sannan suka fito. Abin su. --- rike take da Alqur'ani, tana karantawa. Zama yayi sannan yace mata. "Sultanah idan an kai aya a daure kula ni," Rufe Alqur'anin tayi sannan tace mishi. "Naji an kaiwa Hibban hari shekaranjiya ko?" "Eh wallahi" Ya faɗa cikin sanyin murya. "Haka suka kaiwa Almustapha na, suka kashe min shi ko gawar shi ban gani ba, suka kuma kashe min Abubakar dina gwara shi naga gawan shi, Sannan suka kona min Aliyu Abu turab, don Allah Sultan ka tura mu, Minalik. Na gaji da ganin zuban jinin yarana, Raziyana zata iya rike kanta amma shi bai." "Insha Allah, yana tare da kariyar Ubangiji, Akwai wacce take kula da lafiyar shi." "Taya zaka ce haka? Taya mace zata kula da lafiyar namiji irin shi, ki kamanta idan suka keb'ance." "Yarinyar bata da wannan tunanin, naga fuskarta me dauke da kadaici don Allah karki raya wani abu a ranki." Had'iye kuka tayi tare da kwantar da kanta a kafad'ar shi, ~~~ Kifawa D'anta mari tayi sannan tace mishi. "Alawadaran dakikin ƙwaƙwalwar ka, sannan ka zata mutane irin yarinyar gama garin mutane ne? Yarinyar da ta kashe mana mutanen da suke mana aiki? Abdullahi ashe girman banza gare ka, toh wallahi kaji bazan tab'a ganin wannan abun kunyar ba ka kashe yarinyar sai ka tawo na." "Ammah, yarinyar nan fa ba zata kasu ta dadi ba, domin tana da horon fasahar yaki, sannan koda mun hada dakaru kimananin dubu ba zata kasu a hannunsu ba. Ammah naga yarinyar a cikin dakikai talatin zata iya kashe kartin maza sama da tamanin lokaci guda, kaifin basirarta ya wuce yadda kike tsammani. A cikin dakikai talatin da wani abu ta kashe mutane shida, me kike tunani zata aikata ga lusarin d'an baki da bai iya rike kan shi ba..idan har abinda na Fahimta akan yarinyar gaskiya ne toh tabbas bamu kadai muke bukatar ganin Bayan Rahil ba. Akwai wasu a bayan mu, ko mu muna bayan wasu,.kiyi nazari mana." Shiru tayi sannan ta dauke kanta tare da kurawa Abdul Rahman idanu, tabbas yayi gaskiya. ~~~ Lokacin da aka ni inda Izmah take da gudu ta faɗa kai na, tana kuka. Rungume ta nayi tare da cewa. "Karki damu,ina raye." "Toh kawar mu, fita ki bamu guri a dubata ko" Kallona tayi na rike hannun ta, tare da gyada mata kai. Murmushi tayi sannan ta fita, da kanshi ya cire min rigar jikina, kallon na yake a sace fuskar shi a had'e, ya fara kokarin zare min. Mayafin da na rufe kirjina, da sauri na juyar da hannun shi. Tsalle yayi ya faɗa kai na. A hankali bakin shi ya shiga nawa, bude idanu akan shi, tare da lumshe idanun, jikin shi yana rawa, ya kasa cire bakin a saman nawa sai da na daki kirjin shi na wurga shi. Kamanin wani mutum nake gani, yana min gizo a idanuna tare da murmushi, ture Rahil nayi tare da kallon kofar da ake sallama. Kama gefen cikin shi nayi na murɗa sai da ya saka ihu. "Oouch! Ke wacce irin mutuwa ce?" "Likita yana kallon mu!" "Don Allah Karki gayawa kowa nace ina sonki, Sabida Zubewar darajar gidan mune" Mikewa yayi a kaina yana gyada min kai, Haka ya tashi daga kai na, likitan ya shiga duba ni, yana gamawa. Rahil ya shigo tare da zama ya zuba min ido, can ya b'ata rai. Sannan ya mike tare da cewa. "Na manta ma ina jin haushinki." Ya saka kai yayi ya fita. ---- Alhamdulillahi kwana na biyar na warware, takamaimai bani da abin yi, domin naje har gidan yana hanawa na shiga cikin gidan, wai yana fushi. Ni da na fishi daru, sai na koma shashin bayi abina. "Baba kasan me? Salwah tana d'agawa Rahil kafa, amma bai Fahimci haka ba, wai ya hana a barta ta shiga gurin shi." "Yarinta ke damun shi, kuma har yanzun bai san ciwon kanshi ba." Haka suka yi ta hira, tare da fadan halin Rahil, yadda bai da damuwa. Yau sati na uku, tare da bin gidan mutumin da ya dake ni, Aikuwa na sami gidan, ranar da na warke sumul. Ai ku ranar da misalin karfe biyu na dare na dira mishi. Yana tsaka da barci shi da wata baiwa, tab'a shi nayi ina cin wani tufan da na gani a d'akin. Yana farkawa ya bude baki zai min ihu na zabga mishi naushi. Sannan saka shi a gaba na mishi shegen duka, sannan na bar gidan, washi gari bai tafi fada ba. Yau dan renin hankalin can ya nime na shiga gidan, nima na murza mulkina, naki shiga aikuwa ko awa ba ayi ba, sai gashi, kallona yake kamar ya dauke ni. "Salsabila! Laifin meye nayi miki da zafi?" " Na gaji da zama da sakarai irinka" idanun shi ne, suka cika da kwalla, alamar yaji haushina, tab'e baki nayi sannan na juya, mishi keya. Takowa yayi sannan yace min. "Nan da sati Uku, za ayi wasan shekara, kuma ban iya kome ba, wannan karon na sami labarin Amir Yasir da Yazeed zasu halarci taron, sannan Amir Samir zai yi. Taron duk shekara ake yi, kasancewar Abba Almustapha ya kware a abubuwa guda uku. Fada da takobi, fada da hannun, sai mafi soyuwa a zuciyar shi sarrafa kwari da baka.. Abba Abubakar, ya kware a iya amfani da mashi sai fada da hannun sai amfani da watsa reza, Abba na kuwa masanin fadar da takobi ne, kawai bayan nan sai gashi an kashe su. Ban iya kome ba, ke kuma kin iya fada kuma zaki iya kare." "Waye ya gaya maka nazo ne domin na kare lafiyar ka? Ni nazo ne takanas sabida kai. Dan haka ka tafi ka nimo me tayaka ka aikinka, Ni ban iya ba." Kamar zai fasa kuka, haka yake kallona, tare da sauke kan shi kasa, ya jima a tsaye sannan ya fita, daga gidan, dariyar da naji yasani fitowa daga cikin gidan, wasu matasa uku na gani, sun saka shi a gaba suna mishi dariya, sunkuyar da kai yake hawaye yana shirin zuba min. "A duk inda aka tara taron jakuna, dole sai sun nuna halin su, ku saka kai ku bar gidan nan ko kuma ku tashi da kafar daya hannun daya" "Ai kace ƙaruwar da Abbana ya kawo maka kenan, me idanun mage." Ya faɗa yana kallona. Isa nayi gaban wani bishiya tare da karyan reshen, murmushi yayi yana share kwalla, a hankali na isa gaban su. "Kuyi tafiyarku?" "Babu inda zamu sai mun tambaye shi bana ba zai kare kimar mahaifin shi bane, gwara Abubakar yana da Almirah zata kare kan mahaifin shi. Almustapha kuwa dama bai bar baya ba, dan haka babu me kare kimar shi. Kai kuma lusari." "Zan kare Mahaifin shi, zan kare Almustapha, zan kare shi. Na karb'a kuma sai ku a kara gaba." "Ke Yar uban waye?" Lumshe idanuna nayi, cikin wani irin zafin nama na daki bakin shi, "Ba a zaga min Uba a kwana lafiya" Na yarfe hannuna, tare da kura mishi ido. "Kika dake ni?" "Ubanka ma yayi min ma dukar shi zanyi" "Keee!" "Kai kare! Zan dake ka na daki mazauninka!" Na fada mishi. "Lallai kinyi na kudin ki, kuma zaki biya." "Karka damu, ai na rigada na biya kuma haka zan iya tayawa." Ganin da gaske zan iya karya sune suka fita, tare da kallona suka yi tare da murmushin mugunta, tsayawa nayi a gaban shi. Ina kallon su. Ina jin yadda yake sauke ajiyar zuciya.... ```BOOK one free ne, book two da three na kudi ne 200₦ ta bank 0472282105 ki katin mtn ta wannan Number +2347035133148 ko ta wannan Number 08130269641``` #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: Monday-March-2021 *FURE cikin ƘAYA* _CIGABAN DAULA BIYU_ BOOK TWO _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 10 Akai akai, tausayi ya bani, ina tsaye har suka fita. Suna fita daga gidan, juyawa nayi hannuna a kirjina. "Nagode!" Na fada min a sanyayye, tausayi ya bani. A hankali na daure fuskana nace mishi. "Ba wai ka fadi haka bane, dan sami damar zama a lusarance, dole ka." Wani irin juya ni yayi lokaci guda yayi kamar zai kai ni kasa, hannuna dukka biyu suka wuyar shi, ina zare ido. "Jarumta idan har gadon shi ake dole na gada, Allah bai halicce ni akan ki kuwa hmm!" Ya faɗa tare da d'agani, kasa magana nayi, ko daya bana jin shi a raina, domin sai kana yin abu kake shin shi toh shi koda wasa bana jin shi. Haka na shige cikin gidan abuna, tun daga ranar na hana shi, barci muka fara horon yaki. Amma bana samun lokacin shi, baya nutsuwa. shi da zai nutsu muyi abin sai ya kama kai hannun shi yana wasa da gashina, ko kuma ya kai hannun shi k'uguna, sai uku ina fasa mishi baki. "Don Allah ki daina saurin hannun mana" "Baba wallahi bana son dukar shi, baya nutsuwa ne sam." A hankali lokacin yayi ta tafiya, kwanaki suna kara zuwa. turowa aka yi wai naje fada za a yi mana gwaji, lokacin da muka shirya yana gaba ina baya. Har muka isa fadan. A wani babban filin aka ware domin gwaji, tunda na shiga suka ganin da shigar mata, suka yi ta min dariya. Sultan Mu'allim yana gani na, ya kura min ido. Haka kawai yake mata kallon kurilla. Tare da jin wani irin abu akan yarinyar, har aka nuna mana kwari da bakan, Yayan Sultan Mu'allim, waɗanda da suka rasu, kallon kari da bakar nayi tare da shafawa, wato na Amir Almustapha. Cireta nayi tare da kaɗe ta. "Ki ajiye za a baki wani." "Don Allah ka barni nayi gwajin dashi." Kallon Sarkin kira yayi ya gaya mishi. Shi kuma ya gayawa Amir Sulaiman ya kalli Amir Rahil ya gaya mishi, cikin rawan jiki yace. "A bata ko Baba na" Kallon Abdullahi da Abdul Rahman yayi, harara suka zabga mishi, tare da su Ahmad. Maida kallon shi yayi ga Sultan, cikin sanyin murya ya gaya mishi bukatar shi, murmushi yayi mishi sannan yayi alamu a barta ta dauka. Su Amir Yazeed da Yasir, da samir sunji haushi. Domin shi Yasir dan gurin Raziyana ce. Kallon mutumin yayi sannan yace min. "An amince kiyi amfani da shi, amma don Allah karki karya alkadarin kwari da bakan, domin ta zama na tarihi, me shi ba rago bane, sannan tarihi yake kafawa da ita ba rushe tarihinta ba." Ya faɗa min a sanyayye, amsa nayi tare da kallon shi. Haka kawai nake jin wani bayani yana zuwa min. _Wata rana wannan yanayin zai amfane ta Fudail! Zai amfane ta Rakshan, ku rufe mata idanunta ta harba kwarin jikin wancan bango!_ Kallon gurin nayi tare da jin kalaman kamar yanzun ake gaya min, ban san waye shi ba, amma tabbas zan so Allah ya kuma hadani dashi. A hankali na nake taryo maganar da wasu ma. _Dole kiyi aiki da ƙwaƙwalwar ki sama da zuciyar ki, ki auna nisan inda kike da inda zaki harba kwarin ki, haka zai taimaka miki wurin_ "Magana ake dake!" Juyawa nayi tare da kallon shi, sannan nace mishi. "Kace me?" "Sunyi harbin ko zaki yi!" Kallon su nayi tare da ganin duk sun sami abun da ake bukata saura ni ce. "Akwai kyale ka rufe min idanuna?" Na bukaci haka, juyawa yayi ya dauka domin akwai a jikin inda kwarin yaƙe, dariya suka saka ganin ana rufe min fuskana, Amir Sulaiman kan yasan zan ci, domin yana mamakin baiwar da Allah yayi min. Ana gama rufe min idanuna, na saka kwarin a cikin bakar, sannan na ja a hankali, ji nayi kamar anzo dai dai bayana, an kai hannun kan cikina, sannan aka d'aga hannuna da naja kwarin. _Zuciyarki ta buga kamar yadda zaki dake kwarin, karki fadi domin idan kika fadi asara na ne, so nake Nasara ya aure ki_ Jan karin nayi da karfi, sannan na sake shi cikin wani irin nutsuwa da fitar numfashina, naji karan isar shi gurin domin yayi kara "fitttt" Kafin faruwan haka ina jin karan bushe bushe, amma ina sakewa naji shiru kamar an dauke ruwa. "An gaida sarauniyar baka! Bude idanunki." A hankali na warware abin ina kallon gurin, wato da ya caki abun sai da ya huda shi har wajen idanun. "Ku dauko min ita!" Inji Sultan, har inda yake na isa sakamakon sakani a gaba da dakarun suka yi. Ina zuwa na zube a gaban su. "Yarinya meye sunanki?" "Salwah!" "Ina iyayenki?" Murmushin gefen baki nayi sannan nace mishi. "Ban san su ba" "Kamar ya? Ki iya furucin ki, domin a gaban Sultan kike" "Ni kaina ban san kai na ba, abu daya na sani an kashe min d'an uwana, kuma zanje daukar fansa, bayan nan hatta garin da na fito ban san shi ba. Iya sunana na rike" "Baki iya tuna kowa ne?" Sultan ya tambaye ni, "Mmm!" Na fada tare da sunkuyar da kaina, "Waye ya koya miki harbi?" Damke hannuna nayi sannan nace mishi. "Wallahi ban san shi ba! Kuma na manta dashi baki daya!" "Kinyi harbin da sak Almustapha ne yake iya harbin, dan haka zan saka ayi min binkice akanki." "Nagode!" Na fada. Sannan na mike, tare da komawa gurin. An nuna min yadda zamu yi wasa na biyu, duk sauran suna da masu horon su. Nice daya bani dashi. Takobin katako aka bamu, dan haka tunda ka hada ni da wani, na kayar dashi,.aka kuma hadani da wani na kayar dashi. A take aka fara nuna rashin jin dadin yadda nake kokarin rushe tarihin samari ukun nan, ga baki daya duk abinda aka yi sai na nuna zarra, dan haka muna gama amfani da takobin aka ce zamu yi gwajin damtse. Anan ne mutane da yawa, suka shiga murna dole na fadi, shi kuma al'amari irin wannan dabara ce ba karfi bane, dan haka Ni abokin karawa na, duka daya nayi mishi na biyu kuma sai da na kwantar da shi, sannan na koma gefen, abinda yafi basu mamaki zafin nama na.hakan muka gama sannan aka sallame mu. Duk yadda yaso ya dame ni, hana shi magana nayi, har dare ina zaune sai ji ina son fita, dan haka na shirya na fito, haduwa nayi da samari ka uku nan. "Gwana!" Kallon su nayi sannan na dauke kai na, sake tare ni suka yi, naga zasu bani ciwon kai, Shine na sauki wani karamin itaccen da na a gefen hanya, na shiga hada musu zafin kai dashi, sai da suka gudu da kafar su.. ~~~ SAMAIND Zaune yake yana bitar darasin shi, Fudail ya shigo yau kimanin wata guda har da sati biyu Baya faru, zama yayi a gaban shi, cikin murmushi suka kalli juna sannan yace mishi. "Sultan da fatan na same ku lafiya!" Murmushi yayi sannan ya kalle shi, iya murmushin yayi ne saboda Fudail, zama yayi. Ya shiga mishi bayani ne. Mika mishi wani kaya yayi sannan yace mishi. "Kamar yadda ya faru dai tayi auren, har nazo da abokin shi. Sai dai a daren da muka fito niman su, aka kashe shi. Bari na kira shi" Ji yayi kamar ya cire zuciyar shi ya huta da wannan tashin hankalin, haka Fudail ya shigo da Sarwat. Yana ganin Sultan ya zube tare da fashewa da kuka. "Wallahi iya bakin kokarina nayi amma ban ganta ba, banga dalilinta, lokacin da na dawo na sami Noman kwance cikin jini yace min. Na dauke shi mu bar gurin, kuma nayi kamar yadda yace min, sannan yace min don Allah kar na sake ban nimo ta na kawo maka ita ba, Yasan ba kai ka tura a kashe shi ba, domin bayan faduwar mu, ruwa yaji daya daga cikin mutanen yana cewa. Sun kashe dakarun Samaind, baki daya, saura Fudail ne kuma yasan suna hanyar zuwa, sai yake gaya min, don Allah na gaya maka kayi hakuri da ita, domin ba zata tab'a yarda ku zauna lafiya ba, karka biye mata domin ba lallai bane ta fahimce ka, don Allah kabita a Sannun, sannan yace min idan da hali na zauna a jikinta a matsayin me tsaron lafiyan ta." "Bayan kai waye yasan tayi aure?" Fudail ya tambaye shi. "Waɗancan dakarun sun san tayi aure.". Sarwat ya faɗa. "Zaka iya boye maganar aurenta har abada a cikin masarautan nan?" Jinjina kai yayi, sannan yace. "Eh Fudail!" "Tashi ka tafi!" Cikin sanyin jiki ya bar gurin, kallon Mehran Fudail yayi sannan yace mishi. "Sultan!" Dakatar da Fudail yayi tare da cewa. "Kowa yana da damar zab'ar abinda yake bukata, ita rayuwar ta take bukata ya sabunta, Ni kuma na ajiye ta a guri daya. Shin kana ganin haka zai mana kyau? Shi masoyinta ne, Ni kuma uban gidanta ne, shin nayiwa kai na adalci? Dan haka ka bar kowa yayi rayuwar da ya dace dashi, ya kuma zabi abinda yake bukata, karka tilasta wa wani yayi abinda bai da niyya sabida kai." Cikin damuwa da jin ba dad'i yace mishi. "Sultan Mehran! Amma ai maganar gaskiya idan za ayi ta dole a cire son Rai, kana bukatar yarinyar a rayuwarka, kana Sonta." Wani irin juya hannun shi yayi tare da rike wuyar Fudail, kakari ya fara idanun shi sunyi jajjur, murmushi yayi sannan yace. "Sultan MEHRAN! Kana son Baiwar ka" Ture shi yayi sannan yace mishi. "Karka kuma ambaton soyayya a nan, idan ba haka ba, zan hallaka ka." Cikin bakin ciki da takaicin halin Mehran yace mishi. "Idan kaso karka barni a raye mana kai ka sani, amma kana son Ikram, soyayya me hade da kishi ma kuwa, kai kanka baka san wani irin so kake mata ba" Lumshe idanun shi.yaui ba tare da ya kuma kallon Fudail ba, haka yayi ta magana tare da masifa yadda yake boye shaukin shi. Bayan fitar Fudail, ya sake fuskantar shi kamar zai yi murmushi, sannan ya kuma daure fuskar, murmushin da bai shirya bane ya fado mishi, tare da tuna ranar da zasu bar Madinatul Mah, murmushi ya sake sannan abinda ya faru a ranar ya dawo mishi kamar yanzun abun ya faru. Babu abinda ya fi d'aga mishi hankali, kamar ranar da suka kwana tare, haka kuma Noman ya ratsa tsakanin ta. Wani irin ajiyar zuciya yake saukewa kamar wanda ya sha kuka ya koshi, kuma zunzurutun kishi ne yake damun shi, dan haka ya lumshe idanun shi. Yana kuma hango cikin ƙwayar idanunta. Juya kan shi gurin kunshin da Fudail Ya kawo mishi yayi a hankali ya janyo tare da fara warware shi. Turo kofar da aka yi ya sashi dakatarwa. Mahlika ce dauke da tire na azurfa, sai kofinan shi da yar butar ruwan zafi, tana zuwa ta ajiye a tabirin kusa da shi, ta fara zuba mishi. Da wutsiyar ido ya kalle ta, tana aikin jikinta yana rawa. "Kin zuba min guba ne?" Sake kofin tayi daga hannun ya ya fadi kasa, murmushi yayi sannan yace mata. "Zoki min tausa!" Jikinta yana rawa, ta mike tare da nufar bayan shi, ta kai hannunta a hankali tana mishi tausar wuyar shi. Ta jima a tsaye kafin ya sallame ta, sai da ta kwashe abinda ta zubda ta gyara wurin, sannan ya fita, Cigaba yayi tare da duba kayan, karamar fatar jimina da kayi rubutu a jikinta, nad'ewa yayi kafin idanun shi yakai kan Tambarin kasar marocco, sai wani tafar kura da aka yi rubutun shima da shi. Wanda yaga tambarin Askandariya, juyawa kayan yake tare da kallon su. Ko shi yasa take da tsananin zafin rai, toh amma ai wannan shaidar ba zai tabbatar da cewa ta fito daga babban zuri'a bane, kawai dai sun saka ne domin, mata bayani. Baya tunani me idanun nan kamar tsaka ta fito daga wata babban gida ne.... ```BOOK one free ne, book two da three na kudi ne 200₦ ta bank 0472282105 ki katin mtn ta wannan Number +2347035133148 ko ta wannan Number 08130269641``` #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: Monday-March-2021 *FURE cikin ƘAYA* _CIGABAN DAULA BIYU_ BOOK TWO _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 11 Cikin takaici ya kuma kallon kayan, yana mamakin halin irin nata, sam bai tab'a ganin me taurin kai kamar jaki irin, gashi garin shegen rashin kunyar ta, ya janyo an kashe ta a banza. _Kana tsammanin zata mutu cikin sauki ne?_ Wani shashi na zuciyar shi yayi mishi tambayar, dafe goshinsa yayi, a sanyayye yace "amma kuma ance ta mutu?" _Toh kai ka yarda ne?_ Yayi, tare da dunkule hannun shi, _Idan har ka yarda ta mutu! Tabbas Zuciyar itace zata fara gamsuwa me yasa kullum_ Mikewa yayi dan ya fahimci, matsalar Ikram da shi, zata iya sakawa a fara kiran shi tab'abbe. Koda ya fito falo ya sami Sultanah Fazilatul da Fudail, sai Sarwat da yake basu labarin yadda aka kashe Noman, kallon su yayi tare da isa jikin tagar falon me dauke da furanin, yana gyarawa da wata wukar gyara fure. "Abinda suka fada ya sanyani jin tabbas Sultan Mehran bai mata adalci" shiru yayi tare da jan fasali, kafin ya cigaba da cewa. "Don sanye suke da kayan dakarun Samaind, kuma suka tabbatar mana da cewa, Sultan Mehran ya turo su." "Ba shi bane!" Inji Sultanah Fazilatul nisa, ta faɗa a sanyayye tana kurb'an shayi, kallonta su kayi, sannan ta cigaba da cewa. "Ba dakarun SAMAIND bane, sabida lokacin da kuka fita idan baka manta ba, kun hadu da wani mutum, a wani jirgin ruwa, kusan kunyi tafiyar tare ne!" Shiru yayi yana nazarin abubuwan da ya faru, a hankali ya d'ago kanshi. "Tabbas anyi haka!" Wani boyayyen ajiyar zuciya ya sauke daga can yana jin yadda Sultanah take wanke shi. "Toh mutumin ya biku har inda aka daura auren nan, sai dai bayan ya bar gurin ya dawo, inda zai tafi yayi na shi uzurin,. Bayan ya koma inda Ikram take ya samu an tadda garin, dama na tura shi ya dauko min ita ne! Ko da yabi ku dajin yace ya samu ana ta saran Noman, dan haka ya dawo, a hanyar dawowa ne ya hadu da dakarun Samaind da aka kashe su tare da watsa musu wuta suna ci, sannan haka ya tabbatar mishi cewa wad'ancan ba dakarun SAMAIND bane, domin a cikin masarautan ai mutanen da Ikram ta hana su kwanciyar hankali, ta saka Mehran a Jikinta, ba tare da ita kanta ta sani ba. Zuwan ku ya kara musu kwarin gwiwa, amma dama can an shirya kashe ta a ranar da za a bawa Mehran damar zab'en yan matan da zasu zauna dashi." Cike da mamaki yake kallon ta, sannan ya cigaba da abinda yake idanun shi sun yi jajjur. "Shigowar Ikram masarautan nan, a yarjejeniya sulhu ta shigo. Kuma da aka shigo da ita an tabbatar matukar ta haɗu da Mehran zai yi wuya tafiyar su bata zo daya ba, shi yasa aka barta a karamar baiwa har aka kawo ta shashina." Mikewa tayi sannan ta nufi inda Mehran yaƙe, ta amshi wukar hannun shi tace mishi. "Koma can ka zauna!" Ba musu ya iso gurin su Fudail ya zauna, tare da sunkuyar da kanshi. "Nice na turo ta gare ka? Ina bukatar ta a tare da kai! Duk macen da zata zauna da kai dole ta zama me ilimin addini! Me iya hukunta duk wanda ya aikata laifi! Me iya fada maka gaskiya kamar yadda babu wanda zai gaya maka! Sai abu uku da take tare da shi. Bata da tsoro! Bata da gulma ko munafunci, sannan mafi girman abinda ya ja hankalina akanta bata karya duk abinda zata yi akan gaskiyar ta take yin shi! Bata sakewa da kowa sai da kanta, kuma babu abinda ya dame ta da kai dan kasan ta ko baka santa ba. Wannan shine ya saka Ni na turata gare ka. Ina da yar da naso ta zo gare ka, amma ba zata yarda ka bata wahala kamar yadda ka bawa Ikram ba, ba zata iya jurewa ba, shi yasa naki tazo. A yanzun haka na tabbatar Ikram tana raye,. Abu na gaba da take yi ba mamaki tana faffutikar sai tazo daukar fansa abinda aka mata, tasan halin ka, ka san nata, ka fara shiri kafin tazo gare ka." "Amma kuma Sultanah na duba kasar ruwan baki daya ban same ta ba, nayi iya bincike na, bata cikin ruwan, sannan dakarun da suka aikata hakan sun dubata bata cikin ruwan." Inji Sarwat, Wani irin murmushi tayi sannan ta dauke kanta, daga gare shi. "Tana raye," ta faɗa bayan taja numfashin ta, kura mata ido suka yi, kafin suka jinjina al'amarin. "Ikram ba gama garin mutane bane, tana da juriya da jarumta, zata dawo domin koda ta mutu dole za a kuma haihuwarta, dan haka ku saka a ranku zata dawo, kai ma baka tsira ba, domin duk ranar da ta shigo ta ganka sunanka makiyinta." "Toh don Allah meye nawa? Ikram da dama can haushina take ji wai Ni munafuki ne, ina sane nake barin Noman kula yan mata, balle kuma yanzun ta gannin a gurin Babban makiyinta ina ga cewa zata yi Ni ne na saka baki aka kashe NOMAN." Ya fashe da kuka. Me Fudail zai yi ban da dariya, shi kansa Mehran sai da yayi murmushi. Ganin haka Fudail yayi ta saka shi yana fadan halayyar Ikram, sai ganin Sultan Mehran suka yi ya kishingida yana me sake murmushi. Musamman yadda take tafiya kiwo, tare da yadda take cin kaniyar yan matan dasuka ce zasu so NOMAN, sai gashi sam bai tab'a jin kishin noman ba, asalima jin dadin yadda ake fadan halayyar su yake, inda ya fahimci cewa. Noman yana da saukin hali, kasancewar ita kuma tana da zafi kome kashin abu zata iya dakatar wa. "Sai dai duk da wannan zafin na Ikram a cikin gidan su, kare yafisu daraja." Ya faɗa hawaye na zuba mishi. "Tun bayan mutuwar Mahaifiyar su, sai suka kasance kamar marayu, duk da kowa yasan mahaifin su, shi yake horar da duk wani matashin dake garin Gezira fada, Mahaifiyarta kuma tana horar da Mata yadda ake amfani da kibiya, ban tab'a ganin uwa me son yaranta ba, duk da basu son nunawa yaran muhimmancin rayuwa, kamar a baka damar kayi walwala cikin Arzikin da wadata. Sariya itace baiwar Mamar su, kuma tana matukar kula da yaran, dan haka da Mahaifiyar su zata rasu, ta bukaci mijinta ya dakatar da horan da yake bawa mutane, domin halin da ta tsinci kanta yana da nasaba da horon da suke bawa mutane ne, har wasu matasa daga wani yanki daga cikin garin suka farmake ta, bayan sun mata fyade da tsohon cikin." Kofin da Mehran yake rike dashi na tankarar sai da ta tsage tare da soke mishi hannun shi, yana diga da jini. "Suka wulakantatta, abinda ya saka bawan Allah nan kasa koda motsi, domin sunce zasu koma kan Babbar Yar shi da karamar, haka aka yi ta kokarin daukar mataki ya hana, sannan yace ya barsu da Allah, zai bi musu hakkin su. Bayan rasuwar ta da abin cikinta ne ya auri baiwarta, tun daga lokacin bai da kwanciyar hankali, ana haka wata rana ya fadi a gurin kiwo, " Haka ya basu har labarin yadda aka dauko Ikram akan lafiyar kanwarta. _Ce maka akayi sabida jin dadi nake nan! Rayuwata bata nan! Ina raye ne sabida kanwata da yau zan sami duniya da kome na cikinta tace tana bukata zan bar mata koda kuwa ace abinda nake so yana cikin shi! Ka kyale ni ba zan zauna ba!_ Kusan abinda yake yawo kenan aransu dukkansu uku. Wato Sultan Mehran da Sultanah, da Fudail. "A ranar da ta bar garin Allah ya amshi rayuwar Airan, wanda zuwan mu ne Noman ya gaya mata, bayan nan ba zance ta san abinda ya faru da Mahaifiyar ta ba." "Zata sani! Kuma zata bi hakkin jininsu. Idan ta kyale su sun cutar da ita, dan haka dole ta rayu, dole tana bukatar rayuwa a duk inda take zata so taya nisan kwana" Kallon Fudail tayi tare da kallon Hannun Sultan Mehran, da sauri ya dauko kayan aiki ya fara duba mishi hannun shi. Kallon Sultanah yayi sannan yace mata. "Ina bukatar zuwa gezira!" Kallon shi tayi cikin murmushi sannan tace mishi. "Ina zaka? Daukar fansa abinda aka mata? Indai har zaka iya haka toh ka fara bincikar waye ya kashe Mahaifin ka, idan har kayi haka zaka iya zuwa gezira." Daga hakan ta mike tare da barin gurin. ~~~ Ji nayi an watsa min abu kamar raga, suka dauke ni sama aka nufi hanyar wani gida dani, watsa Ni suka yi a kasa. Fita nayi daga cikin ragar, tare da kallon su, nace musu. "Ni bana son fada, don Allah ku kyale Ni!" "So muke mu baki abinda wancan sakaran ya kasa baki." Dariya na kwashe dashi sannan nace musu "Idan har kuka iya cire koda rigar jikina, nayi alƙawarin da kaina zan kwanta kuyi ta hawa kai na kuna sauka, idan kuma nayi nasara kareraya ku." Dariya suka kwashe da shi, sannan. "Kai ku cire mata kayanta tsaf ku miko min ta" Kai na a sunkuye, badakaren ya miko hannun shi, murɗe hannun shi nayi tare da juyawa nayi tare da karya hannun, sannan na naushi hakarkarin shi. Faduwa yayi tare da jijjiga kamar me farfadiya, mik'ewa nayi domin ina durkushe. Na tsaya ina shafa hannuna, sannan na musu alamun su tawo. Haka muka yi ta dasu..sannan na karya hannun Yazeed da Yasir, Samir kuwa targada mishi kafa nayi. Sannan na juya na bar gurin. Ina shiga gidan mu na bayi, sai ga dakarun. "Ke!" "Kayi kasa da muryan ka sabida mutane suna barci, muje!" A hankali na fita tare da binsu, har gidan da aka kai ni, ina zuwa na samu kujeru biyu babu masu shi, daya kuma Rahil ne jikin shi yana rawa. Ina zuwa na dafa kafad'ar shi, ina lura da yadda ya sauke ajiyar zuciya. "Ke wacece?" Kallon Amir Sulaiman nayi, sanan nace musu. "Zan gaya muku wacece ni, amma shi wannan ku sallame shi. Idan ba haka ba. Zan iya samun kai cikin rashin nutsuwa." "Ke!" Amir Sulaiman ya saka min tsawa, takowa nayi har gaban shi, tare da shafa fuskar Yasir, tare da kai fuskana kan ma shi. "Kasan me? Da ace babu yarjejeniya, da na karya kashin wuyar wannan da yake cewa a kwab'e min kaya yayi yadda yake so dani, tarbiyyar da kai mishi kenan?" Wani tab'e baki nayi sannan nace mishi. "Yadda kuke farautar Rahil ya sani fara shakku akan ku, dan haka ku zuba min ido ko ku rufe idanunku." Daga haka na riko hannun shi muka bar gurin, har mun isa baki kofar na d'ago yatsar hannuna nace musu. "Kar a kuma tab'a min shi, domin zan iya samun damar kashe kowa" Sannan na fita dashi tare da kallon shi, kai hannun shi yayi tare da rungume ni, ina jin sautin bugun zuciyar shi. "Nagode" ya faɗa hawaye na zuba daga idanun shi. Tausayi ya bani na rungume shi. A hankali na cire hannuna a jikinshi muka tafi gidan, har cikin gidan shi na raka shi. Zan fito. Yayi maza tare da riko hannun na. "Ki zauna anan!" Ya faɗa min cikin dakewa, tare da zuba min idanun shi. Haka kawai sai.naji yayi min kwarjini. Dan haka na zauna. Ya nufi ban daki bai fito ba, sai kawai yayi ta tsalla ihu. Da gudu na shiga. Dariya ya saka min tare da cewa. "Toh zoki taimaka min" "Baka da hankali" Na juya zan fito. "Wayyo Allah!" Da sauri na juya, "subhanallahi!" Na fada tare da juyawa da sauri nayi, ina jin takaicin wannan Iskanci tare da fita daga ban dakin. Koda ya fito ina tsaye, zama yayi tare da cewa. "Zoki goge min kai na;" Wato na lura da Rashin mutuncin shi wani yakewa, dan haka ina zuwa kusa dashi na zabga mishi naushi. "Wayyo Allah na, kiyi hakuri!" Ya faɗa kamar zai yi kuka, hmm na ce tare da juyawa zan fita ya finciko ni, na fado kanshi. "Baka san ina d'aga maka kafa bane?" Juyar dani yayi. Kallona yake tare da lumshe idanun shi. Kanshi ya kai wuyana nayi maza na kai hannuna wuyar shi. "Kisan abinda nake ji akanki?" "Don Allah!" Fada muryana na rawa, janye hannuna yayi tare da kallon cikin idanu, murmushi yayi tare da kallon yadda nake zare ido, hancin shi ya kai kan nawa yana gogan nawa. "Don Allah kabari!" "Har yanzun baki sona" gabana ne ya fadi, "Kayi hakuri! So daya tak nayi kuma na binnewa me shi, zuciyata da ruhina yana gare shi, bana jin kome akanka shi daya nake jin tasirin kwayar idanun shi, shirun shi shine Yaren shi a gurina, na manta da shi amma zuciyarta yana rike da dabi'ar shi. Kishin shi akai na a bayyane yake, ban san fuskar shi ba, amma kaunar shi dawammamiya ce..... ```BOOK one free ne, book two da three na kudi ne 200₦ ta bank 0472282105 ki katin mtn ta wannan Number +2347035133148 ko ta wannan Number 08130269641``` #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: Monday-March-2021 *FURE cikin ƘAYA* _CIGABAN DAULA BIYU_ BOOK TWO _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 12 Ganin yadda kwalla ke cika a idanuna yasa shi girgiza min kai tare da cewa. "Kiyi hakuri! Ba zan iya barin ki, ki subuce min ba, dole nayi abinda zaki zama nawa har abada." Cikin wani irin sauri yake kokarin rabani da kayan jikina, riko fuskar shi nayi, sannan nace mishi. "Me yasa kake ganin kamar zina itace saukakkakiyar hanyar da zaka same ni? Me yasa kake ganin kamar idan har ka kwanta dani ba zan guje ka ba, zan zauna domin rufawa kaina asiri? Karka manta ni zuwa nayi nan kasan dalilin zuwan nawa? Baka sani ba, daga ganin mutum a jikin ka har ka bashi zuciyarka, toh kashe nazo yi!" Na fada da karfi. Cikin wani irin tsoro da tashin hankali, ya kalle ni. Tare da sake ni. Yana kallona ilahirin jikin shi rawa yake, tare da nuna ni da yatsa. "Meye nayi miki?" "Sani aka yi! Dan haka karka yi tunanin soyayya tana cikin abinda ya sani nake zaune da kai, ganin ta kowani kusurwan gidan sarautar ku ana niman ranka ya sani bincike inda zan Fahimci meye matsalar su. Hakan ba zai sakani samun damar binciken ba sai na tsaya a bangaren ka, shine dake kai banza ne ka fada soyayya dani, ka kiyayye kanka domin Ni zan kashe ka ne" na fadi haka ina mik'ewa daga gadon, tare da gyara jikina na fita, ina jin yadda yake kuka ya bani tausayi dan haka na fita daga gidan. --- Duk wanda na tambaya meke faruwa, basu bani amsar asalima tsoron tambayar suke, sannan abinda na fahimta, yaran Sultanah Balkisu Ikram sune kusan sadaukai a cikin masarautan, kuma basu nan a raye, dan haka na yanke hukuncin tun karar Sultanah Balkisu Ikram, sai da na bari dare ya raba, sannan na shiga hawarawa katangar gidan sarautar, ban tsaya ba. Har sai da na isa bakin kofar shashin ta, sannan na dake kafadar masu tsaron kofar. Sannan na shiga, a hankali har cikin dakunan sai a wani daki can na same ta, zaune akan abin sallah. Tana kuka, tsaye nayi cak ina kallonta, tare da jin kukanta har cikin kokon raina, a hankali na taka har gaban ta, ya cire mayafin dake kan fuskana na zauna a gabanta. "Me yasa kike musu kuka?" D'ago kai tayi tare da share kwalla tace min. "Barka da zuwa! Amma me yasa kika zab'i shigar dare?" "Ya akayi kika san zan zo?"na tambaye ta, murmushi tayi tana share kwalla, tun da aka ce Sulaiman ya kawo mace da Rahil ya bukata, naji a raina babu makawa zaki bukaci gani na, Idan da namiji ne tuni yayi abinda ya kawo shi, dan nasan ya kawo ki ne ki kashe Rahil, sai dai zuciyar mace ba irin na namiji bane, mace tana da taushin. Ban san sunanki ba?" "Bilqisul Ikram Mustapha!" Cikin wani irin sauri ta d'ago kai tare da rawan jiki, tace min. "Matso na ganki!" Tana kai hannunta fuskana, alamar bata gani, shafa fuskana take son yi dan haka na matsa kusa da ita. "Ina iyayenki?" Ta tambaye ni, "sun rasu!" "Daga ina kike?" "Gezira!" Ajiyar zuciya ta sauke, sannan tace min. "Me kike bukata a cikin wannan gidan?" "Me yasa suka kashe miki Yaranki?" Hawayen da suke zuba tare da tuttukowa daga idanunta ya sani fahimtar kome. "Yanzun me kika fahimta akan Sauran dakunan?" Na tambaye ta, girgiza min kai tayi sannan tace min. "Kasancewar nice matar shi ta farko, kuma yar kasar Habasha, kuma ina zuwa ban jima ba, Yayan shi Sultan Khabir ya rasu, sai aka bashi sarauta, ganin haka ne yasa yaran shi suka fusata me yasa ba zaa bawa Mahaifiyar su magajiyar sarauta ba(Which mean Empress) Sai suka fusata har itama Ummu Kulsum din taji babu dad'i, su kuma sunyi nazarin gidan da tafito ne, ba wasu bane kuma idan aka basu magajiyar sarauta, basu da Addini dan haka suka zab'i Mu'allim, lokacin ina goyon Cikin Almustapha, anyi rikici karshe aka tsayar da magana idan ta gana takaba zata aure shi kuma ya amince. Sanin cewa musulunci bai haramta ba yasani saukar da kaina, har Allah ya sauke ni lafiya, lokacin na haifi Almustapha, a hankali sai mutum suka fara kokuwar ganin ai tunda na fito a cikin gidan da suke da karfin mulki a nahiyar Afirka, dan haka suka fara bani goyan bayan a bani Sultanah, shi kuma Sultanah ana iya samun shi ta karfin mulki,. musamman idan kin hada nasaba da manyan masarautu a jininki, sai Allah ya sanya aka fada abin daidai kai na. Kuma aka duba tarihin kasar mu, babu kowa nawa da yayi bauta, mulki aka haife mu muka taso cikin shi. Dan haka suka bani, tun daga lokacin aka fara farautar rayuwar Almustapha, har na haifi Abubakar, sha'anin mulki dole sai kayi takatsantsar, dan haka duk ta yadda naga mijina zai kauce ina tsaya mishi domin ina da ilimin addini sosai, shima kuma haka, Ikram. Har na haifi Aliyu, ana samun matsala a cikin gidan nan sai da na haifi Raziyana, na sami sauki lokacin Mu'allim ya auri Baiwar shi. Itama ta haifi yara maza Abdullahi da Abdul Rahman, anan aka zafaffa k'iyayyar da ake acikin masarautan. Cikin hukuncin Ubangiji, sai gashi yarana sune Jarumai ko yaki aka tafi sune suke dawowa da tuta, tun Almustapha yana da shekara sha biyar ya fara fita yaƙi, kuma ya jagoranci yaki na fitar hankali, har ya kai matakin shekara ashirin da biyar, su uku suke fuskarta yaki, kowacce iri ne, Allah yayiwa Almustapha baiwar iya fahimtar lamarin yaki, yayinda Abubakar yayi tafiya har kasar ruma, yayi ilimin yadda ake sarrafa, nakiya, shi kuma Aliyu ya kware a iya leken asirin abokan gaba, yara Uku sai suka zama kaf nahiyar Afirka su ake kwantaccen dasu. Idan suka fara yaki har saka maza gudu suke." Murmushi tayi wanda ya fidda mata yan lub'anta, sannan ta cigaba da bani labarin. "A hankali yarana suka kawo ka, Ana cikin nima musu auren Yar Daular Askandariya, aka wayi gari ya tafi farauta daga nan ba a kuma ganin shi ba sai kayan aikin shi. Muna cikin wannan halin Abubakar da yayi tafiya zuwa kasar Sham, a hanyar dawowa ya rasu, Kinga bude wancan akwatin, zaki ga rubutun su kowa ya iya Rubutu, kuma sun ajiye min tarihi." Haka na bude tare da daukowa naga sunan Almustapha, gabana ne ya fadi. Sakamakon ganin rubutun Abba na,.kallonta nayi ina jin hawaye na zuba min, tabbas akwai ranar da na tab'a ganin shi yayi rubutu, sannan ya juya zoben hannun shi wanda yake da wani abu a bayan shi ya kunna wuta ya kona bakin abun ya manna a jikin Takardan. Sai daga alamar wancan da na gani a gurin shi. "Bayan mutuwarsu, dan haka Muka kama Aliyu muka aura mishi yar gidan Abu Ayyub, shekaran su goma sha biyu, aka kona su, Allah ne ya nufa Rahil zai yi nisan kwana, aka samu baban shi ya fidda shi daga cikin gidan, ya turo shi waje! Har yau ba a san suwaye suka musu kawanya ba." Fesar da kukan nayi sannan nace mata. "Me kike so nayi musu?" "A hukunta su idan an same su, idan kuma ba a same su ba, Allah zai hukunta su." Mikewa nayi sannan na taku daya biyu, nace. "Idan aka musu shara'a a fada, zasu sami sassauci, hukuncina dai dai take da hukuncin Shari'ar Muslunci. Idan ka kashe a kashe ka idan ka tab'a a tab'a ka, matukar jini Ya tsaga dole hukuncin ya haura kansu." Ina gama fadar haka na fice daga cikin gidan, na nufi gidan Sulaiman, ina shiga na shiga sumar da dakarun shi, har na isa cikin dakin shi, yana kwance nayi kwance kwance na zuba Mishi duka akan cikin shi. Da gudu ya farka. "Yau nazo na ji bayanin daga bakin ka, saura sati biyu na gama abinda ya kawo ni, idan kuma kayi karya, zan datse kofar numfashin ka." "Wai Ni kam wani irin masifa ce ya sani kwaso ki?" Ya fada yana dukan kanshi. "Waye ya kashe Almustapha da yan uwanshi." Zaro ido yayi sannan ya rufe bakin shi. Yace min "Kasancewar kin tab'a Bala'i zan gaya miki, amma zaki mutu" "Karka damu, a jini na yake wasa da mutuwa,! Gaya min" "Almustapha nina fitar dashi daga kasar baki daya na kai shi iyakar kasar nan bayan mun shiga Algers, domin Amirah Raziyana tana son zama mace ta farko da ta mulki kasar nan, ba zata tab'a samun damar haka ba, dole sai takawar da yayunta, Ni da Almustapha mun taso abokan amana, ba zan iya gani a kashe shi babu dalili ba, dan haka koda na kai shi Algers sai na samu nayi mishi dalilin da ya manta da kome nashi amma kafin nan ya gaya min cewa. Ko bude ko bi jima zai dawo, idan bai dawo ba Allah zai kawo jinin shi. Dan haka ina jin haka na buge kanshi ya fad'i, sannan na yiwa bayin shi barazana da zan kashe su. Sanan daga baya na hana shi da wani mutumin da shi kanshi Almustapha bai sani ba, yayi ta bibiyar rayuwar shi, har aka ce min ya sauka a gezira. Amma ban tab'a zuwa ba, wannan shine zunubin da na aikata, sai Abubakar kuma, Babu ruwan mu a cikin mutuwar shi, domin an hanya tasaka aka kashe shi wannan kan ba ita daya bane har da Abdullahi, Mutuwar Aliyu ma haka har da su. Domin Umma da ta ga lallai Mulkin gidan ya koma kishi a tsakanin zubda jini ta hana mu shiga cikin maganar gidan. Bayan haka toh mun fara jin ƙishin ƙishin, Sultan zai yi murabus, kuma ana zargin Amir Rahil zai bawa, shine na kawo ki." Kukan da nake ya kura min ido. "Wacece ke?" "Bilqisul Ikram! Yar Amir Almustapha Mu'allim! Idan na kashe ka na b'ata kome, zan Barka a raye domin Rahil kuma, zan dawo kamar yadda nace, .maka amma zan karasa aikin da azo yi sai dai ba gawar Amir Rahil bane, gawan mutanen da suka yi wanka da jinin Ahalina zan bar su. Domin akwai sauran aikina." Juyawa nayi na fita daga gidan, nayi kuka nayi danasanin kuntatta mishi, ashe dan uwana ne,nake ta bashi azaba, shi yasa suka ki bashi tarbiyyar sarauta... Haka har na isa gidan, ban kuma kwanciya ba, domin a duk lokacin da na kwanta bana iya barci, sabida Rahil gani nake kamar ina rufe idanu na zasu far mishi. .... A hankali har kwanakin da za ayi gasar ya shiga zuwa, kamar na san ana shiri a kaina, ranar na dauke shi har gidan Amira Raziyana, tun da Samir ya ganni, ya mike zai kama haushi kamar kare. Na sha hannuna a bakina. "Shiiiii! Bana son haushi kamar kare, ka zauna nazo magana ne da Umma ta, Amirah Raziyana, Barka da dai." Komawa nayi kusa da ita tana zaune cikin mulki. Kallona take cikin tashin hankal, zama nayi tare da cewa. "Kamar yadda aka saka mutane bakwai a kashe Abubakar, sai mutuwar Aliyu aka saka mutane biyar, sabida mulki." "Ke....karya!" Dukar bakin shi nayi, sai da ta razana, sannan nace mishi. "Da Farko ba da kai nake ba, amma ka nace sai kayi magana, ki kuma na tsani katsalandan, jibi zamu yi gasar tunawa da Almustapha da Abubakar, tare da Aliyu. Nasan ana shiri akai na, Raziyana. Zan karasa aikin da nazo, kamar yadda kika saka wasu kuka sai na saka ki kuka, mulkin da kike bukata kuma sai na san yadda na haramta miki shi. Sannan na dawo kan Jahilin d'anki na kona shi kamar yadda aka kona Abubakar da Aliyu, ki godewa Allah da baki da hannun a b'acewar Almustapha, da yanke miki hannun zanyi. Mulkin kuma kina ji kina gani za a haramtawa ahalin ki baki daya har karshen rayuwar ku. Ke ba iya ke ba. Hatta Yaranki sai.... ```BOOK one free ne, book two da three na kudi ne 200₦ ta bank 0472282105 ki katin mtn ta wannan Number +2347035133148 ko ta wannan Number 08130269641``` #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: Monday-March-2021 *FURE cikin ƘAYA* _CIGABAN DAULA BIYU_ BOOK TWO _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 14 SAMAIND A hankali ya d'ago kanshi, tare da kallon Darakshan wanda yake sanye Da Kayan alfarma. Kallo daya yayi mishi sannan ya maida kan shi kan Abinda yake yi. "Sultan MEHRAN! Ana gayyatarka fada, domin." "Da kuka Fahimci shine Kusar Yakin ku ko?" Inji Fudail, a fusace Darakshan ya juya kan Fudail. "Kai kare!" Bai rufe baki ba sai da hakoran shi biyu suka sauka a kasa, sakamakon naushin da bai san lokacin da ya amsa daga basamuden hannun Mehran ba. Kamar bashi yayi dukar ba, ya koma mazaunanin shi, yana cigaba da aikin shi. "Kace yana zuwa!" Inji Fudail, juyawa yayi cikin fusata yana kallon Fudail. "Rakshan ba gaba da gaba ba, ko ta baya sai ka shirya, Sultan Mehran murucin kan dutsen ne bai fito ba sai da ya shirya, zaka iya gayawa iyayen farautar ka yana tafe." Fita yayi sannan Fudail ya gayawa Sultan Mehran dalilin da yake tunanin shi zai sanya su nemi shi. Daukar kofin shayi yayi sannan yace mishi. "Kana gani akan yakin da basu san mafarin shi bane zasu kirani!" Ya tambaya yana kallon Fudail. "Eh Sultan! Sabida kowa yasan kai ne kawai zaka iya jagoranta yakin da mutane dari kacal ayi nasara da Iznin Ubangiji, sannan basu da takamaiman Sarkin Yakin da zai jagoranci SAMAIND, shi yasa suke ganin kamar kai ne mafita." Ajiye kofin yayi tare da mik'ewa yana me nad'e hannun shi a kirjin shi. "Ikram!..." Shiru yayi tare da dauke kan shi dan Fudail zai ce ya kira sunan ta. "Sultan kana magana ne?" Tab'e baki yayi sannan yace. "Me kake gani akan hakan?" Ya tambayi Fudail, murmushi yayi sannan yace. "Sultan MEHRAN, hadakar mayakan ne na yankin larabawa, sannan sun ninka Dakarun SAMAIND sau biyar, bayan haka kuma mace ce take jagorantar matakan Sakeenatu binti Abu Waqqas!" "Tana da aure?" Ya tambaya a sanyayye, "Bata dashi!" "Daga ina take?" "Daga Bahrain!" "Ta tab'a soyayya?" "Bata tab'a ba, domin itace Sarkin yakin kasar su." "Ya ka gani idan aka gyarota, a saukakke an fasa yaƙin, idan ta kama ma, zamu hada shimfid'a duk ba laifi bane!" Ya faɗa cikin sanyin murya, wanda zai nuna maka cewa yasan me yake yi. "Sultan!!" Fudail ya kira sunan shi a tsora ce, "Na zata ka barranta kanka ga aikata irin wannan abin? Sultan naga zallar soyayyar Ikram a idanun ka, yanzun zaka dauki nauyin bawa wata halittar ka, gaskiya ina taya Ikram mugun kishi da akan ka aikata haka, gwara mu faffata yaki." Murmushi yayi sannan, ya cigaba da abinda yake, tsakanin da Allah ya hango kishin akan Fuskar Fudail, bai damu da hakan ba, sai can bayan awa daya ya shirya cikin riga doguwa, tare da saukar da gashin shi bayan shi. Rigar farar ce babba har kasa take jan kasa, a hankali suke ratsa bishiyoyin har suka isa cikin fadar, ana ganin shi sai da suka mike, wannan girman dai da Allah ya bashi yana nan tare dashi, kwarjinin shi da kamalar shi tana nan zube a kan fuskar shi. Nutsuwa da kamun kai yana nan a jinin shi, zama yayi tare da kallon su. Duk suka yi tsuru tsuru, suna kallon juna. Wasa yake da hannun shi yana kasa. "Yarona Mehran! Baka ji labarin anyi gobara bane, har Yar Amir Hood ta rasu, sai kuma batun yakin da yake tunkaro mu." Mikewa yayi tare da had'a hannun shi guri guda, murmushi yayi sannan yace musu. "Toh meye nawa a cikin abinda yake tinkarar Daular mu? Naga dai anyi min iyaka da mulkin baki daya, dan haka kowa tasa ta fusheshi, ku nimo wata mafita Ni babu ruwana." "Amma wannan wani irin magana ce? Akan me ba zaka taimakawa kasar ka ba, karka manta duk abinda ya faru da kai talakawa zasu yi kuka?" Inji Amir Hood, "Toh ina ruwana da kukan takalawan? Ko ance muku Ni sakarai ne da zan kashe rayuwa ta sabida ku? Dan haka wannan matsalarku ce ba tawa bace. Dan haka babu abinda ya dame ni lokacin da zaku cire ni baku yi tunanin talakawan ba? Kuka cire ni basu sani ba toh uwar me zanyi wa rayuwar su? Dan haka babu abinda ya dame." .yana gama fadar haka ya juya tare da Bar fadar. "Aamaan!" Cak ya tsaya sakamakon jin muryan Sultanah Hoyam. "Kazo ayi magana daya da kai !" "Da farko dai bani na gayyato kai na ba, sai na biyu ba zan shiga hurumin fada ba, na uku kuma karku kuma gayyato ni, domin zan sare kan duk wanda ya kirani na ajiye a kofar mashigar masarautan nan!" Daga haka ya saka kai ya fita abun shi. "Meye yake nufi?" "Har yanzun yana cikin halin rabuwa da wancan me idanun kifin ne, dan haka ku kyale shi nasan waye shi" inji Mir Jazib, ~~~ Yana sane yaki shiga cikin maganar yakin, domin zasu tattaro su daura mishi nauyi ne, a gefe guda kuwa turawa yayi aka kira Mishi Sakeenatu binti Abu Waqqas, da har tayi gardama amma jin an ce mata Sarkin Samaind ne kuma matashi ne da bai tab'a aure ba yasa ta shiryawa ta fito har inda yake zaune a cikin tantin shi. Tana shigowa ya mika mata hannun, babu musu ta rike nashi tare da kallon shi. Mazauni yayi mata akan cinyar shi, tare da sake mata murmushi, a hankali ta kai hannunta kirjin shi, tana kallon fuskar shi. "Sultan MEHRAN! Ya gayyace ni, tantin shi, nasan ba haka kawai zai bukaci hakan ba. Kuma nasan garin SAMAIND cike take da yan mata da kyawawa." A hankali ya zare wukar da yake gefen cikin ta, ya wurga can gefe. Sannan ya kuma gyara mata zama a jikin shi. "Dakatar da yakin da kika fito nake son kiyi." Ya fadi haka yana zare mata mayafin samar kayanta. Lumshe idanun shi yayi. Duk da tafi wancan mahaukaciyar diri, baya jin kome akanta kuma ba zai iya mata kome ba, kallon kirjinta yayi tare da kai kanshi wuyar ta, yana shinshina turaren ta. "Me yasa baki amfani da miski? Yana da dad'i a jikin mace" "Sultan MEHRAN, yana da bukatar mace ne?" Ta tambaye shi shi. D'ago shanyayyun idanun shi yayi akanta, tare da hura mata iskar bakin shi, sannan ya shiga bi da ita, amma bawai dan ya fahimci ita din bace a gaban shi, gizon da Ikram take mishi a jikinta yasa shi kara rikicewa. Ture ta gefe yayi sabida jin zata saka mishi karfe a jikin shi, ya juya da sauri ya kamata. Tare da rike rigar jikinta, zai yaga. "Bana son tozartaki! Dan haka zan baki damar ki janye yakin da kika zo yi, ko kuma nayi miki mafi munin abinda zai sanya ki bukaci kashe kanki, a yanzun haka dakaruna miliyan daya sun zagaye ku baki daya. Dan haka shawara tana gare ki, idan yayi miki to idan bai miki ba, zamu kuka haduwa gobe Insha Allah." Juyawa yayi zai fita yayi wani irin tsalle ta rungume shi. Sai da tayi nasarar hada bakin su guri guda. Bata kyale shi ba, sai da suka dangana da shimfid'ar shi. Cikin sauri da tashin hankalin, take kokarin kare kanshi, inda suka shiga fada kamar wasu karnuka, sai da ya kai da ta raba kanta da kayanta, sannan ta samu damar yaga rigar shi. Tana me hada jikinsu waje daya. Kan shi ya kau fuskar ta, a tunanin ta, sumbatar ta zai yi. Sai aka sami akasanin haka, domin mayafi yaja tare da rufa mata kirjinta sannan ya mike a kanta. "Wallahi tallahi, yadda ka jefani cikin wannan yanayin, sai na ana d'aya Daga cikin matan ka, haka ka shirya gani na nan da mako me zuwa!" Tsayawa yayi tare da d'an waiwayawa tare da kallon bayan shi kad'an, sannan ya gyara rigar shi yana faɗin. "Ku tattara yanaku yanaku, ku bar yankina" Yana fadan haka ya fita abun shi, dukar shimfid'ar tayi tare da cewa. "Wallahi sai na same ka." Kad'a dawakan su, suka yi tare da barin gurin, baki daya. Suka nufi SAMAIND, yana lura da yadda Fudail yake cika yana batsewa, murmushi yayi cikin son jin bakin Fudail yace mishi. "Sakeenatu binti Abu Waqqas, akwai cikar halitta, gaskiya mace ce ta shaidawa duniya. Naji dadin alakata da ita" "Allah sai ya bi mana hakkin mu" ya faɗa kamar zai yi kuka, yana kallon Mehran, tab'e bakin shi yayi domin haka ya zame mishi kamar jiki ko halitta. "Ni dai naji dadin alakata da ita" "Chaaaaa!" Fudail yacewa dokin shi dan ba zai iya kayan Bakin cikin Mehran ba. Haka suka iso cikin garin, tare da nufar hanyar gida, koda suka shiga gidan, kowa kama gaban shi yayi. ~~~ Misra.. "Kin san me? Na gaji don Allah mu yadda zango mu huta." Inji Izmah, dan ta gaji. "Karki damu ga can garin Misra muna hangowa kibari mu shiga garin" "Wallahi ba zan iya kaiwa har haka ba!" Ta faɗa tana kuka, sauka muka yi gefen hanya, sannan na kafa mana tanti, muka zauna dabino da ruwa muka sha, sannan muka shiga hira. "Akwai soyayyen nama, da Baba ya bani!" Ta wurga min kunshin namar, budewa nayi na fara kallon shi sannan na dauki daya na ci, na mika mata itama taci. Tana dariya, sallah nayi tare da kallonta, duk sai ta diriri ce tace min. "Ina jin kunyar yadda kike Ibadar ki! Kuma tafiya ta haɗa mu, baki tab'a kyama na ba." "Wannan ba matsala bane dan Addinin mu ba daya bane, babu inda aka ce ka saka wani addini dole" murmushi tayi sannan tace min. "Kina da saukin kai kome naki a warware yaƙe!" Murmushi nayi tare da cewa. "Kwanta ki huta, idan babu fada hannun masu sayar da bayi ba, munyi Arziki." Na fada mata ina gyara kwanciya na, murmushi tayi tare da zuwa kusa dani, ta kwanta tare da rike Ni,. A hankali barci me nauyi ya dauke ta, ni kuma na fito daga tantin na zauna ina kallon garin Misra, daga nan ban san inda zamu kuma nufa ba. Nazarin nake amma kuma ban fahimci kome ba, sai da na shiga tantin muka kwanta. Mafarki nake me dauke da ban mamaki. Dan daga kwanciyar nawa na fara mafarkin. Bude idanun nayi cikin gajiya da mafarkin na tashi zaune, dan ban fahimci kome ba. Alola nayi na tadda sallah, ban kwanta ba, sai da aka asuba yayi anan na sami damar barci me nauyi. Mafarkin Noman nayi cikin jini, ina kallon aka sare kanshi. Ihu da nayi ne ya saka ni farkawa, na tashi ina ajiyar zuciya.kai na ne ya sara min, a hankali na mike tare da nufar hanyar waje inda Izmah take zaune. "Izmah" juyowa tayi tana murmushi, ajiyar zuciya nayi tare da kallon ta, fitowa nayi tare da kallon ta haɗa wuta tana, gasa wani abu. "Me kika sa mana?" Na tambaye ta, "Zomo tun d'azun na fita can akwai lambu shine naji kamshin kasa nabi kamshi sai naga suna bayi ne! Anan na ga zomon na kama mana shi." Zama nayi tare da tankwashe kafaffuna, ina kallonta tare da had'iye yawun na. Dariya take nace mata. "Don Allah Karki ja min rai" Na fada a shagwaɓe, D'aga min gira tayi tare da, cizon bakinta tana murmushi, tace. "Zan baki Amma sai kin min alkawarin bani labarin ki" girgiza mata kai nayi sannan nace mata. "Kiyi hakuri na manta wasu abubuwan masu muhimmancin, duk ranar da na tuna zan baki mamaki" "Babu damuwa." Ta faɗa min, tana gama gasawa. Ta mika min dukka, dan haka na raba mana biyu, na mika mata wanda yafi girma, girgiza kai tayi tare da dawowa kusa dani, ta daura kanta a kafadana tana murmushi. "A da ina tunanin idan muna shiga cikin al'umma zaki wulakanta ni, sai gashi kin rike Ni kamar jininki, kina kare lafiya ta, da hakkina. Nagode Salsabilan Amir Rahil." Dariya muka saka tare da kallon juna, muna ci muna tab'a hira..... ```Two three na kudi ne 200₦ ta bank 0472282105 GTBNK Ramlat Abdulrahman Manga ki katin mtn ta wannan Number +2347035133148 ko ta wannan Number 08130269641``` #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: Monday-March-2021 *FURE cikin ƘAYA* _CIGABAN DAULA BIYU_ BOOK TWO _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 13 Ina gama fadar haka na riko hannun shi muka bar gidan, sannan muka fita waje ya kalle ni a tsora ce yace. "Yanzun me kika aikata?" Banza nayi dashi yana kuma tambaya na nace mishi. "Yadda zata yi gunduwa gunduwa da namarka na mata magana" "Me yasa kike son tashin hankali ne? Ba kome ake samar dashi da fada ba, kin fahimta." Ya fadi haka kamar zai fasa ihu. Kallon shi nayi sannan nace mishi. "Sai kayi kuma!" Na wuce abuna,muna shiga falon shi ya fisgo ni tare da had'a Ni da bango..yana kallon cikin idanun na. "Me yasa baki san tsoro ba?" Bin hannun shi nayi da wani irin kallo, ya sashi sake ni yana jefa min tambayar renin hankali, "Abubuwan da ya dace naji tsoron su basu nan, na gaya maka kanwata da aka kashe ta sanadin fyade ko kuma mahaifiyata da aka tsince ta a bakin kogi cikin jini! Ko na baka labarin yadda aka kashe min mijina? Meye ne ban gani ba? Meye kake son na gani da zanji tsoron na boya a bayan wani kato ina rawan jiki? Da ace an haife ni a rangwanta tabbas kashe kai na zanyi da bakin cikin duniya na huta, sai Allah ya taimaka ina da zuciya a...." Tattausar leben shi naji akan nawa. Wanda suke jike da sanyi, cikin nutsuwa yake sumbatar bakina, rike rigar jikina nayi da mugun karfi, ina kallon kwayar idanun shi. *Amir Rahil! Matashin dan shekara ashirin da biyar, kyakyawan saurayi wanda ake ji dashi a cikin Amirai na kasar Maroko, Yarimar da yafi kowani Yarima ina ado da tsari! Tausayi yake bani* Wannan shine abinda Zuciyata take fada min, tabbas tausayi da kasancewar mu jini daya, yana cikin tashin hankali, dan haka ban hana shi sukuni ba, sai dai yadda naga yana shirin ganin ya wuce gaba da bakin ne na nemi dakatar dashi ta hanyar tura mishi goshina, bakin shi ya sauka akan goshina. Wani irin rungume ni yayi tare da kara matse ni yana sauke shashekar kuka. "Kinji dadinki ke jaruma ce, gashi ko takobin ban iya rikewa ba, me yasa bani da karfin zuciya haka?" Hannuna na kai bayan shi tare da shafa bayan a sanyayye, har yayi shiru, matsawa dashi nayo bakin gadon shi dake mun shigo har uwar dakin shi, saka kai shi yayi akan shafaffen cikina.. tare da rungume ni tabaya. "Don Allah Karki tafi ki barni." "Rayuwata a cikin ku bata da cikakkun yawa, ina da rayuwa a wani gurin, don Allah karka min dole." "Me yasa?" Ya tambaye ni tare da kallon fuskana, rike hannun shi nayi tare da durkusawa a gaban shi, na kai hannun shi kan fuskana. "Zan tafi! Idan na gama abinda nake yi, ba zan zauna ba akwai wani abu a gaba na, bana son kana rokona. Amma zan bar maka Izmah ka rike min ita Amana kafin na dawo. A'a bar shi na tafi da ita." Hada goshin mu yayi tare da zubar hawaye, "don Allah kar ki min haka ina bukatar ki." Kauda kai na nayi tare da cewa. "Nima ina bukatar ka, amma bai zai hanani tafiya ba, dan na kudiri aniyar tafiya," ganin zai iya damamin lissafi na tab'a wuyar shi tare da mikewa har ya suma, murmushi nayi sannan na gyara mishi kwanciyar shi na fito daga cikin gidan. Tunda ga ranar ban kuma samun barci ba, har ranar da za ayi gasar. Shiryawa nayi cikin nutsu, sannan na kalli Izmah, nace mata. "Zaku fita da Sabir, zai wuce dake iyakar kasar nan, insha Allah zuwa dare zan iso. Karki sake kazo na samu baki nan, ki kula da kanki Insha ALLAH zan zo" Kai ta gurin Fataken nayi na biya kudin da zasu kaita inda nace, sannan na mika mata kudi da guzurinta, durkusawa nayi na rungume ta, tare da cewa. "Insha Allah ina tafe." Sai da naga tafiyar su, sannan na juya tare da dokin da gudu, na nufi cikin masarautar, gurin shi na nufa, sannan na mika mishi wani abu a kofi, nace mishi. "Ka juye a gora, zai maka amfani. Idan kaga na lashe gasar kayi ƙoƙarin sha, kafin nan zan tabbatar Raziyana da su Abdullahi sun hadu, sannan zanyi wani abu. Guba ce ka tabbatar kasha na hannunka!" Tsoro ne ya kama shi, dan haka na juye mishi a cikin wani karamin goran azurfa, sannan na shirya shi muka fita, koda muka nufi gurin gasar, Niman daya daga cikin yan matan bayin da zasu ciyar da mutane nayi, mukayi magana, sannan na juya na nufi gurin gasar, tare da maida hankali na. Aka fara, ina yi ina kallon Amir Rahil da yake tsora ce, dan tunda nace mishi guba ne kamar na zuba mishi tafasasshen ruwan zafi, haka yake gumi. A hankali gasar yaƙe tafiya, dan haka koda muka tsallake mataki na farko da na biyu duk nice, a hankali mataki da uku dole ko kai ko Raƙumin ka, dole dayanku ya dawo, dan haka ina kai matakin zamu zaga garin nasan za a iya farmaka ta, dan haka na fita da shirina. Juyawa nayi ina kallon Amir Rahil da yake kallona idanun shi jajjur. Tausayin yan uwantaka yake bani ina son d'an uwana, da dangina, amma ba zan iya zama ba, domin Rayuwata tana wata duniyar ban sani ba, ko zan dawo gare su. Ko kuma su zasu dawo gare ni. A hankali na nufi hanyar tare da kad'a linzamin raƙumin, munyi tafiya me nisa aka farmaki ni, dama na san da haka, dan haka duk sai da naga bayan su da takobi, kafin na wuce shigen su. Tafiyar da muka yi tare da zaga birnin ba na wasa bane. Dan haka a can ma ban tsira ba, har dai da na tsalleke matakin da zai maidani cikin gari, sannan na tsinci gawar wata matashiyar budurwa, wacce nake da yakinin ba ajima da kashe ta ba, na cire kayana na saka mata, sannan na fito doguwar riga da mayafin fuskana, na daurata akan raƙumin, tare da rubutawa. *Amirah Raziyana, Abdullahi, Abdul Rahman,na gama muku aikin ku saura mutuwar Amir Rahil babu wanda zai kuma shan gaban ku, Mun kashe Abubakar da Aliyu, Almustapha mun kad'a shi duniya, domin naji labarin Ya mutu dan haka nasa yanzun gubar da muka bashi ya sha zai fara tasiri ita kuma na gama da Tarihin ta* Sannan na kad'a kan Raƙumin ya nufi gari, Ni kuma na nufi inda muka yi da Baba ya ajiye min raƙumin da ya ciro min a garken Amir, sannan na ce mishi. "Bana zan tafi! Amma zan dawo. Ka koma akan lokaci, domin nasan yanzun haka yasha gubar da na bada a bashi, Baba Insha Allah za a dauki fansar Jinin Almustapha da Abubakar tare da Aliyu, don Allah ka saka mishi ido. Zan dawo amma ban san ki ba, ko tafiyar kenan. Allah ya ƙaddara saduwar." Na kad'a raƙumin nai gaba na barshi yana tsaye. "Wacece ke?" "Jinin Almustapha! Jinin Mu'allim da Bilqisul Ikram yake huda jikina, Karka damu zan dawo domin kare kimar Mahaifina." Sannan na kad'a kan Raƙumin muka yi sahara. *Amin zan dawo! Ko ban dawo ba jini na zai dawo! Insha Allah zai dawo zai dawo kuma zai dauki fansan da ban dauka ba* "Tabbas Allah ya baka yar da tafi maza dubu, cikin hikima ta dauki fansan da ba a tab'a samun wanda yayi haka ba. Sarauniyar mu tazo ta wanzar da adalci Muna jiran dawowar ki. Sarauniyar Jarumai." Juyawa nayi tare da komawa gari, tun daga shiga garin ya fahimci akwai matsala.. ---- a can filin kuwa yarinyar da Ikram ta bata guba ta saka mishi ta tabbatar mata da cewa, an bata wani ta saka. Dan haka ta kai ta lungu tayi mata barazana da wuka sannan ta gaya mata gaskiya, dan haka ta karb'i wancan tare da mika mata wani da kuɗi tare da cewa. "Ki saka mishi wannan!" "Toh ai zasu kashe ni!" "Karki damu za a sake ki na miki alƙawarin haka " Dan haka bayan fitar su, akayi ta mika musu ruwan, Amirah Raziyana tana kallon lokacin da aka mikawa Amir Rahil ruwan, bata sha nata ba sai da ta tabbatar da cewa ya sha, tare da zuba ido, cikin damuwa yana kallon hanyar da zata ɓullo. Ganin raƙumi ta, dauke da ita. Amma alamar a mace, kasa tashi yayi ya zuba musu ido, yana kallon yadda take kwance, amai ya fara tare da rike kirjin shi. Sauke gawar aka yi tare da ɗaukar takardan jikin gawar, wacce fuskarta babu kyan gani, karanta wasikar akayi tare da mikawa. Magatakardan masarautan ya karanta da karfi. A zabure suka kalle shi. Dakyar Amir Rahil ya iso kan gawar tare da fasa ihun me mugun karfi, yana me rungume gawar, gashi yana aman jini alamar gubar tana ratsa shi, da gudu aka zo aka dauke shi tare da gawar Yarinyar. "Wayyo Allah na! Salsabila karki tafi ki bar ni." Gefe guda kuma aka maka Amirah Raziyana da Abdullahi da Abdul Rahman, aka tafi da su. Domin ana fara magana Abdullahi da Allah ya daura mishi tsoron ya amsa da ya aikata, kome ma aka tambaye shi ya amsa, Raziyana ce taki magana. Dan haka aka kai su gidan kaso, tare da maida hankalin kan su. --- Jikin Sultan Mu'allim yayi sanyi da yaji yaran shi har da Yar da yake matukar kauna, tana auren d'an Galadimar kasar, da ita ake haɗa baki aka kashe yan uwanta sabida mulki.. Sauran Yaran shi kuka suke tare da bashi hakuri, kar ya zafaffa hukuncin Shari'a akan su. Shigowa Baba yayi tare da mika mishi wata takarda aka amsa sannan ya kalli Sulaiman. A hankali ya fara karantawa, ```Assalamun Alaikum Kaka na, nasan sakona zai iso gare ka, duk da nasan bana raye! Suna na Bilqisul Ikram Mustapha! Yar d'anka Almustapha! Amir Sulaiman ya san kome akan shi da inda ya zauna! Kaka na gashi bana raye balle naga yadda zaka bi min hakkina da na jinin Mahaifina don Allah ka bi min hakkina karka manta muma muna son rayuwar mu aka raba mu dashi! Ya kai Sultan adali karka manta hakkin mu ne zaka bi``` Zama yayi tare da kallon Sulaiman ya tambaye shi ya akayi, nan ya gaya mishi kome tare da bashi labarin Auren da Almustapha yayi da sayo Ikram a matsayin baiwa... Shiru fadar ya dauka, sannan yace musu. "A kira min shugaban Shari'a, ya zartas musu da hukuncin da ya dace dasu." "A'a Sultan! K'iyayyar ba zata kare ba, a sake su. Amma a raba su da jin dadin rayuwar su. A kwace kome nasu. Idan da hali a mai dasu fakirai yadda zasu fuskanci kaskanci a cikin birnin, yadda zasu Fahimci muhimmancin rayuwa domin hassadar su ce ta bayyana musu asalin su " Inji Sultanah Bilqisul Ikram, tana kuka. Take kowa na fadar yayi na'am da abinda ta faɗa, sannan aka koma kan Amir Rahil. Dan dole aka nufi gidan shi. An samu yayi aman gubar domin bata da dogon illa. ~~~ Gudun da nake bana wasa bane, dan haka na rufe fuskana sai iya idanuna, sai da nayi tafiyar Sa'a biyar da wani abu dan ban tsaya yin sallah ba, sannan na nufi iyakar inda na sami, Izmah tana kallon hanyar da zai kawo ni, bata san nice ba sai da nace mata. "Ke Yar masunta!" Dariya me hade da kuka tasaka min sannan na dira akan raƙumin, na durkusa tazo ta rungume ni, tana kukan farin ciki. Sallah na gabatar tare da niman abinci naci, sannan nace mata. "Kinsan Allah, ina kewar wancan sakaran, Sosai domin ya iya kukan banza." "Matsoracinki. Kinga yadda yake shirme, kai amma wannan anyi sha-sha-sha." Dariya muka saka sannan muka dauki rakumina, ta haura gaba na zauna a bayanta muna hira muna nufi wata yanki na daban, muna cikin na duniya, ko ina zamu sake fadawa oho.... kawo karshen Book one Book one free ne, book two da three na kudi ne 200₦ ta bank 0472282105 GTBNK Ramlat Abdulrahman Manga ki katin mtn ta wannan Number +2347035133148 ko ta wannan Number 08130269641''' #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: Monday-March-2021 *FURE cikin ƘAYA* _CIGABAN DAULA BIYU_ BOOK TWO _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 15. "Bana son wulakancin d'an uwana ne fa, kuma bana da ra'ayin auren miji irin shi, ina da da zab'i amma abinda kakanina suka zab'a min shine zab'i na" "Dama duk wannan jarumtar kina da ra'ayin biyayya." Murmushi nayi sannan nace mata. "Tashi mu nufi wancan yankin." ~~~ A hankali yake bude idanun shi, tare da rabawa a kan su, ajiyar zuciya yayi tare da kallon kayan da yake jikin shi, tare da gyara kwanciyar shi. Had'iye yawun bakin shi yayi tare da kokarin tashi zaune. "Kwanta karka motsa, Sannun Rahil!" Lumshe idanun shi yayi sannan ya kuma buɗe ido. "Da gaske itace ta mutu?" Kafin su bashi amsa, sai ganin shi sukayi zai wula, da sauri suka nimo likita, aka shiga ceton rayuwar shi. Tare da kokarin ganin ya dawo hankalin shi. Allah cikin ikon shi ya sami barci, ajiyar zuciya suka sauko gaba dayan su. "Sulaiman shin YARINYAR da ka kawo ce ta mutu!" A firgice ya kalle Sultan Mu'allim, kafin yayi kasa da kan shi yana fadin. "Bani da tabbacin itace ki ba ita ba ce. Sai da yadda na san jinin Almustapha yake yawo a jikin ta, na zata mutu cikin sauki haka ba, Sultan Ikram jinin ka ce, dukda ta hana Ni fada hakan, sabida yadda kome zai zo da sauki." Kura mishi ido tayi tare, jinjina al'amarin yarinyar ana niman dangi ita ta shigo dangin, amma ta tafi wacce irin zuciya ce da ita haka? Meke damun ta da kuruciyarta haka? Meye ta saka a gabanta? Me take nima a duniya? Wannan shine tambayar da yayi tawa kanshi domin baki daya, yayi sanyi ya rasa wanda zai bashi amsa, dan haka ya maida hankali akan nazarin abinda Raziyana suka aikata. ~~~ Mun shiga garin wanda tun da farko shiga naga rubutun Misra, an rubuta Askandariya. Ajiyar zuciya na sauke tare da niman mayafi ka rufe fuskana tare da saka Kudade Izmah ta rufe nata, itama. Sai dai yadda mutane suke kallon mu yasani jin wani iri a raina, muna shiga cikin kasuwar garin, muka gamu da wata mahaukaciya. Kura min ido tayi tare da sake baki tana dariya, sannan ta fara magana tana cewa. "Ai na gaya muku! Zata dawo wallahi ga uwar gijiyata ta dawo, na rantse da Allah itace.". Dake mahaukaciya ce babu wanda ya damu da maganar ta, haka akayi ta ture ta ana wucce. Ita kuma tana bin mu tare da gayawa jama'a yau ga uwar gijiyatar, har gidan bakin da muka sauka, bata fasa bin mu ba. Gashi an hanata shiga, koda muka shiga Izmah tace min. "Ikram! Mahaukaciyar nan maganarta abin dubawa ce fa, gata can tana dambe da masu gadin gidan." D'ago kai nayi tare da kallon ta, sannan nace mata. "Nima ina nazarin maganarta, kasancewar an tab'a min magana akan kamar mu da Yar sarauniyar wannan garin, kuma ina son na bincika ne ko nan ne dangin Mahaifiyata amma babu fada babu rigima duk abinda zai faru karki damu. Kawai sarauniyar nake son gani." "Kina ganin babu wanda zaki markad'a kashin shi! Babu wanda zaki gotar mishi da hannun shi, gaskiya shigowa wannan garin cike yake a kundin tarihin ki. Dan haka babu damuwa za ayi yadda kike so!" Ban kulata ba, har dare ya fara na fita daga dakin na nufi waje, kallon Mahaukaciyar nayi. "Zasu zo su farmake ki, don Allah ku gudu karsu kashe mana ke, muna bukatar ki, kin manta da Ni ce Benazir ce, kin manta baiwar ki me kula da lafiyar ki, karki manta dani, don Allah nice. Da idanun ki na fahimci kece." Warware mayafin nayi daga fuskana, tana ganin fuskana sai da ta zube a kasa tana kuka tare da cewa. "Wallahi kece!" Mikar da ita nayi tare da cewa. "Kina magana akan wacece?" " Amirah Joindatullah!" "Kin santa ne?" Na tambaye ta ina murmushi. "Uwar d'akina ce." Janta nayi tare da zaunar da ita, muka shiga hira, tana gaya min abinda ya faru, murmushi nayi sannan nace. "Ba zan d'agawa Sultanah Amrah hankali ba, kawai abinda zan yi zan baki sako ki kai mata, sannan tabbas akwai matsala a tare da ita, yau zamu bar garin nan." Komawa cikin masaukin mu nayi na rubuta mata sako ta kaiwa Sultanah Amrah ni kuma na tattara kayan mu, muka bar garin domin bana son abinda zai janyo ayi bore a cikin garin, yin haka shine zai iya janyonwa a kifar da tsarin mulkin Sultanah Amrah, ni kuma abinda ba zan yafewa kai na ba kenan, indai har mahaifiyata ta bar masarautan ne dan gudun faduwar mahaifiyarta babu amfanin na..... Amma kuma yaushe zan daina gudu. Juyawa nayi tare da zuwa na nime gidan Waziriyar Sultanah Amrah. Ajiye mata sako nayi sannan na dauki Yarta budurwa, na fito da ita. Nayi tafiya da ita, bayan na rubuta mata. _Ya zaki ji idan har akace tarihin abinda ya faru ya maimaita akan abinda kike burin ganin ya bunkasa! Kiji yadda uwar da ta rasa basadaukiyar Yarta kuma Sarkin Yakin Kasar ta, idan kika iya fadawa al'ummar kasarki abinda kika aikata da shirinki akan Sultanah Amrah Yarki zata dawo gare ki! Na lashi takobi ba zan tab'a ragawa duk wanda yayi zalinci ba_ Lokacin da ta ga sakon ihu tayi tayi tana cewa. "Maza ku duba garin karku sake ta ficce min da Y'ata, karku bari na fita da ita" Tana fada tana ihu, daga nan kuwa ban mu tsaya ba, itama Yar tana barci, babba budurwa ce dan haka koda muka bar yankin muka kuma nutsa sahara bamu tsaya ba, haka muka kwana muka wuni, sannan muka isa wani gari me suna. Hazb. *HAZB* Gari ce wacce take tsakiyar sahara, garin ya kawatu ainun, sai dai muna shiga garin muka fada hannun dakarun garin a matsayin yan gudun hijira, kuma bai zama dole mu kare a haka ba, dole sai a matsayin bayi. "Ina kika kawo ni? Ke wacce irin mahaukaciya ce! Wayyo Mama na?" Ta faɗa tana ihu. Ban mu damu da ihunta ba, sabida tana cika maka kunne, shigowa dakin da aka zubamu aka yi, hasken fitilar ya haska ilahirin jikin ta, wanda take sanye da wata rigar barci ruwan hanta. Dariya mutumin yayi tare da komawa yayi ya kira, Mutanen su. "Don Allah,.Ikram kiyi wani,karsu tab'a lafiyar ta." Inji Izmah, "Babu abinda zan mata, sabida zunubin mahaifiyarta!" Na fadi haka dai dai shigowar su, ihun ta yasa na juya gare ta, wato fincikota suka yi tare da danne ta. "Kuskure ne tab'a macen da bata san hawa ba balle sauka, babba tashin hankalin shine. Karo da zakanya." Tashi nayi tara da maida kafaa baya kasance sun daure mana hannun mu ta baya, ina tabbatar wa na fito da hannun gaba, nayi kokarin kunce hannun, sannan na daure hannuna da igiya. Kallon su nayi sannan na shiga daure wuyar da igiyar dai da na karya musu hannu da kafar su, na kyale su, ashe akwai daya a cikin su da yake rike da wani icce, kafin na ankara sai ji nayi kaina ya bani wata irin sauri kamar an buga karfe sakamakon buga min itaccen da yayi a kaina, ina dafe da keyar da kyar na samu na juya tare da shammatan shi na daki kayan aiki, sannan na mike tare da rufe kofar, na kwanta a gurin. . Ina juya kaina da nake ji kamar ba a jikina yake ba, gani nake duniyar tana juya min. Maganar mutane nake ji a rarrabe, bude ido nayi na kuma rufewa. _Ikram karki bishi! Domin zan kashe shi! Ba iya shi ba duk wanda ya Kuskura ya rab'e ki sai na kashe shi_ _Sultan Mehran! Shi ya turo mu_ _Shi yasa mu mu kashe, shi mu tafi dake!_ _Karku tsaya ku fada ruwa! Sarwat ku fada cikin ruwan_ Fuskar Mehran ce take min gizo, mika hannun nake amma ina, fadawa a cikin ruwan ne ya dawo min, lumshe idanuna nayi, tare da cewa. "Mehran! Me yasa? Me yasa ka kashe min abokin rayuwa ta? Me yasa baka tsaya kai na ba? Lallai jininka ya cancanci zubdawa domin fansan na NOMAN" Daga nan ban kuma sanin meye ya faru ba, sai bude idanuna nayi na gan mu kwal a cikin rana, an shanya mu, Izmah da Nimra suka kuka tare da kiran suna na. Dakyar na bude idanuna, na juya ina kallon su. Dukana dakarun suke tare da kwallo dani. "Don Allah kar ku musu kome nice nayi kisar!" Na fada a wahale, "Lallai kuwa, zamu kashe su, sannan bayan mun kwanta da su." "Kuskure ne zaku aikata!" Ina ƙoƙarin zare hannun daga igiyar, wurgo min da wuka yayi tare da cewa. "Idan kin isa kwace su." Raina ya b'aci da yadda suke musu, musamman Nimra. Ajiyar zuciya nayi tare da mik'ewa, na naushi wuyar daya daga cikin su, dayan na juyowa na yi maza ka yanke makogaron shi, jini ne ya tartsatsi a ko ina. Kallon shi nayi bayan na nufi gaban su Izmah, na tsaya. "Bana son faɗa! Ku barmu haka zamu tafi ma" "Hmm! Tsinanniya zan kyale ki ne?" Murmushi nayi sannan nace mishi. "Haka ba wani abun damuwa bane domin Ni na yanke hukuncin, dole ka amsa." Wurga mishi wukar nayi ta wuce bata tsaya ba sai a kirjin shi. Juyawa nayi a hankali, ja konce su. Sanan na riko hannun su. Muka nufi waje, wasu kartin karennuka muka gani, zasu min ihu na rufe kofar. "Izmah! Koma ki dauko min wuka can, zamu fita." A hankali ta koma bayan ta dauko min, muka fita. Na samu suna gurnani. Murmushi nayi sannan nace musu. "Karku ji tsoron su. Insha Allah zamu fita ku tsaya a bayana." Dan haka na dauki wukar ''tare da nufar karennuka, da gudu suka rufe min. Cikin ikon Allah ban yi kasa a gwiwa ba, haka kawai nake ganin kamar Mehran ne a gabana, yake bin karannuka. Cikin wani azabben sauri na caki wuyar shi, kafin dayan na same shi a cikin shi. Zuɓewa suka yi suna shure shure, haka muka tsallaka su muka fita daga gidan, niman kaya nayi na bawa Nimra, domin duk wannan ƙaddarar ta faru ne sabida shegen kayan barcinta. ~~~ Askandariya. Zaune take aka ce mata tana da Bakuwar baiwa tazo gurinta. Kasancewar bata hanawa a ganta. "Ranki shi dad'e! Ta dawo gashi nan tace na baki." "Wacece Benazir?" "Uwar d'akina mana!" Murmushi tayi sannan ta amshi sakon. _Umma nasan kina kewar Ammyna! Don Allah kuyi kokarin dakatar da waziriyarki! Sannan ki tura sako zuwa Marocco! Kicewa Amir Sulaiman! Kebe Mahaifiyar Matar Almustapha! Wato Gimbiya Joindah! Kuyi zumunci dasu! Sannan ki hukunta Waziriyarki dan itace ta saka a ka sace Ammyna idan na fito zan yake ta jama'ar zasu bata kariya dan haka har nayi tunanin tafiya, sai na dauki Yarta itama taji yadda kika ji! Idan na gama Insha Allah zan dawo gare ku ahalina._ Bilqisul Ikram Mustapha. "Ina take?" "Ai tafi!" Kamar ta fasa ihu, haka ta yasa ta nufi gidan Waziriyar ta, tana saka kanta tana jin kalaman bakin matar da ta bata yardanta dama da na yaranta biyu. Duk duniya babu wanda zai gaya Mata Nairah nacin amanarta ba zata yarda ba, yau taji da kunnenta. "Taya ba zan d'aga hankalina ba, Kuna ganin abinda nayiwa Joindah shine yau ya faru dani, haka na shiga tsakanin su da Sultanah domin na samu yadda nake so dan na fahimci yar ta fara d'ago, abinda nake shirin yi. Amma na mata barazana zan kashe mahaifiyarta ko kuma rusa mahaifiyar ta, shine ta tafi ita kuma Uwar na gaya mata ai tabi saurayin da aka cewa ana ganin su tare, wanda kuma karya ce nayi ne domin na rabasu..... kawo karshen Book one Book one free ne, book two da three na kudi ne 200₦ ta bank 0472282105 GTBNK Ramlat Abdulrahman Manga ki katin mtn ta wannan Number +2347035133148 ko ta wannan Number 08130269641''' #Mai_Dambu [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: kawo karshen Book one Book one free ne, book two da three na kudi ne 200₦ ta bank 0472282105 GTBNK Ramlat Abdulrahman Manga ki katin mtn ta wannan Number +2347035133148 ko ta wannan Number 08130269641''' #Mai_Dambu Monday-March-2021 *FURE cikin ƘAYA* _CIGABAN DAULA BIYU_ BOOK TWO _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 16 "Kuma duk sharri na mata, ina gab da zama Magajiyar sarauta, (Empress) ace yau an wani gari wata ta sace min Y'a ta da itace zata gaje ni, kuce nayi shiru naci kaniyar shirun," Tafiya yayi da baya kamar zata fadi, tana kallon su. Rike bakinta tayi tana kokarin neman jarumtar da ta rasa lokacin da taji abinda zai tarwatsa mata zuciya. "Meye nayi miki da zafi Nairah? Meye kika nima kika rasa? Na baki kome na mallaka miki kome?" Ta faɗa cikin kuka me tab'a zuciya, ta ma kasa tsayuwa da kafarta, jingina tayi da bango. Duk da shekaru sun haura mata, amma da zafi mutumin da ka yarda yaci amanar ka. "Meye nayi miki? Nairah! Na baki damar kiyi mulki a fakaice, na baki karfin da ban bawa Joindah da Zariha ba, na baki shi Na baki kome dan kiyi farin ciki." Mikewa tayi tare da zuwa gabanta, ta kife ta da mari. "Me yasa baki gaya min mulki ne a ranki ba? Me yasa tun tuni baki gaya min kina son kujeran da nake kai ba? Kin san yadda na dauke ki a raina, kin san yadda nake jin girman kaunarki a raina? Ke ba yar Uwata ta nesa bace ganinki nake kamar ciki daya muka fito shine zaki saka min da wannan mugun b'arnan! Wani irin laifi na miki haka ban sani ba?" Goge kwallar ta tayi sannan ta sake murmushi tana faɗin. "A lokacin da kika shirya kifar dani,sai gashi Allah ya kawo min jikata tayi miki shirme ko? Ba zan kashe ki ba, ko na kama ki ba ai mun wucce wannan matakin, ke fa kanki zaki kashe kanki muje zuwa." Tana ana fadar hakan ta juya tare da barin gidan, tana hanya amma kuka take sosai kamar yarinya domin ta kadu ainun da taji irin cin amanar da aka mata, musamman na kusa da ita. ~~~ SAMAIND Shiru fadar ya dauka, an rasa wanda ya yarda da amincewa akan janye yakin da aka yi, gani suke kamar akwai wani shiri ya sa aka ta cewa an janye, kallon juna suka yi kafin suka ce. "Anya wancan kurman bai shiga cikin al'amarin ba kuwa? Dan nasan haka kawai baza a janye yaki ba.' Shiru suka yi sannan Mir Fawwaz ce. "Kuma gaskiya be bana tunanin ya shiga, nafi zargin kawai sun janye daga yakin ne kawai!" "Ni kuma nasan zai shiga, wa mune ba zai bude baki ya gaya mana ba, amma tabbas ya shiga yaƙin." Haka suka yi ta muhawara, karshe dai suka tattara batun suka watsar. Sai batun yaran su da za a kai can din, lokaci guda suka tsayar da shawara da ra'ayi akan nan da sati me zuwa zasu tura yaran su can ina Mehran yake, dan haka suka gama tsara kome. Bayan sun gama da kulla yarjejeniyar aikin su, sannan suka bar gurin. ...... Kallon Jasrah yayi sannan ya mika mata wata yar Kwalba, yace mata. "Wannan a cikin abincin gidan zaki na bawa ana zuba musu, ke karki ci, sabida gubar hana daukar ciki ne, ni ina Son koda zaku zauna dashi dan nasan dole zai bukaci mace, Toh ga shi nan ki zuba musu a cikin abincin su. Ina Son ke ki san yadda zaki shige mishi sauran bayanin zan miki idan kome ya kankama, kafin karshen shekarar nan ki tabbatar kin sami kanshi, sauran matan kuma," Murmushi yayi mata, sanan ya kura mata ido, kafin ya rab'a mata abinda yake bukatar tayi musu. Kuma ta amince. Tare da yin alkawarin sai ta sanya shi farin ciki a rayuwar shi. ••• A can shashin Sultanah Hoyam kuwa, Darakshan ne yake ta gurzanta, bakin su hade da juna, sabida yadda yake gurzanta ihun take yi, gyara zaman shi yayi a Jikinta, tare da maida hankali akan hak'e da yake yi. Bai d'aga mata kafa ba, sai da ya mata wani irin shegen ci na fitar hankali, sannan ya koma gefe yana sauke ajiyar zuciya. "Ina Son ka kashe min Mehran?" Da sauri ya kalle ta, sannan ya fashe da dariya, yana faɗin. "Baki da hankali!" Cikin tsawa ta ce mishi. "Kana hauka ne?" "Nice bani da hankali? Ni sa'ar ka ce? Dan ina kwanciya da kai " "Ke baki da lissafi ne? Mehran din zan kashe miki? Ko ce miki akayi dan kukwaiyo ne da zan kama shi na kashe shi. Hmmm! Baki san waye Jarumi ba! Ko an ce miki haka kawai mayakan hadin gwiwa zasu janye bata tare da wasika sun janye ba, Toh shi ne dai ya saka su janyewa, wani ba. Ana tauna tsakuwa dan aya taji tsoro, bawai dan ka girgiza wanda ihun shi daidai take da tsawa lokacin damina, sauke shi kawai aka yi abokan gaba suka taro mana duk ranar da kuka kashe shi wallahi toka babu wanda zai samu a wannan Daular." Yana gama gaya mata haka ya mike tare da barin d'akin ma, dan haushi, yana shafa inda ya zabga mishi haushi. -----Abincin aka jera mishi cikin wani irin yanayi yake kallon abincin, a hankali ya dauki tsinke sakace hakori ya shiga d'aga abincin, kallon su yayi sannan yace. "Amma yau ba Sultanah bace tayi abincin nan ko?" Kallon shi Shairah yayi sannan yace mishi. "Eh ranka shi dad'e! Bata jin dadi je shine tabarwa Mahlika girkin" Murmushi yayi sannan yace.. "Toh ku dauka dan ba zan iya ci ba" yana gama fadar haka ya nufi dakin Da Fazilatul nisa take, ya kwankwasa, tana kwance. Yana shiga ya hango ta cikin bargo. Fitowa yayi tare da fita can waje, haka yayi ta tsinko ganye har ya gama sannan ya nufi cikin gidan. Malamin shi ya samu yazo karatun. "Malam kayi hakuri, yau babu lokacin karatun nan ina da mara lafiya ne a cikin gidan." "Toh Sultan Mehran! Allah ya bata lafiya." Ya faɗa tare da barin gidan Suna matukar girmama juna, kasancewar shi din malamin shine ɗan haka yake girmama shi, kuma yake Mantawa shi wani ne a da can a baya, gudun kar girman kai ya hana shi moran addinin Musulunci. Shima yana girmama Al'amarin Sultan kasancewar yana bashi girman shi, shi yasa idan zai kwana bai rike karatu ba, baya tab'a d'aga kai yace zai tafi kuma bai tab'a jin dan yafi shi ilimi ya wulakanta kan shi ba, asalima ana girmama juna da mutunta juna, (kuskuren da wasu suke samu kenan, a rayuwa da zaman takewar mu) Bayan ya tafi shima Mehran ya shiga bawa Fazilatul maganin da ya haɗa har da zuba, tana sha yana kallon ta, can yaga tana had'a gumi, dan haka ya gyara mata kwanciya, sannan ya mike tare da barin d'akin, domin ya lura da barci zai dauke ta. Kasa zama yayi a karon farko da yake ganin ina ma da Ikram tana zaune, ya tuna ranar da bai ji dadi ba, tayi mishi wani shayi me hade da kayan kamshi, dan haka ya shiga kitchen ɗin yayi ta duba kayan kamshin, yana gama haɗawa ya shiga zubawa a tunkuyar har da ganyen shayi, ya rufe tare da hada mishi wuta, sannan ya shiga hada mata wani farfen sun nama, karamar dabba. Kasancewar ana iya ajiye nama ya dauki tsawon lokaci a cikin kasar ta hanyar saka shi cikin gishiri, yana tsotsar ruwan jikin shi. Haka ya saka yana daukowa ya wanke tare da jika namar, bayan ya gama ne ya dauki kome ya wanke, yana kallon duk abinda Ikram take, idan ta gama girki bata fita sai ta wanke kayan da ta b'ata, murmushi yayi sannan ya ce. "Yarinya me kama da aljanu!" Haka ya kammala girkin yana me jerawa a tire, sannan ya nufi dakin Sultanah, ya ajiye mata. Sai da ya kawo mata ruwa ta wanke bakinta, tare da zama ta fara shan shayin da ya kawo mata, dan ta sha magani, tana cin abincin tana kallon shi. Murmushi yayi mata domin baya jin wani abu na wahalar da kai kamar yadda take kallon shi cikin tausayi, ganin hannunta yana rawa ya sashi amsa yana bata yana mata hira, har ta koshi. Sannan ya tattara kayan ya nufi kitchen dashi, ya ajiye Narjis ta shigo ta wanke. Sannan ta fara kokarin daura wani ruwan da za'a kuma bukata. .shiga dakin tayi ta mata ya jiki. "Da sauki! Ga shi Mehran ya kula dani!" "Duk mutumin kirki zai so ya kyautatta lahiran shi dan haka ba laifi bane dan ya kula da Uwa kamar ki" inji Narjis, "Allah ya biya mishi bukatar shi ta Alkhairi, ya dawo mishi da abinda ya rasa, ta hanyar Alkhairi" cikin wani irin kunya Mehran ya mike, wai shi nan yaji kunya dan anyi Mishi Addu'ar Allah ya dawo mishi da Ikram, Murmushi suka yi ganin ya fita kan shi a sunkuye yana murmushi, abin yayi mugun mata dad'i, yadda yasan abinda yake. "Sultanah ya kamata kuyi wani abu yarinyar nan ta dawo mishi! Shekarun shi kara hawa suke, zai zauna ne babu mace?" "Ina sane dashi Narjis! Bana son a sami matsala ne, zuciyar shi ita yake so! Su kuma sun shirya zasu turo y'ay'an su, bana son ya zama ya zab'i daya a cikin su. Shi yasa nake addu'a Allah ya kawo ta kafin lokacin ya kure" inji Sultanah, "Ni kuma tsoron kar tazo kome ya sauya nake, tsoron kar ƙaddaran masarautan nan ya shafe ta nake, Sultanah bana son ta zama d'aya daga cikin masu la'antar masarautan nan! Bana son Ikram ta sami karfin mulki, nafi son ta sami soyayya ya gina zuciyarta, Sultanah karki manta matukar karfin mulki ya shige ta. Daga nan kome zai zama ya rikice, babu me iya tankwarata, babu me iya gaya mata sai abinda masu zagaye da ita suka gaya mata, Ikram bata san kome ba sai fada da zafin rai taya zamu barta ta a jikin shi. Bayan" kura mata ido Sultanah tayi tana mamakin yadda aka yi bata Fahimci abinda yake faruwa ba. A jiyar zuciya ta sauke tare da cewa. "Tabbas rayuwa da mutuwa duk tsari ne na Ubangiji, amma bana jin a raina haka shine mafita, Ikram zata dawo jikin Mehran, sabida itace kashin bayan dukkanin mulkin shi. Abinda zai faru yanzun ko wani lokaci, duk sha'anin Ubangiji ne, babu me iya goge ƙaddarar wani da na goge zanen ƙaddarar Ikram da Mehran! Domin ko babu mulki sun cancanci zama da juna, ko babu kome suna bukatar soyayyar gaskiya! Akwai abinda na sani akan wannan yanayin, abu daya ne zai iya karya karfin faruwan Al'amarin Ubangiji." Turo kofar ne ya hanata karasa abinda zata fada wanda shine abinda zai rage karfin tasirin. "Ranki shi dad'e! Anyi baki daga fada!" Inji Shairah, "Toh kace musu ganin nan zuwa!" Ta faɗa a sanyayye, tana kallon Narjis, Saka rigarta tayi sannan ta daura babban alkyaba ta fito daga d'akin, falon suka shiga a razane suka miki, dan basu yi tsammanin tana raye ba. "Fazilatul nisa!" "Zauna mana! Karku damu, meke tafe daku?" Zama suka yi tare da kallon juna, sannan suka ce. "Ai mun zo gurin Sultan Mehran ne, kuma" "Fudail kira shi mana!" Ta faɗa tana kallon su. "Narjis basu ruwa da shayi," "A'a a'a. Mun gode! Haka ma ya ishe mu!" Fitowar Sultan Mehran yasa su, mik'ewa tare da gaishe shi.zama yayi tare da kallon su, mika mishi tiren shayi aka yi ya dauka tare da kaiwa bakin shi yace musu. "Hmm!" Yayi da yayi musu alama da hannun yana jin su, daukar kafar shi yayi tare da daurawa akan daya, yana kallon shayin shi. Basu iya zama ba, suna daga tsaye suka dukar da kansu. "Sultan daga Bahrain! An aiko da sakon." Suka ciro takardan tare da mika mishi. "Karanta shi Fudail!" Inji Sultanah. *Amincin Allah ya tabbata ga Adalin shugaba na kasar SAMAIND! Wannan sakon ta godiya da jinjina ce sannan muka maka albishir da baka Sarkin Yakin Mu Sakeenatu binti Abu Waqqas! Idan ka amince ka amshi wannan sakon da girmamawa! Mun muka fatan Alkhairi da nisan kwana!* Ajiyar zuciya ya sauke tare da kallon Sultanah, bai ce kome ba ya miki abin shi. Domin bai da tacewa sai abinda tace mishi.... _KUYI HAKURI YAU BABU PAGE 2! SABIDA WEEKEND NE ZANYI HIDIMAN GIDA DA NA YARA_ [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 17 *Me yasa bata jin magana? Me yasa tayi iyaka da shi? Me yasa ta zab'i muradun zuci sama da nashi? Me yasa bata tab'a tunanin shi din ba kowa bane matukar bata tare da shi, gurbin da ya zab'a mata gashi nan ana shirin cikewa* "Ku maida musu sakon godiya! Sannan tana da damar shiga masu tsayawa a matan da Sultan kofa a bude." "A'a! Idan zata iya jira nan da shekara goma toh!" Juyawa suka yi suka kallon shi cike da mamaki, wannan wani irin yanayi ne haka. Juyawa yayi tare da barin gurin, ya nufi can back yard na gidan, ya tsaya yana kallon dajin da ke bayan gidan cikin wani irin kewa na musamman. Ba zai iya kamanta iya adadin kewar ta, ba a yanzun ya yarda da cewa yana masifar kaunar ta, amma ba zai iya amai ya lashe ba. Ba zai iya juyawa maganar shi baya ba, ba zai iya kallon tsabar idanun jama'a yace musu yarinyar da tayi aure da wani yake so, waye zai fahimci ainihin sirrin shi? Ita daya ce mahaukaciya kawai, ta lalata mishi kome sannan tayi nesa dashi! "Amma wannan hukuncin da ka yanke ba." Juyawa yayi ya kalle ta, sannan yayi murmushi yana kallon yadda iska yake kad'a ganye, zata kuma magana ya juya tare da kallon ta, yana me nad'e hannun shi a kirjin shi. Dole tayi shiru, amma kuma yanayin yadda fuskarta ta nuna kamar bata ji dadin abinda yayi ba. "Sau dayawa muna iya sauya ra'ayin mu, sai bamu cika son tistawa ba." Ta faɗa a sanyayye, Bai ce mata uffan ba, har ta gama magana, zata fita sai kuma ta tsaya tare da cewa. "Bai zama dole ka dauki abinda nace ba, matukar aka san girma da darajar da ka bata a zuciyar ka, tabbas iya shi ya ishe makiyan ka, buga ka da kasa. Ba tare da sunyi amfani da wani makami ba. Da iya SOYAYYA aka salwanta da rayuwar sarakunan baya, dan haka karka zurfaffa abinda ba zai fidda kai cikin sauki ba." Tana kai aya tayi fucewarta domin lallai ranta ya kai kololuwar ɓaci, kuma bata son ta nuna mishi haka har ya fahimta,. Sam bata kaunar dalilin da zai sanya ya fahimci bata kaunar yarinyar ko soyayyar da takewa yarinyar ya fita a ranta, sai dai kamar yadda ta sha fada a baya. Sarakunan daular kamar wad'anda aka musu tsafi da macen da suke so. Idanun su rufewa yake basa ji basa gani sai sun tsinci, kansu a gaɓɓar mutuwa suke iya gane illar so. Ita kan tana tsoron kar wani abu ya faru dashi domin bata iya jin zata yafewa kanta. Dan haka ko ta halin k'ak'a, sai ta dakatar dashi wannan makauniyar soyayyar da yakewa Ikram, tana tsoron kar soyayyar ya zama illa yadda ba zai iya dakatar da ita ba. Tana shakkar kar makiya da kishi ya kai wasu amfani da Ikram domin cimma manufar su akanta da shi kan sa. Babban dalilin da take iya hangowa domin dakatar da wannan makauniyar soyayyar, ba kome bane matan da suke kokarin shiga rayuwata su da iyayen su ba kananun shu'umar ba ne. Domin iya haka aka barsu da Ikram sun damata sun shanye kuma zasu iya mata dalilin da sai ta tsani kanta da shi kan shi Mehran din. Kai ina bata jin zata barshi haka ya tafi kamar yadda suka zalunci ta dole, su dauki alhakin ramuwar gayya, toh kuwa idan ta rama ba zasu yi hakuri ba zasu suce sai sun ga bayan shi. Ji take kamar ta kumar ihu, domin bata da wata hikima ya tsaya mata cak! "Narjis! Yanzun naga amfanin tsoron ki! Domin Mehran ya makance akan mace don Allah kiyi wani abu! Bana son na rasa shi kamar yadda sarakunan daular suka yi ta rasa rayukansu, idan ta kama ma kar Ikram ta dawo daular nan don Allah kiyi wani abu ina son shi da Ikram amma kuma bana son ya mutu akan so, bana son na rasa shi a matsayina na Mahaifiyarshi zuciyata ba zata dauka ba,.kiyi wani abu nace." Kasa magana Narjis tayi tana kallon kofar dakin, jikinta yana kerma, d'ago kai tai zata mata magana taga tayi mutuwar tsaye, juyawa tayi Mehran ta gani yana kallon su. "Don Allah karka min mummunan fahimta, ka fahimci ni bawai ina nufin zan rabaka da Ikram bane." Murmushi yayi sannan yace mata. "Eh Toh ban ji kome ba! Ban kuma fahimci me kuke nufi ba, naji kina cewa a matsayin ki na Uwa ba zaki iya me ba?" Ya koma yana tambayar su, ajiyar zuciya ta sauke tare da cewa. "Alhamdulillahi! Toh yi maza jeka bada kai nake ba tunda baka ji ba, a bar maganar haka" Bai ce mata kome ba sai murmushin da yayi, sannan ya saka kai zai fita yace mata. "Ban tab'a soyayya ba, kuma bana jin yin shi. Amma akan wacce nake jingina rayuwata bani da dadin mu'amala!" Ya fadi haka tare da barin d'akin. "Sultanah! Kina ganin kamar kuskuren ne idan kika Barsu a tare? Ko kina ganin zai iya dauke kai daga abinda zasu mata, ba zai iya hakuri ba akan abinda yake so ba, Don Allah Sultanah matukar Ikram zata zo karki sauya mata. .. yau kina tare da d'anki ne saboda ita, yau idan kika juya mata baya babu wanda ya isa ya tabbatar mata da nutsuwar da zata samu. Addu'arki itacce zata sauya kaddarar su, don Allah karki bari abinda ya faru da sarakunan daular ya tab'a zuciyar ki." Shiru tayi tana nazarin abinda ya faɗa da kuma wanda Narjis ta faɗa, kusan abu daya ne amma kuma ita Uwace. Taya zata dauki kasadar rabuwa da abinda ta shigo yaki domin shi. Zata iya mallakawa Ikram amma sauran matan fa? Idan za ayi duba na gaskiya zata iya cewa wa Ikram ta haifawa Mehran, ba sauran matan ba, dan haka zata yi kokarin ganin ta boye tsoronta ta maida Ikram wacce zata bi ra'ayin shi. Sai ta nuna mata itace ta dace dashi yadda ba zata kullace shi a ranta ba, zata so soyayyar su ya zama wanda babu wani abu a cikin shi sai tausayi da kaunar Juna. Ajiyar zuciya ta sauke sannan tacewa Narjis. "Bani ruwa na sha" Daukar ruwan ta yi tare da mika mata, tasha sosai kafin ta ajiye kofin tace. "Bari na huta," "Toh Sultanah a tashi lafiya!" Daga haka ta fita. Kasa kwanciyar ma tayi tana tunanin halin da Mehran yake ciki, yaki maida hankali akan abu daya, sam ta kasa gane shi wani irin mutum ne da baya nuna yanayi. Shi. Sai yaki ya fahimtar da kowa waye shi. Sannan a haka ake bukatar bashi mata toh me zai musu? Ko baida lafiya ne? Anya kuwa? Kai haba toh me yasa baya bukatar mace? Da sabida mace daya ka zab'i zama na shekara goma! Kayiwa kanka iya ka da abinda zaka sami nutsuwa dashi. Kasa zama tayi ta kuma fito. Can back yard din ta koma yana tsaye tare da rike alkama yana kiran tsintsaye, yana watsa musu tsabar alkamar. "Mehran!" "Na'am! Anne!" Ya fada a hankali, da sauri ta kalle shi. Cike da mamaki bakinta yana rawa, tace. "Ka kirani da Mahaifiya ce fa?" Murmushi yayi sannan ya cigaba da abinda ake sam bai da wani karsasha ya gaya mata haka ne domin yadda take damuwa da shi, dan haka shima ya damu da ita. Uwa ce kawai take iya damuwa da cutar D'anta, ba tare da taji labarin zai mutu ko zai rayu, shi tashi uwar Mantawa tayi dashi dan haka ya juya tare da zuba mata ido, kokarin maida kwallar da suke son zuba tayi tare da cewa. "Shin baka da lafiya ne irin na sauran mazan?" Cikin wani azzababben kunya ya juya a hankali yana me ji kamar kasa ta tsage ya shige cikin shi. Yau yaji abun kunyar da ta dame shi. Dan haka yaki juya mata domin maganar ta sashi jin mugun kunya sama da kowani kunya, kai ko lokacin da Sultanah Hoyam ta tambaye shi bai tab'a jin kunya haka ba. Kin juyawa yayi, tare da kin magana, gaban shi ta koma shi kuwa ya juyar da kan shi ta d'aya bangaren. "Baka da lafiya ne kamar sauran mazan nake tambayarka? Kaki min magana" Sunkuyar da kai tayi tare da kin d'agowa, ita kanta bata ga abin kunya ba, dan tana tambayar shine a matsayin ta na Uwarshi ba wai wani abu ba, amma sai yaki koda kallonta..dan haka tafito da sauri tana kiran Fudail da Shairah da Narjis. Duk suka hadu. Kamar zata yi kuka take gaya musu abinda ta tambaye shi. Sake baki suka yi suna kallonta, kafin duk suka watsa kamar wanda ta watsa musu wani abun tsoro. "Toh kuma ina zaku? Muna magana zaku gudu ai sai ku tsaya ayi maganar gaskiya!" Su kuma dalilin ganin Sultan yana tsaye ne yasa su guduwa, suna dariya. Wato idan ya fahimci Anne so take ta gayawa duniya dai... "Kai Aamaan Mehran! Shin kana da ra'ayin maza ne?" Murmushi ne ya kwace mishi sannan ya tuna da tsohon zargin shi da ake cewa wai yana bin maza wato (dan luwadi) dan yaji yadda zata rikice, sai ya wani kalle ta, sannan ya sunkuyar da kanshi irin eh din nan. Ihu ta saka tare da kiran Fudail, rike bakinta tayi tana kallon Mehran da Fudail, sannan tace mishi. "Yarona Fudail! Gaya min shin Shugabanka yafi son mu'amala da maza ne sama da mata!". Kan Uba,. Da wani mugun sauri ya kalli Mehran, kashe mishi ido yayi tare da mishi alamar ya amince, da tambayar ta. Cikin wani irin shauki da takaici kamar zai fasa ihu, ya kalle ta sannan ya dauke kan shi ya kuma duban Mehran, ya ɗan ciji bakin shi sannan yace mata. "Labarin yana da tsayi, idan nace zan gaya miki zaki iya faduwa baki shirya ba, amma Sultan kan..... Sai godiya." Ya faɗa ina cizon hannun shi. Dab'as ta zauna tare da cusa hannun ta cikin gashin kanta, taji kamar ta kurma Ihu, dan haka ta nuna musu hanya su bar mata falon bata son ganin su. Da wannan yanayin ya shiga dakin shi. Ya zauna yana murmushi, haka kawai yake jin shi yau yayi nishadi, murmushi ya kuma a karo na biyu, yana tausayin ta. Amma bayana nufin zai bar musu rayuwar shi su gara mishi bane. Dan haka ya kwanta a hankali barci me dad'i ya dauke shi. A bangarori daban daban,.ana kan shirin za a turowa Sultan Mehran mata, dan haka suka maida hankali gurin koyawa Yaran su mata yadda zasu kwace Mehran, karsu bawa wasu damar rab'a ban shi. Idan kaga yadda suke gudanar da abin sai ya baka tsoro, domin shirin da suke zaka zata aure ne kuma duk kawai zab'e ne. ~~~ Askandariya. Shiru fadar Sultanah Amrah yayi sakamakon yadda Waziriyar ta Nairah take bayanin abinda ta aikata, tana kuka. Ita kan Sultan Amrah bata iya magana ba, sai ma sunkuyar da kanta da tayi tana kuka. Tana tambayar kanta meye tayiwa Nairah da zafi haka? Me yasa Nairah bata gaya mata mulki yake so ba? Da ace lokacin ta ce ita mulki take so wallahi da ta bar mata, akan mulkin banza ta rabata da Yarinyar da take kauna babu ita babu yar uwarta, duk sun rasu. Hawaye ne ya zubo mata, sannan tace. "Ba zan iya kashe ki ba! Nasan yadda kowacce uwa take ji idan ta rasa D'anta, a halin yanzun kuwa nasan kina cikin rashin Yarki dan haka babu hukunci akanki, kije Allah zai bi min hakkina indai na zalince ki babu abinda zai same ki, idan kuma ni kika zalunta, Idan nace ban yafe ba na rena iyakar shi ce dan haka Allah yasaka da Alkhairi zaman da muka yi dake!" Ta karshe maganar cikin wani irin kuka me hade da murmushi, domin iya haka kawai zaka Fahimci tana cikin damuwa... #Mai_Dambu 200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641.. Mai_Dambu... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 19 "Me yasa baki Fahimci sabida ke take raye ba? Me yasa baki gane girma da kaunar da yarki take miki ba, sabida kina tare da shaidanun mutane irin Nairah binti Namdar, dan haka kamar yadda taci amanar mu, har ta kai da shirya juya mulki dole mu zartas da hukuncin mu akanta." "Kyale ta Khadim! Kyale ta tayi rayuwa, kyaleta duniya zasu gaya mata abinda na gaza gaya mata" sannan ta fashe da kuka, share kwalla tayi sannan tace musu. "Yar Joindah ta turo min sako, tace na tafi Merocco, naje akwai dangin mahaifinta a can me kuka gani?" Share kwalla suka yi sannan suka ce mata. "Duk yadda kika ce! Mu masu miki biyayya ne babu abinda zaki ce muce miki a'a!" Da wannan ta mike a hankali ta bar fadar, tun da tashiga d'akinta dariyar yaran ta, yadda suke gudanar da sha'anin su na farin ciki a, shi yake yawo a kunnenta. Yadda suke wasa da matashi a dakin shi yafi komai mata dad'i, a hankali ta taka har gaban gadon da yau ya koma mata kamar yau aka kawo dakin, shashekar kuka ta ja, tana tuno yadda yadda Joindah ta maida kanta kamar namiji, hatta maganarta sai da ya sauya. Idan ta dube hannunta ya koma mara taushi da laushi irin na mata, kafarta kullum cikin takalmin karfe yaƙe ko sau daya bata tab'a d'ago kai ta dube irin nasarar da Yarinyar ta samu ba. Tasha ganin ta tana son yanke gashin kanta, amma ta hana ta, sai tace mata. "Ummyn ni gashin addabar rayuwata yaƙe, shi yasa zan yanke amma bawai dan bai hana Ni rayuwa ne ba." Zuɓewa tayi akan gwiwar ta, tana me rike kanta. Tana kallon yadda kome ya tafi yabarta, babu yaran da take mulkin domin su, babu Mijinta da ya bada rayuwar shi domin ita, kawarta Aminiyarta itace taci amanarta, duk Yardan da tayi da ita na tsawon shekaru, yau ta b'are, a hankali ta zame tare da kwanciya a kasa, hawaye na zuba mata. Tana rufe idanunta, zata ji ihu da shewan yaranta, suna dariya da murna musamman idan Joindah ta tafi yaki aka yi nasara, haka zasu yi ta guje guje, har fada. Idan ka ga Joindah sai ka rantse namiji ne domin yadda take yanke sumarta.ya dawo iya dokin wuyarta. Tana dariya, takaici take ji idan ta ga gashin a yanke. Har ta kare wata rana ta mata magana akan yanke gashin. "Yanzun don Allah meye amfanin yanke gashin kanki? Me yasa kullum kike bukatar ganin raina ya b'aci, kefa mace ce?" "Ummyn ni gashin ne yake damuwa, sannan ba a cikin gidan sarauta nake rayuwata ba, kai na wani lokaci sai nayi.wata daya ban saka mishi ruwa ba, muna can muna yaki da jama'a, toh Kinga kwarkwata da wasu kuraje damun kai na suke, amma Insha Allah ba zan kuma ba." Ta faɗa tare da juyawa, sannan ta riko kunnenta. "Karki damu! Duk lokacin da zaki yanke toh kina azumi uku!" Gyada kai tayi, hawaye na ya shiga sauka cur cuur. Dan ba zata iya daukar wasu tashin hankalin bayan wannan ba, ta rasa yaranta biyu. Haka ta mike tare da shiga ban daki wanka tayi da alola sannan ya fito ta sallaci asuba, tana idarwa ta jima tana azkar da yiwa Yaranta da mijinta sai iyayenta addu'o'in, kafin ta koma ta kwanta sabida zazzafar zazzabi ya rufe ta, anan ta kwanta. Lokaci guda aka taru akanta bayan an fitar da sanarwar Sultanah Amrah babu lafiya. Dayawa talakawan sunyi mata Fatan Allah ya bata lafiya, bayan sun ji zunzurutun cin amanar da waziriyarta ta mata, dan haka ba tare da sanin kome ba, suka shirya kashe Nairah binti Namdar. ~~~ SAHARA. Kimanin wata biyu kenan, da shigar mu wannan gari me shegen bala'in tashin hankali, babban damuwata Nimrah, so nake ta koma Askandariya. Shi yasa nake kokarin na fidda ta cikin wannan yanayin. Ita kuma bata da mutunci, rena min hankali take. "Ke Wada! Zoki goge min bakina da nasha madara, matsiyata kun rabani da Mahaifiya ta, sai ta saka an sare min kanku" Buge mata baki Izmah tayi tare da cewa. "Allah wadaran iyayen da basu bawa yaran su tarbiyya sha-sha-sha kawai!" "Ke Ni kike zagi?" "An zage ki!" Tasowa tayi zata nufi Izmah na tsaya a gaban su, "Bana son rashin hankali! Da rashin sanin hakkin d'an adam, kiyi hakuri shikenan!" "Zaki maidani garin mu?" "Ba zan mai daki ba, sabida ina da burin ganinki kusa dani" "Ke wacce irin rashin imani ne dake? Me yasa kika rabani da alkaeyata? Me yasa kika rabani da Mahaifiya ta, kin kawo ni cikin datti da tirbaya ina rayuwa kamar wata dabba, mutanen da basu kai tab'a ni ba, sune suke gogayyar tab'a jikina, meye nayi miki da zafi ne?" "Nimrah! Ki nutsu ba ina nufin na cutar dake bane, kawai nayi haka ne domin gaskiya tayi halinta, idan kin gadama zaki iya tafiya yanzun haka zaki koma in..." "Ikram!" Izmah ta kira suna na, da garaje, "Izmah! Kyaleta ta tafi ko da ta koma kome ya kure, dan haka na gama shirya mata tafiyar tun wata daya da ya wuce." "Taya?" Inji Izmah, Murmushi nayi mata sannan ba nunawa Nimrah hanyar wucewa, rikon hannuna Izmah tayi, hawaye na zuba daga idanuna, rike hannunta nayi, goge kwallar fuskana nayi tare da cewa. "Askandariya suna jiranki Nimrah! Kiyi hakuri da sauyin ƙaddarar ku." Murmushi nayi domin nasan matukar ta shiga Askandariya toh tabbas sunanta babu. Domin har yanzun akwai masu fushi da fushin Sultanah, a hankali ba juya zuwa cikin gari. "Yanzun meye ya rage mana a garin nan?" "Hmm! Lallai kuwa wanda nazo nima har yanzun ina kan niman hanyar haduwa dashi." Haka muka shiga cikin garin, na fara niman mafita, domin haka nake kullum sai na tsokano mutane fada. ~~~ Oman. Kallon shi Nawwas yayi tare da cewa. "Sultan Abrad!" "Kayi min shiru! Taya aka yi kabar Aamaan ya sami damar tunkarar Sakeenatu binti Abu Waqqas? Taya za ayi haka? Har maganar niman aure ya shiga tsakanin su?" "Sultan ka daina tunanin cewa, Aamaan Mehran ba gama garin mutane bane,. kuma yana zaune kamar bai.san meke faruwa ba yana sane da shi. Kuma a halin da ake ciki na wanda aka dakatar dashi a mulkin kasar dole idan Ka sami matsala, dole su nimo shi na taimakawa. Kuma banyi mamaki ba dan Bahrain sun bada goyon bayan ya auri Sakeenatu binti Abu Waqqas ba, don Allah Sultan mu rabu da shi mana, duk wannan rikicin sabida Ikram ce, kuma ta mutu me kake bukata da Mehran? Idan ka nace tabbas Mehran ba zai Barka ba, zai kure maka gudu." Kallon Nawwas yayi cikin jin haushi, tare da cewa. "Sai na sare kan dan iska, sai na ruguza mulkin shi, wallahi ba zan barshi ba sai na kashe shi kamar yadda ya kashe min Ikram dina." Cike da mamaki Nawwas yake kallon Abrad dan ji yaƙe kamar yayi ta dukar banza, ko zai sami sauki, dauke kai yayi sannan yace mishi. "Zan iya fita?" "Hmm!" Yace,. Nawwas na fita ya bishi da wani irin kallo, me dauke da ma'anoni daban daban, kwara yayi sannan ya dauke kanshi irin zamu hadu nan. Shi yanzun ma zargin shi yake gani yake kamar shima yana son Ikram, dan duk lokacin da ya sauko zance Ikram da Mehran, take zai ga sauyi akan fuskar shi. Anya ba zargin shi bane zai zama gaskiya, taya aka yi Ikram ta mutu bayan yana da labarin shine yabi bayan su Ikram, kuma shi ya kama Noman! Ajiyar zuciya ya sauke tare da dauke kan shi tabbas akwai wani boyayyen al'amari da ya kasa fahimtar shi kai tsaye. Koma meye Insha Allah sai gaskiya tayi halinta. ---- "Nawwas!" Azizatul Nissah ta kira sunan shi. "Hmm!" Yace mata. "Wai don Allah meke faruwa ne?" "Yayanki zaki tambaya" ya bata amsa a takaice, "Kamar ya shi? Kai na tambaya ba shi ba." Wani irin iska yaja kafin ya fesar sannan yace mata. "Kin san me? Yayanki yana da son kai, burin shi ya mallaki kome ya hana kowa farin cikin rayuwar shi, toh kanshi yake bata ta kowa. Wallahi koda zan rasa rayuwata da kimata, Ikram ta haramta mishi, dan haka ya cigaba da haukar shi ai mulki ba hauka bane. Da zai saka mutane a gaba yana juya su kamar yaran shi." Ya faɗa cikin jin haushin Abrad, yana ajiye mishi kyauta akan Ikram dan haka ya kuskura ya tinzira shi sai yayi mutuwar danasanin. Domin zai kashe shi da hannun shi. Ya wuce ya barta tsaye cike da mamaki. Shiru tayi tana mamakin meye yarinyar nan tafi sauran mata da har maza suke karo akanta, wacce irin shaidaniyar yarinya ce haka? Wacce irin mutum ce ita haka da ta saka mutane a gaba da bala'i, matukar zata rayu ta dawo su hadu sai ta kashe yar akuya. Tunda ta lura ita karuwancin ta, ba iya kananun maza takewa ba, hatta manyan maza bin su take, Shaidaniya kawai. Ta tsani Ikram. Kuma sai takashe ta idan ya ganta banziya karuwa kawai. Ta faɗa tana fidda numfashin takaici. Koda ta shiga gurin Abrad, abinda ya faɗa mata shi ya kuma kona mata rai. "Ikram!" Juyawa tayi tana niman Ikram din sai da ya dage goshinsa sanan yace mata. "Azizatul Nissah zance kiyi hakuri, na kiraki da Ikram!" Kura mishi ido tayi ranta yayi mugun b'aci, bakinta na rawa tace mishi. "Yaya nice Ikram? Wacce irin asiri tayi muku da har ka manta suna na? Na shiga uku na lalace yau naga masifa da idona, lallai sai na kashe kiran." Ta faɗa tana kuka, kasa magana yayi tare da daka mata tsawa, tafita da sauri tana kuka. Wato abinda Nawwas ya faɗa gaskiya ne, bai san kowa ba sai abinda ranshi yake so. Itakan ta shiga uku bata da uwa bata da uba. Shi da yake d'an uwan ta, kuma mace ta mishi asiri ta mallake shi. Kuka ne ya kwace mata, tunda ya fita take kokawa, domin abin kuka ne ya same su. Akan mace kowa yana jin haushin d'an uwan shi, meye amfanin haka? Me yasa Ikram ta zame musu bakar kaddara? Me yasa ta musu shigar sauri ta rabasu kan su. Kuka take tare da niman damar ina ma Allah zai kawo mata Ikram sai ta mata kisar gilla, lumshe idanun ta tayi tare da zubda kwalla. Me zafi kamar ranta zai fita dan bakin ciki. ~~~ SAMAIND. Cikin tausayi irinta uwa da d'a, take kallon shi. Irin kallon Allah ya dawo min da kai cikin shiryar nan take mishi. Shi kuma dake ya lura da haka, sai wani dauke kai yake. Kamar zata zubda kwalla tace mishi. "Mehran!" Kallonta yayi tare da dauke kanshi yana kallon wajen da dakarun Samaind, kallon su yake yana murmushi wato yaga suna badda horo, shi yadda suke bada horon ne yake bashi dariya, bawai dan wancan maganar ba, kawai sai gani yayi, Sultanah Fazilatul nisa ta rufe labulen falon, tare da b'ata rai. "Kai wani irin mutum ne haka? Meye a jikin Maza da zaka zauna kana dariya! Maza ne fa ba mata ba." Ta faɗa cikin tsawa. Murmushi yayi sannan ya lashe bakin shi kad'an sannan ya juya ya kalle ta, shigowar su Narjis da Shairah sai yan mata, suna zuwa suka fara rawa. Murmushi yayi yana kallon yadda yan matan suke juya k'ugun su, takowa yayi tare da kallon wata yarinya a cikin su, yana nuna mata yadda zata juya k'ugun ta..sake baki Sultanah tayi tana kallon shi wato dai duk ta inda zata bullo mishi ya wuce tunaninta, shi kuma ba kome bane yaja hankalin shi sai tuna Ikram ranar da aka turota fada. Rawar take ne ya saka shi jin haushinta, murmushi yayi sannan ya kalli Yarinayr yace mata. "Karki kuma zuwa nan" "Toh Sultan Mehran!" Ta faɗa cikin sanyin murya, wato wani irin jin dadi, sannan tafito murmushi yayi sannan yace mata. "Anne da maza aka kawo su min rawan nan zai fi dadi akan mata nan, mazan sunfi iya rawa" 🤣😹😂 _Wayyo Allah wai da gaske maza sun fi mata iya rawa🤣🤔😹_ *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu. [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 18 A hankali ta mike tare da barin fadan, zata fita niman yarta, tana murmushi babu wanda ya isa dakatar da ita juyin mulkin da zata yi. Dan haka ta ficce daga fadar ta wuce gidanta tare da tattara kayan ta baki daya. Aka nufi gidan ta da ke wajen gari. Duk Sultanah ta saka a bibiyeta domin tasan tunda tayi shiru akwai wani abinda take aikatawa a kasa, dan haka aka yi ta bibiyarta har zuwa lokacin da ta gama shirya dakarunta masu yawa da zasu ruguza Amrah. Sai dai tun kafin su iso cikin garin, an musu zobe. Sultanah Amrah ce ta isa gabanta, tana murmushin takaici, sannan tace mata. "Nayi zaton dan na baki damar ki fahimci kuskuren ki zaki saduda ne? Na zata idan na baki dama ki Fahimci kuskuren da kika aikata ne, tirr Yarki baki san halin da take ciki ba, amma kina yunkurin sai kin fitar da mulkina meye nayi miki da zafi ne? Meye na tsare miki nida yarana ne? Kin salwantar min da Joindah ban hukunta ki ba, kin yi min sanadin da na auren da Zulaikha bai miki dadi ba, me kike son nayi miki? Zulaikha ma da bata da buri mulkin sai da kika rabani da ita. Kisa sani yarinyar nan na tsane ta, bayan na rabata da wanda take so na bawa Abrad ita, shine zaki dawo ki kashe da sauran numfashina? Meye na tsare miki haka? Indai haka goyon d'an maciji yake Allah yayi min tsari da haka. Kije na kuma baki damarki na karshe Allah ya baki sa'a. Dakarun! Ku bar Nairah karku kashe ta, ku barta idan zata iya rusani karku dakatar da ita. Halayyarki shi zai kashe ki. Daga haka ta juya ta nufi keken dokin ta,. tana kuka a cikin ranta tana kewar Yarta wacce makirci ya saka ta ki kula yarinyar. Yau tana tir da Allah wadaran iyaye masu irin halinta, akan me ba zasu saurari yaran su ba, sai su dauke kai kamar basu gan su cikin wani hali ba. Bayan suna sane kamar yadda tayi ita ta lalata duniyar yaranta ta kyautattawa bare, a hankali ta shiga fadar ta tana kuka, kallon wancan shaidanin kujeran tayi, daga lokacin da aka baka damar zama akan shi, shi kenan an gama da duniyar ka,kana ji zaka rufe idanunka, kana gani zaka toshe kunnen ka. Domin al'ummar ka dole ka ɗauke kanka, yau kujeran bai mata amfanin kome ba, tabawa wasu farin ciki, ita kuma ta rasa nata, ta saka wasu dariya ita kuma yau tana kuka da idanun ta, meye Nairah bata sani ba nata? Meye Nairah bata gani ba, nata amma ta zabi lalata mata kome cikin ruwan sanyi, zama tayi tare da fashewa da kuka tana danasanin mara amfani, tana ji ina da kasa zata bude tabbas cusa kanta zata yi domin.kunyar abinda ta aikatawa Yaranta. Zama tayi a gaban kujeran tana kallon shi bata iya fahimtar kome ba sai lokacin da Joindatullah take ce mata. _Ummyn ya kina ganin gari babu hadiri zaki yi wanka da kashi! Ummyn maliya sun rufe masoyanki! Ummyn karki yanke min hukuncin da zaki dawamma kina kuka! Don Allah ki tashi akan mulkin nan haka iyalinki muna bukatar ki_ Wani irin kuka ta sake lokacin da take ganin irin kallon da Joindah takewa Nairah, me yasa bata dauki matakin bindidigi ba sai da lokaci ya kure mata. Haka suka yi da Zulaikha tace mata. _Kowacce mace burinta miji na gari! Bayan tayi dace da iyaye na gari! Sai dai matsalar da aka samu da hannu ki gurin dauke Kanki aka nima min Abrad mutumin da kowa ya sani bai da kamun kai a cikin daular shi! Nan yazo a gaban jama'a ya nuna zai rungume ni baki dakatar da haka ba sai yau naji bakin labarin kin aura min shi Ummyn yadda kika yi sanadin da Joindah ta bar masarautan nan haka nima zan bari! Kina zaune da makashiyarki, amma baki sani ba zance ki kin sani kin gaza fahimtar zuciyarki! Ke kuma bakar munafuka na dawo kanki! Sai dai ki sani duk sharrin ki Insha Allah Ubangiji zai kawo karshen ki, Azzaluma macuciya, zaki biya abinda kika aikata da kudi mafi tsada._ Kifa mata mari tayi, tare da ture ta. Tana faɗin. "Zulaikha Waziriyar kike gayawa magana?" "Ummyn na gaya mata! Akan me zaku raba ni da wanda nake so? Akan me zaku bani Abrad da bai da kamun kai! Ko abin alfahari ne a ce ka auri mutumin da bai san darajar kan shi ba balle na macen da zai aura!" D'aga hannu tayi zata kuma marinta cikin sauri Nairah ta rike hannun ta, tana faɗin. "Karki dake ta, ai ba kome bane yake damun ta, sai dan zata auri Zab'in mu, kuma wancan ai ba kowa bane!" Cikin fushi Zulaikha ta dauki wata sunduki ya kwalawa Waziriya. Sai da goshinta ya fashe. Kasa magana Sultanah Amrah tayi tana kallon Zulaikha, cikin bakin ciki tace mata. "Daga rana irinta yau! Ni Amrah binti Khirash na haramta miki shigowa masarautan nan har abada." "Ba dai akan ta kika kore ni a cikin gidan mu ba Ummyn? Toh ba makawa wata rana zaki yi kuka da cewa ina da zamu dawo gare ki mana! Zaki yi ta kuka ina kallon ko ina a matsayin me yasa kome ya wuce, kin samu nasara Nairah, mun amince zamu miki duk yadda kike so. Amma Allah baya barci sabida shi ya haramtawa kan shi zalunci dan haka zai isarwa kowa" Wani irin ihu da kuka Sultanah Amrah take yi, wani irin tashin hankali take ji a rayuwarta dama da baya can, me yasa ta kashe yaranta da hannunta? Me yasa ta rusa yaranta da hannunta? Me yasa bata fahimci abinda suke gani ba? Yau tana kuka ne amadadin su ko amadadin cin Amanar ta da akayi . Tuna wata rana da Joindah tace mata. "Ummyn kin cika yarda da mutane, ya Waziriya Nairah zata kawo miki magana ki amsa bayan baki da tabbacin ya faru, kiyi bincike da kai. Ga wannan takardan ba abubuwan da suke faruwa ne a marautan nan kiyi kokari ki duba yana cikin akwatin ajiyar masarautan nan a cikin akwatin takula, amma Ummyn kina bincike kuma karki yarda da kowa, zan duba batun tafiyar yakin nan ne" Sannan ta fita daga dakin Sultanah Amrah, hawaye ne ya zubo mata, tana zaune tare da kallon yadda yan matan yaranta suke farin ciki idan suka hadu su uku! Dariyan su hayaniyar su tare da guje guje, yau duk ya dawo mata kanta, kafin kace me fadar ya cika makil da Emirater councilor, zama suka yi tare da kallon yadda sarauniyar su take kuka kamar yarinya ƙarama. "Meye laifina? Me yasa duk Alkhairin da na mata sai da ta zabi cin amana sama da kome? Shin laifine dan na kaunace ta? Iyayen mu daya? Domin dukkan mu Zuri'a daya ce! Me yasa ta tozartani? Me yasa ta wulakantani ? Me yasa ta rabani da iya abinda na mallaka a duniya? Da yau Nairah binti Namdar ta gaya min mulki take so! Na rantse da Allah maɗaukakin sarki da na ajiye mulkin na zauna a matsayin waziriyarta, me yasa ta cutar da Ni? Bani da matsala amma haka ta saka muka rasa Basadaukiyar da take tunkarar yaki kome girman dakarun yaki kuwa? Yaushe zan kuma haihuwa bayan ba mijin ne da Ni ba? Yaushe zan kuma samun yaran bayan tsufa ta cimma Ni? Meye nayi mata a rayuwar nan? Don Allah idan akwai wanda nayi mishi laifi ya rama? Idan akwai wanda na zalunta ya rama yau ranar ku ce ta rama zaluncin da nayi muku." Ta faɗa cikin kuka me ƙarfi. "Sultanah Amratu! Babu zalincin da kaki yi sama da zaluntar Yaranki biyu rak a duniya? Bayan nan dukkan mu nan kin bamu farin ciki, kin cika mana gida da adalci! Kin bamu damar muyi nasara akan kome naki! Sabida rashin Kusar yaki yasa kika zama kamar yar amshin sarakunan wasu daulolin, domin kare dukiyar alummarki da rayukan su, kika zama mace me rauni! Wanda a da can baya ba haka kike ba sabida kina da Zakanya a tare da ke? Kina da Zakanyar da take hana idanunta barci sabida al'ummar ki! Kowa zai kwanta yayi barci Sarkin yaki tana zaga gari da kewayen shi domin al'ummar ki! Munyi kuka munyi tir da munafukin da ya raba Uwa da Y'ayanta, mun yi bakin cikin yadda aka yi Uwa ta gaza fahimtar yarta har take tambayar ta zata mata juyin mulki ne?". Kasa yayi da kan shi ya fashe da kuka! Sannan ya zauna yana rusa kuka, dan yasan Joindah mutum ce a cikin mutane, jaruma ce a cikin jarumai! Zakwakura ce a cikin zakwakurai! Itace ake mata da lakabin hadarin kaka lalata amfanin masalaci. "Mir Aminuddin! Ba iya wannan ba! Jarumar da ta tunkari yaki tun tana da karamin shekaru take yaki! Tun bayan mutuwar Amidudawlah mahaifinta ta shiga filin yaki da shekara goma sha biyar! Bata tab'a faduwa a yaki ba! Bata tab'a dawowa bata yi nasara ba! Yau aka makala mata sharri yarinyar da ko yaki muka je ita take bawa mata kariya! Da bakinta take cewa. "Ku iyayen mu mata ba zamu kama ku a cikin bayi da fursunonin mu ba, nima mace ce irin ku! Dan haka ba zan kai ku a bautar da ku ba, idan baku yarda ba bari na gwada muku! Kai mazaje ku sunkuyar da kanku Amirah Joindatullah zata sauya kaya." Duk muka juya mata baya, sabida bamu tab'a ganin ta cikin kayan mata ba, koda ta fito muka ganta sai muka dimauce, sabida iya halittar kwayar idanunta abar so ne balle kuma kyau da halittar jikinta, Tun daga ranar ban kuma ganin ta cikin kayan mata ba, sabida yaki ne a gaban ta, nasara ne a gaban yaki! Sarakuna da sarakunan yakin su. Sun sha niman aurenta a filin yaki! Amma murmushi take tace. "Ba soyayya bane mizani na? Nasarar mahaifiya ta, shine nasara ta! Shan bana da ra'ayin aure. Ina tare da mahaifiya ta, dan ta haife ni ne domin na kare lafiyarta. Don Allah ka fahimci abinda na gaya maka." Haka kika juyawa yarinyar da takewa maza kallon yan uwnta ne, haka kika sa ta ajiye takobin Sarkin Yakin Amidudawlah mahaifinta ta ajiye ta juya sakamakon cewa da kika yi ko gawarki baki kaunar ta zo kai! Taje duniya sai ta koya mata darasin rayuwa! Eh da gaske duniya ta koya mata darasin rayuwar. Tunda a wulakance aka sami Sarkin yakin Mu maza shida sun keta alfarmarta. Meye yafi haka muni!" Ya faɗa tare da fashewa da kuka, sannan ya d'ago kai tana murmushi. "Bata mutu ba, sai da ta haifi Guguwar yaki! Sai da ta haifi wacce zata iya karawa da duniya domin kimarta a yanzun haka ta bazama duniya niman fansanta Tun daga lokacin da muka rabu da Joindah nake bibiyarta nakan yi wata uku kafin na isa gare ta, ina kai mata duk wani bayani akan ki! Sannan Allah gwanin hikima sai gashi ya had'ata da Amir Almustapha Mu'allim, duk da nasan labarin karshe sakamakon soyayya ce nayi fatar na gaya miki amma ta hanani! Sun bar mulkin su, sun bar dangin su! Sun bar nasabar su, sun tafi wata duniya domin rufe kofar da za a tab'a kimar ku! Joindah ta kasa gaya miki juyin mulki ake son ayi miki na tsawon shekaru aru aru, sabida ance idan tayi yunkurin fada toh kanta zai koma! Shi yasa aka hada mata sharrin tana boyayyen alaka da wani makiyin mu, wato yahudawan garin Sir. Ke kuma baki bincika ba, dan dama kin san cewa suna niman hanyar da zasu kifar da mulkin kinne shi yasa kika yi tunanin itace zata basu damar haka? Ina Amirah Joindatullah ba haka take ba, ba haka ta koya ba! Kece kika koya mata fadar gaskiya koda zaka ransa ranka ne, kuma.kika gaya mata ita gaskiya bata boya ko an boyeta zata bayyana. Kin nuna mata ita gaskiya hanya ce ta mahadakr da ubangijin ka, toh shi tazo gaya miki wancan ranar! Shi tazo fada miki wannan lokacin da kika sa aka kashe Jermaya! Tare da shirya yaki! Karshe aka yi nasara kin zata sabida dakarunki Allah ya baki nasara! A'a, Allah ya baki nasara ne sabida ita...... How fa🤔🤣 Chakwakiyya zalla ko....... 200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641 Mai_Dambu.. [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 20 "Subhanallahi!" Ta daura hannunta a bakinta, idanunta sun firfito waje, sake kallon shi tayi cikin wani irin tsoro. "Don Allah mata basu burge ka?" Ta tambaye shi cikin kaduwa tare da mugun tsoro, Cuna bakin shi yayi kamar wani yaro karami,, sannan ya wani kwaɓe fuskar shi, ya wani jijjiga kanshi. Zaro idanu tayi kamar zasu fado kasa. Tare da saka hannunta dukka biyu akan fuskarta, tana jijjiga kanta. "Don Allah! Karka min haka" "Kiyi hakuri Anne, nafi" toshe mishi baki tayi tare da tambayar shi. "Tun yaushe kafara?" "Hmm!" Ya faɗa mata, ba tare da ya kuma kallonta ba, fita yayi tare da nufar inda dakarun suke horon. da yayi sannan ya zuba musu ido, ganin yadda suke horon, shiru yayi yana tuna Ikram, murmushi yayi lokacin da suke bawa kansu wahala. Tawowa Mahlika tayi da tiren shayi. Tana zuwa ta ajiye mishi sannan ta koma gefe, tana satar kallon shi, yadda yake jingine da wani matashi, murmushi tayi tana me jin yau zata sami kusanshi da shi Insha Allah, kallonta yayi alamar ta zuba mishi shayin. Cikin sauri ta fara kokarin zuba mishi. "Sultan MEHRAN! Ga Amirah Jasrah nan shigowa!" Aka fada daga bakin kofar shiga gurin da suke. Bayi mata da maza suna bin bayanta, jikin Mahlika ne ya dauki rawa, har ta rasa yadda zata yi da butar shayin. Murmushi yayi daidai shigowar Jasrah, a hankali ya daura hannun shi, a saman na Mahlika, da sauri ta d'ago kanta tana kallon fuskarshi. Cikin Wata irin bazata, dauke idanun shi yayi akanta tare da juye mata shayin a hannunta, cikin sauri ta yarfe hannunta. "Idan kina gaba karki kuma razana, gaba zan kona miki hannun sama da haka!" Gyada kai tayi da sauri, kallon takaici Amirah Jasrah tayi sannan ta harde hannunta a kirjinta, sai da ta bari Mahlika ta mike kafin ta kalli gabanta ta saka mata kamar kamar yadda Ikram ta tab'a mata . Yana halkance dasu, amma ba zaka Fahimci haka, domin hankalin shi yana kan masu rehazal, faduwar kayan shayin sa ita kanta yasaka duk suka dawo da hankalin su kansu. Take mata hannun Jasrah tayi sannan ta durkusa. "Wannan shine haduwar mu ta farko! Kar na kuma ganinki kusa da Inuwar Mehran! Balle kiyi kokarin shayar dashi shayi, idan ba haka ba ni nonar Mahaifiyarki zan shayar dake." Ta fadi haka tana karamin murmushi. A hankali ta cire kafarta daga kan hannun Mahlika, sannan ta sake wata yalwataccen murmushi, tana kallon Mehran. "Ko zan iya zama kusa da Sultan?" Lumshe idanun shi yayi tare da jingina hannun shi akan matashin sannan ya daura kan shi akan hannun shi, yana wata da d'aya hannun shi. Ganin yaki mata magana yasata, kasadar zama a kusa da kafarshi. Aikuwa sai ganinta suka yi can tana dungure, domin shureta yayi da kafarshi. Da sauri dakarunta suka d'aga ta. Suna kallon Sultan. Muryan Fudail ne ya katse musu, shurin da suka yi.ta hanyar cewa. "Zaku iya tafiya da aita, laifi biyu tayi bayan ta ture baiwar shi, sannan kuma ta take mata hannun ta, kana kuma ta nemi zama kusa dashi, bayan bai bata Umarnin haka ba. Shi yasa ta sami damar tashi a raye." A fusace ta juya tana kallon Mehran. "Ni ka tozarta sabida wata kaskantacciyar baiwa? Sai na shayar da kai mamaki kuwa mu zuba mu gani" ta faɗa a masifance. Sannan ta bar gurin tana ji ina ma da zata sami dama sai ta hallaka Mahlika. A fusace ta bar gidan. Tashi yayi tare da kallon Fudail, yace. "Ka turo min ita!" Ya shige abin shi. Koda ya shiga dakin shi zama yayi akan wani kujeran hutawa, kan shi a kasa. Yana fadi a ranshi. _Nasan da kece! Babu wacce ta isa ta takaki ta kwana lafiya! Ina kewarki idan kin mutu kuma Allah ya gafarta miki! Idan kina raye kuma Ubangiji ya dawo min dake cikin koshin lafiya!_ ya faɗa yana me kumshe idanun shi. Karar bude kofar tare da sallama ya saka shi kumshe idanun shi bayan ya kishingida. "Sultan!" Ta faɗa a sanyayye, wanda hakan ya nuna mishi cewa tayi kuka, "Haka zaki cigaba da kuka?" Ya tambaye ta idanun shi kumshe, a hankali ta zube a gaban shi, tana me rike hannunta me ciwon. "Ba dake nake ba ne?" Ya daka mata tsawa, zuɓewa tayi cikin kuka da tsoron shi. Dukda muryan shi bata bayyana b'acin rai, murmushi yayi sannan ya ce mata. "Tashi ki bar nan" da sauri ta mike, har ta fita bai san lokacin da ya sake tsaki ba, a duniya ba zai kuma ganin mace me zunzurutun juriya da hakuri irin Ikram ba, dan haka ya juyar da kanshi yana me jin karin b'acin rai. Wanda ya kashe kiran bai mishi adalci ba kwata kwata, yaso kanshi da yawa, taya yarinyar da babu ruwanta zata fuskanci wannan kisar gillan, gaskiya ba a mishi adalci ba, kuma ba zai tab'a yafe jinin Ikram ba. "Sultan!" Fudail ya kira shi. "Hmm!" Yace mishi. Shigowa yayi tare da mishi magana a kunnen shi, sannan ya kura mishi ido, sabida shima Mehran shi yake kallo. Mikewa yayi sannan yace mishi. "Yau ka bugi cikinta mana!" "Sultan!" "Uhm!" Yace mishi, tare da juya dara darar idanun shi akan Fudail. "Toh zan gwada haka" ya faɗa tare da barin d'akin. "Amma Sultan! Ya batun dayan binciken?" Yadda ya tsuke bakin shi ya saka Fudail shiru, yana mamakin irin wannan kishin Mehran. "Afwa!" Ya faɗa a sanyayye, gyara zaman rigar shi yayi sannan ya juya ya fita abinshi, yana ji kamar ya rufe Fudail da duka, akan me zai tsananta binciken shin Noman ya kwanta da Ikram ko bai kwanta da ita ba, shi sakarai ne za zai yi wannan kuskuren. Da zai aikata wanda ba zai tab'a yafewa kanshi ba. Kuma shima Fudail din bayayi mishi tunin da wata manufa bane, kawai sabida matsalar fada ne.. .... Kallon Jasrah Amir Hood yayi sannan ya sake murmushi. "Akan me zaki tab'a wata baiwa a gaban shi? Ina ruwanki da tab'a wata mace akan idanun shi?" Karki kuma kar na kuma kama ki da laifin haka" ya fada tare da kallonta. Had'iye yawunta tayi sannan ta ce mishi. "Naji Amir!" Ta faɗa a sanyayye, tana share kwalla da yake kokarin zubo mata. ~~~ SAHARA. Dukar kafarta suka yi ta zube a gaban shi. "Takaddirirancin ki yayi yawa, kullum da sabon labarinki nake kwana nake tashi, wacece ke?" Banza nayi dashi ina kallon gefen da Izmah take zaune. "Wacece ke?" Ya kuma daka min tsawa, dauke kai nayi, ya kuma hasala tare da mik'ewa tsaye. "Wacece ke?" Juyawa nayi ina niman da wacce yake magana. "Ina magana kin maidani sakarai?" "Dama dani kake?" Na tambaye shi ina juya kaina gefe, murmushi yayi sannan yace min. "Wacece ke?" Ya kuma tambaya na, murmushi nayi sannan nace mishi. "Ba zan gaya maka kome a kaina ba, sai ka biyani." "Niman kudi kika fito yi ne?" Ya tambaye ni, "Farauta na fito, kuma duk wanda ya dakatar dani, kashe shi zanyi koma waye!" Na fada ina dariya. "Me kike bukata?" "Zaka iya dauka ta a matsayin yar kisar haya, zan kashe maka tun daga kan karamin makiyi har babban makiyi." "Meye hujjar ki?" Ya tambaye ni, yana kallona. "Ka bani umarni na nuna maka irin baiwata" "Na baki! Ki kashe min Irffan bin Aslman!" "Me kake bukata na kawo maka shaida?" Murmushi yayi yana me dauke kanshi ganin irin ba dan iya ba. "Ki kawo min gawarshi!" Juyawa nayi tare da mikawa Izmah hannun, muka fita. "Wannan mahaukaciyar ina ce?" "Wallahi kashe mutum bai da wahala a hannunta, har gwara kiyashi yana da nisan kwana da daraja." Had'iye yawu, yayi tare da zubawa Sarautar Allah ido, .... "Ikram meke damunki? Me yasa ba zaki zubawa Zuciyarki ruwan sanyi ba, bana son wannan yanayin, tsoro nake ji bana jin dadin yadda kike kashe mutane? Wacce irin kaddara ce haka? Ya kin fito daga cikin manyan gidajen duniya kike irin wannan abun? Ikram iyayenki bazasu ji dadin abinda kike aikatawa ba, ba laifi bane fansa, amma kashe wani dan biyan buƙatar rai kuskure ne" Tsayawa nayi na kalle ta, sannan na durkusa muna kallon juna, nace mata. "Ba zaki gane ciwon da nake ji ba, sabida basu kashe miki muradinki ba, idan ina tare sai na cire kan Mehran, nayi ado dashi a mashigar Masarautan SAMAIND!" Murmushi tayi sannan tace min. "Kina kuskre! Kuma baki son gaskiya, zan so na rayu dan na ga yadda zaki Fahimci abinda kike aikata." Banza nayi da ita, dan na gaji da maganarta, haka kawai za zata saka min tausayin kowa a raina ba, dan haka ya share batun ta. Koda muka isa gidan Irffan, ban tab'a su ba, kai tsaye cikin gidan shi na nufa, kamar yadda na sami labarin ya dauke Nimrah, haka na same shi ya wulakantatta tare da ajiye ta a wulakance, jan iska nayi a hankali. Sannan nace mishi. "Kuskure daya kayi bayan shi maza irin ka masu yunkurin aikatawa ba zasu kuma ba, me yasa ka tab'a yarinyar da bata san kome ba? Meye laifinta? Meye taci maka? Me yasa mata basu da daraja a gurin ka? Lallai zaka biya kudin aikin da kayi domin a tsarina bana hakuri. Izmah Kinga dalilin da yasani kai gawan shi can" itama kuka take sosai, sannan na kalle ta tare da cewa. "Rufe min gidan!" Daukar wani mayafi nayi tare da lullube ta, sannan na zaro wasu kananun wuka, na wurga misho har sai da suka shige kirjin shi. "Ban maka kisar da zaka mutu ba, zan kai ka ne can ka mutu a gaban Aabis!" Na fada mishi. Kakari yake sannan na juya abu na, tare da ɗaukar jakar da na ajiye tare da cire wata buhun algarara ma cusa shi, sai da na gama sannan na fito, tare da kiran mutanen shi suka saka min shi akan keken dokin shi. Tunda muka fito, yaran shine zasu min gardama, na rufe idanu nayi ta girbe yan banza, sannan na dauki wacce na biyo bayanta, muka nufi keken sannan muka bar gidan, tunda na kalle ta sau daya ban kuma kallonta ba, har muka isa fadan Aabis, na wurga mishi. Kallona suka yi sannan suka bude buhun, aka ciro shi. Ana fidda shi yana mutuwa, murmushi Aabis yayi sannan yace min. "Daga yau mun zama abokan ciniki!" "Ina fatan babu cin amana?" "Me yasa kike tsoron cin amana!" "Sabida san iya azabar da duk wanda yayi min haka ne?" "Ni kuma tsarinki ne yayi min!" Murmushi nayi sannan nace mishi. "Bana hada harkalla da kai na, da ƙwaƙwalwata nake aiki." "Wai! Toh zan so mu cancare!" "Mmh!" Nayi murmushi me sauti, sannan na juya zan fita, yace min. "Ke makashiya shin zaki fita anan cikin sauki ne? Ko ance miki zan kyale ki ne?" "Aabis bin Ansar, dan gudun hijira daga SAMAIND! Koda yake banga laifin ka ba, zaka iya haka dukda Ni nafi kaunar kashe mutane sama da kashe dabobbin, Sultan Aamaan Abdus Samad Mehran na biyu, ko ba zaka tafi domin daukar fansan mahaifinka bane? Idan ka shirya zamu iya kafa sabuwar harkalla, domin farautar da zanyi na gaba SAMAIND zan dirka a saman wuyar Zakin su. Nayi wasan kura da shi." Murmushi yayi sannan yace. "Ku kama su. Ayita azabtar dasu har sai sun fadi wanda ya turo su." "Zan dawo an jima tayaka hira!" Na gaya mishi haka domin tabbas zan fita daga inda aka ajiye mu. Tunda suka tafi da mu, suke azabtar damu, wallahi na sha wahalar da tunda nake a duniya ban sha ba, sun taramin gajiya iya gajiya amma ban yi musu magana na, har sai da suka gaji da kan su, duka kyale ni, kwanciya nayi ina sauke ajiyar zuciya, domin na gaji da wahala. Zuwa na SAMAIND ba shine matsala ba, yadda zan shiga masarautar shine matsalar, dan haka na koma gefen Nimrah ina shafa kanta, tare da cewa. "Kiyi hakuri! Laifin Mahaifiyarki ce ya shafe ki, gashi baki ji ba baki gani ba kin sami tawayan Sa'a, kiyi hakuri zan maida ke amma ba yanzun ba, dan nima sai na fita daga gidan nan tukun." "Me zanyi nayi a can? Bayan na san mahaifiyata bata aikata daidai ba, laifi laifi ne. Hukuncin da na samu ba wani me yawa bane, gashi nan kin kare rayuwata da lafiyarki ba, ki dauke ni a Matsayin baiwarki .... *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 21 Wani irin tausayi ta bani, domin a girme ta girme ni, amma lokaci guda ta bada rayuwarta domin laifin mahaifiyarta, dauke kai nayi ina share kwalla da ta zubo min. Girgiza kai nayi ina kallon ta, sannan na dauke kai na, ina me kallon Izmah nace mata. "Ba zan iya wannan b'arnan ba, ba zan amshi bukatar ki ba. Ni ba kowa ba ce face, me niman fansa, idan na kammala kuma zan dawo gurin ahalina idan kuma na rasa rayuwata ku zaku iya tafiya inda yayi muku, amma ba zan iya daukar ku a matsayin bayi ba."! Na fadi haka ina me juya musu baya. "Ikram ina tare dake, kuma bana jin zan iya rabuwa dake, dan haka zan biki duk inda zaki shiga a duniya nan" Inji Izmah, matsowa kusa da mu, Nimrah tayi tare da daura kanta a kafadana tana faɗin. "Gashi baki da shekaru masu yawa, amma Allah yayi miki baiwar jarumta, anya kuwa ba kashi daya bane a jikinki? Irinta Sarkin yakin Askandariya?" Murmushi nayi sannan na dauke kai na, sabida aman da nake ji, matsawa nayi, tare da kwara amai sosai.sannan na koma ina me kwanciya a kasa sabida cikina da ya kulle. "Sannun Ikram!" Suka zagaye ni, tare da goge min zofar da ya karyo min, "Ikram! Ko zaki iya zama ne na." "Karki damu wancan d'an iskan zai yi magana!" A hankali barci ya kuma dauka na, bayan na farka na same su a takure, ruwa na nima nayi alola dukda bata wadacce ni ba amma kuma nayi yadda ya sawwaka, sannan na gabatar da sallah da suke kai na. Anan aka turo mana abincin da ake kawo mana kullum, nan muka tab'a sannan suka kalle ni,zasu yi magana na saka musu hannu a baki dole suka yi shiru. Bayan dakarun sun wuce nace musu. "Ku daina yawan magana!" Gyada min kai sukayi . A hankali kwanaki suka yi ta tafi, ina son na fita amma kuma bana son nayi garaje, dan haka nayi kokarin koyawa kaina hakuri domin biyan bukata na, shine kadai mutumin da nasan bai da yar tsama da SAMAIND bawai dan bai da ra'ayi bane, asalima akwai fansa a ranshi dan haka nake son nayi amfani da fushinsa. Da kuma wasu abubuwan da dole sai nayi hakuri zan same su. Ba zai yiwu na same su da karfi ba, dan haka nayi kokarin dauke kai na daga abubuwan da suke min. Duk da yanzun kusan watan mu takwas kenan, a gidan yarin. Kuma bai tuna damu ba. Tun su Izmah basu saba ba, har suka saba. Da na hada jimilar rabuwa na da SAMAIND shekara daya har da watanin, murmushi nayi ina Kuma hango tazarar da take tsakanin mu da SAMAIND, tabbas nisan tayi yawa, kwanakin na kuma tafiya. ~~~ SAMAIND. Duk kwace kwacen shi, wannan karon kan an sami nasarar gabatar da zab'en dan kusan shekara daya kenan da barin Ikram garin kuma a yau za a gabatar da kome, amma idan ka ganshi zaka rantse fuskar shi bai tab'a murmushi ba. Sanye yake da kayan irin na sarakunan larabawa, fuskarshi me yalwacce da kwarjini tayi lub lub, fuskar shi da tafad'a ta taimaka wajen fidda hanci shi har baka. Gefe guda ga wata yar kasumbar da ya tara, yayi wani irin kyau, yana zaune cikin isa da mulki, yan mata hudu ne da Jasrah ta biyar su, lokaci zuwa lokaci yana yawan kallon kofar shigowa harabar, mace d'aya tal yake dako! Shin zata zone? Ko ba zata zo ba? Wannan ita ce tambayar da yakewa kanshi tun da aka saka lokacin da za ayi abun. Yake fatan Allah ya kawo ta, ya kuma kawo sanadin da zata zo, dan haka yana zaune a gurin har aka fara gudanar da abinda aka tarasu suyi. Mikewa Fudail yayi sannan yace musu. "A bisa wannan zab'en da za ayi muna maraba da yan matan da suka zo kama daga wasu yankunan kasar zuwa na nan cikin gidan. Sannan akwai Amirah Azizah tana nan tafe itama, akwai kuma wata wacce Sultan bai bayyana mana sunan ta ba, tana nan tafe. Dan haka wannan zaben ba wani zab'e bane kece zaki zabawa kanki damar zama da Sultan MEHRAN. Kasancewar shi mutum me son cin abinci daga makusantan shi, yasa ya baku daman dafa mishi abinci me sauƙin yi, tare da sarrafa alkama da wasu dangin sa, sannan kowa yasan yadda ake dafa shayi a sha. Toh Sultan Mehran yana cikin mutane masu sun shan shayi, sai kuma wasu abincin da kika san anayi a cikin masarautan ku, zaku iya sarrafa shi indai zaki iya ci kuma Sultan yaci, bismillah.. Sanan a cikin gwajin mu akwai tambaya akan sarauta, dan haka zaku iya farawa kuna da lokaci daga nan har azhar." Tsuru tsuru suka yi tare da kallon Fudail, domin dukkan su Amirorin basu aikin kome a gidajen su. Bayan Amira Jasrah, sai Yasmin Bint Mir Umdatuddawla, sai Ramziya yar Mir Jazib, sai Sawda yar Mir Rabib, shigowar Azizatul Nissah, Kanwar Sultan Abrad. Ya saka Mehran d'ago kanshi da sauri yana kallonta. Dauke kanshi yayi tare da maida shi kan abinda yake gaban shi. Yana jin babu dadi a ranshi. Tabbas ya rasata ya kuma tabbatar da haka ne ta hanyar ganin yadda yan matan suke kokuwar sarrafa girki. Ga kanshi ya cika ko ina, amma a gurin Sultan Mehran ba haka bane, fuskarshi bata da walwala, ya wani sunkyar da kanshi, sake maimaita bayanin da Fudail yayi, sannan ya shiga kallon Azizatul Nissah da tayi tsuru tsuru,kafin ya fara aikin da ke gabanta. Haka suka yi ta aiki tare da gabatar da kome har kusan lokacin salla yayi, sannan aka turo dakaru suka tsaya a gurin dan suma sun idar da sallah. Bayan kamar minti talatin suka kuma dawowa, nan aka shiga kwashe abincin tare da jera su, a gaban Mehran kowacce idan ta ajiye zata rubuta sunta da inda tafito. Murmushi Fudail yayi domin dai kamshi ya ishe shi. A hankali aka shiga dibawa Sultan din tare da zuba mishi a wani tire, a hankali ya dauki data kofi me kyau ya wanke hannun shi,sannan ya dauki abincin yayi loma daya, cak yayi tare da kallon Yan matan da iyayen su da suka zo suma ganin abinda yake faruwa. Kallon Fudail yayi tare da mishi alama ya bashi abinda zai juye abincin bakin shi. Yana juyewa ya kalli, shi sannan ya tura mishi, shima yayi loma daya , zubda yayi tare da ajiyeta a gaban Mir Umdatuddawla, wato abincin Yasmin. Mika mishi abincin Jasrah akayi ya kalli Amir Hood, sannan ya dauki abincin ya kai lomar bakin shi. Kallonta yayi sannan ya dauke kan shi, tare da zubda abincin a cikin abin zubda. Ruwa ya sha, idanun shi sunyi jajjur,dauran kofin ruwa yayi tare da sha sosai, sannan ya mikawa Fudail yana zuba loma ya furza yana niman ruwa. Dauka abincin Azizatul Nissah yayi, ya kura mata ido, sannan ya kai loma daya,.sake kallonta yayi sannan ya maida kan shi dakyar ya had'iye sannan ya mikawa Fudail, shi kuma yaci ya mikawa Nawwas, sai Ramziya. Itama haka aka ajiye nata, kafin aka ɗauki Na Sawda.aka tab'a ajiye mata yayi tare da mik'ewa ya wanke hannun shi. Shayin aka fara jera mishi, dukkan dai ba a cewa Kome, kallon iyayen su yayi sannan yace musu. "Ana tilastawa boya koyan yadda zata iya kyautatta iyayen gidanta me yasa Yaran ku baku koya musu yadda zasu rike mazajen su ba. A cire batun mulki ni mutum ne mai mugun son naci abinci daga cikin muhalina, yau gashi abin kunya yaranku da kike kaunar su, sun gaza bani abinda zancl. A haka kuma idan naji ace min mijina. Toh gaskiya ina son abinci." Ya faɗa tare da dafe goshin sa, sabida ya gaji daga surutun da yake yi..kallon su yayi. "Fudail ka ji dasu." Sannan ya mike tare da barin gurin. "Abisa wannan namijin kokarin da kuka yi, toh mun kara muku shekara daya zuwa biyu,ku koyi yadda ake sarrafa girki, domin koyi girki da zuciya daya karku yi tunanin zaki dawo ki hada mana zafin kai dan ba kyalle ku zamu yi ba. Sannan ku mai da hankalin ku, Allah ya bada nasara, karku manta an sami kusakurai dayawa, a cikin abincin ku. Dan haka wata shekara idan muka hadu ku tabbatar kunyi abinda ya dace. Sannan akwai kyautar da Sultan Aamaan Mehran ya bada a baku kowaccen ku!" Jinjina kai suka yi, sannan ya bawa dakaru umarni a mikawa kowa kyautar da Mehran ya basu, yan kunne ne na duwatsun lu'lu'u da sarkan su. Amsa suka yi tare da godiya. Tunda suka juya suka fita shi kuma Fudail ya shigawa Manyan fada magana yadda zasu fahimta. "Kuma kun ji yadda abincin yake ba? Toh zaku iya taimaka musu, ta hanyar amfani da zaman da zasu na koyan girkin, don Allah su maida hankalin su sosai, idan ba haka ba wata shekara haka zasu yi ta fama da shi. Mutum ne me son cin abincin." Kallon shi suke, cike da takaici dan zunzurutun wulakancin a rasa abinda za a saka yaran su, shine girki. Jinjina qarfin halin Mehran suka yi sannan suka mike tare da barin gurin. Har zasu wuce. Amir Hood yace mishi. "Fudail ka tambaye shi baya tsoron guba ne?" "Ai shi ba matsroraci bane? Mutum ne me wankakken zuciya, da yana tsoron guba da tuni yayi bankwana da duniya, su koyi yadda zasu saka mishi gubar yaƙe bukata." Inji Fudail, Juyawa suka yi suna kallon shi, kafin suka fita, daga gidan. Tabbas sunyi sake barin Sultan Mehran ya sami damar abokin kirki a tare dashi dan haka ba zasu kuma barin yaran su, zama mishi mutanen kirki ba. Domin yin haka zai iya dakushe Muradin su. ~~~ "Toh ya kuka yi dasu?" Sultanah Fazilatul nisa ta tambaye shi. Hannun shi dukka biyu idan kirjin shi, ya juya yana kallon ta, sannan ya sauke ajiyar zuciya, yana kallon waje. Ita kam ta fara gajiya da wannan shegen miskilancin Mehran, ayi mutum magana ma sai kayi mishi jan aji kafin ka amsa, shegen yanga tayi mishi yawa. Had'iye yawun bakinta tayi tare da sake jefa mishi tambayar, Niman gurin zama yayi sannan ya kalle ta, kafin ya sauke idanun shi yace mata. " Basu iya ba!" "Kamar Ya?" Sake dauke kanshi yayi sannan ya cigaba da abinda yake yi, kwana biyu nan ya tsani magana, dan haka yadda yake tambayar shi kamar watsa mishi ruwan zafi take, dan haka yaja bakin shi ya tsuke,duk yadda taso yayi magana fiir yaki tanka mata, kuma yaki d'ago kai yayi magana. Juyawa tayi zata bar gurin, muryan shi ya dakatar da ita, cikin sanyayye yanayi yace mata. "Afwa Anne! Bana son magana ne!" Goge kwallar da yake sauka mata tayi sannan ta girgiza mishi kai tana faɗin. "Babu kome, Allah yasa mu dace!" "Amin!" Ya faɗa a sanyayye, domin ya fahimci tana cikin damuwa, duk da har yau zargin shi take yana bin maza, shigowar Fudail ya katse shiru su. Shi kuma ya koro musu bayanin yadda suka yi da amir Hood. "Hmm!" Yace tare da sunkuyar da kanshi kasa, yana wasa da yan yatsun hannun shi. "Me yasa kai baka son ka fadi abinda yake ranka? Me yasa kake yunkurin rena min hankali? Idan anyi magana sai kace Hmm! Wato ga mahaukaciya kai baka san halin mutumin nan bane da zaka ce hmm! Kasan yadda nake jin damuwar shirunka? Da zance maza ne yanzun zaka dauki maganar da muhimmanci," Kasa danne dariya Fudail yayi yana,toshe baki yayi. Fuskar Mehran a sake, duk da babu fara'a amma zaka fahimci, kalmar mazan da takira ya sanya shi sake ranshi domin ya fahimci ranta ya b'aci, dauke kan shi yayi tare da lashe bakin shi. "Fudail mahaukaciya ka gani ne?" "Afwa Sultanah!" Ya fadi haka yana fita, dan ya kuma tinzara ta, ya bi bayan Fudail da wani irin shegen kallo. "Aamaan!" Ta daka mishi tsawa, da sauri ya dauke kanshi daga bayan Fudail. *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 22 D'ago kai yayi yana kallon ta, tare da hango girmanta da darajarta a cikin kwayar idanun ta, wani irin rike kanshi yayi tare da jin babu dad'i, yadda take kuka tana fada, yayi matukar d'aga mishi hankali sama da kome a duniya. "Ni ban hanaka niman macen da kake bukata ba, amma Aamaan me zaka yi da maza? Meye abin so a abinda Allah ya tsinewa masu aikatawa, Mehran! Baka da burin da ya wuce kaga ina zubda kwalla ko tausayin zuciyata baka yi, ina laifin na sami rangwame da mutuntawa akan idanuna kake kallon wani namijin, wallahi ba zan ji dar dan ka kalli mace akan idanuna ba. Amma babban kuskure ne naga kana bin namiji da kallo, wannan abin babu dadin ji balle gani, na had'aka da Allah ka daina bin maza." Kallonta yake, ya ma rasa yadda zai mata bayani ta fahimta, dan haka yace mata. "Kiyi hakuri!" Daga haka ya mike ya bar mata falon, shi kam bai san me zai ce mata ta fahimta ba, amma shi Allah ya gani babu namiji a gaban shi. Matan ma Ikram ce, kuma yau da akayi taron Nan ya tabbatar ba zata dawo ba, ya sashi tattara kome nata ya nime katon makulli ya bude kasar zuciyarshi ya binne ta a cikin shi, yayi alkawarin duk yadda ya sami me son shi dan Allah zai bata damar zama dashi. Amma ikram kan ya manta da ita a ya ajiye ta a inda baya tunanin zata kuma dawowa rayuwar shi. Shi bawai ya tsane ta bane, amma kuma baya son ta tuna abinda ya kuma hada su a baya can,shi yasa ya dauke kanshi daga ita ya kuma boye ta a cikin mizanin shi. Baya kuma son wani ya tuna mishi ya tab'a ganin ta ma. Sabida Allah ka dai da Fudail suka san yadda yayi ta biyan fatake kudi dan su bincika mishi inda take, sau biyu yana tura Fudail GIZERA, kuma amsar daya ne babu labarin ko tana raye, na farko bayan labarin mutuwar ya riske shi na biyu Fudail da Sarwat, sai kuma fataken da yake biyan su, ana niman ta. Kullum yayi Sallah itace take fara samun addu'ar shi kafin ya daura da iyayen shi da shi kan shi, amma babu kome kamar a wurga dutse cikin ruwa, shi kan shi yasan dai yana cike da kewarta, amma ya bar batunta ya ajiye kome, "Sultan" Fudail ya kira sunan shi, a hankali ya bude idanun shi da suka yi jajjur. "Dama zan baka hakuri ne, da abinda Anne tayi maka, sannan yanzun na sami labarin, wai Ikram." Dakatar dashi yayi ta hanyar d'aga mishi hannu! "Sultan!" Nuna mishi hanya yayi, duk yadda yaso, fahimtar da shi kasawa yayi asalima zuba mishi ido, Fudail yayi tare da cewa. "Allah ya huci zuciyar ka!" Ya fita daga dakin, ya nufi waje. Yana gyara zaman wandon shi wanda haka ya faru akan idanun Sultanah ne. Kasa magana tayi sai yankan jiki tayi, a gurin ta zube sumammiya. Fitowar Mahlika ta ganta kwance shine ta fasa ihu, duk suka taru akanta, yana zuwa ga suka kama kama da ita zasu dauke ta, yana zuwa ya dauke ta cak yayi d'akinta da ita, sannan suka shiga ƙoƙarin ta farka, dakyar ta farka, tana ganin shi ta rintsa idanun ta,tare da juya kanta daga gare shi, tana ajiyar zuciya. Riko hannun ta yayi, ta daka mishi tsawa, sai da ya janye. Wani irin kuka ne ya kwace mata, ta juya musu baya. Duk sai jikin shi yayi sanyi. "Nagode sosai! Ni zaka b'atawa rai? Ni kake kokarin tozartawa, abinda Mahaifinka bai yi ba, Mehran shi kake aikatawa? abinda Abdus Samad bai tab'a gwadawa ba, Mehran shi kake aikatawa? Mehran meye a jikin Namiji?" Hannun shi ya kai keyar shi sannan ya sauke ajiyar zuciya kafin yace. "Ina ganin kamar ai an gama wannan maganar ba? Toh meye na dawo dashi? Ni wallahi ban tab'a abinda kike zargina ba, ni rabona da Y'a mace kusan shekarar goma sha biyar, na gaji wallahi." Ya faɗa a gajiye tare da barin d'akin, ranshi yayi masifar b'aci. Bai tab'a sanin cewa zai iya fuskatar tozarci ko zargi haka ba, sai yau duk sai yaji ranshi ya b'aci, taya da girman shi zai dinga fuskantar matsala haka? Duk kamewar shi sai an jefe shi da irin wannan kalmar,. Baya son tashin hankali da reni yasa shi ƙin amincewa da yaran da aka turo mishi yau, domin yasan halin Yaran da suka taso cikin gidan sarauta ba tarbiyya bace suke samu wadatacce, kawai ana koya musu mulki ne da kirsa da kisisina, sai makirci da iya kwanciya da namiji a gado, shima dan kar a sami matsala ne a goran ta musu, amma tabbas baya sha'awar macen da aka haifeta a gidan sarauta. Domin abinda zata bukata mulki ne.. Shi kuma baya da ra'ayin macen da zata bukaci mulkin yafi ra'ayin wacce zata, shirya musu soyayya da jin dadin rayuwa, shi mutum ne da ya rasa kulawa a gurin Uwarshi, dan haka yake niman kulawar mace da zata damu dashi, kuma zata samu da matsalar shi, bawai wacce zata maida hankalinta akan mulki kacokan ba. Ikram ce ta fado mishi tsaki yaja tare da juyar da kanshi, duk halin da yake ciki itace sanadin haka, domin ita ta gudu ta bar shi, da bata tafi ba tabbas da yana nan ya cika kudirin shi akanta, ya kuma bata matsayin da koda bata so. Amma sai ta zab'i muradun zuci tayi gaba abinda ga abinda tafiyarta ya haifar mishi. Yasan koda Fudail ya wanke shi ba zai wanku ba a gaban Sultanah Ikram ce zata iya wanke shi tass, ta kuma mishi adalci. Ajiyar zuciya ya sauke akai akai. Yana kuma sake jin tsanar dalilin da Yasaka Ikram tafiya ta barshi gashi babu ita babu labarinta, duk inda yake tsammanin ganinta, an je bata nan. ~~~ Merocco. A hankali ake bashi magani, yana sha tare da kauda kanshi, yayi sannan yace musu. "Kun sami labarin ta?" Shiru suka yi, Sultan Mu'allim ya bude baki zai magana ya dakatar dashi. "Don Allah! Ka barni na tafi, ka barni na nimo ta, daga nan na san dole." "A'a ba zan iya barinka ka tafi ba, zan saka mutane su nimo min ita, nima jini na ne Ikram" "Ikram?" Ya tambaya yana kallon Sultan Mu'allim, sannan ya kauda kanshi. "Taya ta zama jininka bayan mu kana da wasu yaran ne?" Shiru yayi sannan ya faɗa mishi wacece Ikram, tashi zaune yayi tare da zaro idanu. Yana murmushin jin dadi kamar bashi yake yada kai kamar an yanke mishi kunne ba, sai gashi yana murmushi da jin dad'i, kafin kace kwabo sai gashi ya ware kamar da wanda ya sha jinya na wasu watanin ba, zunzurutun ya saka Ikram a ranshi, murmushi yayi lokacin da aka rike mishi hannu za a kaishi ban daki yayi wanka, shi daya sai hango daren amarcin su yake, tare da rufe idanun shi. Dakyar yayi wanka ya fito aka bashi kaya ya saka, ya zauna yana kallon su. Abinci aka jera mishi da kanshi yaci bai yarda an bashi ba, yana yi yana murmushi. Har ya gama. Kallon Kakan shi yayi yace mishi. "Sultan yaushe za a fara niman ta, dan gaskiya nima zan tafi" "Me yasa kake azarbab'i?" Ya tambaye shi, dake Rahil irin mutanen nan masu fadan gaskiya kome kayi sai dai kayi bai wani damu ba, yacewa kakan. "Kaunarta nake? Ina sonta a matsayin matan aurena, so nake na ajiye ta a matsayin Uwar yarana, don Allah ka taimaka min?" Tabbas yayi abinda ba kowa yake yi ba, ya fito ya bayyana sirrin zuciyar shi, akan mace rike hannun shi yayi tare da cewa. "Toh ka ajiye haka a ranka indai ina da Iko da ita Insha Allah Bilqisul Ikram Matarka ce!" Gyada kai yayi tare da murmushi. Yana faɗin. "Nagode Sultan!" Mikewa yayi sannan yace mishi. "Ka ci abinci! Kasha magani sai ka kwanta ka huta. Mijin Ikram!" Murmushin jin kunya yayi tare da sunkuyar da kanshi yana dariya. --- Kallon dakarun yayi sannan yace musu. "Ku kira min Waziri." Da sauri suka juya, shi kuma ta shige cikin gidan, yana zaune a babban falon shi, sai ga Waziri. Da sallama, nuna mishi gurin zama yayi sannan yace. "Sultan!" "Wazir!" "Na'am!" A hankali ya warware mishi yadda suka yi da Rahil, shiru yayi yana sauraron shi har ya gama, gyara zama Waziri yayi sannan ya kuma kara nutsuwa, sannan yace mishi. "Allah ya taimake ka! Sai dai kuma ina ganin kamar akwai tilastawa, domin idan tana da abokin rayuwarta ya zamu yi da ita? Ko zamu mata dole ne? Ka ajiye shashancin Rahil, karka koya mishi kome ya nima zai samu, domin ba lallai bace ita ta amince ta zauna dashi." "Zata zauna dashi mana, me yasa kake ganin ba zata zauna dashi ba. A iya fahimtar da nayi na gano itace kwarin gwiwar shi, idan tana kusa dashi, zai zama cikakken namiji, idan bata tare da shine zai kasance mara amfani, kuma a halin da na ganshi yana matukar kaunarta duk da yasan yadda muke iya boye soyayyar mu, amma ya kasa b'oyewa ya gaya min kaunar da yake mata. Don Allah karka karya mana gwiwar mu!" Shiru Waziri yayi domin bawai baya son Ikram da Rahil bane , kawai yana hango yadda zata amshi tayin akan Rahil ne, idan kuma tana da wanda take so ya zasu yi tunda dai ai ba dole zasu mata ba. Dan haka yayi ta mishi bayanin yadda zai fahimta amma son Rahil da tausayin shi na maraicin da ya taso ya hana Sultan Mu'allim hango kuskuren da zai aikata, dan haka wazir yayi shiru yana me binshi da toh, har ya gama bayanin shi, sannan ya sallami wazir. Daga nan shsshin Rahil ya nufa, ya same shi yana cikin nishadi da annashuwa. "Daka ce kana son yarinyar bata da wanda take sone? Karka so kanka matukar ka fahimci tana da abokin rayuwar ta, don Allah ka kyaleta karka mata dole, dan nasan matukar Almustapha ne ya haifeta ba zata tab'a tsallake umarnin Sultan ba." Daga haka ya juya tare da barin shi yana kallon bayan Kakan shi ba gurin Uwa, shi yasa baya jin dadin shi domin sam bai sake mishi kofar da zai sake jiki dashi kullum cikin fada da tsangwama,kullum yayi abu yayi ta mishi fada kenan. Tab'e bakin shi yayi sannan yace. "Ina ruwana, koma waye Salsabila ta wace!" Ya fada kamar wani yaro karami, har da tura baki gaba. Shida ba an bashi ita ba, toh koma meye su suka sani, Ikram tashi ce shi daya kuma babu shegen da zai kwace mishi ita. Har da bin dakin da harara. ~~~ Kowane bangare sun gama gajiya da niman Ikram domin Askandariya ma, tun wani yunkurin da Nairah tayi aka kamata tana gidan yarin, Sultanah Amrah tasha jinya sosai. Sannan ta saka aka tafi har Merocco, aka bincika mata kome akan dangin mahaifin Ikram, sai dai babu Ikram a can. Abinda ya d'aga musu hankali kenan, suka shiga niman ta kamar hauka. ~~~ Yau shekara biyu da wata tara, sannan Wancan mugun ya fitar da mu, duk da mun sha wahala a cikin gidan yarin amma kuma sai da takai na rike shugabancin gidan baki daya, kuma yadda aka mana mulkin mallaka a cikin gidan haka muka yuwa kowa, tare a cin Ubansu. Shi yasa bamu lalace ba, dan da farko ne muka yi wata irin muni, Toh da na fito a asalin tsagerancin sai gashi abincin mu daban da na sauran fursunonin,kome na mu sai da ya banbanta da na kowa, dan haka nasaka Nimrah da Izmah mike kafa suyi abinda ransu yake so, kuma sunyi babu abinda suka sani suna daga kwance aka musu wanki,tausa, abinci ma idan suka tashi sai suce a baki za a basu, Ni kuwa haka dad'i yake min. Ina shimfid'a mulkina cikin Izza da takama, shi yasa yau da aka ce wai zamu fita, sai da mutane da da yawa suka yi kuka. Juyar da kai nayi sannan nace musu. "Karku sani shauki domin wallahi ba zan muku kuka ba, kawai zanyi kewarku ne. Duk wanda muka mishi laifi ya yafe mana, saduwar Alkhairi. Mun gode sosai.... *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 23 Juyawa nayi a sannan nace musu. "Kuyi hakuri! Haka Allah ya ƙaddara mana, Nagode sosai da zaman amanar da muka yi" duk da nasan mun yi zama mara daɗi a farkon shekaran da aka kawo mu. Amma daga baya kuma da na amshi cikin gidan sai gashi da kansu suke nuna min kuskuren su. Har ta kai suna kirana da shugaba, abinda na sani shine bana iya zalinci, kuma bana son naga anyi zalinci. Amma kuma ko yaya ka tab'a wani da sunan zalinci nake jin haka a raina, dayawan su, ba yara bane manyan ne maza da mata, ƙalilan ne yara kangararu irina, lokacin da muka nufi fadar Aabis, yana hakimce a saman kujeran shi, kallon juna muka yi. Sannan yace min. "Barka da fitowa! Ashe zaki ladabtu haka?" Murmushi nayi sannan na zauna cikin nutsawa, "Waye ya gaya maka zan ladabtu cikin sauki? Kawai na zauna ne na huta kuma gaskiya gidan yarin akwai kulawa yadda ya dace, kai dai kawai abinda naso fahimta kananun tsagerun da ka ajiye a cikin gidan ya sani koya musu ladab." "Har yanzu baki ji a jikinki ba?" Kallon shi nayi domin na fahimci bashi da mutunci. "Hmm! Bana son na nuna maka yadda nake rayuwa, dan haka idan baka da abin yi zan tafi kuma idan Yaranka sun isa su dakatar dani!" Na juya zan fita, suka sha gaban mu, maida su Izmah gefe nayi, sannan na gyara tsayuwa na, gatarin da na dauko a gidan yarin na fito dashi, na juya kamar yadda Mehran yake idan zai kai farmaki. "Ku kyaleta! Dawo muyi magana dan na lura mahaukaciya ce ke!" Juyawa nayi sannan nace mishi. "Daga turu nake" na bashi amsa, Murmushi yayi sannan yace min, "Mu shiga daga cikin gidan." Haka muka wuce dashi, wani dakin sirrin shi muka shiga, anan yake bani labarin yadda ya tsira da shida Mahaifiyarshi, bayan kashe Sultanah tace ayi. "Me kake bukata?" Na tambaye shi. "Ki kashe shi! Domin nima ina da gadon sarautar SAMAIND" "Toh duk buri daya gare mu, dan haka zan mishi yadda kake so zan kashe shi akan laifin mu, amma baka da labarin meke faruwa a can!" "Eh Toh ina da labarin cewa, yanzun haka ana ƙoƙarin zab'a mushi mata ne, duk wacce ya zab'a sai ce bata mishi ba, ban san meye nufin shi ba." "Toh ina ganin matar mutuwar shi yake jira gani nan tafe." Na fada mishi. "Taya zaki shiga garin?" "Dabara biyu gare ni, idan na shiga na farko da zamman kashe shi, shikenan. Idan kuma haka bai samu ba, zaka hada min tawagar da zamu tafi a matsayin matar da zata shiga zaben shi." Kura min ido yayi sannan yace min. "Amma kina da fikra!" "Mhh!" Nayi mishi murmushin gefen baki, sannan nace mishi "tafiyar nan da kwana biyu, so nake na cimma matsaya kafin a gabatar da zaben zai iya kaiwa kwana nawa?" "Dan da wata daya ba!" Ya bani amsa, "Idan na kashe shi nan da kwana ashirin da bakwai, na gama aiki idan kuma ban gama ba dole na shiga wancan shirmen." Na fada a hankali, kallon juna muka yi sannan yace min. "Ya angama?" "Eh ina tunanin haka!" Na bashi amsar. "Zaki iya?" Ta kuma tambayana. "Zan iya mana, duk da shi din ba gama garin mutane bane ba, kuma zai iya fahimtar wacece ni ba, sai na nime bakakken kaya domin kare kaina" Da haka muka tsayar da magana, Aabis yasa aka shiga mana shirin da hidimar tafiyar mu, gefe daya kuma aka kai mu gidan da zamu zauna. .... "Amma Ikram ba dai duk sabida wanda ya kashe miki miji kike wannan al'amarin ba?" Kallon su nayi yadda suka kafe ni da Idanu, "Eh mana! Sabida yada zan dauki fansa ne" na fada ina me takaita maganar, "Fansa akan mutum daya? Akan mutum daya zaki sayar da rayuwarki domin rama abinda aka mishi? Akan mutum daya zaki saka zuciyoyin mutane a cikin damuwa? Toh ko an ce miki Sultan Mehran d'an tsako ne da zaki iya watsa mishi hatsi me guba yaci ya mutu ko?" "Wai Ni kam meye Mehran yayi miki da zafi? Gabaki daya kin sauya kanki kamar wata namiji, baki da aiki sai kisan kai, kuma abun haushi har yanzun baki ji kinyi kuskuren ba kullum." Wanka na shiga na Barsu, sunata luguden lebbe, bayan na fito na gyara jikina, sannan na kwanta, ban ce musu kala ba domin yin maganar kamar kara tunzura su yake, haka ma shirun takaicin yake kara musu, dukkan mu muna hutawa aka kawo mana abinci, tashi suka yi suka ci. "Gimbiya ga abinci" "Na koshi!" Maida kaina dan d'agowa nayi ma basu amsa, gyara zaman suka yi, sannan suka cinye tass, kafin suka shiga niman kwanciya. Mikewa nayi na shiga ban daki nayi alola, sannan na fito na gabatar da sallah,.ina idarwa na kwanta a gurin. Tare da tambayar su. "Ina abincina!" Zaro idanu suka yi waje, suna kallona. Murmushi nayi sannan na duba tiren nama na gani gashashe, kad'an naci sannan na kwanta, tare da juya musu baya. ~~~ Kwana biyu muka dauka sannan muka gama shirin tafiyar mu, SAMAIND a karo na biyu. Zan shiga Samaind cikin wani irin yanayi na daukar fansa. Tun da muka bar sahara, bana magana sai dai a yadda nake kokarin ganin na shiga nutsuwa na ne yake yawan damuwa. Domin haka kawai nake jin kamar bana bukatar fansa haka. Zaman mu a garin Madinatul Mah ya sanya ni jikin mutuwar jiki, abubuwan da suka faru a can masu tsayawa a rai ne, bana jin zan kuma samun kyakkyawan damar da ya same ni a lokacin. Bana najin zan kuma jin yanayin da naji zama da shi a hankali, lumshe idanuna nayi ina hango wannan yanayin a idanuna. Hannun Nimrah naji a cikin nawa, a hankali na bude idanuna. Da sauri na sake hannunta tare da wurga mata harara. "Wannan wani irin Iskanci ne?" "Dadi na dake fassara, dalla can ba dan wancan yanayin nake jin na miki magana ba." "Kyale Ni" na fada mata, tare da juya kaina, na lumshe idanuna a karo na biyu, sannan na kwantar da kaina, a jikin keken dokin. "Ki rabu da ita! Tana son yakar Mehran, amma kuma adilar zucuyarta tana tuna mata dajarar shi, mutumin da ya koya maka kare kanka, mutumin da ya roke ka, damar zama dashi mutumin da ya tsaya dom...." "Kanin Ubana ne da zan d'aga mishi kafa?" Na tambayi Izmah, "Idan baki d'aga mishi kafa dan adalci ba, kya d'aga mishi kafar domin raya kaunarku!" Kallon shegen bakinta nayi yadda ta iya zato gundumemmiyar magana haka. "Kuma haka ne fa, Allah kasa naga waye Sultan Mehran din nan, naga yadda za a kwashe soyayya dashi har haka." Inji Nimrah. "Amma dai ku yan iska ne? Ina ruwana da wani shi?" Na fada a fusace, "Ba zaki gane bane, Kinga wannan bakinki? Wallahi idan kika Kuskura ya kama shi, hmmm wallahi na tausaya miki domin kuwa a mutunce zai cinye bakin babu wanda ya isa ya hana shi." Toshe kunne na, nayi domin Iskancin su ya wuce tunani na, matukar zasu zauna toh wallahi maganar banza suke cirewa a bakin su, kuma karki tsammanin ba zasu iya fada bane. Har muka yada zango, muna kwance a daki daya, abinci muka ci sannan muka fada hira. A hankali muna hira ban san ya akayi ba sai ji nayi bakina ya furta Uwaisul Qarni. "Shine mutum na farko da na fara haduwa da shi, bayan na rasa kowa, daga shi sai Sultanah Fazilatul nisa, itama kuma dan Mehran ta bukaci ni," "Toh amma kuma shi Mehran fa?" Suka tambaye ni kamar hadin baki, iska na furza a hankali, sannan na kuma kallon su kafin na dauke kai na, akan su. "Mehran! Aamaan Abdus Samad Mehran na biyu! Banyi tsammanin akwai abinda zan fada akan shi me kyau ba, mutum ne me mugun son kanshi da zuciyar shi. Mutum ne da baya hango cigaban ka sai Allah tashi. Idan na ce zan fada muku irin wahalar da nasha a hannun shi sai kun yi mamaki. Sai dai duk da haka, ya koya min fada da kuma tinkarar yaki. Mehran ya ceto rayuwata sau biyu, ya kuma kare lafiyata, iya wannan yanayin kawai na tuna bayan shi bana tunanin kome akan mutumin da ya kashe min rayuwa ta, domin akan idanuna dakarun Samaind suka kashe min mijina a daren ranar auren mu, zuwa wayewan garin ranar. Ba zan iya yafe masa ba. Ba zan iya yafe mishi ba, zan rama abinda yayi min dai-dai yadda yayi min." Na fada tare da jan mayafina na kwanta, kashe hasken tantin suka yi, a Sannun na soma jin wani irin sanyin yana shiga jikina. A hankali barci mara dadi ya dauke ni. "Barka da zuwa! Yau Allah ya nufa kin tuna Ni?" A hankali na juya ina kallon shi. Ka rasawa kusa dashi nayi, sannan na zauna ina kallon shi. Kuka ne ya kwace min, bai hanani ba. Kuma bai rarrashe ni ba, haka nayi kukan har na gaji, mika min ruwa yayi nasha, tare da sauke ajiyar zuciya. "Kinyi kokari da kika tsayawa ahalinki, amma don Allah ki tsaya mishi wannan lokacin" "Kashe min miji yayi a daren me daraja a gurin." "Shin kin yarda zai kashe miki masoyi? Shin kin amince Mehran zai hanaki farin ciki sabida ranshi? Kina mahauniyar rayuwa, idanun ki sun rufe da son ganin laifin shi. Mutum ne me takatsantsar akan al'ummar shi da kanshi. Ba gama garin maza bane masu aiki da mace. Kinzo a daidai lokacin da ake bukata, Mehran yayi zaman jiranki na tsawon shekaru uku, har yau yana nan bai cire tsammanin ganinki ba. Dan haka idan kin gadama ki, saurare shi idan baki gadama ba ki kashe shi." Daga haka yayi b'acewar shi, Ni kuma ba farka ina jin sanyi sosai, tare da jin zuciyata tana girgiza. ~~~ Kallon shi Fudail yayi bayan gama mishi bayani akan rikicin da ya balle a fada yau, sai ga dattawan fada zasu daku. "Akan me?" Ya tambaya tare da bude Alqur'an, yana dubawa. "Wai akan Amir Hood yace musu Jasrah ce ta cancanci zama Matarka sauran yaran su, kuwa su tsaya a matsayin Kwarkwarorin ka, shine suka ce basu yarda ba, sai dai dukkan su. Su rasaka" "Hmm!" Ya cigaba da abinda yake dan ba zai iya magana ba, yana gamawa ya kalli Fudail yace mishi. "Anne ta sami labarin abinda ya faru?" "A'a ban gaya mata ba" inji Fudail, "Amma kuma me yasa?" Ya tambaye shi yana me kafe shi da fararren idanun shi. Kwarjini yayi mishi, dan haka ya sunkuyar da kanshi, tare da cewa. "Afwa!" "Ka gaya mata yanzun!" "Insha Allah!" Sannan ya juya ya bar falon, har yanzun Sultanah Fazilatul nisa fushi take da Mehran. Duk da har yanzu bai gaya mata baya abinda yake zargan shi, amma ta kasa magana sai ma zuba mishi ido da Tayi, shi kuma hakan yana mishi ciwo, dan da yana cikin walwala da manta Ikram, amma yanzun fushin Sultanah ya saka shi jin kamar bayi da kowa a duniya, kuma baya iya jure kowani irin fushi, ya sha zuwa ya bata hakuri ya mata magana yadda zata fahimta karshe idan ya shiga dakin sai ya rasa yadda zai mata magana, ya wanke kanshi. Koda ya isa gabanta ma, sai ya rasa tacewa duk ta cika mishi ido. Shi yasa ya hakura da gaya mata gaskiyar ma tunda baya iya magana a gabanta. Shafa kanshi yayi yana me jin babu dadi akan haka, dan ya gaji da shirun da take mishi. Ajiye Alqur'anin yayi tare da nufar hanyar d'akinta, ya same ta akan abin sallah, tana addu'o'in. Zama yayi har ya kai karshe, sanan ya kalle ta, ganin yadda ta share shi kamar baya gurin, ya sashi karasawa kusa da ita, ya riko hannunta cikin tsannanin damuwa, sannan ya bude bakin shi wanda yake ji kamar..... *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 24 Ji yayi kamar an cika mishi iska a bakin shi, tare da rashin sanin madafa. Shiru yayi tare da sunkuyar da kanshi yayi tare da damke hannunta, haka ya tabbatar mata da hakuri yake son bata, amma sabida rashin iya mu'amala da mutane ya saka shi kasa ko magana, sai dai idanun shi da suka yi jajjur, jijjiyar goshin shi sun mike rad'a rad'a. Had'iye yawun yayi tare da sunkuyar da kanshi kasa, riko hannun shi tayi sannan ta kalle shi cikin idanu. "Dole ka koyi rarrashi! Dole bakin ka ya iya fadar ayi hakuri! Wajibi ne bakinka ya iya fahimtar da mutane abinda basu Fahimta ba. Aamaan dole ka koyi kula da mace, ba kana son Ikram ba?" A bazata tambayar yazo mishi dan haka yayi maza ya d'ago kanshi yana kallonta, kafin ya isa furta. "Bana sonta, ban tab'a jin sonta a raina ba! Asalima tunda aka ce ta rasu na ajiye kome akanta, na shirya amsar kowacce irin mace matukar zaki yi na'am da ita." "Me yasa kake ganin Ikram ta mutu?" Kasa yayi da kanshi tare da lashe bushashen lebben shi, sannan ya shafa kan shi tare da mik'ewa a hankali, ya nufi bakin kofar d'akin, kamar ba zai magana na, kasa kasa yayi maganar domin idan kana kusa dashi zaka fi jin abinda yace, amma a hakan bai hana Sultanah Fazilatul nisa fahimtar kome da abinda ya faɗa ba. Kalmar dai ta kullum ce da tana raye da tazo. Murmushi tayi sannan tace. "Idan kuma tazo da?" Tab'e baki yayi sannan ya girgiza mata kai, kafin ya fita, dan bai cika son yawan magana akan Ikram ba, yana takura mishi sukuni. A hankali ya nufi dakin shi, ya zauna tare da kai hannun shi dukka biyu haɓɓar shi, yana me nazarin abinda ya faɗa. _Kana son Ikram?_ _A'a bana sonta! Ban tab'a jin kaunarta a raina ba_ Wannan shine kalaman da suka yi ta yawo a kanshi har kusan awa guda,.kafin ya tattara su guri guda, ya manta da su. Dan yayi alƙawarin ba zai kuma d'aga hankalin shi akan Ikram ba. Ya kuma rufe babinta har abada, kai ko itace autar mata ya hakura da damun kanshi akanta. _Dole ka koyi rarrashi!_ Toh waye zai lallab'a? Wacece take buƙatar rarrashin sa? Ai yana ganin iya Anne ce ta dace ya rarrasheta, "hmm." Ya faɗa da dan karfi, kafin ya cigaba da Nazarin abinda yake ganin zai ficce shi, yana ganin gwara ya amshi tayin matan da ake turo mishi zai fi mishi sauki da ace kullum ana samun matsala da shi ba dasu ba, duk da ba laifi sun d'an iya abincin. Shi matsalar shi wacce zata yi abinda da zai gamsar dashi yake nima ba wacce zai kare ruwan jikinta babu biyan bukata ba. Lumshe idanun shi yayi, bai buɗe ba, Karan bude kofar aka yi amma bai ji alamar za a shigo ba, dan haka bai bude idanun shi ba, amma yace. "Don Allah, na gaji!" Dan haka Fudail ya juya abin shi, bai ce kome ba. --- "A gaskiya Sultanah Hoyam ya kamata kiyiwa wancan shegen yaron me mugun taurin kai, magana shekara na uku kenan, kullum bin shi ake da mata yana wulakantawa waye shi? Meye yake ji da shi." "Mulkin da kike ji dashi mana, shi yake ji dashi a jikin shi. Ku kyale shi wannan lokacin ba zai tsallake ba, dole ya zab'i daya daga cikin matan kuma ya haɗa da Kwarkwarorin." Ajiyar zuciya Amir Hood ya sauke sannan yace mata. "Ga wani hikima me zai hana muce idan ya zab'i matar da yake so zai dawo kan kujeran shi" ya faɗa yana me kallonta. Shiru tayi cike da rudani, sannan tace musu. "Duk yadda kuka gani, idan haka shine Alkhairi ba shikenan ba, ya dawo kan mulkin shi ai ya shekara uku ai." Ta faɗa a sanyayye. Murmushi Amir Hood yayi yana shafa gemun shi, cikin nutsuwa domin ya harbo jirginta bata son rabuwa da mulkin, kuma zata rabu dashi ko taso ko taki, shi yasa ya shigo da batun, dan ta san dole wata rana zata ajiye mulkin shi yasa ya sako maganar kuma yaga yadda jikinta yayi sanyi, alamar zata iya sauka cikin lumana. ~~~ Tunda gari ya waye muka karya, sannan muka shiga sabon tafiya, gashi tafiyar ba ta, ruwa bace, dan haka yau babu wani hira, domin tun jiya da ta ga Uwaisul Qarni, take jin babu dad'i. Har suka kusan shiga garin SAMAIND wanda yasata bude tagar keken dokin. Sannan tayi musu alama da su tsaya anan wajen gari su kama masauki dake basu da yawa, su hudu ne. Dan haka koda suka isa asalin garin basu shiga masarautan ba suka tsaya a wajen masarautan suka kama masauki. Bayan sun ci abinci. Suka shirya tare da nufar cikin masarautar, domin binciken. Duk fuskar su a bude yake su uku, banda Ikram da ta rufe nata fuskar da bakin mayafi, koda ta shiga. Tun da suka shiga suke niman yadda zasu sami labarin Mehran, suka gama yawon su babu wani labari, suka fito. Washi gari ma haka suka gama yawon su babu labarin inda yake asalima kamar shakkar tambaya suke, a ranar da suka cika kwana uku da zuwa ne suka, fita kasuwa a hanyar dawowar su. Suka ji wasu matasa suna hira. "Eh Abul Bashar ke koya mishi karatu, yace an fidda shi daga cikin masarautan, shekaru uku da suka wuce, yana can darul AlHarami, yana zaune da dakarun shi. Sai bayi maza da mata." "Sultan MEHRAN din? Yaushe suka dakatar dashi?" Shiru mutumin yayi sannan yace. "Toh Allah kadai ya sani amma baya cikin gidan sarautar gaskiya domin d'an uwana yake koyar dashi." Wuce su muka yi sannan muka koma masaukin mu, kallona suka yi sannan nace musu. "Kusan inda aka kai shi kuwa? Hmm sunso kashe shi ne fa, domin gurin cike yake da kananun dabbobin masu cutar da d'an Adam" "Toh yanzun kinga ko baki kashe shi ba, dabobbi zasu kashe shi." "Insha Allah gobe garin SAMAIND zata amshi sakon mutuwar ka Mehran gani nan akanka." Na fada a hankali, --- Shayi yake sha kamar wanda aka kirashi zai amsa, haka yaji lokaci guda ya kware, tare da jin wani irin bugun zuciya, dafe kirjin shi yayi yana me jin kamar zuciyar shi zata buga, wani irin harbawa take da girgiza, kamar zata diro. Numfashin shi ma, bibiyu take fita kamar wanda yayi mugun gudu, yanayin shi yana wani irin sauyawa, lumshe idanun shi yayi lokacin guda Fudail da Sultanah suke mishi sannun, ajiye kofin ruwan da yasha yayi tare da kallon su. Idanun shi yayi ja, bakin shi har rawa yaƙe. "Kirjina kamar zai fashe zuciyata ta fado!" Ya faɗa a gajiye, rike shi Sultanah tai tana me jin kamar ta fashe da kuka. "Mehran, meke damun ka?" Ta tambaye shi a dame, murmushin karfin hali yayi sannan ya kalle ta, cikin girgiza kai alamun babu. Kasan ranshi sunan Ikram ce, take hawa da sauka kawai. Kwantar da kanshi yayi akan cinyar ta, yana jin kamar ya cire zuciyar ya huta da wannan tashin hankalin. Ya rasa ya zai yi da Ikram a zuciyar shi, ya rasa yadda zai daina jin ta tana motsa mishi zuciyar shi. Yaushe zai huta da kewarta? Yaushe zai daina najin tashin hankali akan ta? Yaushe zai daina zaman jiranta? Me yasa tayi tafiyar bazata da ruhin shi, Ikram ta gama dashi, yasan ko bai furta yana kaunarta ba, zuciyar shi ta gama furta mata, zuciyar shi ta gama amsar ta, toh me zai ce bayan shi kanshi bai da iko ku izinin sarrafa kanshi. Yarinya karama ta hana zuciyar shi hutawa, me yayi mata da zafi haka ya addabe shi? Me yayi mata ta hana shi sakat, Ya Allah ka bayyana min ita na tambaye ta meye nayi mata haka take son ganin karshe na. --- Ina kallon kowa ya kwanta, dan haka na dauki kayan da nake yawo dashi bakake, na saka sannan na nufi bayan masarautan, na shafa maganin maciji da kwari, na haura katangar, ina shiga na sake zarga igiyar da ya kawo ni cikin gidan, na kuma zargawa na sauka Ban tsaya na nufi can gidan da yake da mugun gudu, ina isa naga dakarun da suke tsaron kofar shiga, dan haka na, koma da baya, sannan na haura bishiyar da take jere har katangar gidan,, ina shiga gidan nan dirka ba, dai na koma bin katangar, sannan na nufi asalin saman gidan na haura, kafin na samu kofar da yake bude a sama, shiga nayi sannan na, na fara ƙoƙarin zare makamina. Ina shiga na same shi zaune, yana karatu, jikina ne yayi sanyin musamman jin muryan shi da take karonti suratul hajji, a hankali na isa bayan shi tare da ɗaukar wukar zan caka mishi a wuyar shi yayi maza ya rike hannuna lokaci guda, zuciyar shi ya shiga wani irin bugawa. Tare da murɗa hannun sai da ya juyar dani, anan na shiga kai mishi duka, tare da hargitsa ko ina da fada, Allah ya bani Sa'a na yanke shi a wuyar shi, sannan na samu na gudu, domin yana kai min mugun duka ne kamar zai kashe ni, ina guduwa yabi bayana, tare da haurawa ta saman gidan, babu ni babu labarina, tuni na isa inda nafi wayo, hannuna ne dai na targad'e, koda na isa gidan mu, kwanciya nayi tare da cire kayan dakyar saboda ciwon hannuna. "Mehran lafiya?" Sultanah ta tambaye shi, ganin jini na zuba a wuyar shi. "Wallahi hari aka kawo min, yanzun nan!" Kafin kace kwabo dakarun gidan sun bazama niman wanda ya shigo kisar, har gari ya waye babu alamar wanda yayi yunkurin kashe Sultan Mehran. --- washi gari da kaina naja hannuna, babu wanda yayi min magana a cikin su, dan sun san bazan yarda na dauki shawarar su ba, haka na wuni a ranar babu walwala, da dare ma basu bi ta kaina ba. ... Shiru yayi yana shafa wuyar shi, tare da kallon Fudail, wanda suke tattaunawa akan lallai dole a dauki mata a cikin gidan,domin basu. "Babu matakin da za a ɗauka, zasu kuma dawowa. Zanyi kokarin kama koma waye!" Ya fadi haka tare da rike inda zuciyar shi take bugawa, idan bai yi karya ba, zai iya cewa. Zuciyar shi tayi na'am da me kawo mishi hari, amma me yasa? Yaji ya damu da son sanin waye ne ya kawo mishi hari? Me yasa yake jin bugun zuciyar shi sama da kullum. "Bani ruwa!" A birkice suna mika mishi ruwan, ya sha sannan ya kama tari, me hade da ruwan jini jini. "Innalillahi wa'inna ilaihi rajioun, Fudail nimo mana likitan masarautar." Fita yayi tare da nufar masarautan can, ya dauko likitan, wanda yana zuwa ya saka hannun shi kan goshinsa, sannan ya kuma dafe kirjin Mehran din, kafin ya riko hannun shi, yana me kallon fuskarshi. "Fudail! Sultan MEHRAN yana fama da ciwon zuciya ne, wanda yake samuwa ta hanyar shiga damuwa da firgici,sai yawon tunanin abubuwan da suka faru, sakamakon rasa wani abinda yake so ko ya tashin hankali. Uwa uba, Soyayya tana iya haifar da ciwon zuciya ma. Sultan MEHRAN zaka sami sauki idan ka cire abinda kake b'oyewa a ranka, ko kuma ka rage yawan damuwa da tunani. Idan kuma zaka iya fadan matsalar ka babu damuwa." Lumshe idanun shi yayi sannan ya dauke kanshi ai babban abun kunya ce ya bude bakin shi ya gaya musu, yana tsananin kaunar Ikram, wai gwara ya bar zuciyar shi ta buga, akan ya furta wannan kalmar da zata zame mishi abin dariya daga kan shi har dangin shi, dan haka ya dauke kan shi bai ce musu kalla ba, tunda bawai maganar ce yake jin yinta ba, Sannan yadda ya fahimci bayanin likitan nan, yana daga cikin mutanen da so yayi musu mugun kamu, lallai so bata yi nisa adalci ba, yarinyar da ya gama cewa baya kaunarta, yau aji yayi amai ya lashe.... *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 25 Ina zai kai tilin abin kunyar da ya faɗa? Ya zai fahimtar dasu ba laifin shi bane na zuciyar shi ce da bata da adalci? Ina gwara ya had'iye kome koda haka na nufin ciwon da ke zuciyar shi itace ajalin shi. Da kunya ya bude bakin shi yace soyayya ce ta maka shi da kasa, da wani ido zai kalli jama'ar fadan shi, da wani bakin zai gaya musu ba yin shi bane zuciyar shi ce da bata san Yakana ba, kai tir da wannan kalama me sunan *SO*, bata mishi adalci ba. "Allah ya baka lafiya, ga magani nan za a baka naka sha, don Allah ka rage damuwa da tunani." Ya fada mishi, juyawa yayi tare da hada kayan shi, ya fita daga gidan. Jungu jungu suka yi tare da kallon shi. Lumshe idanun shi yayi yaki magana, dan gani yake kamar zasu kasance tsaf abinda yake damun shi. Shi yasa ya juya musu baya, dan baya son su karato abinda yake damun shi. ~~~ Da gaske Mehran ya targada min hannun, asalima irin targad'en nan na kan wuyar hannun ne, dan haka naji bakin cikin ainun. "Ikram me ya sami hannunki?" Murmushi nayi sannan na maida hannun na rufe. "Faduwa nayi?" Na fada a gakile, "Amma sai wannan bai kama da faduwa ba, sai dai ko an murɗe hannun aka yi, don Allah waye ya miki haka?" Tashi nayi zan koma cikin dakin. Suka sha gaba na. "Ikram! Kin fita daren jiya gidan Sultan Aamaan!" "Babu inda naje!" "Matsala baki iya karya bane dubi yadda fuskar ki yake nuna alamun karya kika yi? Idanun ki juyawa fa suke? Kalli yadda kike kyafta su, wallahi baki iya karya ba, kin yafi jiya ganin Sultan Aamaan ko?" Suka sani a gaba da tsokana, tare da cewa. "A haduwar farko aka targad'en hannun haduwar gaba, ba zata muku kyau ba wallahi!" Suka fada suna dariya, tsaki nayi tare da barin su a gurin ina jin haushinsu. Zama suka yi ina jin su, suna gulma ta, share su nayi ina kula da hannuna, domin bana son damuwa da zata kuma kara min ciwo na. Da dare ma, sun ta zuba ido ko na fita, suka ga ban nuna alaman zan fita ba suka hakura, dole suka kyale ni. ~~~ "Sannun Sultan Mehran! Ashe baka ji dadi, d'azun Darakshan yake sanarwar a fada." Murmushi yayi sannan ya kalle su. Fuskar shi a sake kamar babu abinda yake damun shi, nan kuwa kasar zuciyar shi, Ikram ce take yawo har da ingiza shi akan a duba garin ko anyi baƙi daga wani gurin. Ya bude baki yayi magana yana ganin kamar wani katon aiki ne, shi yasa yake bin su sa ido, shigowar Sultanah ya sashi mik'ewa zaune. "Anne!" Wani irin dad'i taji a ranta,. Musamman yadda yake kiranta da Uwa, zama tayi a bakin gadon. "Mehran! Ga maganinka, sannan don Allah meke damunki? Aamaan ka gaya min don Allah meye matsalar ka?" Murmushi yayi sannan ya juya yana kallon Mahlika da take dauke da tiren maganin, a yanzun yana bukatar mace a kusa dashi, dan haka ya dauke kanshi dan baya jin kome akan ta, duk da yana bukatar mace, baya jin Mahlika takai matsayin Ikram. "Miko min na bashi yasha." Ta mika mata, hannun. Cikin girmamawa ta bawa Sultanah. "Anne barta ta bani!" Ya fadi hakan cikin wani irin yanayi, da ta fahimci yana bukatar nutsuwa, dan haka na shafa kanshi tare da cewa. "Ko Mehran zai barni na kintsa mishi ita?" Kasa d'ago kanshi yayi domin yana matukar jin kunyar ta, ganin bai mata magana ba, yasa ta ajiye maganin sannan suka fita. Bayan wasu mintinan, sai gata ta dawo d'akin. Murmushi yayi sannan yace mata. "Zo nan!" Durkusawa tayi a gaban shi, murmushi yayi sannan yace nuna mata tiren maganin, bayan ta bashi ya sha, sannan ya ce mata. "Zaki min wani aiki ne!" Nutsuwa yayi tare da kallonta, saka hannun shi yayi a haɓɓar ta, tare da d'ago ta. "Zaki shiga cikin gari" Kura mata ido yayi sannan ya kuma kai kanshi fuskarta, a hankali yake yawon da hannun shi cikin jikinta, tare da kai kunnen ta, tare da faɗin. "Kina da kyau!" Wani irin ajiyar zuciya ya sauke, domin kuwa ta shiga cikin wani irin yanayi, tare da rike shi. Wato Mehran wani irin mutum ne da ya san kan tafiyar da mace, domin cikin siyasa da hikima yake birkita mata lissafi,kafin ya bata aikin da zata mishi bayan ya kai goshinsa kan gefen fusakarta. Yana goga hancin shi har zuwa wuyarta, rike rigar shi tayi tare da sauke wata irin ajiyar zuciya. "Sultan!" Ta kira sunan shi, tare da shigewa jikin shi. "Kinji abinda nace miki" "Eh Sultan naji kuma Insha Allah zan yi yadda kake so." Shafa fuskarta yayi tare da cewa. "Maza yarinyar kirki, jeki maza." Jikinta na rawa ta mik'e, kamar zata fadi, fisgo ta yayi tare da cewa. "Zo nan!" Kafaffunta ne taji kamar ba zata iya daukarta ba, shimfid'a ta yayi tare da gyara mata kwanciya, a jikinshi. Wani irin yanayi yake ji, tabbas idan yayi haka kamar yaci amanar zuciyar shi ce, dan haka ya mata masauki a jikin shi, tare da shafa bayanta, har ta fara sauke ajiyar zuciya, kafin ya d'ago kanta. Ganin yadda idanunta tana juyawa, shafa fuskarta yayi tare, da shafa bakinta tare da kallon yadda take kuma tsima, da mugun sha'awar shi. "Ikrammmmmm!" Ya ja sunan kasar makoshinsa, kafin ya d'agota yace mata. "Maza ki tafi inda na Turai" A hankali ta sauka daga gadon, tabbas tana bukatar shi, amma anya jin koda wasa ba zai bata wannan damar ba. Domin wallahi mace daya zai iya bata kanshi da ruhin shi, gangan jikin shi ta da ruhin shi mallakin Ikram ce, dan haka yake jin ba zai iya sake ya bawa wata mace ba. Ita daya ce nata ne kuma baya jin zai bata kuma. --- Gyara zaman igiyar da na zarga hannun a cikin shi nayi ina rintsa idanuna, ga wani uban zufar da nake kamar na had'iye gaushi. Kallon hannun nayi tare da kallon yadda hannun yayi fushi, tabbas sai na mishi illa. Domin bazan tab'a daukar wannan kasadar ba. Kallon juna muka yi da Izmah, murmushi tayi sannan tace min. "Gaskiya Sultan Mehran ya iya mu'amala, kan Uba yadda ya daki hannun nan bana jin zai kuma moruwa." Kwalla ne ya cika min idanu, na miki ina huci. "Kinga Mehran bafa banza Allah ya bashi duniya ba, wallahi baki isa ba, ba irin sakarkarrun da kike musu kisar gilla bane, dan haka karki kuma barin kuyi gamo na biyu, dan na rantse zaki sha mamaki!" Zuɓewa nayi kasar d'akin, kwalla naso zuba min nace. "Billahi azim! Idan na kuma zuwa gare shi sai na karshi!" "Me yasa baki karshi ba? Hmm! Ki daina zafaffawa fa" "Fitar min a daki bana son ganin ku!" Me fada da karfi ina me juyar da kaina, kwalla na zuba min. Domin ban tab'a faduwa irin na yau ba, Mehran ya hanani samun galaba akan shi, goge kwallar nayi dan nan da kwana uku zan koma mishi. ..... A hankali muka sami kwana uku babu wani abinda zan kira na jin zafin Mehran, sai ma tsanar shi da yake kuma samun zama a raina. A ɓangaren Mahlika kuwa wani irin haukacewa tayi da kaunar Mehran, domin idan ta zauna ji take kamar zata gigice. Kamshin turaren shi ya rike kayanta, har yau tana jin hancin shi da yake gogawa a wuyarta, wani irin shauki take ji, bata san lokacin da kuka ya kwace mata ba, domin yau kwana uku tana zaga cikin gari domin nima mishi labarin bakin da suka shigo babu labarin dan kullum SAMAIND bai rabuwa da baki, dan haka ta koma yau zata gaya mishi babu bakin da suka shigo garin. Sai dai ko zata mutu zai ta haɗa shimfid'a da matar da zai kira tashi, kamar yadda zai yi da Kwarkwarorin shi haka itama zata bashi damar yayi da ita, ba zata iya barin ya subuce mata ba, dan haka ta kulla iniyar haka a ranta, tare da zuba idanunta akan shi da kuma matan da zasu zo gare shi. Wannan shine alkawarin Mahlika, kamar yadda mahaifiyar ta, taso yi da Sultan Abdus Samad, yau itama tana kuma alkawarin zata gwada sa'ar ta akan Mehran. (Inda ba kasa nan ake gardaman kokuwa 🤔) ~~~ Ba haka yaso ji daga gare ta ba, kauda kanshi yayi daga kallonta, sannan ya mike tare da cewa. "Jeki!" A hankali ta juya tare da barin d'akin da sauri, tana jin kamar tayi kuka, amma kuma bata da halin haka, domin ita bata ki yace tazo ta kwana dashi ba. A falon kasa ya sami Sultana, "Akwai abinda ya shiga tsakanin ku ne?" Cikin girmamawa, ta sunkuyar da kanta sannan tace mata. "A'a!" Sai dai kuma ba haka taso cewa a'a ba, domin taso ace tace eh domin kuwa bata ki, tayi karya akan wani abu ya haɗa su ba, toh amma sanin cewa ba yarima bane sarki ne guda wanda haka zai iya janyo mata rasa rayuwarta yasa ta amsawa da babu. Domin wallahi ba a Samaind zaka yi wasa da rayuwarka ba, ai ko kura yasan gidan me babban sanda. Safa da marwa yake yana jinjina qarfin halin wanda ya kawo mishi hadi matukar ba ikram bane, toh tabbas babu aikawa yayi biyar cutar shi. Wato yayi niyyar mishi kisar gilla ne fa, domin yayi imani da wukar da za a caka mishi, daukar yayi yana murmushi, sannan ya ajiye wukar tare da kura mishi ido, yayi tare da cewa. "Koma waye zai kuma dawowa!" Dan haka ya dage kirjin shi da yake mishi zafi kadan, sabida damuwar da ya saka na kwana biyu, sakamakon binciken da ya tura Mahlika. Wasa wasa sai da hannun yakai sati daya sannan na iya juya takobi, dan haka wannan karon ina jin sauki na sake murmushin mugunta, sannan na nufi inda kayana suke na ware su. Sai da na bari dare yayi tare da rabawa sannan na nufi SAMAIND. Tafiyar minti arba'in ya kai ni cikin Alharami, ban tsaya bin wancan salon ba, na bi ta bayan gidan, sannan na hango shi tsaye a jikin tagar dakin shi, dan haka na shiga ta babbar kofar da yake sama, sannan na ciro gatarin da nazo dashi. Jin karar cire karfe kawai yayi bai juya ba. A yadda na kai farmaki ya bani mamaki domin kuwa kai min duka yayi tare da dukar kafana ma zube, sake kai min duka yayi a cikina, na hantsila can bakin kofar, kafin na sami Arzikin fita yayi nasarar dukar bayana, na zube a gurin,. Dakyar na mike dan ya tsaya tare da raba kafar shi a kaina,.kwashe shi ya fadi a kaina. Kokarin kwace kaina nake shi kuma yana ƙoƙarin gano fuskana, ganin haka yasani kaiwa abin shi duka, ya tintsira can, yana nishi. Sake mik'ewa nayi ya finciko ni, aikuwa na sake kawai maranshi duka, sai da ya sake wata irin gurnani, wanda ya sani razana. Kamar zan tsaya sai kuma na fita cikin farin ciki, finciko Ni yayi tare da matse ni da kasa, ina ƙoƙarin mik'ewa. "Waye kai?" Ya faɗa tare fisgar numfashin, sake kai mishi duka nayi a cikin shi, wani irin gurnani ya kuma sake min, tare da da cewa. "Meye nayi miki?" Da sauri na kwace kaina. "Ikram!" Tsigar jikina ne ya mike sakamakon jin yadda ya ambaci sunan, da sauri na kwace kaina baki daya bayan na kai mishi duka, a gefen cikin shi. Na fita na barshi dan nasan tabbas sai dai gawan shi ba dai wani ba, na gama da babin Mehran, tunda na samu na bar gidan, haka kawai naji zuciyata ta rabu cikin wasi-wasi, lumshe idanu nayi lokacin da naga tuno abinda yayi min, na tarkato na dawo gida. Duk lokacin da na tuna halin da na barshi sai naji kamar baka kyautattawa kai na ba, taya ya fahimci nice? Taya na san nice? Me yasa ya gane Ni? Babu wani dalilin da na bari da zai fahimtar da nice, domin ko turaren na daina shafawa, gudun kar ja fada cikin matsala, sai gashi ya gane ni. *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 26 Tunda na shiga cikin gidan, na zauna dab'as a kasa tare da cire bakin mayafin fuskana, ban tab'a jin nayi kuka ba, bayan daukar fansa sai yau, zuciyata tayi rauni ainun, naji a karan kai na ban kyauta ba,. amma kuma yadda nake jin zan amshi kuskurena ne bana jin zan amsa cikin sauki domin nasan nayi laifi babba. Amma kuma ya cancanci haka ne, ya cancanci haka daga gare ni, haka da nayi mishi shine hukuncin da ya karb'a amma kuma na kashe shi. Na kashe Mehran. Wani irin bugun zuciya ta take yi, tare da jin kamar zata fadi kasa, kuka nake wanda ya farka dasu daga barci suka tawo kai na, zuba min suka yi bayan sun ga jini a bakina. "A ina kika ji ciwo haka?" "Izmah! Nimrah na kashe shi!" Bakin su a haɗe suka tambaye ni. "Waye kika kashe?" Cikin mugun kuka nace musu, "Mehran!" "Au shine kike mana kuka? Toh an kin kyautawa kanki" kamar hadin baki suka barni zaune ina kuka. Dan tausayi sun ji amma bakin cikin taurin kaina ya saka suka juya min baya. Nayi kukan da tun bayan rasuwar Iyayena ban yi shi ba, kai ko mutuwar Airan banyi kukan ba kamar yadda nake kuka akan na kashe Mehran, ina zaune a gurin har kusan tsakiyar dare, ga garin yayi wani irin sanyi. Kwanciya nayi, ina sauke ajiyar zuciya kuma idanuna basu fasa zubda kwalla ba. Ina tuno lokacin da muke tare kafin mu zama abokan gaba. Duk da bana jin dadin shi, amma kuma yaki barin koda wani abu ya cutar dani, yana tsare lafiyata da rayuwata, Yau shi na kashe sarki guda, wanda ba a tab'a yin matashin sarki irin shi na, shine yazo a karnin na baya baya, me cike da ban mamaki. Matashin da ya haɗa kome ma rayuwa na kashe shi, me yasa nake da bakar zuciya ne? Me yasa ban Nime mutanen da suka kashe Airan ba? Amma nazo.. _Kashe miki miji yayi a daren ranar auren ku! Shin zaki yafe mishi? Idan da ace kun zama abu daya a wannan daren da yanzun kina dauke da Yaron ko yarinyar Noman, shin ke kina ganin ya cancanci a yafe mishi._ Wani irin kuka ne ya kuma dawowa min, dakyar na tashi nayi sallah asuba. Sannan na koma na kwanta, ina jin zuciyata bata min dad'i. Ba laifi bane dan na ɗauki fansa amma kuskure na aikata na kashe babban mutum irin Mehran. ... Bayan tafiyar ikram, Fudail yaga lokacin da aka sauka a katangar gidan, amma bai kawo kome a ranshi ba, dan haka yacewa dakarun. "Ku shirya an kawowa Sultan Mehran hari! Bari na shiga cikin gidan." Da gudu ya shiga cikin gidan, koda yazo ma, ya sami Mehran kwance cikin tashin hankali da gurnani, Kiran Sultana yayi suka kashi dakin shi aka shiga bashi taimakon gaggawa. Fita Fudail yayi tare da dauko likitan masarautan, aka zo dashi. Ya kusan kwana akan Sultan Mehran. Dan ana kiran sallah farko yana fitowa daga d'akin shi. "Ya jikin shi?" Inji Sultanah ta tambaye shi, ajiyar zuciya yayi sannan yace mata. "Alhamdulillahi! Da sauki sosai, sai dai ya sami barci? Taya aka yi Sultan MEHRAN ya fuskanci irin wannan harin? Anso kashe shi ne fa, domin dukar da aka mishi kan halittar shi na d'a namiji aka dake shi zuwa marar shi, sai dukar da aka mishi a kirjin shi don Allah ku kula" Shiru kowa yayi, ran Sultanah ya b'aci domin gani take a garin shegen bin mazan shine ya hadu da shu'umin da yayi mishi wannan dukar. Bayan tafiyar likitan kacokan ta dauki laifin ta daurawa Fudail, Domin gani take shi yake taimakawa Mehran yake sheke ayarshi idan ba haka ba, taya zai iya dauko namiji har zuwa sama, dan haka tayi tafiyarta dakin ta bata kuma zuwa gurin shi ba, sai da gari ya waye tangaran, sannan ta shigo dakin shi, yana ganinta ya sunkuyar da kan shi. "Meye amfanin dakarun da aka zuba su a kofar shigowa? Meye amfanin zamanka jarumi? Meye amfanin bibiyar maza yan uwan ka? Ka ga kenan babu, ba zan hana ka abinda ake so ba, amma matukar ina da iko akanka na kuma ganinka da namiji. Gawata zaka dauka, shine karshen biyan laifin da nayi maka tunda narasa da yadda zan biyaka." Daga haka ta fita daga dakin, lumshe idanun shi yayi tare da kallon Fudail da yake mika mishi abinci. A hankali ya karb'a yana ci bai koma d'ago kanshi ba yacewa Fudail. "Tana raye"ya faɗa tare da d'ago kai, yana kallon bakin kofar shigowa dakin, da sauri Fudail ya rufe kofar, sannan ya dawo gare shi ya d'an sunkuya yana fadin "wacece take raye?" "Yarinyar da tabi SAURAYINTA!" Cikin wani irin azama ya d'ago kanshi, yana me jin ina zai kyaleta ta rayu, juyawa yayi zai fita yace mishi. "Ina zaka?" "Zanje na sare kanta!" "Zata dawo, sai dai bana son Anne ta ji labarin, domin zata iya tsaneta domin idan ta tsane ta, ba zanji dadin ganinta a tare dani ba, kuma itama Anne ba zata ji dadin ganin mu a tare ba. Tunanin ta ya bata cewa ni nasaka a kashe shi, ita kuma tazo daukar fansa, domin irin yadda take niman hanyar da zata kashe ni ba na kananun makasa bane, nasan na koya mata kare kanta, amma ban zata a kaina zata kare ba, na zata zata iya tsayawa kanta ne. Alhamdulillahi tunda yana cikin koshin lafiya, babu abinda ya same ta,. mahaukaciya ta kara girma da taurin kai" ya faɗa yana dafe kanshi sakamakon yawan maganar da yayi, sannan ya lumshe idanun shi, yana jin wani irin abu a ranshi, murmushi yayi sannan kalli Fudail da yake kallon shi cike da mamaki. "Na zare ko?" Girgiza mishi kai yayi sannan ya maida kanshi yana cewa. "Anya itace kuwa!" Murmushi yayi sannan yaja bakin shi kamar ba zai magana na,sanan ya d'ago kai yana kallon shi..yace mishi. "Na tab'a maka karya ne? Na tab'a maka musu ne? Toh ka saka ido nan da kwanaki zata dawo, kuma zaka sha mamaki." Kasa magana yayi yana kallon Mehran, dan gani yake kamar na gaskiya bane, shi yasa ya dauke maganar a matsayin mara muhimmanci. Shi kuwa Mehran, murmushi yake lokaci zuwa lokaci, yana me kallon kofar yadda suka tukwaikuye kan su, sai ya sake murmushi. Yana jin babu wani ciwo da yake damun zuciyar shi sai ta begen ya kuma ganin ta,.da gefen fuskarta ya sani yanzun kuma zai ganta baki ɗaya. Gabaki daya ya nemi ciwon zuciyar shi ya rasa, dan haka Yacewa Fudail. "Ka taya ni rike sirrin ta, don Allah karka sake wani yasan meye ya faru, idan ba haka ba zan dauki mataki mara dadi akan kowa, dan haka ka kyaleta zata kuma dawowa haka da tayi ta nuna min ita jaruma ce, amma zan mata wani abu da zata cigaba da farin cikin har karshen rayuwar ta." Kasa jure wannan yanayin yayi ya juya ya fita, bai kuma bin takan Mehran ba, bai tsaya ba, sai wajen masarautan, ya gama yawon duniyar nan bai gansu ba. Sannan ya dawo gida. ~~~ Ranar zazzabi ne ya rufe ni me mugun zafi, haka suka yi ta fama dani, tare da bani magani. Wajen karfe ɗaya na rana, na ji dadin jikina har na tashi na gabatar da sallah bayan nayi wanka, abinci suka kawo min na tab'a kadan sannan na koma na kwanta. "Gaskiya irin zuciyarki ko a tarihi b'an taba ji ba, kiyi kokarin koyan hakuri ko dan gudun aikin dana sani, Allah kadai yasan abinda kika mishi da Yasaka ki kuka haka," inji Izmah, kasa magana nayi ina kallonta kafin nace mata. "Kin sami labarin ya mutu ne?" "Kai ina bana tunanin ya mutu domin da kinji gaba-daya Samaind ta dauka, kuma Kinga" "Izmah barci nake ji" na fada mata a fusace, domin nayi mamakin da yake raye, wani sabon bakin ciki ne ya kamani, tare da kara jin lallai sai na fille mishi kai zan sami nutsuwa a raina, koda kuwa ranshi na karfe ne, dan haka na d'aga kafa na kwana biyu. Ina sauraron naji ance ya mutu, amma shiru kake ji. .... A can kuwa tara dakarun yayi tare da basu hutu kwanaki biyar zuwa bakwai, domin yana son ya kare mata kallo ne yadda zata shigo gidan, babu masu tsaro, Sultanah kan fushi take dashi, tare da dauke kanta akan shi, duk da yana jin jiki amma haka ta cire tausayin shi ta daina shiga harkan shi, a cikin kwana biyar yaji babu dad'i, amma Alhamdulillahi, dan yaji sauki sosai. Har kwana uku. A ranar na biyar na shirya na dauki karamin wukar yanka tuffa, na tafi dashi ba tare da tsoro ko fargaba ba, koda za a kamani ban damu ba, kawai kaina na sani. Lokacin da na isa gidan naga babu kowa a bakin kofar dan haka na haura katangar kamar yadda na saba, bayan na gama hawa kawai na hango shi a bakin kofar yana zaune tare da kallona, har na isa inda yake. Duk da a tsorace nake, amma haka bai sani na juya ba, sai ma kara kusantarshi nake. "Me kike bukata! Shayi ko Ruwa?" "Ranka!" "Toh Ikram zoki dauka idan har haka zai baki damar samun farin cikin ki har abada, amma da sharadi. Kinsan ba zan tsaya na barki ki kashe ni ba, zan yi kokarin kare kaina, san haka idan kika yi nasarar kashe ni ina miki fatan Alkhairi." Ya faɗa a sanyayye, kallon shi nayi sai kuma naji ban yarda da abinda yake nufi ba dan haka, na kasa aiwatar da kome, takowa yayi har gabana. Sannan ya saka hannun shi dukka biyu a k'ugun shi yana kallona. Cikin zafin nama na kai mishi wukar kirjin shi. Da bayan hannun ya kare, yana murmushi me sauti, a hankali na kuma juyawa zan kai mishi duka ya kare, tare da taka kafana, sai da na sake yar kara cikin wahala, gyara tsayuwar shi yayi sanan ya kalle ni. . Yadda yaja ya tsaya da nasan ma'anar haka da na gudu abina z amma shegen taurin kai da ya addabi rayuwata, ya sani kai mishi duka, tare da kai wukar zan soka mishi, daukata yayi, cikin wani irin yanayi, sannan ya juyar dani yana me hada ni da bango, kamar wacce aka sani na makale mishi da kafaffuna, yadda ya jingina ni, kirjin mu yana gogan juna ya sani kai mishi duka a fuska. Damtse na ya daka. Yake naji kamar an kwashe min da wani kuzarina, daya gefen ya daka shima haka, kifa kaina nayi da goshinsa. "Ina kika shiga?" Ya tambaye ni bayan ya kai ni dakin shi ya rufe, ajiye ni yayi a gadon, sannan ya juya tare da dauko min ruwa, sannan ya mika min kasa karb'a nayi shi da kanshi ya shayar dani, kallon juna musu yi bayan na kumshe ruwan a bakina, yana ajiye kofin ina fesa mishi ruwan a fuska, saka hannun shi yayi tare da cire abinda nake rufe sauran fuskana. Yana murmushin mugunta, tare da kallon fuskana, ajiyar zuciya yayi ta saukewa, bai kuma min magana ba, har sai da yaga na fara ƙoƙarin mik'ewa sannan, yace min. "Toh yanzun meye laifina? Da ake kawo min wannan harin?" Kasa magana nayi domin dai yada yake natsuwa jikina ya soma razana ni, a hankali yake balle rigar shi. Kallona yake har cikin idanuna, had'iye yawu nayi tare da cewa. "Karka kuskura kace zaka tab'a ni, karka yarda kace zaka min abinda ban.." Hannun shi naji akan cinyata, duka na kaiwa hannun ya janye tare da ture ni, yana murmushi yace. "Ki koma ki shirya Mehran kainuwa ne dashen Allah, babu wanda ya dasani sai Allah, Ikram indai har zan baki damar ki huce haushinki ai kin san ba karamin dalili bane, dan haka bana son na kuma ganinki, a cikin Samaind. Idan kuma na kuma ganin ki, zan ajiye kome zan baki kyautar da bai riske ki ba " "Kai waye da zaka ce min na bar Samaind? Ai nazo Samaind kenan sai na kashe ka zan bar kasar nan idan yaso kun kama ni karku min ta dad'i....." *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 27 "Mhh!" Yayi murmushi me sauti sannan ya kuma ware idanun shi akai na, kafin yace min. "Har yanzun ke baiwa tace, dan haka na baki damar barin SAMAIND" "Ni kuma har yanzun niman ranka nake na baka damar kayi rayuwa kafin na dawo gare ka!" Amadadin naga fushi ko fusata haɗe da b'acin rai, sai naga kamar babu abinda ya dame shi. Hannun shi ya kai wuyana, tare da kallon yadda nake kokarin kwace kaina. Matse ni yayi da bango, yana kallon cikin idanuna kurawa juna ido muka yi, ya sake murmushin da zaka Fahimci farin ciki ne zalla a ranshi, a hankali ya cigaba da kallon cikin idanuna. Ban san lokacin da kasala tare da kaifin idanun shi suka saukar min ba, tsintar kai na nayi da lumshe idanuna, na kifa kai na a kirjin shi, ina me rintsa idanuna kamar zan fashe da kuka. Hannun shi ya kai haɓɓa na, tare da d'ago kai na, had'a fuskar mu yayi yana sauke ajiyar zuciya. "Bana son rashin da'a." "Idan nayi maka zaka yanka ni ne?" Janyewa yayi daga jikina, tare da cewa. "Ina lafiya, bazan iya aikin masu hankali biyu ba," da gaske Mehran Magana ya gaya min, dan haka na juyar da kaina, tare da kokarin kwace kaina. "Me yasa kike kokarin gudu?"yadda yayi maganar muryan shi can ƙasar makoshi sai da ya kara jefani cikin wani irin kasala, domin yayi maganar ne tare da fesar da iskar bakin shi, a wuyana. Kokarin kwace kai na nake , amma na kasa domin kuwa matse ni yayi sosai, numfashina yana fita sama sama. Shafa fuska na yayi tare da kallon fuskana sa nake kokarin b'oyewa a kirjin shi.domin wasa gaske Mehran sai da ya kashe min jiki murus. Da sauri na d'ago kai nayi cikin wani irin rawan jiki. "Hmmm! A da kina amfani da miski, me yasa baki amfani da shi yanzun?" Yayi maganar kama wanda yasha abin maye. Hannun shi ya kai fuskana tare da tallabo fuskar. Hada bakin mu yayi tare da lumshe kaifaffun idanun shi. Kasa motsi nayi domin ji nake numfashina yana niman barin jikina, hankalina yayi mugun tashi. Idanuna sun gaza fidda kwalla, rike rigar shi nayi ina sauke ajiyar zuciya. Tunda Uwata ta haife ni ban tab'a sanin akwai irin wannan abun ba. Sannan banda Abrad ban tab'a ganin wanda yayi min irin wannan abun ba, cikin hikima da dabara, sai da ya min masauki a gadon shi sannan ya shiga sumbatar ko ina a jikina, tare da rawan jiki, kamar zan gudu daga gare shi, goga kanshi yake daga wuyana zuwa kirjina, ban san lokacin da na birkice mishi ba, kuka ne ya kwace min, tare da rike hannun shi. "S...." Hada bakin mu yayi, babu duka babu zagi sai da naji kamar bakina da harshe na, rike hannun shi nayi. Ya bude idanun shi fess a kaina, tare da sumbatar wuyana. "Karki kuma yunkurin zaki." "Ka cuce ni! Allah sai ya saka min." "Ai haba? Toh bari mu karasa bidirin a gadon." Zaro idanu nayi tare da fashewa da kuka, ya kuma cigaba da jefani cikin tashin hankali, dakyar ya kyale ni, lokacin aka kiran sallah farko, har ban daki ya kai ni, wai zai min wanka bayan na san ba zan iya ganin kato a tube ba. Sai da ma bari ya shiga kwarin wankar na juyo tare da ɗaukar kayana, tare da barin gidan baki daya. Murmushi yayi domin ko babu kome ya cusa mata tsoro ko ba dukkan ba, wanka yayi wanda rabon shi da yayi hakan tun kafin ya kwanta jinya, ga wani irin iska da yake shigan shi ta ko ina, kaya ya saka tare da gabatar da sallar nafilla, sannan ya fita zuwa masallacin, suka yi sallah. Anan ya koma gefe suka shiga karatun, dan gari ya waye. Duk wanda ya san Mehran sai ya gane yana cikin farin ciki da nutsuwa. Har ya gama karatun, sannan ya nufi gida, koda ya shiga ya sami Sultana tana ta famar nuna yadda za a jera abincin, fuskar shi a sake ya gaishe ta, sannan ya juya ya nufi sama. "Yau ba zaka karya bane?" "Anne kina kirana ne" ya tambaye ta cikin fara'a, yayinda Narjis take kallon shi sosai, nuna mushi tabirin tayi da ido, da sauri ya dauko tare da zama, sai dai duk abinda yake idanun su yana kanshi domin ya kasa boye farin cikin shi. Da yadda yake ciki. Duk wanda ya kalle shi dai ya fahimci, yana cikin farin ciki ainun, duk da ba hira yake ba, amma baya minti biyar bai tsaya ya kalli abincin sannan ya kuma sake murmushi, gabaki daya ranar sun kasa fahimtar kome akan shi babu fushin nan da dakewa, babu dogon miskilancin, sai ma wani irin yanayi na ban mamaki, wanda babu wanda ya sanshi da ita, magana akan aure tare da bawa Fudail labarin ai tazo, kuma sun kusan raba dare suna tare, da farko Fudail bai yarda ba, sai da ya hade rai sannan ya kuma dawowa ya nuna amincewar shi. ~~~ Da bakin ciki da kuka tare da nufar gidan, a hankali naji ina son ganin Uwaisul Qarni, har na isa gida, na sami Izma zaune. Zama nayi tare da dauke kai na, dan gani nake kamar zasu karanci Iskancin da wancan sikagon yayi dani, dan haka na shiga ban daki nayi wanka tare da rage kazamtar jikina,ina fitowa na gabatar da sallah nafilla da sallah asuba, sannan na kwanta wani barci me cike da gajiya suka dauke ni, sai dai ban yi nisa ba, na farka sakamakon ganin Uwaisul Qarni. "Bilqisul Ikram! Ba zaki ajiye kayan yakinki da Mehran ba? Ko kin fi son kullum kina ganin shi cikin damuwa ne?" "Kashe min miji yayi fa?kuma na yafe mishi?" Kura mata ido yayi, da zata ga halin da rayuwarta yake ba zata so d'aga hankalin ta akan Mehran ba, sam bata cikin nutsuwa baki daya, matsalar jinin da ta zubda ya fara bibiyarta, bai ce mata kome ba, sai Addu'o'in da ta tofa mata a cikin ruwan sha, ya mika mata. "Karki sake yunkurin cutar dashi! Idan kika Kuskura kika d'aga hannu domin cutar da shi,, ina me baki tausayin abinda zai biyo bayan, domin kina gab da zama mara amfani." Murmushi nayi tare da bude baki zan ce mishi. Wani abu kawai ya kalle ni tare da shafa fuskana,. Komawa nayi na kwanta, ban farka ba sai kusan azhar, nayi wanka da alola, nayi sallah azhar. Ina idarwa na juya tare da kallon Izmah da Nimra, suna musu. "Yawwa Ikram, nace ba kin hadu da sarakunan larabawa babu iyaka wani sarki ne yafi burge ki da mulkin shi? Ni dai nace ina ga Sultan Mehran yafi sauran," "Ni kuma nace mata na tab'a ganin Amir Rahil, sau daya a wani tafiyar mu aikin hajji." "Duk cikin su babu wanda ya kai Mehran d'an Abdus Samad kyau da jarumta, sai dai mugu ne na gaban kwantaccen" yadda nake gaya musu halin Mehran da haduwar shi. Yasa su sake baki tare da cewa. "Amma taya kika iya rike dabi'ar shi haka? Sannan kuma karki manta da cewa makiyinki ne fa?" Wayo kunya ne ya kama ni, wato jiya inda Mehran ya kai ni ya sani kasa Fahimtar kome sai halin shi da nagartan shi. Na kasa fadar laifin shi, dan haka na juya na kwanta ina cewa. "Ba shi nake magana akan shi ba, Ni akan Amir Rahil nake magana," na fada. "Wai daga baya kenan, yarinya kin amayar da abinda yake ranki." "Bana son shashancin, ki fita bana son ganinku." Dariya suka saka min, sannan suka fita ni kuma na shiga jin babu dadi meye zanyi da mugu, haka na wuni cikin daki da dacin rai. .....Bayan kwana biyu. Ga baki daya Sultan Mehran ya kasa samun nutsuwa, burin shi dai ya fito gari ya ga Ikram, dan haka ya shirya cikin shigar badda kama, shida Fudail suka fito garin. Haka suka yi ta bin gidajen baki da suke wajen gari, har Allah ya kawo shi gidan da Ikram take, suna can wani gidan da babu alamar akwai mutane a gidan, daga bakin kofar shiga gidan ya hangota zaune tayi tagumi. A hankali ya shiga cikin gidan bata sani ba. Dai dai fitowar Izmah. "Kana niman wani ne?" Ta tambaye shi. Cire rigar jikin shi yayi da badda kamar da yayi ya kalle ta, sannan ya juya ga Ikram da bata san dashi ba ma. "Yallabai kai ne Sultan Aamaan Abdus Samad Mehran?" Ta faɗa bakinta da muryan ta yana rawa, kamar zata fashe da kuka,karamin murmushi yayi mata sannan ya kalli Ikram da bata san suna yi ba. "Barka da zuwa Yallabai ka shigo gidan mana" "Hmm! Nan ma ya isa" "Ke! Tunanin me kike? Ga Sultan nan" kamar wacce take mafarki hana na farka ina kallon su, shigowa Fudail yayi ya zuba min ido. Kallon shi nayi tare da sake mishi murmushin jin dadin ganin shi. "Yan uwan Fudail" "Ikram kece a Samaind?" Yayi kamar bai san abinda ya faru ba, murmushi tayi sannan tace mishi. "Gani nan Fudail" nan hira ya kwace a bakin su, tare da Mantawa da Mehran a gurin, wani irin hade fuska Mehran yayi tare da zabgawa Fudail harara,ya juya ya wabi b'ata rai. Yana kallon gidan, tare da cewa. "Hmm!" Ya faɗa tare da fidda wani irin nishi, da sauri Fudail ya koma waje. Ita kuma makira tace mishi. "A'a ka shigo gidan kaci abinci da ruwa!" "Kai basamuden mutum! Jeka abunka bari muzo tare domin Sultan yana son hutawa a cikin gidan." Izmah taja hannun shi suka fito daga cikin gidan, suka barsu a tsaye. Takowa yayi gabanta, tare da jan kumatunta yana fadin. "Karki kuma mun abinda kika yi" "Toh Ubana!" Buge min baƙi yayi, tare da kallon cikin idanuna, kasa nayi da kaina, tare da wasa da yatsuna, *Duk ranar da na sami dama sai na aikaka garin da ba a dawowa* D'ago kai na yayi tare da kallon cikin idanuna, sannan ya hura min iskar bakin shi me dauke da kanshi y'ay'an itacce. *Me yasa ba zaki Fahimci abinda nake tare da shi ba? Me yasa ba zaki gane girman ki a zuciyata ba? Me yasa kike wahalar da zuciyar da bata dauke da sharri sai Alkhairi?* Janye hannuna nayi daga gare shi sannan na dauke kaina zan fita, yayi maza ya riko hannuna, ya juyar dani, bayana yana kwance a kirjin shi, hannun shi ya sarkafe da hannuna ya manna akan cikina, tare da riko daya hannun ya saka akan cikina ya zarge ni a kirjin shi. Kanshi a bisa wuyana, yana sauke ajiyar zuciya akai akai. _Na tsane ka! Bana son ganinka? Akan idanuna kace bani da daraja! Sannan ka kashe min Mijina! Mehran nice ajalinka, mutuwarka a tafin hannuna yake_ Na karshe da shashekar kuka, tare da kokarin fita a jikin shi. "Ki gaya min meye laifina?" Cikin fushi na kwace kaina, tare da juyawa ina kallon shi. "Karka kuma takowa inda nake! Me yasa ba zaka gane bana son ganinka a rayuwata ba? Kai abin so ne? Waye ya gaya maka zan tab'a kaunar ka? Toh ko maza sun kare gwara na koma ga Allah babu mijin aure ka fita a rayuwata nace!!!" Na daka mishi tsawa, ina kuka tare da zuɓewa akan gwiwata, ina kuka. Shiru yayi sannan ya durkusa a gabana, ya riko hannuna..sannan ya kalle ni cikin damuwa kafin yace min. "Gashi kiyi yadda kike so dani! Zanyi alfahari idan na mutu a hannun ki, zanyi farin ciki idan mutuwa ta ya zame miki karshen matsalarki! Amma ban miki alƙawarin koda ina raye zan daina bibiyarki ba, wannan shine alkawari na dake" Kura Mishi ido nayi, na rasa gane wani irin mutum ne shi da bai damu da kanshi ba, sai dai ya kuntatta maka, banda kuntattawa me yasa zai kore Fudail ya kuma ce min na kashe shi salon yaja min magana.. *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 28 Kasa jure idanun shi nayi a cikin nawa, na kai mishi duka a kirjin shi, muryana yana rawa. "Me yasa?" Murmushi yayi sannan yace kai bakin shi saman kunne na, ya d'an kama da hakorin shi, rike rigar shi nayi tare da sauke ajiyar zuciya. Sake lasar kasan kunnen yayi na k'amk'ame shi tare da jin wani irin abu yana yawo a jikina kamar an watsa min tsutsa, kark'ada min harshen shi yayi a cikin kunne na, ji nayi kamar zan zube ƙasa, ya kuma rike ni sosai, Mehran Mugu ne, ba fada dashi bane matsalar. Kwana mita, domin a iya haka ya labtar da gangan jikina, ya kuma sani kuka babu fada babu zagi, hancin shi ya shiga gogawa wuyana, yana magana kasar makoshinsa. "Ba fada zanyi dake ba, kuma ba zan hana ki faɗa dani ba, sai dai ki sani a shirye nake na bawa zuciyarki horon yaki akai na, a shirye nake nayi ta sanya ki kuka akan abinda ba zaki iya bujirewa ba. Tsaf na shirya yaki da zuciyarki har sai ta nutsu akan Abu daya, sannan zan kyale ki. Mara jin magana kawai." Ya fadi haka tare da hura min iskar bakin shi, wani irin kuka ne ya kwace min domin kafaffuna rawa suke, a hankali ya juya ni tare da saka harshen shi akan fuskana, Yana lashe hawayen da suke zuba, tare da cewa. "Ni zan saka ki kuka! Kuma ni zan lashe kukan nawa, duk abinda zai fito daga gare ki nawa ne!" "Kyale ni, wallahi babu abinda zai zama naka ,Ni ba kara bace nice ajalin ka" na fada ina kuka. "Bakin ki yana yawan magana, kuma ina tsoron maganar karta zame miki matsala, harshen ki kamaninki, don Allah ki rage yawan fadar haka. Domin ke baiwa tace." Ture hannun shi nayi tare da kallon shi, kuka nake sosai tare da niman guri na zauna, murmushi yake, cikin jin Dadi. Allah ya gani yana son mace me jarumta, yana kuma son ganin mace tana kuka, cikin damuwa kara mata kyau yake balle Ikram da suka shekara uku basu hadu ba, zama yayi a kusa da ita, tare da matse ta a a jikin itaccen da aka yi gwafa da gidan. Hannun shi ya saka tare da riko hannun na, yana kallon yadda nake kuka. Tare da kallon yadda nake shashekar kuka. Ita take kukan amma jin hawayen ta yake kamar narkakken dalma ake diga mishi akan zuciyar shi. Kai hannu na ya kai kan kirjin shi, yana kallon yadda na sunkuyar da kaina, tare da kokarin zare hannun daga kirjin shi. Matso dani yayi jikin shi. Tare da d'ago kai na, yana goge min kwallar fuskana. "Me kike so?" Kallon shi nayi tare da kasa cewa kome. Bana iya kallon cikin idanun shi na tsawon mintina, lumshe idanun nayi kwalla suka kuma zubowa. "Qurratulain!" Ya ambaci sunan daga kasar makoshinsa, yana ji kamar za a kwace mishi ita, gani yake kamar duk wani dakika na duniya kara nesanta shi ake da ita. "Me kike bukata?" "So nake na kashe ka" na bashi amsa ina kallon cikin idanun shi. Murmushi me zubin dariya yake yana kallo na, yana shafa fuska ta, tare da kai kanshi saman hancina. "Har yanzun baki gaya min me kike bukata ba?" "Na tsane ka" "Anya kuwa?" "Bana son ganinka" "Da gaske?" Kokarin ture fuskar shi nayi tare da sake mishi wata irin siririn kuka.. "Yau nayi nasarar saka Jarumar mata kuka ko?" Mikewa yayi tare da kallon yadda take kuka, murmushi yayi sannan yace mata. "Ban miki alqawarin zan rabu dake ba, domin zanta bibiyar ƙi" daga haka ya juya barni a gurin ina kuka, wanda idan da zaka tambaye ni me yayi min wallahi ban sani ba, kawai dai ina tare dashi kuma ban san lokacin da nake kuka ba. Hannun shi suna zuba cikin rigar shi. Fidda su yayi tare da shafa fuskar shi zuwa kan shi yana lashe bakin shi, sannan ya juya bai kuma magana ba, ya bar gidan. Sai da ya fita na sami kaina da yin shiru, ina sauke ajiyar zuciya. Wato idan kana niman karfen kafa, ka sami Mehran ka gama kome domin lokaci guda ya zuba min wasu irin matakan tsaro, tare da sawa aka bibiyar kome na, bana fita Izmah da Nimra suke kome, ni ya hanani fita, domin da zaran na fito masu tsaron zasu taso min na koma cikin gidan. Akwai wani bikin da ake a garin SAMAIND wato bikin fitilar wuta, dan haka naso na shiga kasuwa na sayi abinda ake hada abin, amma wad'ancan masu kama da bishiyar su, hana ni fita. Kura musu ido nayi tare da cewa. "Zan karya kasusuwan ku! Dan haka ku barni nayi tafiya na" "Idan zaki shekara kina karya kasusuwan mu, ba zamu karya dokar Sultan Mehran ba, mu an kan mishi biyayya bamu damu da rayuwar mu ba" Jikina ne yayi masifar sanyi, dan haka na juya tare da zama a kofar dakin mu. "Ikram!" Juyawa nayi na kalli Izmah, Tasowa tayi tare da zama a kusadani. "Ban tab'a ganin mutum me kirki irinki ba, zuciyarki me kyau ne." "Bar min kewaye kewaye, fadi abin da yake ranki" "Sultan MEHRAN!" "Ai dama nasani" na bude baki zan yi magana kenan Fudail ya shigo da kayan a hannun shi, ya mika mata. Tare da juya kai yana niman Nimrah. "Wannan fa?" Murmushi yayi sannan ya kalle ni yace. "Inji Sultan Mehran!, Wai ku saka kayan zai zo an jima da dare." Yana raba idanun shi, akan kofar mu. "Ina Nimrah?" "Tana ciki kuma ai taji ka,, ka mikawa SULTAN Mehran godiya kace mishi Ikram ta amsa cikin mutuntawa. Mun gode" Murmushi yayi yana kallon yadda na b'ata rai, kamar bani ba. "Ikram" "Me zan maka? Ka dauki kayan tsiyar shi ka maida mishi, jinin mijina ya fi karfin tunanin shi, kar ya kuma kawo min kayan haukar s...." Had'iye maganar nayi tare da dauke kai na, sabida yadda yake kallona kasa kasa. "Sultan MEHRAN. Mun gode Allah ya kara maka bud'i da nisan kwana, Ubangiji yayi maka jagoranci akan duk wani abinda ka saka a gaba, Allah ya baka mace ta gari!" Kamar wacce aka watsa min ruwan zafi haka naji Addu'ar Nimrah. Tsaki naja musu sannan na mike zan bar gurin. Ban san ya akayi ba sai ji nayi kamar an ja kafana. Na tafi zan fad'i. Cikin abinda bai kai dakika biyu ba, naji ni a jikin shi tare da d'ago kai muka kalli juna, wani irin tsume fuska yayi wanda ya saka duk suka bar gida, janye jikina nayi tare da b'ata rai. "Me yasa kake son shige min?" Tab'e baki yayi tare da kauda kanshi yana wani shan kamshi, kamar wani wanda ya ga abin da baya so. "Me yasa ba zaka kyale Ni ba?" Na fada da karfi, kauda kanshi yayi tare da kallon kofar shiga gidan, yaga babu kowa. A hankali ya sake ni sannan ya ture ni har jikin kofar shiga dakin. "Mehran!" Na fada muryana yana rawa, na kira sunan shi. Bakina ya kama, tare da mishi wani irin azazzaben sumbatar da tasani jin kwalla ya zubo min, sabida yadda yake abin wallahi babu tsoron Allah a ranshi. Jin baki na kamar ba ajikina yake ba. Domin kuka tsotsar shi yake yana kuma taune bakina, bai kuma ji a ranshi haka da yake min kuskure ba, domin har harshe na zafi yake min da rad'ad'i, hannun shi kuwa bai fasa yawo dashi a jikina ba, domin jan rigana yake har zuwa sama. Ban tab'a ganin shi a irin wannan yanayin ba, domin da ban mamaki abun yake, Mehran ya tsotse bakina lebbe na kuwa har wani yaji yaji yake min, hannun shi da ya tura cikin rigana, yana kokarin cusa hannun shi cikin daurin kirjina, rike hannun shi nayi, ina girgiza kai na, tare da zubda kwalla. Sai da yaji ina wani irin gurnanin kuka ta cikin wuyana da bakina ya janye bakin shi daga nawa, yana murmushin mugunta da jin dadi a ranshi. Lashe lebben shi yayi kamar wanda aka lasa mishi zuma a bakin. Ya kuma kallona sannan ya juya tare da ɗaukar kayan a inda Izmah ta ajiye, ya mika min. "A cikin kasata, a da'irar birnina a cikin garina a cikin farfajiyar mulkina ke har kin isa ki kirani kayan tsiyata?" Murmushi yayi sannan ya juya har ya isa bakin kofar. "Bayan sallah isha, zan zo kuma idan." Cizon lebben shi yayi sannan ya sake murmushi, sannan yace. "Kina sanya Ni magantuwa" sannan ya juya abin shi yabar gidan. Zamewa nayi daga tsaye na zauna a kasa, duk zaratan da nake haduwa dasu. Ban tab'a haduwa da makiri, miskili irin Mehran ba, dan mugunta ya gama cinye min bakina, tare da sakani kuka kamar zan shiɗe. Shigowar su Izmah suka kalli bakina da yayi ja tare da d'an kumbura. "Laaa! Amma Sultan Mehran ya iya soyayya, dubi yadda ya cinye miki baki, kai jama'a nima ina tausayin kaina, domin ina kewar Firooz." Ta faɗa tana sake wata irin iska. Murmushi Nimrah tayi tare da gyara zaman gashinta sannan ta shige dakin. Kamar zan sake ihu tare da zuba kwalla, ina kallon Izmah sai dariya take, tana kallona tare da cewa. "Wallahi Sultan Mehran ya miki kankati, domin kuwa shi daya ne yake iya saki kuka tare da ya zane ki ko ya miki kome ba, gashi nan kina kuka wiwi." Haka ta gama min wulaqanci, sannan ta shiga magana irinta masu hankali. "Bilqisul Ikram! Maganar gaskiya ki rage kaifin kalaman ki, domin kuwa zata kai ki ta baro ku, kina gaya mishi maganar da yayi miki, karki manta shugaba ne fa idan ya tsaya a filin yaki dakaru kimananin miliyoyin mutane suke take mishi baya. Ikram Mehran ba kashin yarwa bane, Mehran ba haka kawai yake gabanki ba, Ikram baki da kome a kirjin ki, babu nono baki da abinda lafiyayyen namiji zai ganki yaji a ranshi yaga mace. Ikram ki duba yadda rayuwa take tafiya dake, kuma a cikin haka kika yi ta kai mishi farmaki bai tsaya ya duba meye ke tafe dake, ya kalle ki da kyakyawan niyya yana barin fadar shi ya fito sabida ke meye illar shi? Meye laifin shi? Wallahi na rasa gane miki na rasa fahimtar meke damun ki, Ikram idan rayuwar Mehran ne fansar jinin Noman ki tafi ki kashe shi ki huta, wannan wani irin k'iyayya kike mishi? Wani irin k'iyayya ne haka ya shiga tsakanin ku? Me yasa baki tuna abinda yayi miki abaya ba kike nuna mishi gundarin k'iyayyar ko dan ganin ya tura a kashe noman ne? Ni kuwa dan Sultan Mehran yace min kar nabi wani wanda nake so zan hakura domin shi din Shugabana ne, kuma Uban gidana ne shi. Bana jin dan ya kashe shi tsane shi, idan duniya da gaskiya kamata yayi ki bincike waye Mehran meye Mehran yake yi, me ya faru dashi bayan rabuwar ku baki yi ba, shine faidar dawowarki, kina tsanar Mehran ne kawai Amma duk halin da yake ciki sabida ke ce, Ya hakura da mulkin shi sabida ke, domin da suka ce zasu dakatar da shi idan wani ne kin amincewa zai yi kuma ya nuna musu karfin mulki. Amma sai ya juyawa mulki baya, a tsawon shekarun shi kamata yayi ace yana da matar da zata dauke mishi bukatar shi da kewar shi, sai gashi yayi fatali da matan da ake kawo mishi, duk shekara watsi yake da mutane haka kawai ba dan kome ba sai dan yana jiranki ki dawo gare shi." Kasa da murya tayi tare da rarrafawa gabana ta riƙe hannuna tana kallon fuskana sanan tace min. "Zunzurutun yana da muradinki ya hana a fitar da kin auri wani namiji. Meye kike bukata yayi miki? Meye kike so yayi miki? Meye nufinki akan shi? Mehran mutum ne guda ba b'ari ba, mutum ne da ya amsa sunan shi. A shekarun shi kamata yayi ace yana da Kwarkwarorin babu adadi amma yana zaune domin ra'ayin kanshi meye nufin shi da kawo wancan kayan? Saboda macen da take da daraja ake bawa, amma gabaki daya tunanin ki baya baki lissafin da ya dace kin tsane shi Allah ya baki sa'a da lafiya ki ta tsanar shi. Ba zaki gane illar abinda kike ba sai ranar da kika yanke shawarar da har ki koma ga Allah ba zaki daina kuka ba shine idanunki zai bude.." *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 29 "Kyaleta Izmah! Bata ga ni'imar da Allah yayi mata bane, shi yasa take butulce mishi da tasan tarin baiwar da Allah yayi mata da hikimar da ya tsara ba zata tsaya tana musguna mishi ba. Domin na gama nazarin abinda yake tsakanin su ban ga laifin shi ba, sai ma tarin girmama al'amarin ta da yake yi amma baiwar Allah nan ta rintsa idanun ta. Meye kike bukata a duniya? Mehran yayi ya kuma amshi hukuncin da kika aikata laifukan da ya dace naki ne amma shi ya amshi laifin akanki, Ikram meye matsalar ki da k'iyayyar da kike mishi, na rasa gane meye ya miki da zafi haka, wallahi ko ni da Mahaifiyata ta miki laifi baki min tsanar da kikewa Mehran. QpAmma kin rufe idanunki a madadin amshi kiran shi kin zauna kina juya halin ki a yadda shi kanshi dole wata rana ya gundura da halinki tir da ma ace Mahaifiyata ce ta haife ki sai nace kin sha mugun hali a nono ne ba a gurin kowa ba, amma abun ai jini yake bi, shi yasa kika dauki kad'an a halin ta." Ina jin su ina kuma jin yadda suka sani a gaba da gaya min magana, sabon tsanar shi nake ji a raina. Mehran ya saba kwace min farin ciki na, yau ma ya kwace min kawayena Insha Allah yau zamu yita ya kare ya rabu dani yayi tafiyar shi nagaji da halin shi, duk abinda na samu na farin ciki sai Mehran ya rabani dashi ya saka Ni kuka ya saka zuciyata kunci bai ishe shi ba, yau kawayena da na rabo su da ahalin su. Sune suka juya min baya. Kura musu ido nayi tare da sauke kai na kasa, kwalla ne ya zuba min daga idanuna. A hankali na d'ago kai na, zan yi magana kuka ne ya kwace min tare da shashekar kuka, ina jin kamar na had'iye zuciyata na huta. "Ku koma gurin Mehran!" Na fada musu a tsawa ce, ina share kwalla da take sauka min, ma tsani mutumin nan iya karshen rayuwata. Kuma wallahi ba zan tab'a kyale shi ba sai na ga bayan shi. Haka na shige dakin ba kyale su baki hangame da mamakina. ~~~ Merocco. Ga baki daya tun da aka nime Ikram aka rasa ya koma kamar karamin mahaukaci, yanzun ma a gabanta Sultan Mu'allim yake. Tare da narke Mishi. "Rahil har yanzun bamu da labarin ta dan ko har aika Sultanah Amrah tayi daga Askandariya, amma babu wani labarin da aka samu. Kayi hakuri ka kara hakuri insha Allah tana bayyana zan aura maka ita." Tun bayan tafiyar ta Sultanah Amrah tazo har masarautan tare da tambayar bayanin Ikram, suma suka tabbatar tabbas tazo amma kuma ai nata zauna Kamar yadda suka so ba, dan basu sami labarin ta ba sai bayan tafiyar ta, dan haka suma suke nimanta. Sannan suka daukarwa juna alkawarin matukar aka sami labarin ta, daga kowacce gefe su tabbatar da an tuntube juna. Toh har yanzun dai haka ake ta bincike akanta kuma babu labarin ta. Takai har niman masana kuma gogaggun masu iya zanen aka yi tare da zama hotonta ko za a dace. Dan haka aka yi ta rabawa kasuwanni da wasu guraren domin niman ta. Idanun shi cike da kwalla yacewa SULTAN Mu'allim. "Don Allah ka taimaki rayuwata, duk duniya bani son wata mace sai Ikram, don ALLAH Sultan ka taimake ni akanta kar na rasa rayuwata" Tausayin jikan nashi da kuma abinda yaron yake ji yasa shi rike hannun shi, cikin tabbatar da abinda yake nufi yace mishi. "Ni nake da iko da kai, haka itama ina da iko da ita, dukkan ku a karkashina kuke, don haka babu wanda zai shure dokana da sanin shi, iyayen ku basu shure doka na ba, ku y'ay'an su baku isa ku shure abinda na kafa ba." Sake karya wuyar shi yayi tare da kallon shi yace mishi. "Allah ya taimake ka, nasan ni ina jin tsoron kar ta haɗu da wani namijin ne, ina gudun karta hadu da wani da zai yi nasarar nisanta ta dani ne, Sultan don Allah idan aka ji labarin inda take a barni na wakilce ku, domin na dawo da ita, anan nake son kafa kai na, domin bana son tazo ana dolanta mata ni." Ya faɗa tare da zubda kwalla, sabida Allah ya gani yana mugun kaunar Ikram, kuma duk rintsi duk wuya sai ya mallake ta, nasiha Sultan Mu'allim yayi mishi sannan ya shafa kanshi ya tabbatar mishi da cewa, yana taya shi da addu'a, sannan Insha Allah Ikram tashi ce. ~~~ A wannan lokacin Sultan Abrad ya nime wata yar gwamnar yankin shi me suna Aseelah, kyakkyawar mace ce. Na gaban kwantancen, tunda ya hadu da ita yaji ya manta da Ikram. Dan haka suka baje amarcin su na wani lokaci. Yanzun ya manta da wata Ikram,.sai ma hidimar gaban shi yake da cusa Kanwar shi izuwa Daular su Mehran. Dan yaci alwashin ko bai sami damar kashe Mehran ba, sai ya shiga cikin mulkin kasar yayi kane kane, yadda zai ji dadin kuntattawa Mehran tare da takalar shi rigima idan yayi magana ya tinzara, sauran yankunan jazziratul Arab su yaki Mehran. Domin yayi alƙawarin sai ya dagula al'amurran Mehran. Dan haka a sauran kwanakin da suka rage zab'en matan sarki ya fara shirya Kanwar shi tare da nuna mata hikimar da zata yi na girki, tare da kiran manyan masu girki na kasan ana koya mata, duk wani nau'in girki da nuna mata yadda ake girmama al'amarin sarautar SAMAIND. "Sultanah!" Murmushi tayi domin tana jin dadin yadda suka fara kiranta da Sultana. Dan gani take dole itace zata lashe gasar. Kuma tayi tafiyar bazata da zuciyar shi. Murmushi tayi sannan tace musu. "Ina jinki Rubina!" Cikin jin dadi baiwarta Rubina tace. "Sultanah a yadda zab'en yake matukar kika samu nasarar zama matar da zai aura za a killace ki na wasu kwanaki a gama niman bayanin asalinki, sannan zaki kasance me lura da al'amuran Sultan har kwanakin da zaki yi a killace su cika. Sannan ba a son a wannan tsakanin ki kasance dashi ta shamfida, sabida idan kika kasance matar shi ba zai yi daukin ki ba, an fison ki hakura da shi wa Kwarkwarorin da zasu shiga zab'en. Sannan a cikin wannan yanayin babu ruwanki da shiga al'amuran gidan, babu ruwanki da shiga al'amuran Kwarkwarorin shi, babu ruwan ki da duk abinda zai yi da Kwarkwarorin shi, har ranar bikin ku ya kama a dawo dake masarautan shi." "Wannan dokar fa? Tab haka zan hakura da mijin da zan aura gaskiya babu wanda ya isa ya shiga tsakanin mu, domin wallahi ba zan yarda ba." Ta faɗa cikin fada da gatsine, sunkuyar da kai duk bayin suka yi tare da zare idanu. "Allah ya gani ba zan iya ba, wallahi ba zan iya ganin shi da mace na kasa hakuri ba." "Sultanah daga ranar da kika zama matar da zai aura, toh zaki iya sauya kundin tarihin masarautan, sannan zaki iya tafiya da ra'ayin kowa ko kuma yi fatali da ra'ayin su, ki kafa naki ra'ayin." "Kai Rubina idan na zama Sultanah uwar magajin sarauta zan yantaki har na baki me bani shawara na hannun dama na," ta faɗa tare da sake murmushin jin dadi. "Kai Nagode Sultanah Uwar Magajin sarauta." Murmushi tayi sannan tace mata. "Karki damu daga yau kuna da damar yin abinda kuke so, har mu tafi SAMAIND." "Sultanah mun gode! Azizatul Nissah mun gode ainun." Haka tayi ta murna sannan tace mata. "Toh bayan nan dole zaki daura damara da sauran matan, domin zasu ta kawo miki hari, tare da makirci kala kala, da munafunci. Idan har haka ne toh ba makawa zaki zama me, juyawa tayi tare da kallon sauran bayin sannan tace mata, Sultanah bani kunnen ki" nan suka rad'a munafuncin su , sannan suka kalli juna. Murmushi suka yi wanda zai nuna maka akwai wata a ƙasa, kafin suka ci-gaba da tattaunawa. ~~~ Ina kwance suka gama shiryawa, tare da dauke kaina akan su, dan naga ba karamin dukiya bane a jikin kayan, musamman rigunan aka dinke su da duwatsu lu'lu'u, sai azurfa da aka makala a wuyar hannun rigar, tare da saka musu digon karfe zinari. Sunyi kyau. Lumshe idanuna nayi amma kayan ne akan idanuna. Tsaki naja, sannan na juya baya abuna. "Ikram! Ki tashi ki shirya mana." Inji Izmah, "Kar wata ta min magana." Na fada a fusace, murmushi suka yi kafin suka shirya dan tunda nayi sallah isha nake zaune a gurin, kuma babban damuwar su na tashi na shirya. Amma fir naki. Juya baya nayi abinda daga kallon da suke min na rashin mutunci. Ya jima a bakin kofar shiga cikin dakin, murmushi sukayi tare da d'an dukawa suka gaishe shi, sannan suka daga d'akin. Kamshin turaren shi ne ya fahimtar dani yana cikin ɗakin. A hankali ya zare alkyabar shi ya ajiye a jikin kofar d'akin, sannan yayi zaman raƙumi a bayana, yana kallona, fuskar shi babu walwala. "Ki tashi" Banza nayi dashi tare da kin motsi. Gyara zaman shi yayi tare da rungume gwiwar shi, yana kallon yadda nake kwance. "Bana son gardama." Banza nayi dashi a karo na biyu, iskar bakin shi ya furza. Sannan yayi shiru. Ina jin idanun shi a kai na, ji nake kamar zane ni yake yi, kasa jure idanun shi nayi na tashi tare da kallon shi ina murguda mishi baki. "A daina cinye ni da ido!" "Hmm!" Ya faɗa a kasar makoshinsa, tare da lashe bakin shi, alamar haka a jikin shi yake. "Ni dai ka fita min a d'akin" Kamar da dutse nake magana yaki ko motsi, tare da sake murmushin jin dadi. "Don Allah ka fitar min a daki." Wani irin mayyen kallo yake bina dashi, kamar kura taga d'anyen nama, tare da lasar leben shi ba kasa,wanda nake hango yadda take rawa, tsoro ne ya sani mik'ewa da sauri tare da shiga ban ɗakin, bai damu ba sai ma sake murmushin da yake alamar yarinyar ta fara laushi daga horon idanu. Wanka na fito, yana inda na barshi bai matsa ba. Tura baki nayi tare da hararan inda yake, sannan na fara gyara jikina, haka na gama shiryawa fuskana ban yi mishi kome ba, ina gamawa ya kalli inda kayan yake sannan ya kalle ni. "Ni bazan saka ba!" Na fada kamar zanyi kuka, murmushi yayi sannan ya gyara zama. Shi yana kallon ta, ai maganin biri karen maguzawa, dan haka ba zai tab'ata ba balle tayi tunanin dan jikinta yake tab'ata ko daya, shi kawai dole ne ayi yadda yake so, idan mutum yaki zai ji a jikin shi. Yadda ya zuba min ido ya sani kwashe kayan daga cikin dakin zuwa ban daki. Ban fito ba sai da na shirya, sannan na fito ina yatsina fuska. Murmushi yayi sannan ya janyo alkyabar shi ya saka, tare da kallona. Nufin shi na daure mishi igiyar, kallon shi nayi baki sake ban san lokacin da na kwashe da dariya ba. Ina kallon shi. "Nice zan zo na daure maka zaren alkyabar?" Murmushin gefen baki yayi tare da nad'e hannun shi a kirjin shi yana me kallona da ido. _Yau duk abinda zaki yi sai kin daure min shi domin nafiki rigima dan mulki nake ji yau_ ya faɗa a ranshi. *Ni ba zan daurewa makashina alkyabar ba, matukar zan daure maka toh ba makawa sai na shake ka* Na fada a raina ina murmushi, takowa nayi tare da kallon fuskar shi, domin nasan matukar na isa gurin sai wuyar shi ya gaya mishi. _Bilqisul Ikram! Kome zaki yi ina shirye dake! Ina jiranki_ ya faɗa yana murmushin mugunta. Takowa nayi na isa gaban shi na saka hannuna da niyyar daure mishi igiyar, yadda na sarkafe tare da zarga mishi zaren, sai da ya matse ni da kirjin shi har ina jin yadda numfashina yana wani irin kamar zai fasa Kirjina. "Mehran!"""" [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 30 A razane na kira sunan shi, tare da jan numfashina dakyar, kan shi ya kai wuyana tare da sake min wani irin numfashi me hade da nishi, k'asa k'asa yace min. "Hmm! Na iya nima" d'ago kai nayi tare da kallon shi. "Hmmm!" Ya kuma cewa, alamun dai ma mishi abinda ya sani, kamar zan fashe da kuka haka na daura mishi sannan ya sake ni, muka fito daga cikin ɗakin. A hankali muka fito daga gidan, muna tafiya bai damu da yadda ake kallon mu ba, tare da kallon yadda mutane suke hidimar su na bikin ranar, duk da tafiyar kurame muke haka bai hanani jin wani irin nutsuwa ba, duk inda muka wuce shagali ake, ashe ni ce ma nake damuwa dasu domin kuwa jama'a kowa hidimar gaban shi yake, har muka isa inda ake ta soya kayan ciye ciye, kallon shi nayi ina son tambayar shi su Izmah, amma ganin yadda bai bani fuska ba ya sani jan bakina nayi shiru. Tsayawa yayi tare da kallon inda ake sayar da wani, wani abu kamar panke, abin yayi min kyau, muna tsayawa a gurin wasu matasa suka kalle mu. Tare da cewa. "Keeee! Kyakkyawa, idan zaki ci gashi." Satar kallon shi nayi da wutsiyar ido, mika min panken matasan suka yi. Ni kuma dake ina son na b'ata mishi rai kawai na amshi panken tare da sake murmushin mugunta. Faucewa yayi tare da wurga da abin a kasa yana hararar Matasan. Cikin isgilanci suka ce mishi. "Dalla malam mun ga kayan aiki kace zaka hanamu, yan mata kinyi mana! Kuma gaskiya muna sonki." Cikin murmushin jin dadi na bude bakina zanyi magana, ya cire hular alkyabar da ta hana mutane fahimtar shi, kamar wanda ake jiran ya cire gabaki daya mutanen gurin suka sauke wuta, kallon su yayi tare da girgiza kanshi yana fadin. "Ku watsa!" Jikin su yana rawa suka shiga watsawa, baki daya gurin ya zama babu kowa sai shi da dakarun shi. Shi kanshi me sayar da panken jikin shi rawa yake, dan kamar zai sake fitsari. "Darda bashi jakar tsaba nan!" Ajiyewa mutumin jakar kudin sannan ya koma gefe yana faɗin. "Ka zubawa Amirah Ikram abinda take bukata" "Ba zanci ba, baba ka rike amadadin kashe maka kasuwa da aka yi" murmushi mutumin yayi tare da cewa. "A'a Amirah wannan dukiyar ta isheni, koda zan shekarar goma banyi sana'a ba wannan zai ishe ni, nagode sosai Sultan Ubangiji ya kare rayuwar ka." Ya zuba min abin tare da mika min. Ganin yadda yake damun sai naci ya sani karb'a ina kallon Sultan. Dauke kanshi yayi tare da hango Jasrah tare da wasu bayinta, dan ta hango mu. D'ago kai nayi dan mishi magana naga hankalin shi yana kan ta, ajiye tasar nayi tare da mik'ewa na tsaya a gefen shi. Har Jasrah ta iso gurin. "Sultan MEHRAN kai ma kafito kallon wasan ne, Barka da kasancewa da kai a wannan lokacin." Murmushi yayi sannan ya kalle ni, tare da kallonta. Nad'e hannun nayi a kirji ina kallon su. "Ikrammmmm! Bake bace aka ce kin bi saurayi ba." Satar kallon shi nayi naga fuskar shi babu wani abu na sauyi, murmushi nayi tare da cewa. "Eh laifi ne?" Dariya tayi sannan tace. "A'a ba laifi bane, amma shi Sultan Mehran ya san cewa kuskure ne babba macen da take kasar ikon Sultan Mehran ta bijire mishi, duk da kuwa Sultanah Fazilatul nisa, tayi kokarin d'aga miki daraja kika zab'i bin saurayi koda yake ba laifi bane tunda matsayinki na bawa ce." Murmushi nayi tare da matsawa jikin shi sosai, sannan nace mata. "Eh Toh wannan ra'ayinku ne, ra'ayin shi ya gaya min, ban sani ba ko akwai wani abu bayan haka Mehran." Yadda na shiga jikin shi tare da manne mishi. Kura min ido tayi tare da kasa cewa kome, murmushi nayi mata tare da janyo hannun shi ka makala a k'uguna, ina murmushin jin dadi. Kasa jure ganin mu a haka tayi kawai, kamar wacce aka ingizo ta zata fadi a jikin shi itama, kayi maza na ture shi baya ita kuma ta fadi a jikina, murmushi nayi mata sannan nace mata. "Sannun karki ji kome, zan tare ki, Mehran ne dai baki isa ya tare ki ba." Ya ture ta, bayinta suka tawo da sauri suna ce mata. "Sannun Amirah," Kallon mu yake cikin jin dad'i, a ranshi, amma kuma ba zaka tab'a ganin wannan abun akan fuskar shi. Tasowa tayi tare da d'aga hannun ta zata mare ni, rike hannunta nayi tare da cewa. "Ki duba kwayar idanuna baki isa ba, Amir Zuhair bai isa ba balle kakan ku Amir Hood, ni dince ban sauya ba." Na wurgar da hannunta tare da jan hannun shi muka bar gurin, ina murmushi, muna karawa gaba na kalle shi cikin jin haushi na ja alkyabar shi na rufe kan shi, duk da kuwa ya fini tsayi. "Wallahi ni ba dan kai kayi fada na ba, nayi ne dan ra'ayina, kuma ka mayarda hulan kanka." Na fada ina tura mishi baki. Share ni yayi tare da wuccewa abin shi, a ranshi yana faɗin. *Magulmaciya zaki gama gulmarki! Amma tabbas yau naga abinda kike boyewa ina jiranki,* Haka muka yi ta zaga garin har kusan tsakiyar dare sannan ya dawo dani gida, tun muka iso yaga ina hamma, zama yayi tare da kallon yadda nake kokarin shiga daki yayi, ganin zan gudu na barshi ya sashi finciko ni. "Ni barci nake ji!" Zaunar dani yayi tare da saka kaina gefen kafadar shi, bai ce min kome ba, bai kuma nemi nayi magana ba, hannun shi a cikin nawa, yana murza yatsuna. a hankali har barci ya dauke ni me karfi. Yana zaune a gurin, har aka fara kiran sallah farko, kafin ya dauke ni zuwa cikin ɗakin ya kwantar dani, ya ja min bargo. Tare da shafa fuskana, sannan ya juya ya fita daga dakin. Dake na gaji sosai ban ma san har ya kawo ni dakin ba, sai da Nimrah ta tashe ni daga barcin sannan na mike a hankali na nufi ban daki nayi alola, bayan na idar da sallah ne na kalle su. Sun sayi abinci, tare da zama suna hirar yadda suka sha yawo da Fudail, ban saka baki a maganar su ba, sai da naji suna cewa. "Amma naji ance kamar an samu yar karamar rikici, tsakanin Amirah Jasrah da tawagar Sultan Mehran, wai da gaske ne?". Bude idanuna da yake cike da barci nayi sannan nace. "Ki tambayi Aamaan Mehran,!" "Kai Ikram amma baki da kunya kowa Sultan Mehran yake kiran shi ke kuma Aamaan Mehran, sai kace sa'arki!" Tab'e baki nayi sannan nace mata. "Aamaan Abdus Samad kike magana akan shi." Na fada tare da dauke kaina ina murmushin mugunta, dan naga yadda suka gwalallo idanu waje, na kuma sake samun damar na kwafta rashin mutunci a silalle. "Wai Aamaan Abdus Samar kuke faɗa?' kasa amsa min magana ta suka yi suna kallona, tare da cewa. "Dama haka kike baki da mutunci?" "Gado nayi a gurin Wancan d'an bakirin" na fada ina murmushi, Watsewar zabi sukain tare da min fatar shiriya, dan ganin mahaukaciya suke min. ~~~ Karyawa Mehran yake bini bini yana sake murmushi, gyara zama Sultanah tayi sannan tace. "Sultan dina anya baka fara soyayya ba?" Ya kuma sake murmushi a karo na babu adadi, yana daukar soyayen kwai ya saka a bakin shi yana me sake murmushi me sauti. "Fudail meye gaskiyar magana yau kimanin kwanaki masu yawa bana ganin shi da maraici,idan ya dawo kuma zai ta sake murmushi wacce barauniyar ce tayi sa'ar sace zuciyarshi?" Kallon juna suka yi tare da dauke kai. "Nifa kamar uwace! Idan baku gaya min wacece ita ba waye zai gaya min?" Ta tambaye su. Sake kallon juna suka yi kafin suka shiga kallonta an rasa wanda zai gaya mata gaskiyar maganar. Murmushi tayi sannan ta cigaba da cin abincin ta, tana me cewa. "Ikram itace mafarkinka, ba zanyi mamaki idan nace maka nasan tana cikin lardin nan ba, amma kuma ban san me ya dawo da ita ba, dan nasan dai haka kawai ba zata zo ba sai dan daukar...." Zuba mata ido yayi tare da rike cokalin hannun shi da mugun karfi har sai da ta lankwashe. "Karka damu! Ni ba a zalimar mutum bace, ina bawa kowa ra'ayin shi." Matsanancin kunya ce ta kama shi, tare da kasa kallon kallonta. "Toh Fudail idan Shugabanka yayi aure kai waye zaka aura?" Diriricewa yayi ya kasa tsayuwar guri guda, sai kallon gefe da gefe. "Nimrah" Mehran ya faɗa a sanyayye, kamar bashi yayi maganar ba, da sauri Fudail ya bar falon. "Dawo nan! Kayi min bayani daga ina take." "Sultanah tare suke da Ikram!" Inji Darda, "Hmm!" Ta faɗa tana murmushi, Mehran kan kasa cin abincin yayi, duk ya takure guri guda. "Bari na baka guri" ta faɗa tana murmushi, "hmm" yace mata, tana jinjina wannan karfin halin shi, toh ya yake yi da Ikram dan hira tsakanin mafadaciya da Miskili irin Ikram akwai matsala, dan kowanen su gwani ne akan halin shi, zafi da sanyi zasu haɗu guri daya, murmushi tayi a karo na biyu. Sannan ta shiga d'akinta. Tana zama tana son ganin Uwaisul Qarni, dan haka ta shiga addu'a kafin can tayi imani da Allah sannan ta ambaci sunan shi. Cikin hukuncin Ubangiji ya bayyana a gaban ta, a saman fatar damisa. Yana murmushi. "Ikram!" Cikin girmamawa tace mishi. "Barka da warhaka Baba na, eh itace!" Kallon tausayin yayi mata tare da girgiza kai, tare da cewa. "Kiyi ta addu'a, Allah ya taikaita tashin hankalin da yake tare da alaƙar su." A hanzarce tace mishi." Akwai damuwa ne?" "Idan Ubangiji ya so al'amarin shi, babu makawa sai ya faru, duk abinda yazo muku, ku amshe shi da hannun bibiyu, a duk inda ƙaddara take, toh yana da kyau bawa ya amshe shi hannun bibiyu, Wani al'amarin dole sai Ubangiji kadai zai warware miki shi, SOYAYYA ce me tattare da kalubalen rayuwa, soyayya ce da kema idan baki yarda da Allah zaki iya shiga al'amarin Ubangiji, soyayya ce me cike da raunin zukatan al'umma. Soyayya ce da zata kashe masoya ta kuma raya makiya, ban tab'a ganin irin wannan al'amarin ba, duniya cike take da kalubale, rayuwa cike take da tashin hankali. Wallahi babu wanda ya isa goge zanen ƙaddarar da ya zana. Dan haka karki yarda ki shiga wannan lamarin." Hawaye ne ya zubo mata, tana faɗin. "Yanzun babu hanyar da zan dakatar da wasu abubuwan?" Murmushi yayi sannan yace mata. "Eh mana! Kin isa ki aikata abinda Allah ya ƙaddara? Baki isa ba? Baki da ikon tafiyar da rayuwar wasu, kiyi addu'a, kiyi hakuri karki yarda wani abu ya shiga tsakanin wutar da zata kono a tsakanin wasu, karki yarda wasu su fahimci cewa akwai wutar da ya kama a cikin gidan ki." Ya faɗa tana tsare ta da idanu, kasa tayi da kai. "Nasan kina kaunar Ikram, dole wata rana zaki iya Mantawa da wannan tunanin, nasan zaki iya juyawa kome baya domin wani dalili, ina tausayawa lokacin da wasu abubuwan zasu juyawa wasu dalilai baya, na tausayawa tafiyar da za ayi ta a cikin tsananin zafin sahara, babu ruwa babu Uzuri, rayuka zasu koka zuciya zata kasa jure kome, tunani zai tsaya cak. Mafita zata yi ƙaranci, ba lallai bane na riski wannan yanayin, bai zama tilas na san lokacin ba. Domin lokacin tafiya na ya kusa, zan tafi baki daya." Ya faɗa a sanyayye, yana me juya kanshi ya ce mata. "Idan irin wannan lokacin ya riske ki, kiyi kokarin maida alamarinki ga Ubangiji, Insha Allah Ubangijin zai amsa miki kuma zai kawo miki ɗauki, karki yarda a juya miki nazarin ki. Insha Allah zaki yi farin cikin samun Ikram a rayuwarki." Gaba daya ta rasa abin cewa, ita kanta tausayin kanta da kanta take ji, dan haka har ya tafi bata iya fahimtar kome ba, sai hawayen da take zubdawa..... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 31 Ita kanta bata san iya adadin lokacin da ta dauka tana kukan tashin hankali da damuwa wanda bata san daga inda zai ɓullo mata ba, alola ta mike tayi tare da gabatar da sallah nafilla, ta jima tana kaiwa Allah kukanta, kafin ta fito daga dakin. Sam bata jin dadin ranta, tana fitowa ta sami Shairah da Narjis suna magana akan zab'en da za ayi, da yadda ake shirya bikin domin Fudail ya gabatar musu da wasu abubuwan da za ayi. Suna ganin Sultanah suka yi shiru. "Meye Mehran ya sauya a cikin tsarin?" Shiru suka yi tare da kallon shi. "Sultanah dama ya ce a cire maganar lallai sai anyi gwajin budurci ne?" Shiru tayi sannan tace musu, "babu wanda zai goge abinda aka kafa, dole yabi tsarin masarautan" ta faɗa musu, "amma Sultanah!" Suka fadi haka lokaci guda. D'aga musu hannu tayi sannan tace musu. "Dokar masarautan ce,bai isa ya take ta ba, ko Ni da na haife shi ban da ikon karya dokan balle shi din banza, doka ce babu wanda zai karya ta" "Toh Sultanah" haka ta zauna bata ce musu kome ba, ita dai wallahi da ana sauya ƙaddara tabbas da ta sauyawa Ikram da Mehran, sam ta rasa mafita lumshe idanu tayi tana nazarin me ya dace tayi ba tare da ya shafi rayuwar su ba. Sannan taya Ikram zata kashe masoya ta raya makiya. Ga baki daya ta rasa tunaninta. Dafe goshin ta tayi kamar wacce take fama da ciwon kai. Nan kuwa ƙwaƙwalwar ta ne yake aikin hargitsa mata lissafi. ~~~ Shiru suka yi tare da kallon Mehran, kafin suka shiga kallon shi an rasa wanda zai gaya mishi dalilin kiran shi fadar, asalima duk sun razana da yadda yake muxurai. "Sultan MEHRAN yana da uzuri fa!" Fudail ya gaya musu, "kai d'an mashawarta waye yayi dakai?" Murmushi Fudail yayi sannan yace mishi. "Darakshan! Bani da abinda zance maka, amma wata rana zaka biya ladan aikin ka" sannan ya kuma duban mutanen fadar yace musu. "Wani dalili kuke niman Sultan Mehran?" "Shi Sultan Mehran bai da bakin Magana ne inji Sultanah Hoyam?" Ta kalli Mehran, wanda kanshi yake sunkuye yana matsa hannun shi, kamar baya fadar. Kuma har ila yau sun kasa fadar abinda yasa suka nime shi, kasancewar ya zabga musu gargadi tun lokacin yakin da yankunan jazziratul Arab suka nemi shiga musu, ya dakatar. Dayawan su dattijai ne, da suka manyanta amma kasuguman munafukai ne. Dan haka da gayya yaki magana kuma dole sune zasu fadi dalilin da yasa suka kira shi, amma kuma babu wanda yake da zarrar bude baki yayi magana. Abin dariya sai wannan ya zunguri wannan, shi kuma ya zunguri na kusa dashi haka sukai tayi, karshe Amir Hood ne yayi shahadar kuda ya mike tare da cewa. "Jiya Jasrah ta gaya min cewa taga Sultan Aamaan Mehran da wata mace wacce taci mutuncin shi a cikin masarautan nan, sannan ta keta Alfarmar masarautan nan akan idanun kowa bayan ta kasance daya daga cikin fadar nan, shin Sultan Aamaan Mehran ya yarda da ita ne har ya iya yafe mata, ko ba saurayi ta bi ba? Sannan kuma ba girman SULTAN Mehran bane yana yawo cikin gari da kaskantacciyar baiwa a cikin jama'arsa, kar Sultan Mehran ya manta yana cikin dokar hana fita ne me yasa zai karya doka ko ya manta akwai Amirorin da suke jiran ya bada kayan bikin fitilar al'ada a kai musu, amma anga kaya masu daraja a jikin Ikram da kawayenta shin wata irin matsayi take dashi haka? Sannan abisa al'ada ba a yarda wani sarki ya auri macen da tayi mu'amalanci wani namijin ba, kuma ta bayyana ƙarara Ikram namiji tabi, sannan kuma dokar masarautan nan ne, babu batun auren bazawara ko karuwa mafi munin lalacewa ace Sultan Aamaan Mehran ya kwana a gidan ƙaruwai, wannan Zubewar mutuncin masarautan nan ne, mafi munin abu ace Sarki Guda ya kwana a gidan Ƙaruwai? Don Allah ku duba wannan lamarin" Lumshe idanun shi yayi yana jin kalmar karuwa da ya danganta Ikram dashi, jin yadda kalmar take dukar shi kamar ana saka bulalar k'aya karfe. Idanun shi yayi jajjur. Mikewa yayi tare da sauka akan kujeran shi dake fadar,.Yasaka kai zai fita daga fadan."kai waye da zamu yi magana ka mana shiru?" Suka daka mishi tsawa, wannan shine girman kuskuren da suka aikata mishi, dan haka ai ance shiru ma magana ne, dan haka ya fice daga fadan. Tunda yake babu wanda ya tab'a gaya mishi abinda ya saka shi bakin ciki sama da kowa ba, dan haka koda ya koma gida, Daki ya wuce ba tare da kalli inda Sultanah take, tunda ya shiga dakin bai kuma fitowa ba, domin kuwa baya son magana, fahimtar haka da Sultanah tayi yasa ta hana kowa yayi wani abun da zai saka ayi hayaniya ko wani magana me karfi. A bakin Fudail suka ji labarin abinda ya faru, tashi tayi tare da shiryawa tayi zata fadar Fudail ya ce mata. "Sultanah a halin da yake ciki baya son karin damu, matukar zaki nufi fadar toh ba makawa kin lalata kome, dan haka ki zuba ido kiga abinda ya shirya. Yakin masarautan nan Sultan Aamaan Mehran ba zai iya shi daya ba, sannan kuma ke idan kika shiga mishi zasu iya aikata wani abu kuma su makala miki, ni tsorona daya karsu kaiwa Ikram hari domin kuwa zasu aikata haka kuskuren da zasu damu da kansu." Ya fadi haka a raunane, domin yasan haka ce zata faru. Idan ba wani ikon Allah bane ya hana faruwan haka. Numfashi ta sauke tare da kallon shi tace mishi. "Ina Ikram din take?" "Tana wajen garin SAMAIND!" "Toh ka kai mata dauki mana, ko a tura mata dakarun da zasu kula da lafiyarta ". "Karku fara haka!" Ya fadi hakan lokacin da ya fito daga dakin, yana me shirin barin gidan. "Akan me?" "Ba mace kawai bace ita!" Yana gaya musu haka ya ficce daga gidan baki daya, can wajen gidan ya nufa, dan baya son abinda zai tinzira zuciyar shi. Cikin yanayin bakin ciki yake kallon dajin, da yadda kome yake zaune cikin tsarin Ubangiji da ikon shi, yau yayi danasanin kasancewar shi daya daga cikin gidan sarautar ƙasar shi. Damuwa tayi mishi yawa, bai san ta lokacin da ya b'ata a gurin ba, kuma ba zaka tab'a tsammanin yana gurin ba, dan ya saje da gurin baki daya, ya rasa inda zai cusa kanshi. Dan haka da ya gaji da zama ya mike zai dawo gida ne ya hadu da Fudail yana niman shi, kallon juna suka yi sannan yace mishi. "Sun kaiwa Ikram hari" Rab'a gefen shi yayi tare da barin guri a hanzarce ya isa gidan, kayan shi ya sauya sannan ya dauki gatarin shi ya nufi wajen gari. Gani yake dokin da yake kai bata gudu, duk da kuwa saurin da yake yi bai hana shi ganin nisan gidan da Ikram take ba, jike kamar ya cire zuciyar shi ya gulla tsabar tashin hankalin, koda ya isa ya sami dakarun da suke kula da lafiyar ta, duk an kashe su, yana shiga ya same ta zaune akan saman gawarwakin mutanen da ta kashe, jini na d'iga daga gefen cikinta. Ajiyar zuciya ya sauke sannan ya tako a hankali,yana murmushi ganin yadda take rike da takobin salon shi ta dauka, wato tayi kujera da mutanen. Ganin su Izmah da Nimra a gefe bakin su a fashe ne ya sashi kallon su da son karin bayani. "Muna zaune suka shigo, wai ance su kashe Ikram, shine tace inji waye? Sai suka ce mata Sultan Aamaan Mehran, ya umarce su, suka kasheta.mu kuma muka ce karya ne ba zaka tab'a sakawa a kashe ta ba, shine suka rufe mu da duka, daga nan ne ta ce su kyale mu ita ta yarda a kashe ta. Shine kawai suka juya kanta da dukka. Har da janya, bayanta ma jini na zuba. Ganin sun kama mu zasu shigar da mu d'akin ne domin kudirin su, shine ta fara kashe su, wallahi bana son naga tana kashe mutane haka, dabi'ar tai mata yawa, mace ce kuma hakkin jini ba zai tab'a barinta ta huta na." Izmah ta karshe maganar cikin kuka da tashin hankali. "Ikram bani takobin" ya mika mata hannu, bata d'ago kai ba, balle ya saka rai zata amsa mishi, a hankali ya taka har gaban ta, ya saka hannu ya tab'a kafad'arta, biyo shi tayi tare da zubewa a jikin shi. A kidime ya d'ago kanshi, tare da kai hannun shi bayanta, yaji wuka a suke a bayan ta, a hankali ya zare wukar. Kallon Fudail yayi sannan yace mishi. "Maza ka koma ka dauko keken dokin" da gudu ya fita, tare da kallon su Izmah da suke kuka. Kamar me, gani yake kamar Fudail baya dawowa, kamar yayi kuka haka yake ganin ta, dan ma ya tab'a wuyarta yaji tana raye, amma zubar jinin yana d'aga mishi hankali. Dan haka ya kalli Izmah da itace zata iya bashi amsa Nimrah kan tsoro ya cinye ta baki daya. "Basu kira sunan wani ba?" Shiru tayi tana nazarin abinda suka fada tare da kallon shi, girgiza kai tai tare da cewa. "A'a" shiru yayi tare da sake wata tsaki sabida ganin har yanzun Fudail bai iso ba ji yaƙe kamar ya kurma ihu, dan haka ya dauke ta cak zai fita da ita sai ga Fudail nan. "Afwa Sultan Mehran, dakyar suka barni na fito!" Ya kalli Izmah sannan yace musu. "Ku fito!" Ya juya tare da bin bayan Mehran, yana fita aka bude kofar keken ya sakata a kujeran sannan ya juya tare da riko hannun Izmah ta shiga sannan ya kalli Fudail da yake rike da Hannun Nimrah da take kuka. "Ina da abin yi!" Ya gaya musu a gaggaucce, da sauri sauri itama ta shiga cikin keken, hawa dokin shi yayi, Fudail ya hau gaban dokin. Basu B'ata lokaci ba suka nufi masarautar, inda dakarun suka nemi hana Keken shi kasancewar Sultan Mehran yana baya, ganin shi ya dawo gaba duk suka zube akan gwiwar su. Tare da niman afwa. Nufar gidan Mehran yayi da ita, shi kuma Mehran ya nufi gidan likitan masarautar yana shiga yayi karo da Amir Hood. "Zo muje ka duba min mara lafiya!" Ya faɗa a sanyayye, ko kallon Amir Hood bai yi ba,shima likitan haka, bai kalli inda Amir Hood yake ba, zasu fita yace. "Aamaan ba dai akan karuwar na bace kake damuwa?" Murmushi yayi sannan yace mishi. "Bani da lokacin ka!" Suka fita a fusace, Amir shima ya fita daga gidan yana jin lallai dole ya kashe Ikram, wannan itace bakar kaddarar da aka ce zata shigo masarautan. Kuma ya fahimci haka ne tun daga ranar da Sultan Aamaan ya saka aka hukunta Zuhair, sannan bayan an konata Aamaan ya dauke ta suka yi balagoron har Madinatul Mah, wannan yasa shi kara fahimtar haka akanta. Amma baya fatan abubuwan da ya aikata su biyayya har yarinyar ta sani. ~~~ Tunda likitan ya isa gidan yake famar bata kulawa har ya dinke ciwon jikinta, Mehran yana tsaye akanta tare da sintiri, idan kana gidan sai ka fahimci yadda Mehran ya dawo, bayan wani lokaci likitan ya fito yana faɗin. "Insha ALLAH zata samu sauki, sannan a kula da bayanta da kuma cikin ta." "Zata ji sauki nan da sati biyu?" Mehran ya tambaya a dame, "Eh Toh ya danganta da yanayin jikinta ne" rike bakin shi yayi sannan ya kalle shi, yace. "Babu wani matsala bayan Ciwon jikinta?' "Babu gaskiya" "Mun gode!" Inji Sultanah, Yana fita ta shiga dakin tare da kallon ikram, zucuyarta a raunane yake akan Yarinyar, amma tsoron goben D'anta take, tana gudun abinda zai je ya dawo mishi. Ikram itace ta dace da Mehran, amma idan ta duba yadda rayuwar su take, zai yi wuya kome bai faru ba, tana jin ciwon yadda kome ya cab'e mishi . Shigowar shi da yayi ne ya sata dauke kanta daga Ikram. "Naji kama tambayar zata sami lafiya nan da sati biyu. Meye kike nufi?" "So nake ta shiga cikin zab'en matan da za ayi." "Akan me?" Zuba mata ido yayi sannan ya sake murmushi. "Sabida ta zauna a matsayin shugaban Kwarkwarorin na!" "Yarinyar da take da sa'ar ce zata zauna a kwarkwarah? Hmm!..... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 32 Ta tambaye shi tare da kallon shi,bakin shi ya gaza furta kome, sai zare ido yake. "Mehran ba zan hanaka abinda kake so ba, amma ya girman hatsarin shi a rayuwarka, iya yanzun ma an fara samun matsala ina kuma ta shiga harkokin cikin masarautan? Ka duba abinda nake nufi akan Ikram kayi hakuri ka rabu da ita, bata da Sa'a a rayuwarka. Idan so ne a duniyar nan babu wanda ya kai ni sonka da kuma kaunarka da Ikram, amma dole ce Kanwar naki zata sani na iya dauke kai na daga Ikram, don Allah ka rabu da ita" Girgiza mata kai yayi, sannan ya juya tare da barin d'akin, numfashi ta sauke sannan ta kalli yadda ikram take barci cikin wahala, kafin ta juya ta fita. A gaskiya bata kin Ikram amma halin da zata jefa rayuwar shi ce take jin tsoron Allah akan haka, kuma tasan zai yi wuya ya rabu da ita, shi yasa take jin kamar ta kori ikram idan taji sauki ko kuma ta saka a a lalata mata jarabawar da zasu yi. Amma kuma idan ta tuna yadda yarinyar ta b'ata lokaci tana zaune da Mehran sai taji jikinta yayi mugu mugun sanyi, taji bata da wani hanyar da zata iya cutar da ikram, sai dai kuma ba zata iya daukar kasadar barin shi ya zauna da ikram ba, Allah ya gani ba zata yarda da wannan tunanin ba, gwara duk abinda zai faru ya faru, amma tabbas zata raba su Insha Allah. Dan haka ita zata zauna da ikram har ta warke ta kuma maida ita garin su ta gaji yanzun son D'anta take bata jin zata bar shi ga kowa. *** Kura musu ido yayi tare da cewa. "Akan me zaku ce min Sultanah ta hana a cire al'adar duba al'urar mace? Gaskiya ba zai yiwu ba a cire shi ko kuma." "Indai akan ikram ce kake wannan zakewar ba dai kai ka ba, domin haka da zaka aikata shi zai sanya kowa ya zargi wani abu daga gare ta, dan haka ka ɗauke kanka akan Ikram ko kuma na sanya a fidda ita daga Masarautan nan baki daya." Inji Sultanah, shafa kanshi yayi tare da kallon kasa, tabbas yana tinzira ta, domin bata tab'a juyawa muradin shi baya ba, sai wannan karon. "Shi kenan, amma ba zan lamunci kasawa ba, dan wallahi idan aka min kuskure za a ga mugun tashin hankali.".ya fadi haka a zuciye, sannan ya bar gurin su.... ..~~~ a cikin wannan yanayin aka fara shirya abubuwan da za ayi, duk da kuwa an fara tarb'an baki daga yankunan kasar. Musamman y'ay'an gwamnonin shi, Sakeenatu binti Abu Waqqas da Azizatul Nissah, sune kawai suka rage basu iso ba. Gefe guda kuwa zamu iya cewa Alhamdulillahi domin jikin Ikram ya d'an samu sauki, sai dai bata iya jure tsayuwa ko kuma wani abun da zai sanya ta zauna na wani lokaci. Sannan wani karin tashin hankali yadda take wasu abubuwan kamar tab'abb'iya, domin zata iya daukar wasu lokuta bata yi magana ba, idan kuma ka bata abinci zata na kallon shi kamar taga dodo, dan haka wannan yanayin ya sanya shi shiga tashin hankalin da ya kasa fahimtar kome. Itace dai yake sakawa a gaba da tunanin halin da zata kasance. Ganin haka yasa Sultanah ta kuma niman Uwaisul Qarni, sunyi magana sosai har ya gaya mata cewa. "Ku godewa Allah da iya haka ne ya same ta, domin ban da Allah ya taimaka na bata addu'o'in kwanaki ba da wallahi sai abin yafi haka, dan haka ku kai mata wannan, sannan karki zata abinda kike bukata zaki samu, karki kuma yunkurin rabasu, hakan kuskuren ne babba, karki nunawa Ubangiji wayonki, shi da ya had'a su shi yasan yadda zai yi da kowannen su. Dan haka kar na kuma jin kin ce zaki raba su, domin wani tunanin dake ranki." Da wannan yayi mata sallama, tare da barin gurinta, haka ta kai wannan ruwan addu'o'in dakin Ikram ta bata, sai da ta shanye sannan ta fita. "Anne meke damun tane?" Ya tambaye ta ranshi a jagule, ajiyar zuciya ta sauke sannan tace mishi. "Jini yake bibiyarta, amma Insha Allah idan tayi barci ta farka zata ji sauki wasu abubuwan." Kasa jure bayanin da Sultanah tayi mishi, dan haka ya juya ya bar gidan. Bai tsaya ba sai shashin da Su Izmah suke ya shiga ya same su a tsaye Mahlika tana cin kaniyar su. "Waye ya baki damar hukunta wasu?" "Afuwa Sultan ba zan kuma ba!" Dauke kanshi yayi sannan yace musu. "Muje" haka suka bishi, cikin jin dadi ya kawo musu dauki. Bayan sun bar gidan ya kai su lambun da yake cikin gidan, suka nufa. Tun da suka zauna yayi shiru kafin ya tambaye su. "Izmah meye faru da Ikram domin na Fahimci kun jima tare," gyada mishi kai tayi sannan ta fara bashi labarin abinda ya faru, lumshe idanun shi yayi sannan yace musu. "Lallai biri yayi kama da mutum, sai yanzun na fahimci dalilin da yasa take saurin fushi, dalilai na rayuwa sun sauya ta, Ikram din da na sani ba ita bace wannan,wancan Yarinyar bace da nasani, halin wannan ya banbanta na wancan." A hankali yake gaya musu abinda ya faru, da yadda aka kashe Noman ba tare da sanin shi ba. Amma yasan koda yayi mata bayani ba kula shi zata yi ba, dan ranta yana kan fansa, dan haka ya kyale ta tayi yadda take so. ~~~ Sintiri take hannun shi goye a bayan shi, tun sati biyu ya sami labarin Ikram tana cikin Samaind bai yarda ba, sai da ya tura amintattun bayin shi mutane biyu, suka je har can suka binciko mishi ita, dan haka ba zai iya kyale ta ba, dan wallahi sai ya kuma dawowa da ita rayuwar shi. Shigowar Nawwas ne ya katse mishi shirun shi. "Sultan Abrad!" "Hmm!" Ya faɗa kamar zai zunduma ihu, kafin yace mishi.. "Ikram tana raye!". Cike da mamaki ya d'ago kanshi tare da kallon shi sannan yace mishi.."waye ya gaya maka?" "Na tura har mutane biyu sun duba min ita, amma tana cikin masarautar bata da lafiya, ka tabbatar sunyi aure da Noman?" Ya tambayi Nawwas yana me kallon shi. "Eh na tabbatar sunyi aure aka kashe shi." Murmushi Abrad yayi sannan yace mishi. "Kace min a daren amarcin su ko?"ya tambaya tare da kallon Nawwas, had'iye yawun yayi sannan yace mishi."eh Sultan Abrad" wani irin murmushin mugunta yayi tare da kallon Nawwas sannan yace mishi. "Dole Mehran ya bar min ita, domin an ce min zai gabatar da ita a zab'en da zai yi, ya ka gani idan na fasa cewa ta tab'a aure?" "Amma wannan kuskure ne babba, karka yi amfani da abinda kake ji akanta ka cutar da ita mana! Kayi mata adalci idan." "Kayi min shiru! Ikram tawa ce!" Ya faɗa da karfi, kafin ya shiga wasu zautattun bayanai kamar tab'abbe, yana gaya mishi abinda yake ji akanta, tare da yadda yake ji duk wanda ya shiga tsakanin su, sai uwar shi ta haifi wani amma tabbas sai ya kashe shi. "Sultan MEHRAN kuma sai na tsaya da karfin tsiya na raba su, ko kuma na raba mishi hankalin shi akan mulkin shi." "Gaskiya kana sonka ka da yawa, da yarinyar nan tana da ra'ayinka dangane da zama da kai da Nan zata dawo, amma dake bata da ra'ayin ka, gurin shi ta nufa, don Allah karka shiga abinda zai dame ka har karshen rayuwar ka" ya fadi haka a sanyayye. "Shawara kake bani ko gargadi na kake?" Murmushi yayi sannan yace mishi. "Abrad bani da ikon baka umarni sai dai shawara idan zaka dauka idan na zaka dauka ba kabarshi Allah ya kyauta, an jima zamu bar garin!" "Ka kira Samim! Zamu bar mishi garin zan biku!" D'ago kai yayi yana kallon Abrad cikin mamaki me tattare da damuwa. "Shi kenan!" Ya faɗa mishi, sannan ya bar d'akin. Wani irin murmushi yake irin na samun nasara akan abokin gaban ka. Yau zai je ya sami Ikram. ~~~> Yau saura kwana uku, A hankali na kalli Sultanah Fazilatul nisa, sannan na maida kai ma ga maganin gaba na, ina sha. "Yau ma gani a gabanki kamar can baya, nazo domin Mehran yana bukatar ki shiga cikin zab'en." "Tab" na fada tare da tab'e baki, "Me yasa kike son ganin sai na sami kusanci da shi? Wato dan d'anki ne ko? Toh gaskiya ni ba zan shiga dan shi ba, zan shiga ne dan biyan buƙatar kai na, dan haka ki kyale ni ba zan shiga dan shi ba sai dan rad'in kaina." Kallonta Sultanah tayi tare da jin babu dadi. "Amma me yasa baki jin Magana? Me yasa kike wahalar da mutanen da suka damu dake? Shi kenan, kiyi yadda kike so, amma ki sani, Allah ba zai tab'a barin hakkin shi ba, wallahi matukar kika jagoranci wulakanta shi, Allah sai ya saka mishi." Kasa nayi da kaina sannan nace mata. "Lokacin da ya kashe min mijina baki tausaya min ba, baki san yadda naji a lokacin b.." Bamu san shigowar shi ba sai ji nayi ya shake wuyata ranshi a jagule. Huci yake kawai dan bai iya magana ba, sai ɓari jikin shi yake ya bani tsoro sosai. "Sake ta nace" ta daka mishi tsawa, cikin fushi ya fita daga dakin bayan ya sake ta. Itama fita tayi daga d'akin, Izmah da Nimra da suke bakin kofa suka shiga d'akin. "Amma baki mutunci ko daya? Wallahi ba haka Mahaifiyar ki take ba, duk da sanin yarinta nayi mata Wallahi bata da rashin da'a, ke wacce irin shaidaniyar yarinya ce? Me kike bukata a rayuwarki? Kin san halin da Sultan Aamaan yake ciki? Ko damuwa da mutanen da suka kashe miki Mahaifiyarki baki yi ba, kin zo kin Buwayi rayuwar shi? Sabida ke yake rayuwa a nan,.sabida ke ya zabi ya xauka babu mulki wallahi Allah sai ya saka mishi, mutumin da bai ji ba bai gani ba kika tsana akan mutumin da bai kai iyayenki daraja ba,.na zata zaki tafi daukar fansan kanwarki ashe ke gurin bawan Allah zaki tsaya, jahilar banza jaka dabba, idan kin so karki shiga dan Mehran ki shiga dan ki kashe shi wawuya doluwa wacce jahilci da rashin kunya ya cika mata kai,Mahaifiyarki koda ta kasance Sarkin yaki bata yi aiki da hauka irin taki ba, idan kin so karki bar Mehran a raye. Ban da shima da damuwa meye zai tsaya samun damun kanshi da yarinyar da babu mamora a jikinta. Dube ki har zaki kira kanki da mace, banziya kawai." Sake baki nayi ina kallon yadda ake tijara, domin tsakani da Allah suka zage ni tass, sannan kuma suka rabu dani. Ban kuma ganin su ba, sai ma suka daina shigo min, har ana gobe za ayi abun lokacin Sultanah Fazilatul nisa, ya ajiye ranar zata bayyana kanta. Sai dai bata da kwarin gwiwar haka,.ina zaune Fudail ya zagayo bayan gidan da nake zaune, zama yayi sannan yace min. "Gobe Insha Allah za a gabatar da abubuwa da yawa,. Sannan Mehran zai so ki lashe zaben baki daya, Ikram Mehran yana raye cikin makiya ne, duk yadda nake son ki fahimta ba zaki gane ba, dan haka iya yau kike dashi tare da saka ido idan an gama zaben abinda sakamakon ya bada kina da karfin iko kashi talatin da biyar cikin dari, dan haka wannan damar da kike dashi ya isa ya tabbatar da cewa zamu sami sabon sauyi a Samaind, sannan don Allah karki saka idanu akan sauran matan, ki zuba musu ido idan suka tab'a ki ne zaki tab'a su karki yarda su miki tambarin da zai kai ki har fada domin matukar kika shiga makiyan Mehran da wasu zasu bayyana a rayuwarki..... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 33 "Sannan karki yarda wani yasan batun kinyi aure, idan ya fito daga cikin masarautan nan zamu dakatar idan ya fito daga wajen masarautan nan zamu kashe koma waye, Ikram Mehran ya shirya tsaf domin baki rayuwar shi, don Allah karki bari wannan damar ta subuce miki domin na rantse da Allah, mutane dayawa suna niman kusancin su da Mehran amma Allah bai nufa ba, ke da kika samu kina mishi rikon sakainar kashi, Mehran yana da kirki kuma yana da hakuri, rayuwa da kika ga yayi tsara mishi aka yi wanda Allah ya tsara mishi kuma aka ruguje shi don Allah karki juya mishi baya lokacin da yake bukatar ki, don Allah ki taimaka mishi wallahi yana cikin damuwa ainun." "Yana ina ne?" Na tambaye shi.. "Yana dakin shi da yake sama" ya faɗa tare da barin gurin, a hankali na mike tare da nufar cikin gidan, dakin shi na wuce. Samun shi nayi a dakin shi. A hankali na bude kofar d'akin shi. Karatu yake dan naji muryan shi yana tashi, da sallama na shiga d'akin. Ajiye Alqur'anin yayi tare da amsa mata, daga haka ya cigaba da abinda yake, tun da na shiga tare da niman guri na zauna. Ganin ya cigaba da karatun shi ya sani kallon dakin da yadda yake cikin. Kome a shirye yake sai kamshin turaren shi yake, ga wani sanyin dad'i da dakin yayi. Ya bada wani irin yanayi, me wiyar fassaruwa. Lumshe idanu nayi tare da ware su akan wani loka, haka kawai naji ina son ganin abinda yake cikin shi. Dan haka na kai hannuna zan bude naji yace min. "Kinyi min ajiye ne?" Juyawa nayi tare da barin bude kofar, kallon shi nayi yadda ya tara kasumba, idanu shi sunyi zuru, faffarar kirjin shi me cike da gargasa, ya kara cikowa sakamakon tarin kwanjin da suka cika kirjin. Sunkuyar da kaina tare da cewa. "Kayi hakuri da abinda na aikata" juya bayan shi yayi tare da Cigaba da abinda yake, domin idan ya cigaba da kallonta, ran shin ba zai so yadda take nuna nadamarta ba, dan haka ya juya abin shi zai bar dakin. Shan gaban shi nayi tare da cewa. "Ya ina magana ka share ni?" Na tambaye shi, "Me kika ce?" Ya tambaye ni cikin gajiya da gani na, eh mana ya gaji da gani na, idan na gajiya ba meye zai wani ce bai ji me nace ba. "Kenan baki ji me nace ba?" Na kuma kuma tambayar shi a karo na biyu. Tab'e baki yayi sannan ya girgiza min kai, da naga da gaske shiga ban daki zai yi nayi maza na tare kofar, zuba min ido yayi sannan ya bude baki zai min magana na riga shi. "Kayi hakuri mana" "Toh bani hanya na shiga wanka," matsawa nayi daga jikin kofar, da yazo shiga cikin banɗakin. Tsayawa yayi tare da bude kofar zai shiga. Riko hannuna yayi muka shiga tare, tunda muka shiga na fara hada mishi ruwan wanka, bayan na gama, na kalle shi. "Zoki goge min baya!" Ya faɗa min haka yana shiga ruwan wankan, zama nayi a saman gurin wankan na shiga wanke mishi kanshi tare da taimaka mishi har na gama na fito shima ya karasa, ina gamawa na fito daga dakin shi. Sannan na sami tawada da alkalami na rubuta musu karamar wasika, sannan na bar gidan tare da su Izmah basu so haka ba, amma babu yadda suka iya dani. Lokacin da ya fito yaga Anne da sakon ta karanta, murmushi tayi sannan tace mishi. "Yarinyar nan tana da kaifin basira, zata shiga amma bada ikon ka ba, zata shiga da ikon Aabis Bin Ansar, Sarkin sahara. Kenan idan ya shigo da tambarin wata masarautan." "Amma lallai Ikram mahaukaciya ce, kinsan daga Masarautun da tafito? Daga Askandariya da kuma Merocco ne fa, taya ba zata shiga da ahalin ba? Me yasa ba zata iya tsayawa danginta ba,.idan tayi kyau sahara za a kira idan ta ɓaci kuma wa za'a kira?" Ya faɗa a zafaffe, yau da Ikram tana gaban shi babu abinda zai hana shi ya mare ta, domin ya tsani renin hankali. "Ba zata so tab'awa daularta suna ba, sannan idan ta tsayawa danginta ta fadi abin kunya ce a gare ta,.idan kuma tayi nasara Cigaban su ce, dan haka ka kyale ta,.muga tsarinta tunda gobe za'ayi abin." Ajiyar zuciya ya sauke tare da kallon Sultanah, "Ni yanzun ban," "gidan Mahaifiyar Fudail ne zasu zauna domin ina ganin yau sahara zasu tawo da wakilar su." Haka suka shiga tattaunawa da yadda abin zai tafi yadda ya dace. --- Tunda na shiga dakin mahaifiyar Fudail,nake murmushi sabida dattijuwar tana da kirki da addini, tana yawan ganin yadda Nimrah ta takure guri guda, ni da Izmah kuwa hiran mu tayi da ita. shigowar Fudail ya kura mata ido, sunkuyar da kai tayi tana murmushi, murmushi mahaifiyar shi tayi tare da cewa. "Fudail itace Nimrah ko?" Kunyar Maman shi ce a kama shi yace min. "Ikram Sultan Mehran yana farfajiya." Fuskar damuwa nayi sannan na mike tare da yafa alkyabar ta, ina fita ha hango shi hannun shi cikin aljuhun wando shi, ya jingina da bishiya, tare da juya min baya. Tausayi ya bani a karo na farko bayan na dawo da niyyar sai na kashe shi. A hankali na taki bayan shi, na tsaya. "Amincin Allah ya tabbata a gare ka" "Kema haka ya tabbatar a gare mu baki daya, sarauniyar yan taurin kai, wallahi Ikram ina tausaya miki ranar da zaki shiga hannuna, Kinga kwana biyu ban saka ki kuka ba ko? Shine kike min yadda kika so? Sama kin bani hakuri zaki bar cikin Harami ne? Me yasa kike son nunawa duniya baki da daraja ne?" D'ago kai nayi sannan nace mishi. "Na sani mana, taya zan kai kaina cikin dangina nace musu nima daya ce daga cikin su? A'a kawai dai na zab'i muradun zuci ne nayi nisan da zasu nime ni ban sha'awa ace na kai kaina suyi tsammanin nazo yaudarar su ce!" Ta fadi haka a matukar sanyayye, rike hannun ta yayi cikin nashi yana kallon yadda take sunkuya da kai kasa, "Kina da hankali amma ba me yawwa ba, domin haukarki tafi yawa" murmushi nayi, bance mishi kome ba. Kuma ai bani da abinda zan ce, kawai dai na cigaba da zama kafada da kafada da shi, duk da hiran ta kurame ce amma kuma yana matukar muhimmanci. "Ashe kin iya fada haka ranar da nazo ma zata zan samu an yi gunduwa gunduwa da yar kwailata sai naga ashe kwaila jaruma ce har ta iya salon Mehran?" Kallon mamaki nayi mishi domin mutum ne da baida yawan magana, amma yadda yake surutun sai abin yazo min wani sabon a gurina. "Ki daina irin wannan dabi'ar mazan, ke mace ce bana son ki gaji mahaifanki. Sultanah nake so ki zama ba wata bardiya ba." "Kana sona ne?" Na tsinci bakina da tambayar shi, kallon juna muke tare da kasa furta kome, "kiyi hakuri! Ban tab'a sonki ba, kawai ina bukatar kine a rayuwata, kuma nasan kema kina bukata na a rayuwar ki!" Sunkuyar da kai nayi ban kuma cewa kome ba, kawai dai nasan nayi kuskuren tambayar shi, amma kuma me yasa kowa yake ganin kamar yana sona ne! Bayan shi ba sona yake ba, kawai ra'ayina yake. "Ki daina abubuwa dayawa ki zama mace sosai, na bawa Fudail sako yabawa Umman shi zata miki bayani," juya fuskana yayi tare da hura min iskar bakin shi yana me kallon kwayar idanu na, d'ago kai nayi tare son zan mishi magana, ya zira min harshen shi cikin bakina, zaro idanu nayi cikin wani irin tsoro da shaƙar shi. Iska ta hancina hannun shi yakai keya na, ban san lokacin da na cusa hannuna cikin rigar shi ba, tare da shigewa jikin shi. Ban tab'a jin yanayin da nake ji ba, mun jima a haka kafin na janye jikina daga cikin nashi, riko hannuna yayi tare da cewa. "Don Allah ki tuna da wannan gobe karki bani kunya,!" A hankali ya mike tare da mikar dani, hannun shi ya kai k'uguna. "Ina bukatar ki daina wannan dabi'ar mazan ki koma mace, duk cikin su kin fisu yarinta, so nake ki zama yarinya kamar yadda nake so." Kallon shi nayi tare da jin tausayin shi, sam bana jin dadin kusancinsa dani, an haka dai na daure muka shiga cikin gidan, har cikin gidan, nan aka kuma buɗe sabon hira, duk idanun shi yana kai na, tare da kasa cewa kome. A hankali muke satar kallon juna, sabida yadda muke da d'an tazara a tsakanin mu, murmushi nayi sannan na kalle shi, shima murmushi yayi tare da kallon na, yana min magana da idanu. Girgiza kai yayi tare da nuna min Izmah, lumshe idanuna nayi tare da gyada mishi kai. A hankali muke tare da kallon Izmah da take kallon mu, mik'ewa yayi tare da kallon Umma yace.. "Zamu tafi umma!" "Toh mun gode Sultan Mehran!" Murmushi tayi sannan ta bishi da addu'a, haka ya fita tare da kallon inda nake, dauke kai nayi tare da cewa. "Allah ya kai mu lafiya" Haka suka tafi,ina jin a raina tausayin shi yana rinyana, sunkuyar da kai nayi, wato tunda suka fita yaja tunga ya tsaya, duk ya rasa me zai ce, can kuwa yacewa Fudail. "Hmm, baka yi mantuwan ba?" Dake shima ya harbo jirgin shi, sai yace mishi. "Ban manta kome ba, sai dai ko kai?" "Hmm! Ina jin kam nayi mantuwa a cikin gidan." "Toh na kira maka Ikram sai ka saka ta ta dauko maka abin." "Hmm! Manta kawai mu tafi dare yayi" haka suka suka bar gidan babu wani armashi a fuskarshi. ---- Tunda suka tafi muke hira da Umma take min bayanin abubuwan da zanyi amfani dashi a cikin daren zuwa gobe da safe, sai kuma yadda take buƙatar nayi wasu abubuwan, kama daga tafiya na, kasa magana nayi ina kallon ta, har ta gama. ~~~ Da asuba su Abrad suka iso, garin SAMAIND ta jirgin ruwa, babban masauki aka tanadar musu, sannan suka kwanta Huce gajiyar su. Amma Allah ya gani baya ta matar shi,.Ikram ce yake bukata a lokacin. Dan haka ya kwanta da mafarkai akanta, washi gari suka shirya tsaf sannan aka ɗauki Azizatul Nissah aka tafi da ita su kuma suka take mata baya, A hankali ya'yan shuwagabannin yankunan da suka yi ta wucewa, wurin hatsi Sakeenatu binti Abu Waqqas ta iso, itama ta wuce sannan. Nima banyi tsammanin zan sami tawaga ba, aka turo na fito. Haka na fita sanye da wata rigar da aka kawo mintin daga Masarautan Sahara, tare da shigar alfarma wanda idan ka ganin zaka Fahimci lallai tabbas na fito daga babban masarautan,haka muka nufi cikin masarautan. *** Cikin shigar alfarma yake kallon yan matan da suke zuwa, har ya cire rai da zata shigo, domin ya kalli Fudail ya kai sau bakwai, kafin aka sanar cewa ga Amirah Bilqisul Ikram daga Masarautan Sahara. Yadda aka kawo ni tare da fitowa na, Yasaka zukatar mutane dayawa ya girgiza, dan haka na sunkuyar da kaina, tare da nufar inda aka ajiye mana kujerun mu, su Izmah da Nimra suna kallona, Idanun Abrad kuwa ya kur akan Ikram, yarinyar ta kuma girma da kyau, sai wani sheki take, ga wani shegen annurin da take fitarwa, a gurin dai ta zame mishi fitilar shi. Haka yayi ta kallonta tare da jin cewa tabbas ya mallake ta, kowa kuwa haka zai kuma tinzira zuciyar su ga yaki ne sai ya amshi abin shi, dan haka ya sauke ajiyar zuciya, tare da yarda da cewa, dole ya kawo karshen Labarin. Domin koda taci kome bazata zama matar sarki ba sai Kanwar shi. A ɓangaren Mehran kuwa hankalin shi a tare yake. A ranshi kuwa tambayar kanshi yake. _Wani irin Girma kike dashi ne a zuciyata Ikram?_ Ya kasa samun amsar domin kuwa, ya gama lallubar kome.... *Ana dara ga dare yayi.....* [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 34 MEROCCO Da sauri wani Bafade ya shigo tare da zuɓewa a gaban Sultan Mu'allim, tare da sadda da kanshi, jikin shi yana rawa. "Huzaif lafiya?" Amir Sulaiman ya tambaye shi, "Allah ya taimaki Sultan, An sami inda Ikram take." Jikin Rahil na rawa ya taso kamar zai fada kan Huzaif yace mishi. "A ina? Tana ina ne? Waye ya bada labarin ganinta? Ina yaƙe?" Yayi tambayar jikin shi yana rawa, "Tana SAMAIND!" Ya faɗa a sanyayye, kallon kallo aka shiga yi da dattawan fadan, bakin shi na rawa yace mishi. "Me ta jeyi a can?" "Ta shiga cikin zab'en matan sarki da..." Wani irin duhu ya gani tare da jin faduwar gaba, kaman zai zube kasa, haka ya kasance dashi. Idanun shi da suke cike da kwalla, yake lumshe su. Rike shi aka yi tare da shafa kanshi. Amir Sulaiman yake yana kallon shi. Tausayin Amir Rahil suke gabaki daya ya sussuce musu. "Nifa kawai ku tashi muje, kar mukara dan wallahi ba zan barwa kowa ita ba. Don Allah ku tashi mu tafi." Haka suka wuce dashi cikin gidan, nan suka shiga tattaunawa daga nan suka ajiye maganar yadda zasu tinkari SAMAIND ba tare da sun sami matsala ba. Duk da sun so ba zasu tafi da Amir Rahil ba, amma suka hakura domin matukar suka ce ba zasu tafi da shi ba, zasu iya samun labarin ya mutu. A yanzu ma ya aka kare dashi. Dan haka zasu tafi dashi. Sai dai sun san ba tafiyar yau bane dole su hakura sai gobe. A ranar aka kuma tura wani bafade har askandariya. Domin kuwa idan ba haka ba babu wanda zai kaiwa Sultanah Amrah labarin. ~~~ SAMAIND. Shiru gurin taron yayi kafin Fudail ya fara musu bayani kamar yadda ake yi, tare da nuna musu inda kayan abincin yake zasu diba. Sannan aka saka musu lokacin da zasu fara aikin. Haka kowa yaje ya dauki nashi cikin ladabi. Sai dai yaran shuwagabannin yankunan ne basu da dad'i. Domin magana suke gaya min, dan haka ban damu ba. Na nufi inda zan dauki nawa kayan aikin ne na samu sun kwashe kome. Juyawa nayi tare da kallon su, sannan na tafi na dauki ruwan da duka bari, haka na dauka tare da dawowa na rufe shi. Sai dariya suke min tare da kallona, ban damu ba ban kuma ji a raina zan fadi ba. Fitowar Sultanah ya saka mutane dayawa mik'ewa cikin tashin hankali da dimuwa, cikin su har da Amir Hood, tare da Sultanah Hoyam. Zama tayi a inda Fudail ya ajiye mata kujeran domin kallon yadda ake gabatar da abubuwan. Awa daya ya wuce sannan aka kuma samun awa biyu yazo. A lokacin kowa ya fara alaman ya gama abincin, ina kallon su. Mik'ewa suka yi nima haka, sannan Fudail yazo ya fara kwashe abincin yana kaiwa ana jerawa, tare da saka tambarin gidajen su. Da aka zo kaina suka dauki ruwan,. "Me yasa haka?" "Bani da zab'i." "Baki tunanin zaki fadi!" Murmushi nayi mishi sannan nace. " Allah zai tsaya min,Nasara a jini na take." Na fada mishi. Juyawa yayi gurin sauran ya musu magana sannan ya wuce. An fara gabatar da abincin da kuma tambayar kowa yadda suka hada, babu laifi wannan karon sunyi bazata, domin idan kaci abincin wannan ,.ka kuma cin na wannan sai kaji na wannan yafi na wancan. Haka ayi ta jingina musu musamman iyayen su. Ruwa ka gabatar mishi , kallona yayi cikin tuhuma. Sunkuyar da kai nayi, sabida yadda ake dariya daga manyan gurin har zuwa yaran su, sai Sultanah Fazilatul nisa ce ta kalle ni, Fudail yace min. "Ikram muna jin hujjar ki na kawo ruwa a madadin abinci." Mikewa nayi tare da rike hannuna, sannan nace Mishi. "Mulki ba iya abinci yake bukata ba ga talakawa, suna bukatar tsaro da kula da hakkokin su, sannan dole duk wacce zata kasance matar sarki ta kasance me tunanin rayuwar al'umma, babu wanda zai fito daga sahara ka dauki abinci ka bashi, sannan kayi tunanin zai yi rayuwa cikin nutsuwa. Ruwa yake bukata, kana bashi ruwa tamkar ka warware mishi duk wani abinda ya dauko ne daga can. Sannan muhimmanci ruwa Yasaka ake mishi kirarin ruwa abokin aiki, duk abinda zaka yi dole sai ka bukaci ruwa a cikin shi. Hatta masana kiwon lafiya su tabbatar da cewa. Kaso mafi yawa a jikin mutum ruwa ne, sai jini dan adam ba zai iya rayuwa babu ruwa ba, kamar yadda zai iya rayuwa babu abinci matukar akwai ruwa zai iya samar da abinci. Ba zaka gane baiwar da Ni'imar da Allah yayiwa Ruwa ba sai ka shiga sahara babu ruwa dai abinci nan zaka ga mutane da yawa suna mutuwa, amma idan da akwai ruwa zaka samu zasu kai labari duk lokacin da zaka ci abinci dole ka bukaci ruwa, dukda dashi ake sarrafa abincin, wannan shine dalilina na amfani da ruwa a cikin tsarina." Shiru kowa yayi musamman yan matan da suke ganin kamar sun lashe zab'en, sai juyawa suke suna kallona, wato nayi abinda basu iya ba, bayan an gama wannan sai aka bukaci mu dafa shayi. A tare muka tashi. Da haka iya ganyen shayin ne sai zuma. Tashi nayi tare da nufar Lambun da yake gurin na tsinko ganyayyekin masu kyau da kamshi, sannan na fara dakawa a hankali ina maida hankalina akan abinda nake, a cikin ganye akwai janye minnan nas, akwai ciyawar lemo,.akwai ganyen citta, da ganyen kanumfari, sai ganyen na'ana dan haka duk na dake su, sai ganyen ciyawar lemo ne ban saka ba, na barshi sai da shayin na dauko dafuwa na saka, a hankali kamshin ya cika gurin su kansu yan matan kallona suke kamar zasu yi ihu. Dan haka ina gamawa na zuzzuba a cikin kofunan sannan kuma na d'iga musu zuman,a hankali aka yi ya kai na sauran kafin aka zo kaina, suna zuwa Fudail yace. "Sannun da ƙoƙari." Murmushi nayi mishi sannan suka wuce da shayin, kai na a sunkuye na zauna,.ina jiran sakamakon. Kamar yadda aka raba na kowa haka aka kai nawa ya dauka a hankali yana kallon yadda na sunkuyar da kaina. A hankali ya kurb'a, dadda'ar d'and'ano da kamshi me gamsar da zuciya Yasaka shi d'ago kai yana kallona, kurb'an shayin yayi sanan ya kuma kallon yadda kowa yake shan shayin cikin gamsuwa, musamman Abrad da yake jifar Ikram da kallon duk da bata san yana yi ba. A hankali suka tashi suka fara bayanin su,.duk kusan abu daya suka yi dan haka ina mik'ewa nace musu. "Gabaki daya ganyayyekin da nayi amfani dashi yana magani. Domin dukkan su, ana mana abinci da shi. Sannan ita kanta wannan shayin idan mura ta dame ka, aka hada maka kana sha da Yardan Ubangiji zaka ji sauki sosai, shi yasa na hada shi sabida nasan dayawa ana fama da ciwon mura. Kasancewar muna yankin da take da yawan dusar ƙanƙara. Ita kanta maganin sanyi ce." Zama nayi domin sun yarda da abinda na faɗa, can aka kuma zuwa da wani bayani. Inda Darakshan ya kawo bayanin kamar haka. "Kasancewar kina matsayin Sultanah sai sarki ya tafi yaki, kuma bai talakawa babu abinci a tare dasu, kayan abincin su ya kare, gashi Sultan bai bada Umarnin a raba ba, sabida haka ke a baki tunanin me zaki iyawa talakawa? Sai manomin da yayi noma tare da saka tsammanin abincin shi zai kai labari, sai aka wayi gari d'an shi bai baida lafiya kuma yana da saniyar shi na hud'a, dan haka sai ya saka.saniyar shi da abincin shi a gaba wane zai sayar? Sai na uku, mutane uku sunyi laifi kuma ba a san waye mai laifin ba, dan haka sarki ya basu wasika akan su tafi can wajen gari su bawa dakarun. Sai kafin su isa sai aka fara ruwan sama, dan haka sai fada ta kama su. Har takai sun sake wasikar su a sunyi musayan wasikar, daya kuma yana rike da wasikar shi. Dan haka da suka isa gurin dakarun sai suka maida abinda ya kawo su, sannan aka amshi wasikar dayan su, aka duba..su kuma aka yanke musu hukuncin kisa? Bayan kuma daya ne mai lafiyan shin taya zaku gano me laifin?" A hankali Sakeenatu binti Abu Waqqas ta mike sannan tace. "Idan Sultan bayan ba zan tab'a dukiyar masarauta ba, sabida babu hurumina a cikin wannan yanayin. Na biyu kuma manomi zai sayar da saniyar shine domin lafiyar d'an shi. Na uku kuma a kashe su dukkan su biyu, domin koda za a tsananta binciken ba za a gane ne gaskiya ba. Wannan shine hujjata." Azizatul Nissah ta mike sannan tace. "Bazan yi katsalandan ga shiga harkan tallafawa talakawa ba, ai daman tun kafin a fara yaki dole zasu bukaci su tanadar da kayan abincin su. Na biyu manomi zai iya sayar da saniyar shi domin idan ya sayar da abinci bai da abinda zai ci,saniyar kuma ba zata isha shi ba. Na uku, wanda za a kashe shine wanda yazo da wasikar."dafe kai Abrad yayi. Sabida sam amsar ba haka ban. A hankali akayi ta tafiya har aka zo kaina. "Idan muka duba dalilin da yasan manomi zai fidda kayan abincin shi da saniyar shi ba ƙaramin lalura bane, domin abincin nan idan yayi tattalin shi zata kai shi har kafin faduwar damina me zuwa, dan haka babu hujjar sayar da saniya, abincin zai raba gida biyu ya sayar da rabi tunda yayi noman a wadacce, saniyar kuma da ita yake aikin nomar idan ya sayar da ita bai da wanda zai miki kwaftu, saboda dan shi bai kai wanda zai iya noma ba, shi kuma karfin shi ya kare. Kuyi min hakuri na fara da amsar manomi ne.. A matsayina na Sultanah, aka wayi gari Sultan Mehran ya tafi yaki kuma bai ce min kome ba dangane da al'ummar shi, gashi akwai kayan abinci a cikin Baitul Malin masarautan! Zan duba soyayyar su da kaunar su ga Sultan Mehran,.zan saka ayi ta diban abinci cikin dare ana kai musu kofar gidajen su, domin ya rage musu zaman dar-dar da suke yi. Bayan nan idan suka gani washi gari addu'o'in su itace kashin bayan dukkanin mulkin shi da nasarar shi. Sai batun masu laifi, akwai wani dabi'a na mai laifi ban sani ba ko wasu sun fahimci haka, amma idan mutum ya aikata laifi yana iya fin kowa firgice, sannan da zaka saka kanka a kirjin shi bugun zuciyar shi yafi na kowa, sannan abinda na Fahimta shine Mai laifin da ya fahimci shi za'a kashe shine ya dauke wasikar wancan, badan kome ba yasa ni fadar haka sai dan hujjar da nake da ita. Duk yadda akayi mutane biyu da suke jajjayan nan sun bude wasikar su..shi na ukun su bai san meke faruwa ba, dan haka su biyu sun san meye a cikin wasikar su.daya ne za a kashe ba dukkansu ba." "Shin ko Ikram zata gaya mana taya zata iya gane mara gaskiya, duk da, sun kafe akan cewa wasikar su ne?" Amir Hood ya min tambayar. Dan mik'ewa nayi tare da gaishe shi, sannan nace mishi. " Bayyana nayi bayanin domin mara gaskiya duk inda yake zaka iya d'ago shi, idanun shi yana yawan budewa, sannan shi kansa baya iya tsayawa guri guda ba, jikin shi kuwa rawa yake yi, tsoro takan zame mishi shimfid'a akan fuskar shi. Bayan haka yafi kowa zakewa da rantsuwa." Na fada sannan na zauna sai lokacin na kalli Mehran da ya haɗa ya dunkule hannun shi, yana kallona, fuskar shi ta bayyana farin cikin shi. Dayawan dattawan gurin magana daya suke, yarinyar yayi kokari tana da basira. Murmushi nayi ina me jin dadin nasarar da na samu, a hankali.suka yi ta bayyana mana sakamakon mu, karshe dai aka bankad'o tafiya na da nayi shi ya saka ban samun damar tsayawa a.matan shi sai suka barni a shugaban Kwarkwarorin shi. Mikewa Fazilatul nisa tayi sannan tace musu. "Wannan sakamakon bai yi ba, dan haka Ikram itace matar Mehran, ko kuma allura ta tono garma.., *Toh fa wata sabuwa....* [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 35 Cikin fusata Sultanah Hoyam ta mike tare da kallon ta, cikin fushi mara iyakata tace mata. "Wacece ke da zaki saka mana ,doka Mu kuma mu bi?" Murmushi tayi tare da gyara zama sannan ta kalli Ikram tace mata. "Kin cika duk wata sharudan da ake bukata, dan haka kece yau zaki gana da Mehran! A matsayina na mahaifiyar shi, na baki shi gudan shi ba b'ari ba." Kallonta gabaki daya Emiraters councilors din, suka yi domin abinda suke gudu kenan shigar Fazilatul nisa cikin harkokin Masarautab,. Tunda da suka ji labarin bata mutu ba suka san cewa tabbas tana raye ne domin fansar ta, dan haka suka mike tare da kallon ta, kafin suka ce. "Mun amince Yaran mu zasu zama Kwarkwarorin shi, sanan muna rokon Sultanah arzikin karta bawa Ikram karfin da zata juya a kalar masarautan." "Karya ne, Mehran d'ana ne dan." "Bani da lokacin ki, Ita wancan Yarinyar nake da Muradin a bata matsayinta! Ko kuma hmm!" Fazilatul ta sake murmushin mugunta. Cike da mamaki nake kallon ta, domin dai nasan tana da nata Muradin idan ba haka ba, me zai saka ta kafe akai na. "Toh an bar mata matsayinta a bisa sharadi guda uku! Sharadi na farko dole ta kasance budurwan! Sharadi na biyu dole ta kasance yar da tafito daga Masarautan? Sharadi na uku karmu kama ta da wani kuskure ko muji labarin wani mugun abu yafito idan ba haka ba. Hmm!" Yayi wani irin murmushi hade da kumshe bakin shi, yana kallon ta. Murmushi yayi sannan yace mishi. "Insha Allah! Na yarda da Allah kuma na yarda da ita, kuma Allah zai bamu sa'a." Ta faɗa tana murmushi. "Shin wai ince wannan kika tsayawa? Wannan kika tsayawa? Lallai kina bukatar nazari. Amma lokaci zai nuna mana." Takowa tayi daga sama, inda take zaune ta tawo har inda yaƙe, sannan tace mishi. "Mir Umdatuddawla ko kana da matsala da ita ne? Dan naga Yarka Yasmin kake taya kishi! Duk wanda yayi magana tabbas yayi magana ina da yakinin Yar shi yake tsayawa kishi, dan haka kowa ya zuba ido." Shiru duk suka yi tare da sunkuyar da kai, sannan ta juya kai ta kalle ni. "Daga ranar da kika amshi matsayinki na Sultanah ina son ki shiga binciken sanadin mutuwar Abdus Samad, idan kika amshi ragamar Sultanah ina son ki bincika mike faruwa a cikin masarautan nan! Idan kika yi haka zaki taimakawa mijinki gurin bincike! Kina da damar tuhumar me yasa aka dakatar da mijinki akan muqamin sa? Bayan nan kuma ina rokon adalci daga gare ki na bi min hakkina akan kazafin da aka min. Ina tayaki murna." Daga haka ta juya daga gurin taron, tana me jin dadin ta wanke abinda yake ranta, tabbas tasan ba zasu iya dakatar da matsayin Ikram ba, kodan tsira da mutuncin su. Sannan ba zasu so asirin da suke aikatawa ya fito fili ba, dan haka ta barsu da tashin hankali. Domin kuwa matukar suka barta tayi magana. Zata iya fadar abinda zai daure su har karshen rayuwar su, dan haka suka yi farin ciki barin ta gurin dan tana magana da yawa, duk yan matan an kira su tare da karrama su.. sannan aka kirani daga karfe aka bani kyautar da yafi nasu, bayan na amsa ni dasu Izmah da Nimra muka bar gurin. Takawa Abrad yayi har gurin Mehran, ya kura mishi ido sannan ya mika mishi hannun, cikin girmamawa yace mishi. "Kana ta farin ciki zaka auri budurwa ko? Koda yake naji an cire gwajin budurci. Domin wasu yan matan zawarawa ne, idan kuma dattawan masarautan ka suka ji labarin Sarki Abrad ya tab'a kwanciya da ita fa? Hhhh koda yake shima wancan ai sauran Abrad ya samu. Ka tambaye ta, tun bata kai haka ba, na saka mata girmana jikinta kuma ta dauke ni cif. Dan haka kasan dole sai ta cika sharadin budurci ko kuma hukuncin kisa ya haura kanta. Itama zata so na rufa mata asiri dan haka ka ajiye a ranka zaka fara jin kararrawan tashin hankali. Matukar ina raye Ikram tawa ce ni daya." Kura mishi ido Mehran yayi tare da sunkuyar da kan shi kasa, yana jin kamar ya dauki takobin shi ya dauke mishi kai cikin tashin hankali yake murza hannun shi, kafin ya d'ago kanshi yana murmushi yace mishi. "Zan iya cewa haushin ka rasata yasa ake gaya min magana haka ba. Dan haka babu damuwa koda a gidan ƙaruwai na samo ta, tabbas zan zauna da ita." Cikin fusata ya kalli Mehran sannan yace mishi. "Tabbas zaka yi kuskuren da ba zaka manta ba, domin zan kashe duk wanda yake tare da ikram, domin ita mallaka ta ce" "Ina ga baka tab'a kowa Askandariya ka tambayi ina Yar uwan matanka take ba ko? Zanga yadda zaka iya hada kazamtar da kake shirin aikatawa." Daga haka ya juya tare da barin gurin, domin jin kirjin shi yake kamar zata fashe, yana shiga ya hango ikram daga nesa, wani irin tausayin kan shine ya kama shi. Meye laifin shi da kaddarar ta yake walagigi dashi? Me yasa ba za'a barshi ya huta da ita ba, sai tashin hankali da damuwa. Kura mata ido yayi yaga yadda take dariya da farin ciki. Ji yayi wani kamar zai fashe da kuka domin kuwa yana hango yadda Abrad ya kwanta da ita, tare da hango Yadda Numan yayi ta juya ta a shimfid'ar shi. Wato maza biyu sun keta mishi alfarman shi, sunci mutuncin shi sama da yadda ake cin mutuncin wani a duniya, da takalmi suka dauka suka dake shi da shi ba zai mishi ciwo irin wannan da Abrad yayi mishi ba, ji yayi duk wata alfarmar da yake dashi ya tsinke gani yake kamar duk wata mutuncin shi sun tsinka mishi. Duk da yasan tayi aure baya jin haka yayi mishi ciwo kamar yadda Abrad ya nuna mishi ya kwanta da ita..mafi kololuwar ɓaci rai da ya tab'a ji a ranshi kenan. Dan haka ya bar abin a ranshi kafin yasan mafita. *** Had'iye yawun Abrad yayi tare da juyawa yana kallon taron jama'a da suke watsewa. Ba dai Ikram Yar Joindah bace? . tabbas idan yarta ce ta haramta mishi, innalillahi wa'inna ilaihi rajioun me yasa haka ya faru dashi. Lallai dole ya dakatar da kome ya tsaya Domin rusa Mehran da ya ikram, idan ba haka ba tabbas zai yi biyu babu, ya kwadaitu da jikin Ikram, dan haka koda zai mutu ya dawo wallahi sai ya shiga ya mata faca faca da ruwan jikin shi. Wannan shine tunanin da ya tsaya a ranshi, dan haka yayi wucewar shi zuciyar shi daya..yana haduwa da Nawwas ya gaya mishi abinda ya faru. Ba karamin kaduwa Nawwas yayi na, tare da cewa. "Wallahi baka da kirki! Me kake shirin aikatawa? Yarinyar da babu aure a tsakanin ku shine zaka shirya mata mugun makirci haka..toh wallahi zan gaya mata gaskiyar abinda kake shirin aikata mata domin ta farga daga abinda kake shirin aikata mata ai wannan rashin imani ne idan kanwarka aka yiwa haka ba zaka ji dadi ba, dan haka wallahi dai na gaya mata idan ban sami ganinta ba zan gayawa Mehran dan yaji abinda kake shirya musu.. son kan ka yayi yawa toh wallahi ba zan tab'a barin ka, ka lalata musu rayuwa ba, tunda kai kana da naka rayuwar!" "Nawwas ni kake gayawa Magana? Toh naga wanda ya isa ya dakatar da ni." Ya faɗa da karfi, nan fada yaso kaurewa a tsakanin su, dakyar wasu daga cikin dakarun suka raba su. Cikin fushi Nawwas yace mishi. "Wallahi ina sane da kome da ka aikata, kyale ka nayi kawai amma wannan karon zaka sha mamakin abinda zai faru." Cikin mugu mugun fargaba ya kalli Nawwas, sannan ta danne abinda yake ranshi. "Na gina ka da hannuna, sannan Ni zaka kashe. Tabbas kai butulu amma zan baka lokaci ka nime yafiyana kafin na fusata akan ka." Inji Abrad. Dariya Nawwas yayi cikin takaici da haushi yace. "Wato kai har dama ake bani na nemi yafiyarka? Toh karka yafe min, ka zauna a gurin na kyale ka ne, amma tabbas idan akwai wanda ya dace da Ikram ni ne ba kai ba, domin ni na fara sonta lokacin da na sayo ta." Hannun shi ya saka a cikin aljuhun shi sanan ya ciro jakar kudin da Abrad ya bashi lokacin da ya tura ya sayo mishi ikram. "Wannan Shi ne, jakar kudin da ka bani, ita kuma da kudina na sayo ta, dan haka karka kuma alakanta kanka da ita, domin ni na barwa Mehran ita." .ihu Abrad yayi tare da kaiwa kasa duka, yana fadin. "Wallahi baka isa ba, Ikram tawa ce wallahi sai na kashe ku dukkan ku, akan Ikram sai kashe kowa domin ita tawa ce. Kai ma ka fara gudu domin na kyale ka zanyi ba." Wannan rigimar bata yi musu dad'i ba, domin karfi da yaji suka zama abokan gaba, kuma Abrad yayi alƙawarin sai ya kashe Nawwas shima kuma yayi alƙawarin sai ya fadi gaskiya kafin ya kashe Abrad. Da kyar aka fidda Nawwas daga cikin gidan, domin fadar sun tayi ƙamari Sosai. ~~~ Yana zaune yayi shiru tun da ya idaar da sallah, yake kallon waje yana son ganinta amma idan ya tuna zantuntukarka Abrad sai yaji kirjin shi yayi zafi, shigowar Fudail a karo na biyu ya sashi d'ago kanshi yana kallon shi. "Sultan MEHRAN! Ikram tana son ganawa da kai." "Kace mata ba yanzun ba." Ya faɗa fuskar shi a daure, "Toh sai yaushe Mehran?" Na tambaye shi lokacin da na shigo d'akin, juyar da kai yayi tare da cewa. "Ka fitar min da ita bana son ganinta." Ya faɗa tare da juya min baya. "Akan me baka son gani na? Meye nayi maka da zafi da kak'i kallona, ko baka so na zama abinda kake bukata bane?" Na tambaye shi muryana yana rawa, Mikewa yayi tare da nufo ni, bai yi wata wata ba, ya riko damtsen hannuna ya turo ni waje, sannan ta kalli Fudail shima ya fita dan baya son magana. Kasakai nayi ina kallon kofar Mehran, na rasa gane abinda Mehran yake nufi dani, kallon Fudail nayi domin shi daya ne kawai zai fidda Ni cikin duhun da nake ciki. "Karki ga laifin shi. Sultan Abrad yayi mishi wasu maganarki wanda ban san me ya gaya mishi ba." Bakina yana rawa na kura mishi ido, sannan na juya tare da barin shashin sa, na nufi inda nake da zama, a hanyar wucewa ta naji Kwarkwarah shi wato Sakeenatu binti Abu Waqqas tana faɗin. "Idan mace ta isa bata bin namiji shi yake binta" halin da nake ciki bana jin zai barni nayi magana kawai na kad'a kai nayi gaba abuna, sabida ba zan iya daukar tashin hankali biyu ba, ga nashi ga na wad'anda ban san kansu ba. .... Tunda na zauna nake kallon madubi, abisa ka'idar zan kai mishi abinda da kuma zama dashi dan hira, sai dai shigowar Sultanah ta zuba min ido. "Me yasa Mehran ya bukaci Jasrah bake ba." Murmushi nayi sannan nace mata. "Eh naje d'azun nan kuma gaskiya ni bana son na amshi ragamar shi sai ranar da aka daura min igiyar shi a kaina, su kuma suna da damar shiga gare shi. Tunda matar da zai aura ce ni kamata yayi nabi tsarin addini da na Ubangijin." Takowa tayi gabana, sannan ta zauna kamar yadda na zauna..kafin tace min. "Addinin ki da Ibadar ki yasani mishi kwadayin ki, idan ba wani abu me karfi ba,.nayi imani da Allah ba zaki juya mishi baya ba, domin kuwa babu kwaɗayin duniya a ranki don Allah ga Mehran nan ki tsaya mishi Insha Allah zaki yi nasara." Murmushi nayi domin kuwa ban san me zance mata ba, amma kuma ina tunanin zan mata yadda ta bukace ni. *Ana dara ga dare yayi....* [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 36 Kasa gane kan MEHRAN nayi kowa yana jin dadin mu'amala dashi ban dani, tun Fudail yana ƙoƙarin gano yadda zai magance matsalar mu ya kuma sassanta mu, abin yaci tura. A cikin kwana uku kacal Mehran ya nunawa kowa baya tare dani, domin kuwa Zanyi kokarin tinkarar shi domin magana yana gani na zai mike ya nemi hanyar barin gurin. Ko kuma yana gani na zai tsira fushi da b'ata rai. Bana jin dadin haka ko babu kome bai dace sabida Abrad ya gaya mishi magana ya nemi juya min baya, ranar da ya nime jasrah. Dan sai da tayi kwana uku a cikin turakar shi, kafin hudun ta fito, nan ne tana fitowa aka bata matsayin (Lady royal) tafi kwarkwarah ta kuma fi karfin a kirata da kuyanga, matsayi ne wanda yafi na kwarkwarah. Shi yasa tana fitowa ta fara gudanar da aikinta yadda ya dace. Abinda ta fara shine ta turo da wasikar lallai sai dai ina fitowa cikin su ina cin abincin. Sannan ta zab'a min bayi mata guda biyu, sannan ta turo min su. Ajiye takardan nayi sannan na kalle su, a tsanake kafin nace musu. "Nagode! Sannan ku gaya mata bana bukatar kowa, ina da yan uwana na jikina bana bukatar masu taimakona. Batun cin abinci kuwa kice mata shima na gode ni mace ce kamar zinariya baka cin abinci a gaban kowa sai wanda ya ajiye ni da kuma yan uwana." Haka suka fita abinsu, ban san me ya faru ba, sai gata tare da Mahlika. Suna zuwa basu yi wata wata ba, tasa aka rufe Izmah da Nimra da duka. _Dole zasu biyo ki! Musamman yadda suka fahimci kina da matsala da Mehran, kiyi kokarin dauke Kanki kansu_ inji Fudail. Dauke kai nayi haka suka musu lillis, kafin suka juyo kai. Tare da takowa har gabana, sauran matan suna bayan ta. "Na saka doka kuma dole kibi yadda nake son domin nice budurwan masarautan. Idan zaki ga Mehran dole sai kin biyo ta hannuna." Ban kalli inda suke ba, dan haka suka juya suka fita. Da sauri na isa gurin su Izmah zanyi magana tace min. "Karki damu, ai Sultanah ta gaya mana. Dole zaki fuskanci wannan yanayin, ta bamu hakurin mu tayaki jurewa, Babban matsalar ki kama Mehran a hannunki, idan kika kama shi har abada ba zaki kuma fuskarta matsala ba." Hawaye ne ya zubo min tare cewa. "Dole na nimo Abrad, naji meye ya gayawa Mehran haka?" Kallona suka yi sannan suka ce. "Babu Matsala a fitar ki? Don Allah Karki kuma yin abinda zai jefa ki cikin matsala." "Babu kome zanje ba zan jima ba. Kayanki zaki bani Nimrah." Had'iye yawun tayi sannan ta mike ta cire, sakawa nayi sannan na fita a saɗaɗɗe. Ina samun na bar harami na sauke ajiyar zuciya. Ban tsaya ba, sai masaukin su. Ina zuwa na sami Nawwas yana tare da wasu dakarun. Ka rasawa nayi gurin shi. Sannan nayi mishi magana. "Ikram!" Ya ambaci sunana da mamaki. "Ina Abrad?" "Yana cikin gidan!" Nufar hanyar cikin gidan nayi, ban tsaya ba sai da na dangana da cikin dakin da yake. Tun a bakin kofar shiga, na dauki takobin shi. Ina shiga na same shi da mace shi banyi wata wata ba, na saka mishi tsinin takobin a kirjin shi. "Meye ka gaya mishi?" "Dama nasan zaki zo aiki, abinda na gaya mishi kike son sani?" "Maganar banza nake son ji?" "Wannan kuma duk ke ta shafa, dan haka ina tayaki murna domin tarko na d'ana miki kuma yanzun haka Mehran yana bayanki! Zai zo ya same ki a cikin gidan nan." Cikin fushi na yanke shi da kaifin takobin, cike da mamaki yake kallona idanun shi waje. "Ko zaki kashe ni ba zan fasa gaya mishi magana ba, kuma zaki gani da idanun ki idan ya karaso!" Cikin mugun b'acin rai na kuma dukar shi da kasar takobin, abinda ya bashi damar riko hannuna, daidai lokacin da Mehran ya bude kofar dakin kenan.. shi kuma ya fisgoni na fada kanshi. Ya kuma yi amfani da karfin ya juyar dani akan idanun Mehran. Juyawa yayi tare da barin kofar d'akin, ina mik'ewa na kai mishi duka a gaban shi dai da ya suma..sannan na fita na damu yana tafi ko dokin shi yaki dauka haka Fudail shima ya kasa hawa kan dokin Nawwas yana bin shi tare da mishi magana. Amma bai kula shi ba. Da sauri na sha gaban shi. "Aamaan ka saurarre Ni, wallahi yadda kake tsammani ba haka bane." Dariya ya saka wanda tunda nake dashi ban tab'a ganin shi yana dariya ba, sai murmushi. Sosai yake dariya har da dafe bishiya. "Aamaan don Allah ka saurarre ni, wallahi nayi kuskuren zuwa amma kayi alakari da abinda ya baro ya kawo ni gurin shi." Kura min ido yayi sannan yace min. "Kiyi yadda kike so! Gashi nan nan da sati daya zaki koma inda ake bukatar ki." "Mehran me yasa kake son tilasta zuciyarka ganin laifin da ba nawa ba?" "Akan me ba Zanga laifin ballagaza karuwa makashiya, sha-sha-sha me kwanciya da mijin Kanwar mahaifiyarta? Akan me zan yiwa kaina adalci bayan ta sani kawo datti cikin masarautan da babu dad'i a cikin shi. Ke kazama ce. Wallahi da iya auren Numan kika yi zan yarda na zauna dake akan kwanciya da wancan kazamin, zaki iya tafiya. Amma karki yarda ki bar min kome da yafito daga hannunki." Ban tab'a ganin abinda ya sani kuka har na kasa hawaye ba, sai kalaman Mehran, yayi min zafi da ciwo. Ina kallon shi ya bar ni a gurin kuka nake sosai. Kamar raina zai bar jikina Mehran ya min mugun zato. Haka suka tafi Nawwas kadai ya zauna a kusadani yayi ta bani hakurin. Karshe haka na mike tare da barin gurin. *** Tunda na shiga cikin gidan ban kuma sha'awan fita ko kofar gidan ba, sai da naji labarin ana bikin maidawa Mehran kujeran shi, ban ko leko ba Kwarkwarorin shi suka yi ta bidiri, a lokacin Fazilatul nisa ta Fahimci akwai tashin hankalin a tsakanin mu, ta same shi ayi magana yaki bata lokacin shi sai uzirin da yayi ta kawo mata, ni kuma na kasa cewa kome. Ranar da akayi bikin da yamma Baƙi daga Merocco da Askandariya suka zo. Kukan da nake sabida farin ciki ya kasa misaltawa. Tunda suka shiga falon shi. Yake juye- juye, yana niman ta inda zata fito. Cikin shigar alfarma nayi sallama a katon falon shi. Suna zaune. Da sauri ya mike tare da nufar inda nake yana faɗin. "Salsabilah na." Rungume ni yayi tare da sauke ajiyar zuciya. Kuka ne ya kwace min tare da kai hannuna na rungume shi..ina kuka sosai. "Kiyi hakuri, gani nan nazo gare ki babu wanda zai kuma saka ki kuka kinji.". Jinjina mishi kai nayi tare da rike rigar shi. Kokarin danne tashin hankalin da yake ciki yake amma tabbas da ace mutanen gurin zasu Fahimci halin da yake ciki da su da kansu zasu bukaci Amir Rahil ya sake Ikram dan ji yake kamar kirjin shi zai fashe da tashin hankali. Zafin da yake ji ya hana shi sakat, dan haka ya dauki ruwa ya shanye tass, sannan ya dauke kanshi daga gare su. Janye jikin nayi tare da kallon yan uwa da dangin mu, zama nayi a kusa da sultanah Amrah,. Wacce kamar ta daya da Ummyn mu, zama nayi ina me jin kuka yazo min tunda na kifa kaina a kafad'arta nake kuka, domin nayi imani da Allah idan na tafi ba zan kuma dawowa SAMAIND ba. "Ya isa haka?" Ta faɗa min a sanyayye, Wazir din Merocco ne ya fara bayani a hankali tare da girmama juna, sannan ya kuma faɗa mana makasudin zuwan su. "Alhamdulillahi mun gode Sultan Mehran, gashi zamu dauke maka ita, sannan muna me baka hakuri abisa abinda zamu gaya maka. Mun yiwa Ikram Miji Amir Rahil. Wanda shine Sarkin mu na gaba, dan haka zaka yi hakuri da yadda muka zo a makare." A razane na d'ago kai na, ina kallon Rahil da yake ta zabga min murmushi. Sannan na maida kai na, ga Mehran wanda ko a jikin shi babu abinda ya dame shi. Cikin dakewa ya kalli inda nake amma kuma zuciyar shi sai girgiza take, sannan ya fesar da iskar bakin shi kafin tace musu. "Babu damuwa! Allah ya bata zaman lafiya..Insha Allah nima zan so zuwa bikin" Kura mishi ido nayi hawaye na zuba daga cikin idanuna. Ina kuma kallon shi. Dani zai yi Yakana??? A kaina zai saukar da YAKANA?? Wato sabida rashin adalci ya gwammace ya hakura da aurena saboda na tab'a mu'amalantar wani da namiji, rike hannun na, Sultanah Amratu tayi tare da cewa. "A duk lokacin da muka ga hawaye a kan idanun jama'ar muna da yakinin suna cutuwa ne da mulkin mu. Amma idan aka wayi gari munga wahale akan sarauniyar mu, tabbas muna da yakinin abu biyu ya sata kuka. Farin ciki da bakin ciki,. imma soyayya mara iyaka,.indai akwai daya cikin biyun da nayi magana akai toh wajibi ne Ikram tayi hakuri tare da YAKANA!" Yadda take maganar babu wanda zai fahimci magana take sabida yadda take yi a sanyayye, share kwalla nayi sannan.. na sake mata murmushi, kafin muka nufi cikin gidan. Muka shiga hada kayana,. Ita kuma Sultanah Amrah ta nufi Shashin Sultanah Fazilatul nisa, anan suka shiga hira, mazan kuma aka kai su masaukin su. Banda Rahil da yace babu inda zai je, ina zaune ya turo naje. Tunda na isa gurin a bakin wani tafkin da agwagi suke wanka, muna zauna dashi. "Tun bayan tafiyar ki nayi ta jinya." "Toh Sannun;" Rau-rau yayi da fuska, kamar zai fasa ihu. "Na zata zaki tambaye ni akan me nayi jinyar?" "Toh kayi hakuri, ?gaya min akan me kayi jinyar." Dariya yayi sannan yace min. "Akan sonki mana" kallon shi nayi domin banyi mamaki ba, amma kuma ni bana jin wannan yanayin a tare dashi, ji nayi kamar ana kallon mu na juya. A hankali, sake labulen tagar shi yayi. Nima a sanyayye nake kallon ruwan gabana. Ina me jin zafi da ciwon abinda ya faru. --- Kallon yake tun da suka fito yake kallon su, bai tab'a ganin mutanen da suka dace da juna kamar Rahil da Ikram, a hankali ya sauke ajiyar zuciya bayan ta juyo tana kallon shi, sake labulen yayi.sannan ya kalli Fudail ya ya jima da shigowa. "Me yasa kayi shiru ba tare da ka gaya musu yadda kake kaunar ta ba? Me yasa ka xabi'a YAKANA akan kaunar da kake mata? Wannan babu adalci.". "Ya isa haka. Karka manta na ce maka na rabu da ita, na rabu da ita har karshen rayuwata, dan haka karka kuma kawo min batun wata Ikram." Ya dakawa Fudail tsawa, ka rabu da ita kake leken ta? Ka rabu da ita ka gaza rike hawayen Soyayya! Dubi Cikin idanunka zaka Fahimci itace muradinka don Allah karka kashe abinda ba zaka iya raya shi ba. Zaka iya kashe so amma raya shi nada matukar wahala, don Allah karka rabu da ita, ka koma ka gaya musu ita ce zab'inka zasu Fahimce ka." Kamar ya daki Fudail yake ta huci, shi dai bai fasa ba kuma bai daina gaya mishi gaskiya ba, har dai da ya kore shi daga dakin sannan yace mishi. "Kaje ka aure ta, na yafe maka ita." Dariya Fudail yayi sannan yace mishi. "Tun duniya na kwance naso aurenta Allah bai nufa ba dai yanzun da nasan tana cikin zuciyar Mehran. Kawai kayi wani abu a gyarota." "Ba zanyi ba! Ba zan iya ba. Ba zan tab'a yarda na zubda kimata ba dan haka ka barta ta tafi. Ni dai na yafe Ikram har karshen rayuwata. Ta zalunci rayuwa ta, ta lalata min rayuwa,tayi nasarar jefani .... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 37 "Wani irin rayuwa ta lalata maka? Wannan ni banga wani laifin da kake danganta da shi ba, sabida ai a baiwa tazo masarautan nan, kai kana da tabbacin." Kasa fadar abinda yake son ya faɗa yayi tare da kallon Mehran dan yasan maganar ya yi mishi girma. "Ba budurcin ta nakewa hidima ba, itace nakewa hidima. Idan har zan iya hakura da shugabanci na, domin laifinta an kansa bata da abinda zan iya samun a gare ta fansan abinda na rasa, kawai na hakura da ita ne." Ya faɗa a sanyayye. Sannan ya juya, yabar gurin baki daya. ~~~ "Sultanah ga koshi ga kwanan yunwa, domin kuwa nasan Ikram na barin SAMAIND Za'a daurawa Sultan Mehran Jasrah abinda ake gudu zai faru." Inji Narjis. Cikin dakewa tare da ɓoye tashin hankalin ta, ta sake murmushi sannan tace mata. "Allah yana tare da Mehran, shi yasa koda an ɓullo mishi ta wani gurin ,zai kauce ta wani gurin. Ita kuma Jasrah karki damu da ita." Ta faɗi haka tare da ɗauke kanta. Wato kuka take son yi, amma bata son Narjis da Shairah su karaya,. Balle shima Uban garin yaji labarin. Kasa dannewa tayi ta mike zuwa ban daki ta zauna tare da fashewa da kuka. Kuka irin me tab'a zuciya da ruhi, kuka take tare da jin ina wannan ranar bata zo ba,.me yasa Ƙaddarar su take da zafi ne haka? Ga baki daya bata da inda zata kama tace gashi shine mafita a gare ta. Tana ji tana gani zata kuma rasa Ikram, a hankali ta wanke fuskarta tare da fitowa d'akinta, ta same su. Suma kuka suke, cikin juriya ta zauna tana kallon su. "Idan Allah ya baka lafiya sai kai ta jin dadi da farin ciki, idan kuma ya baka Arziki baka da kwanciyar hankali, idan ya baka mulki kai da farin ciki har abada. Gashi ya bashi kome amma ya hana shi farin cikin rayuwar shi, soyayyar da yake riritawa itama ta subuce mishi. Mulkin da yake kai ya rasa, dukiyar da yake da ita bata amfane shi da kome ba, sai tarin tashin hankalin da damuwa. Ita da nake ganin itace kwarin gwiwar shi ashe ba haka bane.." ta karshe maganar cikin rawan murya alamar zata yi kuka. Duk wanda yake dakin sai da ya zubda kwalla. Dan haka suka zube gwiwar su a kasa suna kuka. Murmushin tausayin MEHRAN tayi sannan ta juya tare da cewa. "Ku kira min Ikram" Da sauri Narjis ta fita. ...“Mace idan ta isa mace ta zauna a daularta ba sai ta biyo namiji ba, amma ayi mace mara daraja da kima, don Allah ku hada kaya ku koma can." Kallon Yesmin nayi sannan na sake murmushi kafin nace mata. "Zan bar muku Aamaan Abdus Samad Mehran na biyu, zan tafi na barshi kamar yadda nazo na same shi." Dariya ne ya kwace min sannan na cigaba da cewa. "Idan na tafi kunyi ban kwana da farin ciki, kun daina ganin dariyar shi da murmushin sa. Kuma ai dama ba ma'abocin yi bane dan haka sai kinyi danasanin mara amfani." Shigowar Narjis ya sani kallonta, kafin na juya zan tafi tace min. "Amirah Ikram!" Juyawa nayi tare da amsa mata. "Sultanah tana mahaifiyar Sultan Aamaan Mehran, tana son ganawa dake. Sirikae mafi soyuwa a zuciyar Sultanah Fazilatul nisa" .kallon Jasrah nayi sannan na juya kai na, kafin nace musu. "Mulki ya haife ni, amma yadda nake jin shi ko kuda aka haifa cikin masarauta ba zaku nuna min mulki ba. Uwar Mehran! Mahaifiyar Aamaan Mehran take don ganawa dani. Daga mahaifiyar shi sai ni kaf daular nan babu wanda ya isa ya kira shi da Mehran! Dan haka kadangarun bariki bani da lokacin da zan b'ata akan shi ina kishi. Duk macen da bata had'a zakuna a gabanta suna yaƙi akanta ba. Sunanta lusara jakar mata macen da ta isa da kanta take haɗa zaratan maza! Ko yau Mehran bai isa yace na biyo shi dan soyayyar shi ce, kudirina ya kawo ni gare shi bayan haka bani da wani abin da zan ce nazo daukar daga gare shi." Ina gama gaya musu haka, na fita tare da barin su a gurin suna mamaki na, nauyin da yake raina na sauke tare da jin nutsuwa a raina, sannan na Barsu da kallona. Har muka b'ace. "Ne yarinyar nan take nufi? Wato duk cikin mu babu wacce zata iya kiran shi da Mehran." Inji Sawda, "Ga alamu nan, dukda nasan na tab'a haduwa dashi amma ban sami zarrar kiran shi da Mehran ko Aamaan ba, amma kiga ita yadda take kiran sunan shi gaskiya Sultan Mehran ya bata dama dayawa." Inji Yasmin. Jasrah bata ce musu kome ba, amma kuma a hankali take fuskarta abinda suke tattaunawa, ita dai tasan ko kwanakin da tayi a dakin shi bata iya d'aga kai ta kira sunan shi ba, a iya kwanakin da tayi bata da wani sabon abu da zata iya nunawa nacewa yana tare da ita, domin duk zamanta a dakin babu abinda ya haɗa su. . Sai tausa da bashi ruwa da wasu labarai har ta cika kwanakin babu abinda zata ce gashi ya faru a tsakanin su. Shi kuma dan ya tuzira Ikram ya bawa Jasrah damar zama wani abu a jikin shi sannan yace ta iya da bakinta ta nuna cewa kome a tsakanin su ya faru, sannan ya tara mata manyan gwala-gwalai ya sallame ta dashi tare da bata wani babban daki wanda ya kusan kai na Ikram girma. Duk yayi haka ne dan ya tinzira ikram, kuma ya yi nasarar haka, domin kuwa ranar da tafito take farin ciki tare da habaici. Kasa barci Ikram tayi, kuka kuwa dannewa tayi tayi, a cikin daren sau uku tana zuwa turakar shi yana cewa ace yana aiki ne ta tafi sai ya sami lokaci zai kirata. Har yanzun yau da yaki sauraronta, tana jin zafin haka balle kuma da ya kamata da laifin zuwa gidan Abrad. Shi yasa yaji ta bashi haushi baki daya, yaji ya tsane ta baki daya, baya kaunar ganinta koda wasa, amma kuma haka bai hana shi jin tashin hankali da damuwa ba, domin kuwa yana jin ba zai iya hakuri ya rabu da ita ba,.idan ya tuna abinda take aikatawa sai yaji kamar ya cire zuciyar shi ya huta domin kuwa yana zaune kalau ta haɗa mishi tashin hankalin da bai taɓa kawowa a rayuwar shi ba. ...... Koda muka isa dakin Sultanah, Narjis ta gaya mata abinda matan suka min. Murmushi tayi sannan tace mana. "Ita ikram kallon su tayi bata ce musu kala ba?" Sunkuyar da kai kasa tayi tare da rike hannunta tace mata. "A'a ai tana da kaifin basira ta gaya musu abinda ba zasu iya ba koda zasu shekara dubu da Sultan Aamaan Mehran" "Hmm!" Tace tare da kallona ta nuna min guri na zauna, shayi ta mika min. Na amsa cikin nutsuwa tare da cewa. "Nagode!" Kurb'a tayi tare da kallona. Ina juya kofin a hannuna, nakasa sha. Kallon fuskana tayi tayi. Ganin yadda damuwa da firgici ya cika kanshi tam. Murmushi tayi sannan tace min. "Baki son komawa gida ne?" Da sauri na d'ago kai tare da kallonta, sannan na maida kaina kan kofin nace mata. "Ina son komawa!" Shiru nayi nakasa koda furta kalama daya ne. "Gaya min meke faruwa?"ta kuma tambayana, "Laifi na mishi wanda har ta kai ya tsane ni a duniyar shi!" Na faɗi haka ina jin kamar na fashe da kuka. "Kina son shi ne?" Da wani irin sauri na d'ago kaina, girgiza mata kai nayi sannan nace mata. "Kallon Ɗan uwana nake mishi ban tab'a jin son shi ko kaunar shi a rai na ba." Na fadi haka kamar zanyi kuka. "Wato keda shi kuna kokarin kashe junar ku, wannan lafazin zai iya tab'a darajar ku keda shi. Amma babu damuwa, Allah yasa hakan itace mafi alkhairi. Amma ki sani zamu yi kewar ki ni da sauran mutanen cikin gidan nan!" A hankali na mike tare da mata godiya sannan na fice daga dakin. A hanyar d'akinta muna hadu ni zan fita shi kuma zai shigo. Kallon juna muke tare da kasa furtawa juna koda da kalmar sannun ce, karshe sai gashi mun tsincin kan mu da kasa bawa juna hanya idan ya kuma gefe nima zan koma gefe,. .idan ya tsaya zan tsaya karshe ture ni yayi gefe ya shige abin shi ina kallon shi. Wannan wacce irin rayuwa ce haka? Meye nayiwa Mehran da ba zai yafe min ba yake bani wahala har haka? Zan tafi zan yi nesa dashi yadda zai gane bani da laifin da yake zargina, amma tabbas Mehran ya zalince ni sosai. Babu kome Allah zai bayyana gaskiya koda bana tare dashi. Duk tsawon lokacin da na dauka, da fansar da nace zan dauka na ƙasa daukar haka sabida Mehran yau gashi sabida abin da yake da yakinin bai faru ba, ya kirani mazinaciya, karuwa, datti,shara, bolar kowa. Share kwalla nayi tare da barin kofar d'akin, na nufi hanyar da zai fitar dani, Fudail muka ci karo. "Ikram yanzun ɗan uwanki yake ta niman ki kamar wani karamin Yaro." Murmushi nayi sannan nace mishi. "Rahil rigima!" Har zan wuce yace min. "Kiyi hakuri! Kishi yake damun Sultan Mehran, amma kece rayuwar shi." Ganin shi muka yi a gaban mu, jikin shi yana kerma. "Waye kake magana akan shi? Ni Allah yayi min tsari indai ni ne, wannan itace rayuwata? Kishinta nake?" Riko hannuna ya yi tare da jana zai kai ni cikin Kwarkwarorin shi ya tozartani. Sai ji nayi an rike hannuna, tare da fisgo ni. Dukkan mu a tunanin mu Fudail ne. Amma abinda mamaki Amir Rahil ne. Cikin b'acin rai,.wanda tunda nake ban tab'a ganin shi ita ba. Fuskar shi har wani jajja jjaa tayi. Ya karasa takowa gaban Mehran ya. ya janyo ne jikin shi tare da sakala hannun sa a kafadana, yana kallon Mehran. "Ba zaka wulakantatta ba, matukar ina raye. Muje Salsabila ke kadara ce me tsada baki yi wannan arahan nan da za a tozartaki ba. Dan haka muje cikin Zuri'ar mu kiga yadda ake kaunarki. Mulki yake yawo a jininka shi yake yawo a jininta. Ya zaka ji idan na gaya maka ita kanta Sultanah ce a kasar Masar! Ya zamani idan mace maka ita Sultanah ce a Merocco. Dan haka karka tozarta ta, domin zan iya sare hannunka." Ya faɗa mishi yana kallon cikin idanun sa, juyawa muka yi tare da fita daga gidan baki daya. Kukan da nake rikewa ne yazo min, sosai nayi tare da kifa kai na a kirjin shi. Har muka isa masaukin su, anan ya ajiye Ni a dakin shi, yayi ta min hira tare da bani labarin abinda zai sani da dariya. Nayi kokarin koran b'acin rai da damuwa, akan fuskana amma a zuciyata kawai ina jin babu dadi. Dan haka nayi ta biye mishi muna ta hira har ya ga nasake ina dariya. Tausayi ya bani sabida yadda yake nuna min so ba karya bane, kaunar da yake min yana shimfiɗe akan fuskar shi. Dan haka yake kokarin sai ya sani dariya kota halin k'ak'a. ~~~ Har suka bar gidan yana tsaye kamar gumki, idanun shi jajjur. Dan ji yaƙe kamar an tafi mishi da zuciyar shi, niman faduwa yake. Fudail ya rike shi. Kallon shi yayi sannan yace mishi. "Sultan MEHRAN! Kayi kuskure babba. Duk abinda za a gaya maka akan Ikram bai dace ka dauka ba, sannan itama kanta taje taji meye ya faru har ka tsane ta haka. Mehran ko yanzun haka Nawwas yana jiranka zai maka bayanin abinda ya faru, amma ka sani sai ka cire wannan tsanar da kake mata, tare da fahimtar wacece ita. Sai ka haɗa abinda ya gaya maka da mahaunin hankali matukar kace ba zaka yi haka ba, tabbas yanzun ka fara nadama, domin zaka yi ta kuka har karshen rayuwar ka...... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 38 Kallon Fudail yayi cikin damuwa, amma kuma idan ka kalli yadda ya ɓoye haka zaka iya rantsewa har da Allah babu kome a ranshi, Mehran yana cikin mutanen da Allah yayi musu baiwar ɓoye damuwar su, zai yi wuya ka zauna dasu su ka gane akwai damuwa a tare dasu dan yana da irin zurfin cikin nan ne wanda idan ba shi yayi magana ba ba, ba zaka yi yarda ba. Sannan yana iya ɓoye abin a ranshi ba tare da ya gayawa kowa ba, yayi ta cin shi ba tare da kowa ya fahimci haka. Ko Fudail yana saurin d'ago shi ne ta hanyar tsananta binciken motsin shi. Wannan d'anyen halin nashi ba karamin damun Sultanah FAZILATUL gani take kamar da gayya yake k'in faɗa mata, ita bata damu da kanta ba, koda wani zai iya gaya mishi. Amma fir yaki nuna damuwar shi sai dai ya rufe kanshi a daki yayi ta zaman kunci. Duk lokacin da ya shiga wannan yanayin, kowa yana shiga damuwa. Shi yasa basu son Ikram tayi nesa da shi. Kuma da alamu haka ce zata faru, tunda ya kasa furta kalmomin da ya dace, gashi nan danginta zasu tafi da ita. Juyawa yayi yana kallon waje. Kalmomin Abrad ne yake yawo a kunnen shi. _Ko mijin da ta aura ba zai iya cewa shi ya dauke abinda kake hari ba! Ka tambaye ta ni na fara kwanciya da ita! Ni na bude idanun ta. Ni na nuna mata yadda namiji yaƙe_ Rintsa idanun shi yayi tare da jin bakin ciki dama da kullum, ji yaƙe kamar ya cire zuciyar shi ya huta, ga baki daya ya tsani kanshi da Abrad ina ma da yana da damar kashe Abrad tabbas sai ya kashe shi. "Sultan!" D'aga mishi hannu yayi tare da cewa. "Bana son ganin shi." "Amma wannan kuskure ne kake tafkawa, kana kuskure ne babba. Me yasa ba zaka Fahimci yarinyar nan ba? Me yasa ba zaka gane meke faruwa ba, Idan abinda kake zargi haka ne me yasa ba zaka ajiye shi a wani guri na daban ba, kake kuntatta mata da hanyar da bai dace ba! Gaskiya baka mata adalci ba. Shi kenan Allah yasa haka shine mafi alkhairi ga sakon daga Fada Amir Hood ya baka auren jikar shi. Amma sai nan da wata uku zuwa huɗu. Tunda sun sami labarin Ikram an mata bai ko da Amir Rahil. Allah ya tabbatar da alkhairi." Daga haka ya juya tare da barin d'akin, tunda ya fara magana bai juya ba, har sai da ya bar dakin sannan ya juya yana kallon kofar tabbas yana son ganinta. Yana son jin meye ta sauke shi. Yana son ganinta kome dare ba zai ya fita da rana tsaka ba, dole ya fita cikin dare ya isa gare ta. Amma kuma meye makomar shi. Ajiyar zuciya ya sauke tare da dauke kanshi kasa. Yana shafa kan shi tare da murmushi. ~~~ Kasa magana nayi ina kallon yadda Sultanah Amrah take kallon Nimrah, mayar da Nimrah baya nayi. Sannan na tsaya a gaban ta, nace. "Kiyi hakuri Ummyn, bata da laifi. Kuma nasan ke me adalci ne." Dakatar da ita tayi ta hanyar d'aga mata Hannun, tare da kura mata ido. "Ban ce zan mata kome ba, amma ina tsoron abinda Mahaifiyarta tayi mana ne, domin ba lallai bane ta fahimci abinda ta aikata." "Insha Allah, Nimrah ba zata aikata kome ba, wallahi ki yarda dani bata da wannan tunanin a ranta ban dai sani ba, amma babu wannan karsashin a ranta." Haka nayi ta lallab'a Sultanah Amrah kafin ta sake jiki, tana kallona daga lokaci zuwa lokaci. Musamman idan ta fahimci na shiga yanayin damuwa,.sai ta ce min. "Kina son zama da Mehran ne?" "A'a nafi son zama daku." "A'a Ikram bamu shiga hakkin ki ba?" "A'a" nace tare da mik'ewa zan bar dakin domin na tsani hirar da zata kawo min zancen Mehran. Shi yasa bana son zama koda su Izmah ne domin rabin hiran su akan shi suke min. A waje na hadu da Rahil ya kawo Abrad, dan haka ban yi mamaki ba, dan nasan yazo gaida Ummyn ne, har cikin gidan ya shiga suka gaisa, sannan suka shiga tattaunawa akai na, wanda duk hiran akan yadda ake shirya min tarb'a da bikin da za ayi mun ni da Rahli. Bai ce komai ba, amma daga yadda ya rasa nutsuwar shi har ya gama hiran da ita, muna zaune a harabar masaukin. Zama yayi a kusa dani tare da zuba min ido. Dauke kai na nayi daga gare shi sannan na cewa Rahil. "Ina son zan sha madara! Amma bana son bayi su kawo min" na fada cikin sakakkiyar murya. Mikewa yayi tare da cewa. "Zauna ki huta mata na, ba zata tab'a wahala ba. Domin ita din sarauniya ce zan kawo miki." Ya faɗa tare da nufar hanyar cikin gidan. Gyara zama nayi sannan na kalle shi. "Kayi ƙoƙarin raba ni da Mehran, ka dasa mishi k'iyayyana. Sai dai kayi kuskuren mafi girma domin kuwa kayi abinda ba zai tab'a barin ka ba, daga yanzun daga wannan lokacin ka fara boya, kayi ta gudu karka tsaya. Domin tsinin takobin shi sai ya huda kirjin ka. Ka fara gudu karka tsaya inda zai same ka. Nayi danasanin fadawa hannunka, domin babu wanda ya kashe ni da rayuwata sama da kai. Babu wanda ya lalata min rayuwa sama da kai. Sannan sauran da yarage kazo zaka lalata min su! Meye nayi maka da zafi? Meye na tsare maka da zafi haka? A sanina ka auri Kanwar Mahaifiyata toh meye kake son daga gare Ni? Amma masu iya magana since idan ajali yayi kira ko ba'a ciwo za aje." Daga haka na mike , rike hannuna yayi cikin zafin rai na tsinka mishi mari sannan na wuce abuna, duk akan idanun Amir Rahil ne, ina shiga ya zuba min ido. "Meye ya haɗa ki dashi? Meye Matsalarki dashi? Yau zan dakatar da shi." Gudun kar a kuma aikata abinda Ya faru yasani rike shi tare da kallon shi nace. "Karka damu. Ya wuce na koya mishi yadda ake mutuntawa." Murmushi yayi tare da mika min madaran muka shiga zaga gidan, wai duk sabida kar na saka damuwa a raina. "Wai dama an miki baiko da wancan basamuden ne?" Kallon shi nayi tare da murmushi kafin nace mishi.o "Eh amma kuma sawun giwa ya badda na Raƙumi ba" shima kallona yayi sannan yace. "Ban gane ba?" Murmushi nayi a karo na biyu, sannan nace mishi. "Zaka gane mana." Dariya yayi sannan yace min. "Amma kuma" "Amma kuma me?" Na tambaye shi, "Amma kamar kuna son juna da wancan basamuden?" "Me ka gani?" "Kin dawo min da tambayana" "Kamar ya?" "Kamar yadda na gani da idona" "Lallai kayi kuskuren" "Banyi kuskuren ba sai gaskiyar da na hango." Kasakai nayi ina kallon shi.kafin nace mishi. "Babu wata soyayya a tsakanin mu, kawai kana ganin haka ne amma ban ga!" "Da gaske baki son shi?" Ya tambaye ni, tsayawa nayi ina kallon shi. Tambayar da yayi min iya gaskiyar shi ce, amma kuma bana jin zan bashi amsar wannan tambayar dan haka na juya tare da barin shi a gurin, bakin ruwan da yake gudana a gurin na isa sannan na zauna tare da saka kafana ina nazarin maganar da muka yi da Rahil. Zama yayi kusa dani, sannan yace min. "Kiyi hakuri da sakaki surutu da nayi, sai dai kowani mutum me hankali da sanin ya kamata zai so ya ajiye irinki a gefen shi ko badan mu'amalar aure ba, ana bukatar mutum ya ajiye mace irinki na farko zaki bashi garkuwa, na biyu zaki bashi farin ciki a rayuwar shi, na uku kuma..." Murmushi yayi sannan ya cigaba da cewa. "Sai nan gaba zaki Fahimci abinda nake nufi" Girgiza kai nayi sannan na juya tare da kallon cikin ruwan, ina jin babu dad'i domin Allah ya gani son Ƴan uwantaka nake mishi ba son kauna na aure ba, kuma ba zan iya bijirewa iyayen mu ba, tunda abinda suka yanke kenan. Amma ko ya ya bai kamata su zartas da hukuncin haka ba, idan suka yi dubi da ni bakuwa ce a cikin su. "Ikram ko na takura miki ne?" Ya tambaye ni cikin damuwa, "A'a baka takura min ba, sai dai kana da hawa kai" na fada ina kallon shi, "Toh kiyi hakuri! Ban san yadda zan nuna miki farin cikin da yake raina bane, amma kuma ina jin nutsuwa a zaman mu nan."ya faɗa cikin sanyin murya, duk sai ya bani tausayi, tabbas akwai matsala domin nasan dai ba zan hada maza biyu ba, amma kuma yadda Mehran yayi min ban ji dadi ba, dan haka na juya ina wasa da ruwan. Kasa hakuri yayi tare da zama kusadani kamar zai shige jikina, kallon shi nayi kafin nayi magana ya jingina kan shi akan kafadana, tare da riko hannun na, yana me matsawa a hankali. ...... Ya saba da ganinta tana sintiri dan haka yau da bai ganta ba, duk sai ya damu dukda ya ganta lokacin da ta fito dakin Sultanah, amma kuma zuciyar shi da ruhin shi suna begen ganinta, ƙwaƙwalwar shi tana yawan hango mishi.wasu abubuwan akanta, dan haka ya mike tare da sauya shiga izuwa kayan dakarun kasar ya fita daga gidan. Gidan bakin dake cikin masarautan ya nufa, tunda ya shigo ya hango yadda suke zaune da Abrad, sai yaji kamar ya koma, amma kuma ya fasa bayan ta gama gayawa Abrad magana yana mamakin yadda take iya sarrafa maza, dan yasan haka kawai ba magana me dad'i ta gayawa Abrad ba. Bayan fitar Abrad, ya hango suna magana da Rahil. Sam Mehran bai dauki Rahil a wani namiji can ba, amma ganin yadda Rahil din yake ta damunta da surutu sai yaji tsoron kar abinda ta rasa a gare shi ta samu a gurin Rahil tunda soyayya ta tasa kuma idan ta samu a gurin Rahil shi bai da wani abun da zai gwada mata. Suna tafiya yana bin bayan su har gurin ruwan. Duk da bai san meye suke fada ba. Amma kuma tabbas abinda suke fada akwai muhimmanci dan haka ya nace sai yaji abinda suke fadi. Bayan ya matso ne yaji lokacin da Rahil yake gaya mata kowani namiji zai so samunta a rayuwar shi. Take hankalin shi ya tashi domin shi ya dace ya fahimci haka, amma baƙin kishin sa Ya saka shi kasa fahimtar kome akan haka. Yana kallon su har ya daura kanshi a kafad'ar ta, a lokacin sai da yaji kamar zuciyar shi zata dirko daga kirjin shi domin babu abinda ya tsana kamar yaga namiji a jikin ta. Yau gashi akan idanun shi wani yake jingina kanshi a kafad'arta. Ji yayi kwallar bakin ciki ya cika mishi ido. Dan haka ya juya tare. Da barin su a gurin tabbas bai da sa'a shi yasa ya rasata a karo na biyu,a da yana tunanin ya sami kanta ko bai gaya mata yana sonta ba, zata iya furta mishi ashe hasashen shi ce, ba tunaninta bane. Bai yarda da abinda Sultanah ta gaya mishi ba sai yanzun da ya gani da idon shi lallai yayi sake d'an zaki ya girma yayi kuskuren barinta ta rayu da wani, da tun lokacin ya kafa gwamnatin shi babu wanda ya isa ya rab'e ta, amma ya zauna sai tsanarta mata amfani da yake ji. Da wannan tunanin ya bar masaukin.. Haka kawai naji kamar Mehran ya zo har inda nake dan haka ba juya tare da kallon wani badakare yana tafiya. Haka kawai nake mishi kallon kamar Mehran ne, har na juya zan cigaba da wasa da ruwan sai kuma naji bari na kuma juyawa dan kamar yana kallona, koda na juya yana nan a tsaye. Sannan ya kasa tafiyar shi. [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 39 Juyawa nayi sabida idanuna da suke min gizo, a hankali kwalla suka cika min ido. Tabbas Matsayin Mehran Babba ce a zuciyata ya, shi yasa na kasa Mantawa dashi. Saka hannun shi yayi tare da tare kwallar da take sauka akan fuskana. "Waye ya tab'a min ke?" Murmushi nayi tare da goge kwallar nace mishi. "Ina kewar Airan ce, kuma kaga dole nayi kuka domin itace kawai ta rage min gashi ba rasata ga kuma Allah ya bayyana min dangin mu." "Ikram!" Ya ambaci sunana a hankali yana kallona, sannan yace min. "Bana raba daya biyun kina tunanin Mehran ne" Kura mishi ido nayi, da gaske haka ne amma kuma ɗan na karya ta abinda yake tunani a kaina yasani faɗin. "Tir wannan wacce irin magana ce? Na rasa wanda zanyi tunanin shi sai mutumin da bai da wani amfani a rayuwa ta, kawai dai kana zargina ne, amma idan ba haka ba me zai sani tunanin Mehran." Cikin fushi na mike zan bar gurin, riko hannuna yayi tare da zaunar dani. "Kiyi hakuri!" Ya faɗa min a sanyayye, sannan yace min. "Dole naji babu dad'i, babu namijin da zai so yana yana tare da mace amma zuciyar ta yana ga wani mutum na daban, Kinga kuwa zai cigaba da ganin haka kamar rashin adalci ne." Tabbas ya bani haushi amma kuma yana da kyau na tausaya mishi domin gabaki daya ya addabi rayuwata da naci, dan haka na sassauta fushina nayi sannan na zauna ina kallon shi. "Ke kamar Uwace a gare ni, kin bani kwarin gwiwar da na rasa akan me zaki yi fushi da Ni? Bayan ke bani da wanda zan ƙalla nace shi Masoyina ne. Amma ke kuma na ambace ki da kalmar me tsada da girma,don Allah karki yi fushi da d'an uwan ki." Na rasa me zance domin duk wata kalmar da zai yi amfani da ita,rudurduga min zuciya take, duk wata harafin da zai ambata kamar kunawa zuciyata huta yake, gabaki daya sai naji ba zan iya ganin shi cikin rashin nutsuwa ba, zan amshi auren shi duk da ina da zab'i amma kuma shi din zab'in kakanni na ne, hannuna yakai fuskar shi sannan yana faɗin.. "Ki dube ni da idanun rahama, karki juyawa tayina baya" Hawayen da nake b'oyewa ne suna sauko a hankali tare da kura mishi ido, tabbas kome ya kare min dan haka na rike hannun shi tare da cewa. "Ba zan tab'a juyawa tayin ka baya ba, ina tare da kai kuma zan zauna da kai." Ina gama fadar haka na mike zan bar gurin. Shima mikewa yayi sannan ya saka hannun shi dukka biyu ya rungume ni. Yana shafa bayana. Mehran yana kallon mu. Juyawa yayi tare da barin gidan baki daya. Idan ka ganshi zaka dauka bai da lafiya ne. Hamas shiga Harami ya nemi faduwa, tare da jin wani mugun sanyi ya shige tare da zazzaɓi me mugun zafi. Fudail da yaga fitar shi, shine ya fara ganin shi san yana harabar gidan. Ya rike shi zuwa cikin gidan. "Fudail kirjina zai fashe." "Sannun Sultan! Ina kaje haka? Ko kamanta kana da ciwon zuciya ne? Gashi a karon farko zaka kashe kanka." Ina kasa magana yayi sai juya kai yake, yana jin kamar kirjin zata fashe, a dakin shi aka kwantar dashi. "Fudail, Ikram" ya faɗa a sanyayye dukda idanun shi a rufe suke amma bai hana shi. Kiran sunan Ikram ba, gabaki daya ya zauce baya gane kome sai sunan Ikram,har akayi sallah magarib da isha Mehran baya cikin hankalin shi. Matan da aka zab'e mishi kuwa kasa hakuri suka yi. Sai da suka magantu. Amma haka bai hana Mehran kiran Ikram ba, tun ana zata zafin zazzaɓi ne har suka gane cewa ita din yake bukata, gashi dare yayi sosai. Dan haka suka yi ta fama dashi, daga karshe dai Sultanah da Fudail suka fita har gidan bakin. ...... Ina kwance banyi barci ba amma kuma zuciyata babu dad'i dan haka na tashi zaune, naja labulen gadon ina kallon su Nimrah da Izmah, da suke kwance can gefe guda. Kallon su nayi naga suna barcin su. Wato sai kana da nutsuwa kake samun damar barci idan baka da shi kuwa. Kai da barci har abada. Buga kofar dakin mu akayi na sauka a gadon sannan na bude tare da kallon Ummyn da Sultanah Fazilatul nisa. "Ikram! Don Allah zoki taimake mu. Mehran zai mutu." Ban tab'a sanin akwai rudewar da zata sani niman fita daga cikin gidan babu suturar Arziki a jikina ba sai da aka gaya min Mehran zai mutu. Riko hannuna Rahil yayi cikin dakewa sannan yace min. "Baki da lafiya ne? Dubi yadda zaki fita? Koma ki shirya ina jiranki!" Haka nayi kamar yadda yace min, tare muka tafi har da wasu dakarun. Tunda muka shiga cikin harabar gidan, Rahil ya riko hannuna. "Karki manta akwai alkawarina akanki. Dan haka kiyi kokarin kare girman alkawari." Kallon shi nayi domin na kasa Fahimtar me yake nufi, a lokaci guda naji ya fice min a raina. Hawayen da ban san yaushe ya sauko min ba. "Kasan girman shi a cikin idanuna? Kasan yadda nake jin shi a raina? Da kasan yadda nake kokarin kyautata mishi ba zaka tab'a sanya min sharadi dan zan ganshi. Ka tsaya a matsayin ka na wanda aka mana alkawari karka tinzira zuciyata izuwa aikata abinda ba zan iya daukar shi ba. Sultan MEHRAN wani shashine na rayuwata. Don Allah karka raba abinda yake a haɗe." Ina gaya mishi haka na shige cikin gidan. Na sami Kwarkwarorin shi a bakin kofar, suka gani na suka shiga matsa min a hanyar. Shiga dakin nayi na same shi rike da kirjin shi. "Ikram! Ku kawo min ita" ina shiga matan shi suna shigowa. Tsayawa nayi a bakin gadon ina kallon yadda yake dafe kirjin shi. A hankali na zauna a bakin gadon. Na kai hannuna tare da riko hannun shi. Ajiyar zuciya ya sauke tare da ƙamƙame ni. "Ikram!" Ya kira suna na idanun shi a rufe. "Na'am Sultan Mehran!" Bude idanun shi yayi sannan yace min. "Mehran zaki ce, ki ce min Mehran." "Meke damun ka?" Hannu na yakai bakin shi ya sumbata, sannan yace min. "Kece ciwo na. Kece magani na" ya fadi haka, kallon sauran matan Fudail da Sultanah suka yi tare da musu alamar su fita. Fuuuu suka fita daga dakin, ina rike da hannun Mehran, tashi yayi tare da dawowa kan cinya ta, yana sauke ajiyar zuciya. "Karki tafi! Kunne na yana min kai-kayi, ko zaki susa min" Shafa kan shi nayi tare da jin saukar kwalla daga idanun shi akan cinyata. "Kayi hakuri! Ni zan tafi gobe Insha Allah..sannan ka rungumi matan da aka baka, Insha Allah zaka sami wacce zata fini tsayin daka." "A wani matsayi kika ajiye Ni?" Ya tambaye ni tare da damke hannuna. Shafa kanshi nayi a hankali tare da jin tashin hankalin a raina. "Mehran! Kai kamar Uba ne a gare ni, bana son na ganka cikin tashin hankali da damuwa, Mehran ina zaune ne domin kai bayan haka bani da hurumin zama a cikin Masarautan SAMAIND, amma kuma sai naji kunyar abinda ka aikata min. Mehran na tawo da niyyar daukar fansa akan abinda kasa aka aikawa Numan." D'ago kai yayi tare da kallona. _Me yasa ba zaki gane bani da hannun cikin kisar gilla da aka yiwa Mijinki? Me yasa ba zaki gane ban san kome akan kashe shi ba! Nayi kuskuren furta sai na kashe shi amma bani na aikata ba_ Shiru nayi tare da janye idanuna daga cikin na shi, sannan na cigaba da cewa. "Haka bai sani ajiye makamina ba, na amshi aikin da ka sani ba. Mehran sai da na gama tsalleke duk wani mataki da iyaka, amma ka juya min baya, alhalin kasan ba zan yi abinda kake zargi na ba, Mehran ko daga cikin gidan ƙaruwai la dauko ni,.zaka min uzuri balle kuma kai da kanka kasan ba haka nake ba. Ka kira Ni da sunaye masu kazamta da muni. Kayi hakuri Mehran amma iya yau nayi domin Mahaifiyarka ce da Aminin ka, bayan haka Akwai alqawarin auren D'an Uwana, don Allah kayi hakuri. Kai Ubane a gare Ni bayan haka bana jin akwai bukatar na kara maka wani matsayin." Na fada mishi haka ina had'iye kukan da ya taso min, sannan na cusa hannuna cikin gashin kanshi ina wasa dashi. Hawaye na yana zuba akan gashin kanshi. "Ban yi laifin da kake zargina ba. Amma ka kasa fahimtar kome a kaina, kayi hakuri nasan nayi laifi da kuskuren fita daga harami zuwa gidan da Abrad yaƙe, amma yadda kasame mu da shi babu wani abinda kake tunanin ya faru, nasan bai zama dole ka yarda dani ba, amma iya gaskiyar kenan." Tashi yayi zaune tare da kallona, idanun shi jajjur bakin shi yayi fari sol kamar wanda ya jima yana jinya. Mikewa nayi sannan na dauko mishi ruwan na mika mishi. Riko hannuna yayi tare da haɗawa da nashi ya kai ruwan bakin shi ya sha, sannan ya janyo ni jikin shi yana kallon fiskana da take jike da kwalla. Tari ya fara tare da daidaita tsayi na da fuskar shi. "Meye matsayina?" Kallon shi nayi sannan na fara ƙoƙarin mik'ewa, sake murmushi yayi tare da cewa. "Meye matsayina?" Kwalla ne suka shiga tuttukowa daga cikin idanuna, bakina yana rawa na bude zan bashi amsa, sai jin harshen shi nayi cikin bakina, tare da lumshe idanun shi, ya rike kai na gam. Wani irin kuka naja tare da ajiyar zuciya. Ina kallon shi har cikin idanuna. Abinda nake hangowa ba abin wasa bane, ba kuma karamin abu bane. Amma zurfin cikin da YAKANA sanya shi b'oyewa. Gani yake idan ya fitar duniya zata iya zage shi. Shi yasa yake kokarin ganin ya adana abin a idanun shi da zuciyar shi. Amma abin yaki ajiyuawa, dan ba gama garin sirri bane da ake iya boye suka zauna lafiya. Da kanshi ya sake min bakina da yasha tauna a gurin shi, haka ba sabon abu bane a gare ni amma kuma kuma tambayar anan shine meye yasa Mehran yayi min haka? Me yasa ya kasa yarda dani? Meye yake kokarin b'oye min? Kasa nayi da kaina, domin bani da amsar da zan bawa kaina, amma daya biyun ina kara fahimtar kaunar da yake lullube da kishi na akan idanun shi. Hannun shi naji cikin rigar jikina. Da sauri na rike tare da kallon shi. "Me ye matsayina?" Bakina yana rawa na kalle shi tare da cewa. "Shugaba na!" "Hmm! Ban yarda ba" "Allah da gaske nake gaya maka" sake tura hannun yayi zai kuma tab'a min jikina nayi maza na mike ina gyara zaman rigar jikina. "Ina zaki?" "Na bar Rahil a waje kuma nasan yanzun dare yayi." Tab'e baki yayi sannan ya dauke kanshi. "Baki gaya mishi gurina zaki zo ba?" "Ya sani rakoni yayi!" "Toh gaskiya babu inda zaki a daren nan, a nan zaki kwana." Ya nuna min gefen shi. "Amma Mehran!" "Na gama magana idan kuma ban isa ba zaki iya tafiya dama ai bani da daraja da matsayin da zaki zauna dani ko ance miki ban san labarin zaman za kuka yi dashi a cikin gida daya bane, wato ni aka maida sakarai, ayita zagawa ana cin amana Na, idan nayi magana ace na cika zargi bayan kowa ya sani Salsabilah yake kiran ki, wato koramar shi. Ni kuma d'an iska ban san me zance ba." Matse hannuna nayi a cikin juna, ina jin wani irin takaicin Mehran da haushin sa, kafin na d'ago kai nace mishi. "Kai ma ai kana da naka sunan da kasa min kamanta ne?" .wani dauke kai yayi cikin jan aji irin ya manta dole na tuna mishi. A hankali na dan sunkuya ina kallon shi.. "Sultan MEHRAN!" Da sauri ya juyo yana harara ta, sannan yace min. "Qurratulain!" Murmushi nayi sannan nace mishi..... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 40 Karshen book 2 "Me yasa kake son tilasta min zama da kai bayan kai baka yarda da ni ba? Kasan girman kuskuren da ka aikata? Da a ciwo a.." Yatsar shi ya saka akan bakina, yana kallon yadda nake kokarin cire idanuna a cikin nashi. "Kamar yadda kike zargina da kashe Nu'man haka nayi domin." Jan iskar bakin shi yayi tare da mik'ewa yana me kai hannun shi kan fuskana ya d'ago ni tsaye. Dukka hannu bibbiyu ya zuba a k'uguna, yana me ben fuskana da kallon me cike da sanyin yanayi. "Duk yadda naso kare kai na, baki bani damar haka ba, sai ma kuma tinzara da kike. Ikram na baki damar shiga rayuwata ce a karo na biyu dan ki zama alkali a rayuwar mu, don Karki hukunta ni da laifin da ban aikata ba" ya faɗa muryan shi can kasa tare da saka kanshi a kafadana. D'ago shanyayyun idanun shi yayi a karo na biyu, yana kallon yadda nake kokarin janye jikina daga gare shi. Juyar dani yayi tare da daura kanshi a kafadana. "Na san na fada a kashe shi! Amma kuma ban ba da damar kashe shi ba. Ki dube ni da idanun rahama karki nisanta kanki da ni" ya faɗa yana me kai hannun shi dukka biyu kan cikina. Ina jin yadda zuciyar shi take bugawa, kan shi kuwa wani irin zufa yake fiddawa, narkewa nayi a jikin shi tare da lumshe idanuna, ina kuma jin kamar nacewa Sultanah Amrah ni kawai su tafi ba zan bisu ba. Juyawa nayi zan fita ya kuma tare kofar. "Me yasa kike saurin tafiya gurin shi?" Sunkuyar da kai nayi tare da maida gashin kai na baya, sannan na d'ago kai na, kafin nace mishi."Mehran kayi hakuri akwai alqawarin auren shi a kaina..." Wurgi yayi da kayan abincin shi. "Alqawarin banza, ko Ni bani da zuciya ne da ba zaki fahimci halin da nake ciki ba? Ce miki akayi dadin Kowa nake ji bayan ke? Toh jeki kawai jeki Allah ya baki zaman lafiya. Kije ki aure shi." Cikin jin haushi ya turo ni waje daga dakin shi ya rufe kofar d'akin shi. Yana cikin dakin sai barna yake kamar yaro karami. Juyawa nayi tare da barin gurin, har na sauko kasa Kwarkwarorin shi suna kallona, ganin yadda suke b'ata rai ya sani dauke kai na abuna, sabida duk cikin babu wacce ta taki sa'ar da na samu, dan haka babu wacce zata min iyayi ko kankanba. Ina fita na hango Rahil zaune shi dasu Shairah da Fudail sai Darda. A hankali na isa gare su, sannan nayi musu bankwana. Ina lura da yadda jikin shi yayi sanyi musamman yadda na same su, suna hirar Mehran. A hankali muke tafiya yana me sauke ajiyar zuciya a kai a kai, ba zaka tab'a jin bai sauke tare da fitar numfashin sa ba, kuma yaki kallona, abinda na fahimta matsanancin kishi yake. Domin ina lura da yadda yake naushin hannun shi har muka isa gidan. Saka kai nayi zan wuce masaukin mu naji ya riko hannuna, juyawa nayi tare da kallon shi. "Me yasa baki da tausayi da jin kai? Me yasa ba zaki gane yadda nake kokarin kyautata miki ba? Kin fi son bare a kaina? Tun da kika shiga cikin gidan kika manta da batu na, sai yanzun kika tuna dani, gaskiya ina da zafin kishi da zafin rai idan na kuma ganin haka zan aikata abinda ba zai miki dadi ba." Kasakai nayi ina kallon bawan Allah nan, wato sun mai dani sha tara, kowannen su buga ni yake kamar tamola, meye nayi musu haka da kowannen su yake jin zafi na? Nima cikin fushi na bar shi a tsaye,ban saurare shi ba,balle yayi tunanin zan bashi hakuri ko wani abu makamancin haka. ... A wannan daren mutane uku basu rintsa ba, gabaki dayan su kowanne da abinda yake ji, dan haka gari na wayewa. Mehran ya fara fitowa yana kallon masaukin da suke ciki. Har zuwa lokacin da aka fara fidda kayan Ikram, a lokacin Abrad ya shigo gidan. Babu shiri Mehran shima ya fita tare da nufar hanyar gidan. Tare da wasu manyan dakarun shi suna dauke da manyan akwatin karfe, sai bayi mata da suke bin bayan Fudail dauke da tire a lullube da jan kyale. Tun safe Izmah da Nimra suke kallona, "Toh wai meye suke nufi dake ne? Domin ga Abrad da Mehran suna Wajen sai Amir Rahil." Zare tagumi nayi tare da cewa. "Wallahi sun addabi rayuwata, musamman Abrad ya hana rayuwata sakat, Mehran kuwa bani da damuwa dashi. Sabida na gama zama dashi." Shiru nayi ina kallon su, kafin na cigaba da cewa. "Amir nake tsoron kar Abrad yayi mishi renin hankalin da." "Amirah ana jiran ki!" A hankali na mike tare da hada abinda zan iya, sauran kuma su Izmah suka hada min, fitowa nayi na sami Sultanah Amrah, tana karyawa,zama nayi dan sam ban lura da falon dauke yake da mutane ba, sai da na zuba ruwan shayi, na tsinkayo Muryan Mehran. "Ko zaki hada dani dan ban karya ba." Caaaa suka min da ido, shi kuma yadda ya zauna tare da saka hannun shi ya kishingida kamar yana falon shi, d'ago kai nayi ina kallon shi. Kafin na mike tare da hada mishi jikina yana rawa, tasowa yayi tare da nufar inda nake hada shayin ya kai hannun shi zai rike ni. "Har yanzun tana karkashin kulawata ce, idan ta fita daga Cikin SAMAIND ta shiga da'iran kulawar kowa, anan babu wanda ya isa ya tab'a ta a gaban D'an Abdus Samad." Had'iye yawun nayi ina kallon Amir Rahil da yazo rike ni, sosai na kadu da yadda Fuskar Mehran ya sauya, dan haka kafin Amir Rahil ya rike ni, na kauce sannan na nufi inda Mehran da kofin ruwan zafin. Duk abinda yake faruwa Sultanah Amrah da Abrad suna kallon mu, sake shan kaina Amir Rahil yayi, ture shi Mehran yayi tare da kallon inda nake, ya mika min hannuna. A sanyayye na isa gare shi, rike hannuna Rahil yayi. "Akwai baiko na akanta dan haka na fika iko akanta." "Ni kuma baiwata ce, naga wanda ya isa ya min iko akanta." "Wai kai waye ne? Meye nufinka da ita? Bilqisul Ikram Mustapha matar da zan aura ce! Dan haka baka isa ka tab'a min matar da zan aura ba." Karb'an ruwan shayin yayi tare da ajiyewa, ya fisgo jikin shi. "Aamaan ka sake min mata na" Amir Rahil ya daka mishi tsawa, Tsakiyar su Abrad ya shiga tsakanin su, kallon Mehran yayi cikin nutsuwa da jin dadi, muryan shi kasa kasa, yace mishi. "Fanko ce kake harzuka akanta, shima idan yasan wacece ita. Fasa auren ta zai yi. Karshe dai Ni ne dai zan karasa ab...." Tass Mehran ya dauke shi da mari, tare da shake wuyar shi. Kamar mahaukaci ya rufe shi da duka, abun sai ya bamu tsoro da mamaki. Domin kuwa Amir Rahil ya kamata ya daka, amma ya bige da dukar Abrad dama yana cike dashi, kokarin shiga tsakanin su nayi amma Abrad ya riko ni, dai-dai Mehran yaja hannun shi zai naushe shi. Ganin yadda ya rungume ni yasa shi tsayawa cak. " Sarkin Karfi gata a kirjina dake mu, nace ka dake mu. Ga Ikram din ta faɗa da bakin ta" da sauri na juya ina kallon shi tare da girgiza mishi kai. "Karka tozarta ta! Na yarda kayi min kome amma karka wulakantatta a gaban jama'ar ta." Ya faɗa tare da sauke hannun shi. Kallon su nayi na ma kasa magana, hawaye Masu zafi suke zuba a cikin idanuna. "Abrad meye nayi maka da zafi haƙa?" Na tambaye shi bayan na kwace kai na, kallona yayi sannan ya fashe da dariya, bude baki yayi zai magana na kifa mishi mari, hawaye na zuba. "Meye nayi maka da zafi? Meye na tsare maka da kake niman hanyar da zaka wulakantani? Ka gaya min meye nayi maka!" "Zaki biya abinda kika aikata." Takowa yayi gaba na, tare da kallon fuskana yace min. "Kina jin kunyar Kakarki ce? Ko kina tsoron kar kashe gimbiyar da tayi mu'amalanci wani namijin? Ko zaki iya tuna abinda wannan hannun yayi miki shekarun baya, da na tura shi." Ji nayi kamar zan fadi,.dan wani irin jiri ne yake niman kayar dani, Lokaci guda Mehran da Rahil suka kawo min dauki, murmushi yayi sannan yace min. "Sai na hanaki sukuni." "Abrad wannan wani irin wawanci ne? Ikram din ce kake mata irin wannan haukar ka manta matsayinta ta ne a gurin Sariya? Yar Yayar matar ka ce fa. Wannan wacce irin hauka ce mara to ..." "Kul! Idan kika yi wasa abinda zan fada sai ya saka yan majalisar ki sun sauke ki a kan mulkin ki, sannan kuma itama Ikram din Askandariya sai tayi mata wahalar shi, kai kuma Mehran kamar yadda na gaya mata haka kai ma. Kai sha-sha-sha bani da lokacin ka, sabida mutanen da suke da iko nake yi dasu. Abinda na sani baka isa ka auri Ikram ba. Amma zan baka damar niman taimako na yadda zaka aure ta. Idan ka shirya." Yana gama abinda zai yi ya fita yana dariya wai shi yayi nasara. Sai da ya fita na sami damar fashewa da kuka. Kamar yadda naso yi. Mikewa Mehran yayi tare da barin gidan, Rahil kuwa kasa magana yayi. Kawai sai damke hannuna yayi tare da cewa. "Ba zan tab'a barin ki cikin matsala ba matukar ina raye." Sultanah kuwa kasa d'gowa tayi domin kuwa tana me jin kunya da bakin cikin abinda ya faru, ita da kanta ta kashe Zuri'ar ta, yau tayi abinda zai kaita ya baro ta. Rike rigar shi nayi tare da fashewa da kuka, Abrad ya wulakantani, Mehran ya juya min baya, bani da zabin da ya wuce Rahil ko naki ko naso Rahil shine ya dace da rayuwata, ba zai tab'a bari na cikin kuncin rayuwa ba. Dan haka ya taimaka min na mike tare da kai ni har waje inda aka jibe mana kayan da Mehran ya kawo min yayi tafiyar shi. Haka su Izmah da Nimra suka kwashe kayan aka zuba a saman rakumai, sannan na shiga keken dokin shi, su kuma suka shiga cikin na Sultanah Amratu. Muka bar masaukin bayan an hada mu da rakiyar dakarun Samaind kimanin dubu goma sha biyar, har Askandariya zasu rakani inji Sultan Mehran. Tunda na shiga cikin keken nake kuka, wanda nasan ba na abinda Abrad yayi min bane, a'a zunzurutun rabuwa da Mehran ne da zanyi. Ji nake kamar na sauka nace musu bani tafiya ko ina zan zauna da Mehran. Tun kafin mu bar da'iran SAMAIND. Naji jikina yana bani tare dashi muke tafiya, dan haka na bude labulen jikin keken. Kurawa juna ido muka yi, sanya yake da kayan dakarun ƙasar. Hannun shi ya kai tare da riko hannuna. Sannan ya sake linzamin dokin shi ya saka min zoben da ya ciro daga aljuhun shi. Tare da sumbatar hannun. "Ina tare dake har karshen rayuwata." Daga haka ya sake min hannuna. Ina gani muka yi ta tafiya muka bar shi a can baya. Hawayen da nake dannewa ne ya zubo min. A hankali nace. "Ina sonka!" Haka muka bar shi a gurin. ....... Hawayen da bai tab'a zaton zai zubda akan So ba yau ya zubda su. Rike d'an kunnenta yayi tare da kallon shi, ya tuna ranar da tazo amsar tayin shi take zata bude inda d'an kunnen yake ya hanata, kwallar shi ce ta sauka akan d'an kunnen. Ya damke a hankali. Tare da sumbatar shi, yace. "Ina Sonki! Mara iyaka. Kece fitilar rayuwata." Ya fada a hankali, kamar wani na jin shi. Tabbas sai yanzun ya kuma fahimtar shakuwar da take tsakanin su, bata wasa bane. "Abrad!" Da sauri ya juya linzamin dokin shi ya nufi SAMAIND a guje tare da tuna ranar da ya fara ganin Ikram...... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ Littafi na uku 01 Tunda ya bar masaukin su Ikram ya sa aka hada musu nasu kayan suka bar gidan da suke, sai da suka kusan barin cikin garin SAMAIND. Yasa aka kama Nawwas. Kallon juna suka yi kafin yacewa. "Na sami labarin ka gayawa Fudail duk abinda ya faru, sai dai kayi kuskuren domin ba zan barka a raye ba, shi yasa nayi gaggawan barin SAMAIND domin wancan mahaukacin idan ya ritsani sai ta Allah." Dariya Nawwas ya saka yana kallon Abrad, tare da nuna shi da yatsa kafin yace mishi. "Kai tsaye ka mu'amalancin Ikram, Ni kuma a ruwan sanyi Mu'amalanci kanwarka tare da dauke abinda yake jikinta. Bamu bar SAMAIND ba sai da na tabbatar da na kuma buɗe tsakanin kafarta na jefa linzamina. Yadda koda na mutu dole na bar baya da kura." Dariya ya kuma fashewa da shi, yana mai maita abinda ya faru,, yana kuma gaya mishi abinda ya aikata da Kanwar shi. Babu abinda ya kai wannan abin tashin hankali. Idanun shi ne suka cika da kwalla. Wanda ya kasa jurewa har ya kai da ya zuba masa. "Meye nayi maka Nawwas? Da kayi min yankan baya haka? Nawwas meye na tsare maka hakan da ka zab'i cilla rayuwar kanwata cikin tashin hankali? Nawwas me yasa baka yi a kaina ba." "Hahaha... Hmmm, ka zata zan zuba ido ne ka tozarta Ikram? Ko ka zata zan zuba ido ne ka cigaba da abinda ranka yake so? Wannan shi ne kishi a tsakanin zubda jini. Idan kana tunanin ka zubda jinin Nu'man dan jin dadin ka da kuma cusgunawa Mehran dan Ikram ta tsane shi wannan kuskure ne babba karka manta kamar yadda ka mayarda da Ikram a shimfid'ar ka, hakan na mayar da Amirah Azizatul Nissah. Na maida ta kamar matar da na biya sadaki me daraja dan haka karka yi tunanin Mehran zai yarda da wata mace bayan Ikram! Kamar yadda kake da kwarin gwiwar rubutawa yan majalisar Masarautan SAMAIND haka nima na gayawa Mehran alakata da Kanwar ka, dan haka sai ka jira abinda zai biyo baya domin dai SAMAIND ba kanwan lasa bane. Kayi kuskuren hadamme kome, Ni kuma nayi ƙoƙarin bayyanawa duniya waye kai, Ikram yanzun tayi maka nisa kanwarka zaka yi kokarin ganin ka fito da ita daga SAMAIND idan ba haka ba". Cikin wani irin fusata Abrad yaja takobi bai yi wata wata ba, ya sokawa Nawwas a kirjin shi sai da ya hudo bayan shi. Zuɓewa yayi akan gwiwar shi, ya kuma sake jan takobin ya soka mishi sai da jini ya fito ta bakin Nawwas. A lokacin ya tuna da Abinda Nu'man ya gaya mishi. *Ban san meye muka yi ba kuka raba mana rayuwar mu! Sai dai nasan wata rana kai ma haka ce zata mamaye ka! Yadda kayi min haka kai ba za a maka* Hawaye ne ya zubo mishi tare da kallon Abrad cikin tsannanin azaba. "Ni nayi haka ne domin al'ummar Daular Umayyad! Nayi wannan aikin ne saboda Banu Umayyad. Sai dai kuma nayi imanin yadda na zubda jinin bawan Allah haka nima rawa jinin ya salwanta. Kai kuma Banu Umayyad za a shafe baki daya. Sai kayi gudun da babu macecin ka. Abrad ni abokinka ne tun yaranta ka kashe ni da hannunka. Ba iya ni ne matsalar ba, rayuwar Kanwar ka anan zaka Fahimci muhimmancin rayuwar wanda kake so yaƙe" Kasa magana yayi sakamakon jinin da ya cika mishi baki, mika mishi hannu yayi amma fir yaƙi amsar hannun. Juya baya Abrad yayi kwalla na zuba mishi. Bai san ta yadda zai taimakawa Azizah ba, babban tashin hankalin shi Azizatul Nissah. Juyawa yayi cikin tsannanin fushi ya sare kan Nawwas, ya fadi can jini yana zuba kamar da bakin kwarya. Zama yayi tare da sake takobin ya fashe da kuka. Domin Nawwas ba kashin yarwa bane, ba kasafai ake samun irin shi ba. Nawwas abokin tarayya ne na kwarai. Mutum ne da ba a cika samun irin shi ba. Shi yasa yake kuka, sai kuma yadda Nawwas yaci Amanar shi yayi ta tarayya da Kanwar shi. Sannan ya kwashi sirrin shi ya gayawa Mehran, "Me yasa Nawwas yaci amanata?" Ya tambaya da karfi cikin tsorata da yanayin shi duk suka ja baya, sai daga can asalin amintaccen bawan Nawwas yace mishi. "Sabida shi ya fara son Ikram! Ya kaunace ta sama da kaunar da yakewa rayuwar shi! Ya bada rayuwar shi ne domin ita? Ya kuma saka duk wani matakin da zai bawa rayuwar ta taimako koda baya raye. Sultan kayi hakuri amma kaunar Nawwas ga Ikram gaskiya ce. Soyayyar shi ga Ikram gaskiya ce, tabbas yaso ta tun daga ranar da muka sayo ta, har zuwa yau. Ya gaya maka gaskiya kamar yadda kowa ya kasa fahimtar da kai haka ne. Amma tabbas bayi kuskuren ba, samun masoyi irin shi ma sai an tuna." Yana fadar haka ya shiga tattara gangan jikin Nawwas da kanshi yana zubda hawayen bakin ciki, da tausayin abinda ya faru. Ya tuna abinda Nawwas ya gaya mishi jiya. "Karka sake ka gaya mishi gaskiya akan alakata da Azizatul Nissah! Zan gaya mishi abinda zai fusata shi. Domin ya bar Ikram ta rayu da Mehran, naso Mehran ya tsaya muyi tsayayya magana dashi amma fir yaki. Dan haka zan gayawa Fudail Insha Allah zai saurare ni. Amma kasan me? Hmm idan Abrad yaga zai rasa Ikram zai sauya tsarin gudanar da abinshi ka saka ido kayi kallo. Don Allah Rab ka kula min da Azizatul Nissah da abinda zata haifa." A kidime ya kalle shi sannan yace mishi. "Shugabana ka manta matsayinta ne a yanzun? Har kake batun abinda zata haifa" Murmushi yayi sannan yace mishi. "Ba da ita ga Mehran ba shi yake nufin ita din mallakar shi bace, ita da abin cikin ta nawa ne, kuma mallakina ce, don Allah karka sake wani abu ya shiga cikin rayuwar su, fatana idan ka bar Oman kayi ƙoƙarin tsayawa Ikram, ka same ta da batun kome, kuma na roke ka don Allah ka tsaya a bayanta karka bari wani ya tab'ata. Ita kuma zata tsaya a gaban Azizatul Nissah." Wani irin kuka ne ya kwace mishi me ƙarfi yana me kuma rungume kan Nawwas, tare da jin tashin hankali sama da farkon faruwan kome, kara rungume kan yayi yana faɗin. "Me yasa kayi haka? Me yasa ka bada rayuwar ka domin wasu. Baka tuna bayanka ne? Me yasa kika zab'i zubda jini sama da kome ne?" Ya faɗa da karfi, yana kuka tare da k'amk'ame kan Nawwas, juyawa Abrad yayi tare da zuba mishi ido, tabbas sun zabi zubda jini sama da kome akan mace! Akan Ikram, koma waye za a kashe! Akan Ikram koda kuwa rayuwar shi ce zai iya badawa, wani irin kwalla yake zubdawa tare da kallon gawan Nawwas, mutum na farko da ya fara ankarar dashi kuskuren abinda yake aikatawa ya kashe mutumin da bai hada shi da kome ba ya kashe mutumin da zunzurutun kaunar shi da shi ko barci yake sai ya tashi idan ya tura a kira shi ya kashe. Ya kashe mutumin da yaso shi da gaskiya, ihu ya takarkara a cikin jirgin ruwan, sai da duk suka toshe kunnen su, ya kuma fashe da kuka yana faɗin. "Jininki fansa ce ga jinin Aminina" ya faɗa yana kuka da bakin cikin abinda ya aikata , Rab yana jin shi, tabbas ya fara dauko haske akan abin da Nawwas ya gaya mishi. Shiru cikin gurin yayi babu wanda ya kuma magana, mik'ewa yayi tare da cewa. "Ku dauki gawan shi ku wurga a ruwa!" "Sultan Abrad!" A fusace ya juya ga Rab, had'iye yawun yayi sannan ya sunkuyar da kanshi,bai kuma cewa kome ba. Amma tabbas wannan shine abinda ba zai iya dauka ba, dan haka yana ganin an dauki gawar Nawwas, aka fito dashi shima yabi bayan su da gudu, kafin yayi wani yunkuri an wurga cikin teku bayan dakaru sun rike shi. Ihu yake tare da kokarin kwacewa a hannun su, amma suka kara rike shi, yana ji yana gani gawan Nawwas ya nutse cikin ruwan, kuka yake tare da ihun. Buga mishi kasa takobi Abrad yayi. Bai kuma fahimtar inda kan shi yake ba. *** Wurgi yayi da takobin hannun shi, tare da fasa kara yana huci. "Tabbas Abrad yasan zan dawo na bi takan shi, wato shine ya gudu. Fudail Darda ina Nawwas din?" "Sultan MEHRAN! Tun jiya muke binka akan Nawwas, amma baka tsaya munyi magana ba, shi yasa da ya gaji yayi tafiyar shi bai..." Yadda ya kafe Fudail da ido ne, yasa shi sunkuyar da kai kasa, yana had'iye yawu. "Sultan MEHRAN!" "Ina jinka, meye yace?" Ya tambaye shi, tare da kallon gefe. Fita suka yi daga cikin gidan..sai da suka yi tafiya me nisa, sannan yace mishi. "Sultan MEHRAN! Nawwas bai gaya min kome ba!" Cakume wuyar shi yayi tare da fidda huci. "Ni zaka mara da takalmin kafarka? Ko zaka samu damar boye min abinda yake ranka? Gaya min meye laifina da kuke boye min abinda ya dace na sani." "Kayi hakuri bai gaya min kome ba, amma yace na nime bawan shi Rab." Wani dirkeken naushi ya kasake a jikin bishiyar da Bayan Nawwas yake jingine. Sai da hannun shi ya farfashe. Sannan ya takarkare ya fasa ihu. Sai da dajin ya amsa. Zafi biyu yake ciki, babu wanda zai gaya mishi gaskiya kenan? Ya rasa Ikram ya rasa wanda zai gaya mishi abinda ya faru kenan, dan haka ya tashi cikin tashin hankali ya juya zai tafi. Ya kuma juyawa ya kalli Fudail, sannan ya saka kai zai bar gurin. Ajiyar zuciya Fudail yayi sannan a ranshi ya ayyana cewa. *_Ba zan tab'a yarda na gaya maka gaskiya ba! Sai har na gama gabatar da abinda yake gaba na, ba zan tab'a yarda na kyale wanda ya cutar da ikram koda da bakar magana ce balle da farar magana! Kayi hakuri Sultan Mehran_* Ya faɗa a sanyayye, yana me jin tausayin Sultan Mehran. Domin a yanzun gaskiya yake nima idanu a rufe, kuma baya jin zai gaya mishi koda kuwa zai rasa rayuwar shi, Dole kuwa Azizatul Nissah taji a jikinta itama. Abin kunyar da suke amfani dashi ga rayuwar Ikram itama taji yadda tozarci yake. Amma kuma idan ya tuna rokon da Nawwas yayi mishi sai yaji tsoron kar haka kuma ya tab'a kimarta. Dafe goshin da yayi tare da bin bayan Mehran, yana tafiya yana zancen Zuci. Har ya isa inda dokin shi yake, dan yanzun kan yasan Mehran yayi mishi nisa, koda ya cilla dokin shi ya hango su, dab da Masarautan. Amma kuma koda ya isa Fir dakarun suka hana shi shiga. Wannan shine karon farko da Mehran ya mishi hukunci me tsauri ta hanyar amfani da hana shi, shiga SAMAIND! Dan haka bai yi fushi ba, ya zauna a gurin gashi garin da alamun shigowar damina. Duk sai yaji babu dad'i a ranshi, yau shine Mehran yayiwa wannan hukuncin, dan haka duk dai yake gani kamar tozartawa ne, ga wani muzancin da yake ji a ranshi. Kanshi a sunkuye har aka fara yayyafi. Bayan wani lokaci ruwa ya fara me mugun karfi da yawa. Yana tsaye a bakin kofar shiga masarautan.. ---- Tunda ya shiga cikin gidan, ake mishi magana kome ya gani fatali yake dashi, har ya shiga cikin dakin shi. Huci yake ya rasa yadda zai yi da Fudail idan kowa zai ci amanar shi yana tunanin ai Fudail ba zai tab'a yarda a cutar dashi ba. Kuma yayi imani da Allah akwai da yake boye shi, kuma ba zai tab'a yarda da munafunci ba, domin idan ba munafunci ba akan me zai boye mishi maganar da yake bukatar yaji, dan haka babu abinda zai hana shi bai hukunta shi ba, sai ya hukunshi sosai domin kuwa ba zai yarda da wannan wulakancin ba, tsaki yayi tare da kutufal da kayan shayin gaban shi, yana jin ana buga kofar shi amma fir yaki buɗe sabida yayi fushi anci amanar shi... (See me see trouble😹😂😹🤣 ta ina aka ci amanar ka Yau ga D'an Uwan Jamal🤔) +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 02 Kaiwa yake yana komowa, tsabar yaji haushin abinda ya faru. Jin cidan hadari tare da rugugi ya sashi zare ido cikin takaici da bakin ciki. "Duk irin zaman da muka yi da.". Bude kofar shi da aka yi yasa shi had'iye sauran maganar da da zai yi, ya zubawa kofar ido. Shigowa tayi tare da ajiye mishi ruwa. Sunkuyar da kai tayi cikin girmamawa tace mishi. "Sultan MEHRAN gashi." Kallon ta yayi tare da tuna abinda Abrad yayi mishi dan haka ya a nufi ruwan bai ce mata kome ba, ya dauka ya shanye tass. Ya ajiye kofin kafin ya zauna yana kallon ta. "Me yasa yayi min haka?" Kallon shi tayi a razane tare da ja da baya, tana girgiza mishi kai. "Ni." "Tambayar ki nake zaki dawo min da tambaya na" wani shegen tsoro ne ya lullube ta, tare da zaro idanu waje, jikinta yana rawa. Tabbas duk rayuwarta da tayi bata tab'a ganin wanda iya tsawar shi abar firgita ce kamar Mehran. Shin dan ya kasance Shugaba ne? Koko dan ya kasance Zaki ne kisabo, wallahi ita har tsoron had'a idanu take dashi. Ganin taki fita ya sashi fahimtar akwai abinda take buƙata, bai tsaya da tunanin shi ba, yaji marar shi kamar an daure mishi. Wani azazzaben sha'awar kasancewa da mace ya taso mishi. Kura mata ido yayi ganin yadda take kallon shi. Komawa yayi saman kujeran ya zube yana sauke numfashin sa. A hankali ta tako gaban shi, tare da tsayawa tana kallon yadda yake lumshe idanun shi, wato shi ba zai kira mace ta taimaka mishi ba, ya gwammace koda zai mutu ne gwara ya mutum, zare kayan jikinta tayi suka zube a kasa. Sannan ya taimaka mishi suka shiga d'akin. A wannan lokacin shi kanshi idan ka tambaye shi wani hali yake ciki bai sani ba, amma tabbas yaji a ranshi yana kwance da mace. Sai dai har yau kamar can baya da yaki matan dan kanshi ya kyamaci haka a ranshi. Duk da kyamar bai hana shi buga mata isa ba. Ya kasance ta da iya karfin shi da lafiyarta, tun tana kallon haka a matsayin abin da bai kai ya kawo ba, har ita da kanta ta fara dukar shi tana kuka. Shi kuma wai yayi haka bane dan lafiyar shi, haka ya faru ne dan abinda ta bashi ya sha, shi yasa ya rasa tunanin shi ya hake mata Sosai. Komawa gefe yayi tare da kwanciya rub da ciki. A hankali barci me nauyi ya dauke shi. Kallon shi tayi sannan ta mike a hankali. Bata tsaya wanka a dakin shi ba, ta saka kayanta tare da fita daga d'akin bayan ta ajiye mishi wani tambarin da zai iya wargaza mishi kome har karshen rayuwar shi. ~~~ Sai da ruwan nan ya kare tsaf akan Fudail ya shigo Masarautan, koda ya shiga shashin sa ya nufa yayi wanka da ruwan zafi sannan yana wankan tare da murmushin abinda Mehran yayi mishi bai wani damu can ba, sabida ko shi aka yiwa haka iya hukuncin da zai yanke kenan. Dan haka babban abinda yake shirin akan Azizatul Nissah ce. ~~~ Munyi tafiya me nisa wanda muka bar yankin Farisa sannan muka nufi kuduncin jazziratul Arab, anan muka yada Zango. Tunda muka tsaya aka gama shirya mana tantin mu. Na shiga gurin Sultanah Amrah, na zauna duk da ba hira muke ba, amma kuma haka yana sani jin kamar ina tare da Ammyn na ne, dan haka bayan munyi sallah na kwanta a gurin, ita kuma ta cigaba da abinda take, lokaci zuwa lokaci tana kallon yadda nake barci. Hawaye ne ya zubo mata, ta girgiza kai sannan ta cigaba da aikinta, tana tuna abubuwa dayawa akan yaranta da mulki yasa ta manta da su. Tabbas mulki matukar baka nemi Izni Allah akan shi ba, zai iya kai ka ya baro ta, Kamar yadda ya kaita ya baro ta, sai dai ta wani gefen zata iya godewa Allah tunda akwai Ikram da Ilham, Yar gidan Abrad. Murmushi tayi bayan ta shafa kanta, tana me jin kewar Yaran ta. ... Zan iya cewa barcin da nayi me cike da gajiya da mafarkai marasa kyau da dad'i, karshe dai haka na farka da sunan Mehran. Da gudu Rahil ya shigo tantin. Da sauri ya iso gabana, fadawa jikin shi nayi ina haki. "Me ya faru?" "Mehran!" Na fada kamar zanyi kuka. Juyar da kan shi yayi. "Ba zaki daina kwadayin ganin shi ba?" "Karka raba ni da shi, zuciyata halittar shi ce." Matse bakina yayi idanun shi cike da kwalla. "Ni kuma sabida ke aka halicce ni, ina sonki Ikram. Nasan idan ba zama daya muka yi ba, ba zaki daina kwadayin shi ba" ya faɗa bayan ya cire hannunsa a bakina, kokarin hada bakin mu yake na kawar da kaina. "Meye kike nufi? Ba zaki." Ture shi nayi tare da mik'ewa, ya kuma tasowa yana kallona. Kamar zai yi kuka yace. "Meye yafi Ni dashi? Meye na rasa da ba zaki amshi tayi na ba, wallahi yau sai na dasa miki kaunata a ranki." Fada sosai muka yi da Rahil domin ya kafe sai ya fahimtar dani yadda yake sona. Ni kuma na rantse ba zan yarda da wannan tunanin na shi ba haka muka gama dakyar na kwaci kai na. Sam na kasa nutsuwa a raina, domin kuwa, haushina yake ji kamar ya kashe ni, bayan fitar shi Sultanah Amratu ta shigo, fadawa nayi jikinta ina kuka. Tare da cusa kai na a jikinta. "Zuwa yanzun ya kamata ki cire Sultan Aamaan Abdus Samad Mehran, a ranki domin kwanaki ƙalilan zaki kasance matar Rahil. Don ki daina tunawa da sultan Aamaan." Kallonta nayi baki sake, kafin na sauke idanuna kasa, ina kuka. "Ummyn!" Yatsar hannunta ta saka min akan bakina, tare da girgiza min kai. "Kowa yasan cewa kece kwarin gwiwar shi, ki taimaka ki sauko ayi kome cikin ruwan sanyi." Hawayen da nake tarewa suka daga cikin idanuna, na kasa magana baki daya sai kallonta nake. "Tsarin masarautar mu, cike yake da kawaici da YAKANA karki yarda ahalin Mahaifinki su fahimci kin sayar da zuciyarki ga wanin su. Domin haka tilin abin kunya ce gare mu!" "Toh dole ne sai na rayu cikin mulki? Me yasa ba zaku gan.." d'aga min hannun tayi tare da kallon, yadda bakina yake rawa. Kifa kai nayi a tafin hannuna, na fashe da kuka. Ina girgiza kai, Tashi tayi tare da bar min tantin kuma ta hana kowa shigo min, domin tana ganin matukar suka shigo min zan iya tsarewa. Gurin yan uwan Baba na, ta nufa suka tattauna. Anan suka ajiye shawara ita zata wuce Asakandariya su kuma su wuce dani can Merocco. Idan ita mace ce mai rauni tausayina zai iya sakawa ta bani abinda nake so. Su kuma ahalin mahaifina babu wannan yanayin a tare dasu, dan haka su tafi dani. Bayan ta dawo ne, take kallon yadda na kifa kai ka a saman gwiwar kafana. "Zaku wuce Merocco." Da sauri na d'ago kai na, zanyi magana ya juya min baya bata bani damar ma tambayarta ba, ta cigaba da abinda take, ni kai na nasan ba zan iya tababa da ita ba, amma kuma ya kamata su fahimci abinda nake so. Bayan mun huta aka kuma tadda tafiyar. Ina ji ina gani ta tafi da Nimrah. Ni kuma muka tafi da Izmah, bayan mun sha kuka. Tunda muka dauki hanya, banzan can yake wani shige min. Ko kallon shi banyi ba, har muka wuni a hanyar, dab Magarib muka shiga garin, wanda tun kafin mu iso labari ya iso musu muna kan hanyar mu, sakamakon wani mahayi da aka turo shi. Dan haka garin ya kasance kamar ana bikin sallah, wani irin biki ake me cike da shagali. Haka muka isa har fadan, inda aka muka yada zango a falon Sultan Mu'allim. Mika min hannun yyi. Da sauri na isa gare shi. Ina isa na zube gwiwata a kasa, kai na a bisa kafadar shi, na sake kuka me cin rai. Takaici yasa Rahil fita a gidan. Kuka nake wanda idan ka tambaye ni ba zance maka ga abinda aka min ba, amma kuma a cikin raina, ina kuka ne domin na rasa Mehran. Yadda nake kukan ya sashi sake murmushin jin dadin. Sannan ya shafa kai na, yace. "Kiyi hakuri! Haka muke tsara miki baki rayuwar. Da karen layi gwara Zakin gidanka koda kuwa zaka zane shi da bulala ne, kiyi dan mahaifanki da kanwarki. Ba akan ki da soyayyar ki ba. Mun rigada mun yanke kuma al'adunmu sun sha banban da kowane, mukan iya binne abinda muke so! Mukan iya boye abinda muke kauna, matukar hakan zai bamu damar fuskantar matsalar. A tsarin mu, bai zama dole mace ta samu abinda take so ba, matukar zata bawa Mulkin mu. Gudunmawa dan haka na zab'i ra'ayin shi sabida ki bashi gudunmawa. Yanayin ku yayi daidai da mulkin, abinda ake bukata domin mulki kin hada, dan haka ki amshi Rahil a matsayin abokin rayuwar ki." Hawaye ne ya shiga zuba min, na kasa magana tare da sunkuyar da kaina, domin yayi min kwarjini. Haka aka fitar dani har dakin Bilqisul Ikram, tankwarata. Shafa kaina tayi sannan ta kira amintattun bayin ta, suka shiga dani ban daki. Aka hada min wani irin ruwan wanka tare da turaruka masu dadi. Sai furen kamshi da wanka aka watsa a ruwan, sannan suka shiga cudani. Hawaye na zuba a idanuna. Shi kenan na rasa Mehran. Na rasa Jarumina, me yasa tun tuni ban amsa mishi ba. D'ago kai nayi sannan nace a raina. _Toh amma ai bai ce yana sona Ba? Toh amma kuma ai duk abinda yake min duk na soyayya ce! Kishi da zafin rai akai na duk abinda masoyi ne kaɗai yake yin shi! Toh Ni me yasa na shiga zab'en? Kenan bawai na shiga dan shi bane sai dan ina son shi?_ Kwalla ne ya zubo min, ban san lokacin da na fashe da kuka ba, haka suka taimaka min nayi wanka na fito bayan sun bani wani yadi na lullube jikina, tare da fitowa daga ban ɗakin, tunda na fito suka shiga shafa min wani abu kamar mai kamar sabulu, ina zaune ina kallon su. Kwallar da nake sharewa a kai a kai, yasa Bayin suka shiga rarrashina, kamar dama jiran su nake na fashe da kuka. Hannun daya daga cikin su ta saka min a bakina. "Abin kunya ne babba ga Sultanah Balkisu Ikram aji cewa babbar Yar D'anta na farko tana kuka akan SO kinsan yadda muke boye kalmar a ran mu kuwa? Toh koda kuwa zaka rasa ranka akan sone yana da kau kayi hakuri da shi, idan baso kike mulkin kasar nan ta gagari Amir Rahil ba. Don Allah ki hakura da Sultan Aamaan Mehran. Mun san yadda kike son shi, amma duk wanda zaki gani a cikin masarautan nan yana da tab'on soyayya, dan haka karki sake a Fahimci zuciyarki tana ga wani da namijin domin abin kunya ce ga Kakarki." Haka suka kashe ni da magana tare da nuna min illar abinda nake aikatawa, nayi kuka da sunan Allah kuma nayi bakin cikin zamowa ta, daya daga cikin ahalin babban gida. Ina ji ina gani ranar aka mai dani kamar wata yar tsana, zunzurutun wanke nan shafe ne. Ana gyara min jikina. Har kusan tsakiyar dare a sannan nayi wankar karshe tare da sallah na kwanta,. Ranar barci na zance kacokan mafarkin Mehran nayi tayi. Ina kuka ina kome haka zan farka naga bayin nan suna rarrashina. ..... Washi gari ina farkawa kafin nayi sallah asuba, suka bani madara dafaffiya,, sai da na wanke baki na shanye tass, sannan na shiga wanka tare da Alola ina idarwa, aka kuma kawo min yankanken y'ay'an itacce, wanda aka zuba madara da zuma na shanye shi, ina ji suna faɗin. "Kirjinta muke son ya cika kafin zuwa bikin su." Shiru nayi domin bani da bakin magana sai yadda suka yi dani... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 03 Wato ma'ana bani magani suke tare da abinci me gina jiki, duk abinda suke idanuna a rufe suke, bana budewa wani lokaci haka zasu yi ta magana ina jin su, bana tanka musu, idan suka gama min kuwa a gurin nake kwanciya. Ina kuka duk taurin zuciya ta da taurin kai na, sai da ya kai komi kashin b'acin rai kuka yake sani. Rabona da Izmah kuwa sai dai na shafe kwanaki goma kafin aka barta ta shigo min dakina, lokacin da ta ganin sai da ta firgita, tana mamaki. "Ikram! Baki da lafiya ne? Kinyi kyau amma kuma kinyi mugun rama, meye yake damunki? Me aka miki? Don Allah gaya min" Zama tayi a jiki na, ban san lokacin da na fashe da kuka ba, nace mata. "Izmah Mehran nake son gani" kamar wacce aka dasata, haka take kallona. Bakinta yana rawa tace min. "Sultan MEHRAN?" Ta kuma tambayana, gyada mata kai nayi tare da rushewa da kuka, rike hannuna tayi tare da kwantar da kaina a kirjinta. "Ikram!" "Don Allah Mehran;" na katse mata abinda zata fada, duk sai ta rasa abinda zata ce min, ta kuma bude baki zata yi magana, Amir Rahil ya shigo cikin ɗakin, yan mata na biye dashi. Mikewa tayi zata fita na rike hannun ta. "Kiyi hakuri zan jira idan ya fita zan shigo muyi Magana." "Wacce magana zaku yi? Ai akan wancan Jahilin da ya kasa miki uzuri ko? Ko akan Abrad da ya gama da budurcin ki? Kinga Ikram. Ina Sonki shi yasa zan dauki duk abinda ya same ki, amma kika Kuskura kika shigo da Mehran yake ko Aman yake? Wallahi Billahi azim, zan kashe wannan abin" ya nuna min Izmah, sauka nayi daga gadon na zube gwiwata a kasa, tare da rungumo Izmah, ina kuka nace mishi. "Kayi hakuri! Ba zan kuma maganar shi ba, amma karka tab'a lafiyarta. Idan nice na amince." Na fada cikin kuka, murmushi yayi tare da nunawa Izmah kofa ta fita, tunda ya shigo inda nake ya d'ago ni. Kallon kayan jikina yayi yadda ya fitar da surar jiki na. Nayi kyau na fitar hankali. Duhun fatar da nake dashi ya washe nayi wani irin haske me ban mamaki. Matsalar kawai rashin nutsuwar da bani da shi ne ya janyo min rama. D'ago kai na yayi tare da kallon fuskana. Kan shi ya kawo da sunan zai hada bakin mu na kauda kaina, murmushi yayi tare da cizon kunne na, rike rigar shi nayi tare da jin saukar kwalla daga idanuna. Na bakin ciki dan Allah ya gani bana son shi a mijin aurena, a dan uwan na dauke shi amma bai Fahimci haka ba, yayi ta shige min. "Ai da wancan banzan ne ba zaki na kuka kamar karamar yarinya ba, dake baki kaunata shi yasa kike kuka. Ikram me yasa baki sona? Ni dan uwanki ne kuma zan iya bada rayuwata domin." "Ba zaka iya, shi daya ya bada rayuwar shi domin ni, don Allah." Dama abinda yake nima kenan, kuma ya samu. Dan haka banyi wani abun da zai nuna mishi jin dadi ko bakin ciki ba, na dai rufe idanuna. Ya gama sumbatar bakina, sannan ya janye daga jiki na, ganin har lokacin idanuna a rufe suke, ya sashi fita daga d'akin yana murmushin jin dadi. Haka rayuwar mu yayi ta tafiya, ina zuwa shashin Sultan Mu'allim, yana bani wasu abubuwan da ya zama mallakar mahaifina, tare da wasu kyautattakar, haka zan dawo shashin Sultanah Balkisu Ikram, na zauna, shima sabida wancan wahalallen nake haka, idan a d'akin ta, domin yana shigowa zata kore shi. Haka ya sani tarewa a d'akinta, duk da kuwa d'akina na kallon nata ne, haka akayi ta gabatar min da y'ay'an gwamnonin nahiyar, tare da manyan mutanen ƙasar. Har zuwa lokacin Mehran shi yake da kaso mafi girma a zuciyata, na kasa cire shi a raina. Na sha tambayar kaina me yasa lokacin da nake tare dashi ban ji haka ba, sai da bamu tare? Wannan amsar har yau na kasa bawa kaina amsa. Kullum da wannan nake kwana nake tashi. "Ciki abincin mana!" Kallon Sultan Mu'allim nayi tare, sunkuyar da kaina, na tsakuri abincin na kai bakina. "Rahil yace min har yanzun baku fahimci juna ba?" Sunkuyar da kai nayi tare da kasa kai abincin bakina. Ajiyewa nayi zan mike yace min. "Zauna." Komawa nayi ka zauna, tare da damke hannuna, jikina yana rawa. "Kar na kuma jin labarin kinyi magana akan SULTAN Mehran! Idan kuma hakan ya faru, zamu kashe baiwar da kike kauna, domin idan bamu fito miki a asalin mutane ba zaki kunyata mu. Bamu son muyi miki dole shi yasa muka baki damar ku fahimci juna. Nan da wata biyu muka baki ki fahimci waye shi idan ba haka ba." "Taya zan Fahimci abinda kuke so? Bayan ni din ba mallakarku bace, ni bana son lusari." Dukar tabirin yayi tare da kallon Sultan Mu'allim. "Atta kana jin abinda harshenta yake faɗa." Kallona yayi sannan ya kuma maida kanshi ga Ikram. "Haka zaki zauna dashi domin baki da mijin da ya wuce shi." Mikewa nayi zan bar gurin Rahil ya taka rigar jikina, karar yagewar jikina, naji kallon shi nayi ban san lokacin da na wanke shi da mari ba, sai da ya firgice. Tabbas yayi kuskuren babba, amma kuma marin da tayi mishi shine mafi girman wulakanci da aka tab'a mishi. Shafa fuskar shi yayi sannan yace. "Atta! Marina tayi." "Me yasa ka taka mata rigarta? Matar da zaka aura bata bukatar tilastawa, kasan tana da wanda zuciyarta yake so kai kuma ka same ta ne a sama. Karka sake haka ya kuma had'aku." Juyawa yayi sannan ya cigaba da cewa. "Ke kuma za aka kaiki gidan horo." "Atta!" Ya kira sunan Sultan Mu'allim, murmushi yayi sannan ya d mishi. "Idan na yanke hukunci ko kaina bana saurarra dan haka, Bhaiq kazo ka tafi da ita." Ban yi gardama ba dan haka na amince aka tafi dani. "Atta don Allah." "Matar da zaka zauna da ita ta mare ka, me kake tunanin nan gaba zata aikata? Dan haka ka bari a nuna mata girmanka da darajarka." Jikin shi a matukar sanyayye ya bar gurin cin abincin, bai tsaya ko ina ba, sai gidan kakan shi na gurin Uwa wazir. Zama yayi cikin nutsuwa sannan ya gaishe shi, tare da yin shiru. Kasa magana yayi yana kallon yadda Rahil din ya nutsu, kafin ya ce mishi. "Ina jinka!" "Dama dama dama.." "Ka nutsu kayi min magana!"inji kakan shi, nutsuwa yayi kafin ya fadi abin da ya kawo shi. Da kuma dalilin da yasa aka rufe Ikram. Kallon son kai yayi mishi, tsantsan domin kuwa banda son kai babu abinda ya hango a maganar Rahil. "Tun lokacin da ka bayyana soyayyarta a ranka na gaya maka cewa ka rabu da ita, amma fir ka kiya, sai ma goyan bayan da kasamu daga danginka, ba wai Ikram nace bata sonka kai ne baka dace da rayuwarta ba, ai duk wanda yaga yadda ta bar kasar nan bayan ta gama maka aiki har ta kai da ta nuna ita ta mutu zaka fahimci akwai soyayya a cikin tafiyarta, amma zuciyarka dake a rufe take kaki yarda akan lallai ita kake buƙata " "Amma kuma taya gida bai koshi ba za a dauka akai waje? Taya ina sonta zan kyaleta ta tafi yanki mafi hatsari da ganganci da rayuwa? SAMAIND cike take da rayuwa da mutuwa! Kuskure daya idan mutum yayi mutuwa tafi kome sauki a rayuwar shi. Uwa uba zunzurutun makircin da yake cikin masarautan. Kaka nazo ne domin niman hanyar da Ka fidda ikram, idan ba zan samu ba na hakura nayi tafiya ta" Kallon shi yayi na tsawon lokaci kafin yace mishi. "Ta yaro kyau take bata karko, Ba zan daina gaya maka ba Ikram bata dace da rayuwar ka ba, Ka barta tayi rayuwarta da wanda take SO Ni dan taimaka maka, amma ba zan tab'a tilasta mata ba,.kuma ba zan mata dole kamar yadda kuka mata ba, zan bata goyan baya ta auri wanda take so." Mikewa yayi cikin fushi zai fita, har ya isa bakin kofar kakan Yace. "Kai ake bukatar ka zama sarki, idan har baka san yadda ake sadaukarwa ba yaushe zaka yiwa Al'ummar ka adalci? Ita saboda jarumtarta ake bukatar ta a jikinka, me yasa ba zaka zama jarumi ba kamar ita? Amma karka tilastawa zuciyarta yake cike da kaunar wani. Domin kana ji kana gani zaka yi danasanin rayuwa." Fita yayi daga cikin gidan, ya nufi can babban shashin. Inda ta zube a gaban Sultanah Balkisu Ikram. "Me yasa bani da Sa'a? Me yasa kowa yake min kallon mahaddami? Ni ne ban dace da Ikram ba ko ƙaddara ta ce bata dace da ita bane? Sultanah a tunanina ni Maraya ne, samun Ikram ne ya sani fahimtar ni me galihu ne, me yasa Ikram ta sani nake jin ni ba kome bane? Me yasa a kullum nake jin nayi son kai? A duk lokacin da na kalli Ikram sai na dinga jin a raina nayi son kai sama da kome a rayuwar mu, tunda ta dawo cikin gidan nan ban tab'a ganin ta dauki takobin domin kare kanta ba, me yasa?" "Sabida zuciyarta tana wani guri na daban, kaunar da take mishi ba boyayya bace, yadda take kuka akan shi ya tabbatar min ita din ba kowa bace a fagen SOYAYYA! Zai yi wuya ka hada soyayyar da Jarumta, amma kuma ana ana iya hada soyayya da yaki koda kuwa haka zai bada damar a shafe alkarya guda! Akan soyayya tana iya haifar da juyin juya halin a cikin masarautan! Akan soyayya akan iya shayar da sarki guba domin cimma manufar Soyayya! Irin soyayyar Ikram da Mehran! Idan ba ayi takatsantsar gurin nuna musu bambanci rayuwa ba, dole dayan su yayi rayuwa dayan su ya mutu? Soyayya ce ta shiga tsakanin zubda jini! Kasancewar dukkan su sun kasance, a cikin lambu. Ba zance shine ƙayar ba amma tabbas haka ya nuna min cewa soyayyar su kamar fure ne cikin ƙaya. Gashi da kyau amma kuma haka za a hakura da shi,.idan kuma ka nace kana so. Ba makawa kayar zata illata ka. Idan kuma ka hakura dole haka zaka ji ranka ya raya maka soyayyar furen da take ciki ƙaya. A halin yanzun..Ikram ta kasance fure cikin ƙaya ce. Duk inda Mehran yaƙe yana faffutikar ganin ya iso gare ta, idan ma shi bai isa gareta ba, ita tana kokarin isa gare shi" "Taya bayan tana gidan bada horo? Haka ba zai yiwu ba " Ya faɗa tare da kallon kakan shi. "Zai yiwu mana, kai abinda ka sani kenan. Ita kuma abinda ta sani zata aikata. Kayi hakuri da Ikram domin ita zuciyarta tana ga Mehran..kai ma ai akwai shukrah da take sonka me yasa ba zaka hakura da Ikram ba?" Ka sake yayi yana kallon kakar su, kafin yace mata. "Me yasa kika ce haka?" Gyara zama tayi sannan tace mishi. " Kai anan gabaki daya cikin masoya da dangi kake, Mehran kuma cikin makiya yake rayuwa, da ace yana cikin dangin shine da suke kaunar shi ba zata tab'a komawa gare shi ba" " Amma kuma ai dan daukar fansa ta koma gare shi. Domin rama abinda yayiwa Nu'man." Dariya tayi sannan tace mishi. "Waye ya gaya maka k'iyayya ce ta kaita gare shi? Duk wanda ya gaya maka ta koma ne domin rama abinda yayi mata toh yayi karya, soyayya ce ta maida ita da ɗaukar fansa ne ba zata tab'a amsar tayin shi ba, da ɗaukar fansa ne ba zata tab'a yarda ta amshi ragamar auren shi ba, kasan inda ake kurman Kaunar! Toh ka zuba ido zaka ce na gaya maka Allah ya bamu nisan kwana" "Yanzun Nanna duk soyayyar da na mata ya tashi a banza Kenan? Na sota iya so babu algus me yasa na rasa ta? Soyayyar ta nake mata babu cutarwa a cikin shi amma me yasa ba zan same ta ba? Don Allah Nannah ki taimaka min na same ta. Dan itace abokiyar rayuwa ta...." [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 04 Murmushi tayi tare da ɗaukar ruwan da yake gabanta ta kurb'a, sannan ta dauke kanta kana ta cigaba da cewa. "Ba zan ce ka hakura da ita ba, domin ba a san maci tuwo ba sai miya ta kare, wayallah kayi nasara wayallah kuma ka fadi wannan shine abinda zan gaya maka." "Amir SULTAN yana niman ka" a hankali ya juya tare da kallon Bhaiq, sannan ya tashi tare da bin bayan shi. Suna shiga ya zauna a gaban Sultan Mu'allim da Wazir. Shiru duk suka yi sannan Sultan yayi gyaran murya yana faɗin. "Kaje ka tawo da ita" "Toh Atta mun gode." Daga haka ya juya ya bar gurin su, yana kara godiya. Bayan fitar shi Wazir ya kalli Sultan."ina ganin me zai hana ka hakura da wannan hadin da zaka yi ka barta ta akan zab'in ranta, tunda shi Rahil yana da masoya babu amfanin a tirsasata yin abinda bai dace ba." D'ago kai yayi sannan ya sake wata wadatacciyar murmushi kafin yace mishi. " Koda Rahil bai ce yana sonta ba, bana jin zan barta ta auri wani bayan shi, tunda kuma yace yana sonta sai naji faduwa tayi daidai da zama, abinda nake buƙata ne Allah ya kuma biya min bukatar, dukkan su mallakina ne!" "Allah ya huci zuciyar ka, ba wai ina nufin wani abu bane, sai dai idan har aka bata wanda take bukata haka kamar karin daraja ce ga masarautan mu, Yar mu tana auren Sarkin Samaind ka duba abinda idanun basira mana." Lashe bakin shi yayi tare da sunkuyar da kanshi yana wasa da furfuran kanshi, sannan ya kalli Waxir ya sake wata ƙaramar murmushi yace mishi. "Eh na hango katin ci-gaba amma bana jin a raina haka wata masalaha ce, babu cigaban da zata kawo ma, sannan babu wani abinda zai bayyana mana na cigaba dan tana auren Sultan Aamaan Abdus Samad Mehran! Kawai haka ba wani abun azo a gani bane dan babu wani Cigaba da za a ce an samu dan kawai tana auren Sarkin Samaind!" Shiru Wazir yayi yana kallon yadda Sultan Mu'allim, kasa yayi da kan shi ya kuma cigaba da cewa. "Sultan akwai matsala domin Ikram bata son shi da Aure a matsayin d'an uwan ta dauke shi, kuma haka ba zai tab'a kawo zaman lafiya, ido da ido kuke wariya akan ta, kuna nuna mata dan ita mace ce, ba zata zab'i abinda take so ba, sai shi? Haka zai sanya tayi ta mishi kallon ya fita daraja a gaban ku, sannan haka zai sanya tayi ta jin ina ma bata dawo gare ku ba, ban san yadda zan gaya maka kuna cusa k'iyayyar ku a zuciyar ta ba, amma tabbas babu adalci a tsarin ku." Shiru yayi sannan yana nazarin abinda Wazir ya faɗa. ... Ina zaune sai gashi ya shigo, kallona yayi sannan ya sake murmushi yana faɗin. "Bilqisul Ikram!" Dauke kai na nayi ina murmushin bakin ciki, takowa yayi har ina nake zaune. Durkusawa yayi tare da kifa min mari, sannan ya d'ago kai na, tare da yana kallona. Murmushi yayi sannan yace min. "Baki isa ba! Kinyi kaɗan Ikram marina kika yi? Idan da kin dake ni, yanzun baki isa ba." Tofa mishi yawu nayi tare da kallon shi har cikin idanun shi. Share fuskar shi yayi tare da wani irin murmushin takaici. Mikewa yayi sannan tare da cewa. "Ku kunce hannun ta, tare da kawo min ita shashina." Ya faɗa tare da ficewa daga dakin, tunda suka kunce hannun, suka tasa keyana har shashin shi, tunda nake da Mehran bai tab'a nuna min karfi ba, bai tab'a kawo min farmaki ba, yau sabida soyayyar shi Rahil yake nuna min karfi. Tunda na shiga ya saka ni a gaba da bala'i, domin karfi da yaji ya fara kokarin keta min rigana. Dakyar na kwaci kaina, yana ganin haka ya kuma shake ni tare da matse min nonuwa na, kuka ne ya kwace min tare da kallon shi. "Me yasa kake son lalata min rayuwa? Tunda nake da Mehran bai tab'a kawo min hari ba, kullum mutuntani yake tare da girmamani, na kwana a daki daya da Mehran na kwana a jikin Mehran hannun shi bai tab'a isa cinyata ko kirjina ba, bai tab'a kawowa a ranshi zai iya amfani da karfi ba. Yau d'an uwana yake son keta min mutuncina sabida nace bana son shi!" Murmushi yayi sannan ya mike tare da ture ni, ya nufi ban dakin shi yana ji kamar zuciyar shi zata fita, bai dan me yasa yake jin babu dadi akan Ikram ba, kuma ba kome ya janyo haka ba, sai dan yadda take nuna soyayyar Mehran a sama da kome. bata tausayin shi kamar yadda take nuna mishi da, yanzun ga baki daya ta tsane shi sabida Mehran, da zai ga Mehran tabbas sai ya kashe shi. Ya tsani Mehran ya tsani rayuwar shi. Kuma Insha Allah sai ya raba ta da kimarta koda kuwa ba zai same ta ba. Kafin ya fita na tashi tare da ɗaukar alkyabar shi na saka, sannan na nufi shashin mu. Tunda na shiga na zube a tsakar dakin na sake wani irin kuka me mugun cin rai, ina tuna Mehran. Ga baki daya naji na tsani kai na, me yasa a daren da nake duba shi ban bashi kai na ba, koda kuwa ace haka zai janyo min jifa ranar Amarcina. Kuka ne ya kuma kwace min, shigowar Ruwaida da Izmah ya sani juyawa ina kallon su, zama suka yi sannan suka ce min. "Abinda kike babban Abin kunya ne, ace yau kina kuka akan SO, WALLAHI ABIN GORI KIKE AIKATAWA UWAR DAKINA DON ALLAH KARKI KUMA ZUBDA HAWAYEN KI SABIDA SO" Dafa kafana Izmah tayi sannan tace min. "Kiyi hakuri Ikram!" Rintsa idanuna nayi.tare kifa kaina akan cinyar Izmah tana shafa min gashina, sallamar Ruwaida tayi tana kallon yadda nake zubda kwalla. "Ikram ki daina kukan nan, kiyi hakuri Insha Allah idan Mehran ne rabonki zaki mallake shi idan kuma ba rabonki bane shi Allah ya sassauta miki halin da kike ciki." Haka tayi ya rarrashina, har barci ya dauke ni. Gyara min kwanciya tayi tare da jera min matashin a kaina. Kallon Ikram tayi cikin damuwa, tana tuno abubuwan da suka faru, a baya tabbas wannan kadai ya ishi me hankali fahimtar hikimar Ubangiji, duk wannan zafin yanzun duk babu. Sai sanyin da tayi gabaki daya ta zama wata iri mara amfani. Bata iya fada bata iya rigima babu zafin rai babu kome sabida so tayi watsi da kome. ~~~ SAMAIND Kimanin wata daya kenan, kallon juna Jasrah da Mahlika suka yi cike da mamaki, jin likitan masarautan yana tabbatar musu da cikin da Azizatul Nissah take dashi. Saka su mutuwar tsaye. Shi kan shi Mehran kura mata ido yayi. Tabbas ya kwanta da ita tun daga lokacin da ya sha maganin ba sau daya ba ba sau biyu ba. Yasha Narjis ta kawo mishi ita, amma kuma bai tab'a kawowa a ranshi zai mata cikin ba. Domin idan ya tuna duk abinda yake da ita bawai yana mata yadda zata ji dadi bane yana mata yadda zata wahala ta gudu ne ya sami abinda zai kafa hujja dashi sai ga cikin shi ya isa kafa hujja. Wani irin yanayi yake ji na gamayyar damuwa ko tashin hankali. Kallon Azizatul Nissah Fudail yayi domin ya fara gajiya da tashin hankalin da yarinyar ta Kunno mishi wanda shima yasan laifin shine da ya gayawa Mehran wancan lokacin da yaci Ubanta amma yanzun ko ya faɗa zasu kira shi da d'an dakin Ikram ne, shi yasa ya zuba mata ido, yana kallon yadda take kokarin daurawa Mehran cikin da bana shi ba. Babu babban wawa sai shi. Yayi kuskuren barinta da cikin bai gayawa Mehran ba, da ya gayawa Mehran da kome bai faru ba, kuma dan kayan haushi ko Sultanah Fazilatul nisa bai gayawa,.yaja bakin shi yayi shiru dan wauta. "Sultan MEHRAN! Muna taya ka murnan samun Magaji Allah ya sauki Amirah Azizatul Nissah lafiya ta haifa mana Yarima." Cikin karfin iko da mulki tace musu.. "Insha Allah sai dai Na haifi Sultan Abdus Samad Aamaan Mehran, na biyu." Kallonta suka yi tare da kauda kansu, idan. Suka ci-gaba da tsayuwa zata iya saka su fidda abinda yake ransu. Dan haka suka juya tare da barin d'akin, suna mata fatan Alkhairi. Zama yayi a kusa da ita yana kallonta. "Ya jikin naki?" Murmushi tayi sannan tace mishi. "Da sauki, ina son cin abinci amma ina tsoron kar a bani guba sabida kishin rashin samun damar daukar cikin ka." Mikewa yayi tare da barin d'akin, murmushi tayi sannan ta shafa cikin Jikinta, kallon Fudail tayi da ya kura mata ido, tabbas badan kar yayi abinda zai sanya Mehran ya kullace shi ba, da yayi ta dukar cikin jikinta, har dai ta mutu. Amma a halin yanzun kana tab'a cikin kamar ka sayi mutuwa je da hannunka,domin Mehran ba zai tab'a barin ka a raye ba. Amma kuma taya haka ya faru? Cikin a sanin shi na Nawwas ne, kuma sai gashi ya juye tare da komawa na Mehran,.kuma babban damuwar shine meye ya faru ranar da ta fara kwana da Mehran. ---- Kallon ta Sultanah Hoyam tayi sannan tace mata. "Kamar Ya Azizatul Nissah tana da ciki? Kina nufin yayi tarayya da ita ne! Ko kina nufin." Zuɓewa Mahlika tayi tare da rike hannunta cikin juna jikinta yana rawa tace mata. "Sultanah! Duk abinda kike tsammani haka ne". Ture kayan gabanta tayi tare da cewa. "Na aike ki ne ki zo ki gaya min matar da suke kewayen shi.tana da ciki ne? Meye amfanin abinda na baki kina saka musu a shayin su? Wato ga sakarya nan bata san me take yi ba, Yanzun meke tafiya a harem?" "Kiyi hakuri abinda ke faruwa babu dad'i domin dai ta kwace duk abinda ake yi, sannan kuma ta hana kowa shigowa shashinta. A takaice dai hatta abincin da zasu ci sauran matan daga gare ta yaƙe.". Sake wurgi tayi da kayan marmarin gabanta. "Wani irin hauka kika yi ne? Me kika aikata min haka? Baki da hankali da zaki bari kome ya koma hannunta, ni kuma nawa aikin fa?" Sake damke hannunta tayi iyaka razana ta razana, amma bata iya ko tari ba, domin Sultanah Hoyam ta isheta riga da wando, dan haka ta sunkuyar da kanta, sannan tace mata. "Ki gafarce ni!" "Tashi ki fita!" Ta daka mata tsawa. Da sauri ta mike tare da barin d'akin, ta nufi harem. Ajiyar zuciya ta sauke yafi sau uku. Sannan ya nufi Harem, tunda ta nufi hanyar gidan, take jin kamar zuciyarta zata buga, tana shiga tayi karo da Rubina babban baiwar Azizatul Nissah. "Ina kika tafi? Toh muje zaki yabawa aya zakinta, tunda da zaki fita baki gayawa Sultanah Azizatul Nissah ba. Wato anje kitsa munafunci ko?" Bata ce mata kome ba, har ta shiga gurin Azizatul Nissah, kanta a sunkuye. Tana shiga ta tsaya daga bakin kofar shiga d'akin. "Da izinin waye kika fita daga Harem?" Shiru tayi tare da wasa da warwaron hannunta. "Kinawa Ikram Aiki ne?" Da sauri Mahlika ta d'ago kanta, tare da girgiza kai tana faɗin. "Me kuma zanyi mata bayan bata nan!" "Ki min shiru! Koda yake ba mamaki kinawa Jasrah aiki ne ko? Toh zo nan." Durkusawa tayi a gabanta, tare da matsawa kusa da ita. Babu tausayi ta shiga marin Mahlika, sosai fa tun yarinyar tana jurewa har ta kasa jurewa, bata fasa ba, shigowar Mehran ya sata sauke hannunta da ta d'aga, zata kuma marin Mahlika. "Meye haka?" "Sultan MEHRAN! Abu ta kawo min da guba, wai ikram ce ta bata sakon duk lokacin da ta sami labarin ina da ciki ta zuba min nasha." Ta faɗa tare da sake kuka. Wangale baki yayi tare da kallon su, kara kallon Mahlika yayi yasan yace mata. "A sanina baki shiri da Ikram meye gaskiyar abin da ta faɗa?" ... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 5 Jikinta ne ya dauki rawa, tana kallon sharri kiri kiri. Amma bata da ikon kare kanta, kallon ta yayi a karo na biyu fuska babu alamar wasa yace mata. "Ba dake nake ba?" Ya faɗa da dan karfi, haka ya sanya ta kuma rud'ewa tana zaro idanu. "Sultan!" Ta kira sunan shi jikinta yana wani irin rawa."Fudail!" Ya kira sunan Fudail ko rufe baki bai yi ba, sai gashi shigo d'akin. "Yawwa bawa Fudail ka tafi da ita,.ka kuma tabbatar ka hukuntatta, domin tayi yunkurin zubda min cikin jikina ko Sultan Mehran" ta ambaci sunan Mehran tana kallon shi. Dauke kan shi yayi tare da zama ya kasa cewa kome. "Zaku iya tafiya!" Ta kuma fada, tana murmushi. Matsowa tayi kusa dashi, ta zauna tana me sake mishi murmushin jin dadi. "Sultan MEHRAN! Kaga ikon Allah baka ta samu haihuwa ba sai a kaina, kuma." Juyawa yayi yana kallonta,.kafin ya dauke kanshi yana me jin b'acin rai akan yanayin da yake ciki. Haka tayi ta damun shi da magana, ganin yaki kulata yasa ta mike tare da barin d'akin, bin bayanta yayi da ido, ita kuwa tana fita bata tsaya ko ina ba, sai Shashin Sultanah Fazilatul nisa, tana tare da Shairah da Narjis, suna tattaunawa ta shigo. Murmushi tayi sannan ta nemi guri kusa da Sultanah tace mata. "Nazo ne ki albarkaci jikanki da yake cikin mahaifana" A matukar mamaki suka kalle ta, bakin su sake. "Sultan MEHRAN bai gaya miki bane? Ai wata biyu da suka wuce ya..." "Toh ya isa!" Inji Shairah, ya daka mata tsawa. Gyara zaman tayi cikin fusata tace mishi. "Kai waye? Bawa dan daudu, ni zaka dakawa tsawa? Lallai kana son na saka a maka koran kare." "Ya isa haka, me kike bukata?" Inji Sultanah Fazilatul nisa. Tana kallonta, Dariya tayi sannan tace mata, "Bana son a kuma barin Mehran yayi mu'amala da wata mace! Sannan bana son ana shiga shirgin shi. Idan da hali a fita hanyar shi. Domin nice Magajiyar sarauta nan gaba, Uwar Yaron shi da yake kwance mahaifana!" Ta mike tare da zaga dakin tana murmushin mugunta, tana faɗin . "Mugun hukunci zai tabbata a kan wanda ya Kuskura ya shiga lamarin Mehran. Zan gyara mishi tunanin shi da nazarin shi, kar na kuskura naji mugun labarin akan haka, a sanar da matan da suke dakon ya kwana dasu." Tana gama fadar haka ta bar dakin cikin jin dadi tare da jin ta isa domin ta kaftawa Sultanah Fazilatul nisa kashedi kuma hakan zai taimaka mata, domin idan ba haka ba tana ji tana gani sauran matan da suke hareem zasu iya daukar cikin Mehran. Koda ta fita, kallon matan da suke hutawa tayi, sannan ta zauna tana gyara gashin kanta, tana murmushi. Baiwarta Rubina ta kalle matan gurin ta shiga musu bayanin cikin Azizatul Nissah, take Jasrah ta mike tana faɗin. "Karya ne, baki isa ki" "Kawo min ita nan" inji Azizatul Nissah, babu musu aka kawo ta, jefata aka yi a gabanta, mik'ewa tayi a hankali, tare da kallon ta. Murmushi tayi sannan tace mata. "Kika ce me?" "Kar..." Kifa mata marin da tayi yasa ta had'iye maganar da zata yi. "Rubina, ki zane min ita." Inji Azizatul Nissah wai a zane Jasrah. Duk sauran matan hatta Sakeenatu binti Abu Waqqas, sai da jikinta yayi sanyi, domin tunda take rayuwa bata tab'a tsintar kanta cikin mugun yanayi ba, sai da ta shigo cikin Samaind. Akan idanun su, aka zabe Amirah Jasrah irin mugun dukar nan da babu wanda ya isa yayi maka ita sai mugu. Shafa Jelar gashin kanta tayi tana faɗin. "Ya isa haka, ba ita ba hatta ku idan kuka kuskura kuka d'aga min murya zan ba kowa kyautar hukuncina, ku dauke ta ku kaita shashinta." Cikin wani irin tsoro da fargaba tabbas Azizatul Nissah ta shirya fuskarta kowa kuma a cikin wannan yanayin, ta gaya musu ciki ne da ita, dan haka kar kowa ya taka shashin Sultan Mehran sai da izinin ta. Gyada mata kai suka yi. Domin babu wata hanya da zasu mata bori. ---- "Meye ya hadaki da ita har ta sako Ikram a maganar ta." Fudail ya tambayi Mahlika. "Kawai sharri take son yi mata, kuma tasan a halin da Mehran yake ciki na kewar Ikram zai iya tsanar." Rike bakinta tayi tana kallon shi. Murmushi yayi sannan yace mata. "Karki damu. Yanzun me kike ganin zaki yi?" Shiru tayi sannan ta sunkuyar da kanta kasa, tana me jin kamar tace mishi zata koma Madinatul Mah, sai kuma ta d'ago kai tana faɗin. "Babu abinda zanyi." "Ni kuma zan sakaki aiki" ya faɗa mata yana leka hanyar, a hankali ya matsa tare da gaya mata abinda yake son tayi mishi, zaro idanu tayi sannan tace mishi. "Zanyi amma da sharadin. Zaka hada ni da sultan Aamaan! Murmushi yayi sannan yace mata. "Ba zan iya hadaki dashi ba, mutum ne me ra'ayin kanshi, idan kika sami damar ya gayyace ki toh idan kuma baki samu wannan damar ba, ina me tuna miki aikina da na baki. Sultan MEHRAN yana cikin kewar Ikram ne ko yayya aka tunzura shi zai iya aikata wani abu bayan haka." Yana gama gaya mata haka ya juya abin shi ya barta a gurin. Shiru tayi na wani lokaci kafin ta bar gurin tana jin itama zata tsayawa kan. ...... A can cikin gidan kuwa, kallon Juna ake tsakanin Sultanah Fazilatul nisa dasu Shairah. Kura musu ido tayi kamar tana son gano gaskiyar abinda Azizatul Nissah ta faɗa, sai kallon su take kamar tana hango abinda. "Ina Mehran? Maza ku nimo min shi." Ta faɗa da karfi. Kallonta suka yi kafin suka ce mata. "Yanzun lokacin hutawar shi ce, idan muka." "Nace ku nimo min shi ko?" Babu musu suka fita, shashinta suka nufa, inda Shairah yayi karo da Sultanah Hoyam, itama tana kokarin shiga shashin Sultan Mehran. "Dama kana raye?" Murmushi yayi sannan yace mata. "Ina nan daram." Ya bata amsa. "Toh haka ma yayi, sai dai har yanzun baka gaji da bautawa matar da bata san ƙaruwar ku bane." Murmushi yayi sannan yace mata. "Gaskiya labarin da nake ji bai kai adadin abinda zaki bani ba, koda yake ai girman jiki gare ki bana shekaru ba, idan kika sake mummunar alaƙar da kike da Darakshan ya fito tabbas." A firgice take kallon shi. "Karka min Sharri!" Sassauta muryan shi yayi sannan yace mata. "Karki damu, babu wanda ya fahimci haka sai ni, kuma babu wanda zai fahimci abinda kike aikatawa sai har kin tonawa kanki asiri." Daga haka ya wuce ta bai kuma mata magana ba, karshe bata shiga gurin Mehran ba, ta koma da baya. .... Yana shiga ya same shi zaune ya faɗa cikin mugun tunani me shegen zurfi, dan ya jima akan shi kafin ya mishi magana ya farka. Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya kalli Shairah. "Sultanah tana son ganin ka!" Kurawa Shairah idanu kamar wanda yayi mantuwa, a hankali ya janye daga kallon shi tare da gyada mishi kai, fita yayi cikin tausayin MEHRAN, domin baki daya yayi laushi. Tausayin yadda soyayya ta maida shi yake. Ya jima yana nazarin abinda yake damun shi wanda yayi itifakin Babu shakka Ikram itace rayuwar shi, sannan bayi da wani kuzari sai idan tana tare da shi. Ya san a wannan lokacin tana tare da Rahil. Suna soyayyar su. Haka kawai idanun shi ya shiga hango su, suna hira a lambun suna soyayya. Watsi yayi da kayan gaban shi,yana haki. Kwalla ne ya cika mishi ido, a hankali ya kai hannun shi kirjin shi yana jin kamar zuciyar shi zata buga. "Innalillahi wa'inna ilaihi rajioun Ubangiji ka yayye min, ka kuma kara min hakurin rashin ta. Ya Allah ka jarabce ni ta inda ba zan iya cinyewa ba. Ya Allah na tuba ka yafe min." Ya faɗa tare da jin kwalla nason zuba daga idanun shi mai dasu yayi, tabbas yana cikin wani hali, Ikram ta shiga rayuwar shi. Ya jima sosai a gurin kafin ya daidaita nutsuwar shi yayi sannan ya fita daga dakin. --- tunda ya isa shashin Sultanah, bai ce kome ba sai dai duk tambayar da tayi mishi baya ko motsi balle ta saka ran zata sami amsar tambayoyinta. "Aamaan" ta kira sunan shi kamar ,zata fashe da kuka tana cewa. "Meye gaskiyar abinda." "Anneh bana son kina shiga cikin al'amarin gidana." Daga haka ya mike zai bar d'akin tace mishi. "Amma me yasa ba zaka gaya min abinda yake damun ka ba?" Juyawa yayi tare da sake murmushin takaici, sannan ya bar dakin yana ji kamar ya had'iye zuciyar shi ya huta, ranshi ya kai kololuwar ɓaci, baya ganin gabansa. Yana shiga cikin d'akinta ya tokari kofar shi, kallon shi tayi a razane. Amma ta dake, juyawa tayi tare da kallon bayin d'akinta. Da sauri suka fita, Da sassarfa ya isa gabanta, zai kamo wuyar ta, tayi baya tana girgiza mishi kai. "Duk abinda aka gaya maka karya ne, tunda suka ji labarin samuwar cikin jikina suke kokarin ganin bayan shi, sabida." "Na tambaye ki ne? Nace kiyi min magana ne? Meye ya kai ki shashin Mahaifiyata." Ya tambaya ta a tsawace. Diriri cewa tayi kafin ta saka mishi kuka, tana faɗin. "Ita Fazilatul nisa ce Mahaifiyar ka?" "Tauuu!" Ya kifa mata mari, wanda yasa ta ganin taurari, a hargitse ta d'ago kanta, wani shegen tsoro ne ya kamata bata san lokacin da ta sunkuyar da kanta ba, gwiwarta zube a gaban shi. "Na kuma jin labarin haukarki ta kwashe ki har kofar shashin ta, sai na karya ki na maida ke yankin ku, kije can kuyi ta haukar ku sakarya." Yana gama fadar haka ya juya tare da barin d'akin, tunda ya fita yake jin kamar ya tattara ya bar SAMAIND ko zai sami sauƙin damuwar da yake ciki, amma ina. ---- Dan haka ya tattara ya koma can gidan shi da ya tab'a zama, dan anan yake jin zai iya samun nutsuwar da ya rasa. Tare da Fudail suka koma sai masu kula da abinda zai ci, sam baya son magana ko da kuwa a cikin mutane ne, yafi son ya keb'e kanshi yayi shiru. ---- Merocco. Da wani zai gaya min yadda rayuwata zata koma ba zan yarda ba, dawowar Nimrah bai kara min kome ba, sai damuwa domin tunda tazo bata da wani aiki sai kukan halin da ta sami Mahaifiyarta, ga kuma soyayyar Fudail da ya kamata, kwanciya tayi a jikina. Tana zubda kwalla, tare da gaya min halin da take ciki. Shafa kanta nayi domin ita kukan dad'i take, kuma nasan zata sami abinda take so ni kuma fa? Waye zai bani abinda nake so? Sam mulki da nasabarta bata dace da rayuwata ba, ni rayuwar Yanci nake so. Bana bukatar kome bayan Yanci, shi yasa da zan mallaki Mehran tabbas zamu bar SAMAIND har karshen rayuwar mu, mu shiga inda ba za a kuma ganin mu ba, muyi rayu daga mu sai Yaran mu. Wannan shine tsarin da nake shirya mana,.kamar Yadda iyayena suka bar gidajensu, haka mu ma zamu bar cikin daular mu. Muje mu kafa kanmu tare da boye asalin mu. "Assalamun Alaikum!" Sallamar Rahil ya katse min nazarin da nake. Lumshe idanuna nayi kamar ina barci, shigowa yayi tare da zama yana kallon yadda na sunkuyar da kaina, murmushi yayi tare da cewa. "Toh meye laifin sallamar da ba za a amsa min ba?" Ya tambaye ne ni, tare da tsare Ni da ido. Mikewa Nimrah tayi tare da kallon shi tace mishi. "Barka da shigowa Amir Rahil," d'aga mata hannun yayi yana murmushi, a hankali ta bar d'akin. Dawowa gabana yayi tare da zama ya zuba hannun shi akan cinyata. "Me yasa kika fi son shi akan Ni? Meye bani dashi? Dame ya fini da kike zubda hawayen ki sabida shi?" D'ago kai nayi ina kallon shi sannan nace mishi. "Kai zab'in kakannin mu ne, shi kuma wani shashi ne na rayuwa ta, zan amshi aurenka ne...[5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 25 Ina zai kai tilin abin kunyar da ya faɗa? Ya zai fahimtar dasu ba laifin shi bane na zuciyar shi ce da bata da adalci? Ina gwara ya had'iye kome koda haka na nufin ciwon da ke zuciyar shi itace ajalin shi. Da kunya ya bude bakin shi yace soyayya ce ta maka shi da kasa, da wani ido zai kalli jama'ar fadan shi, da wani bakin zai gaya musu ba yin shi bane zuciyar shi ce da bata san Yakana ba, kai tir da wannan kalama me sunan *SO*, bata mishi adalci ba. "Allah ya baka lafiya, ga magani nan za a baka naka sha, don Allah ka rage damuwa da tunani." Ya fada mishi, juyawa yayi tare da hada kayan shi, ya fita daga gidan. Jungu jungu suka yi tare da kallon shi. Lumshe idanun shi yayi yaki magana, dan gani yake kamar zasu kasance tsaf abinda yake damun shi. Shi yasa ya juya musu baya, dan baya son su karato abinda yake damun shi. ~~~ Da gaske Mehran ya targada min hannun, asalima irin targad'en nan na kan wuyar hannun ne, dan haka naji bakin cikin ainun. "Ikram me ya sami hannunki?" Murmushi nayi sannan na maida hannun na rufe. "Faduwa nayi?" Na fada a gakile, "Amma sai wannan bai kama da faduwa ba, sai dai ko an murɗe hannun aka yi, don Allah waye ya miki haka?" Tashi nayi zan koma cikin dakin. Suka sha gaba na. "Ikram! Kin fita daren jiya gidan Sultan Aamaan!" "Babu inda naje!" "Matsala baki iya karya bane dubi yadda fuskar ki yake nuna alamun karya kika yi? Idanun ki juyawa fa suke? Kalli yadda kike kyafta su, wallahi baki iya karya ba, kin yafi jiya ganin Sultan Aamaan ko?" Suka sani a gaba da tsokana, tare da cewa. "A haduwar farko aka targad'en hannun haduwar gaba, ba zata muku kyau ba wallahi!" Suka fada suna dariya, tsaki nayi tare da barin su a gurin ina jin haushinsu. Zama suka yi ina jin su, suna gulma ta, share su nayi ina kula da hannuna, domin bana son damuwa da zata kuma kara min ciwo na. Da dare ma, sun ta zuba ido ko na fita, suka ga ban nuna alaman zan fita ba suka hakura, dole suka kyale ni. ~~~ "Sannun Sultan Mehran! Ashe baka ji dadi, d'azun Darakshan yake sanarwar a fada." Murmushi yayi sannan ya kalle su. Fuskar shi a sake kamar babu abinda yake damun shi, nan kuwa kasar zuciyar shi, Ikram ce take yawo har da ingiza shi akan a duba garin ko anyi baƙi daga wani gurin. Ya bude baki yayi magana yana ganin kamar wani katon aiki ne, shi yasa yake bin su sa ido, shigowar Sultanah ya sashi mik'ewa zaune. "Anne!" Wani irin dad'i taji a ranta,. Musamman yadda yake kiranta da Uwa, zama tayi a bakin gadon. "Mehran! Ga maganinka, sannan don Allah meke damunki? Aamaan ka gaya min don Allah meye matsalar ka?" Murmushi yayi sannan ya juya yana kallon Mahlika da take dauke da tiren maganin, a yanzun yana bukatar mace a kusa dashi, dan haka ya dauke kanshi dan baya jin kome akan ta, duk da yana bukatar mace, baya jin Mahlika takai matsayin Ikram. "Miko min na bashi yasha." Ta mika mata, hannun. Cikin girmamawa ta bawa Sultanah. "Anne barta ta bani!" Ya fadi hakan cikin wani irin yanayi, da ta fahimci yana bukatar nutsuwa, dan haka na shafa kanshi tare da cewa. "Ko Mehran zai barni na kintsa mishi ita?" Kasa d'ago kanshi yayi domin yana matukar jin kunyar ta, ganin bai mata magana ba, yasa ta ajiye maganin sannan suka fita. Bayan wasu mintinan, sai gata ta dawo d'akin. Murmushi yayi sannan yace mata. "Zo nan!" Durkusawa tayi a gaban shi, murmushi yayi sannan yace nuna mata tiren maganin, bayan ta bashi ya sha, sannan ya ce mata. "Zaki min wani aiki ne!" Nutsuwa yayi tare da kallonta, saka hannun shi yayi a haɓɓar ta, tare da d'ago ta. "Zaki shiga cikin gari" Kura mata ido yayi sannan ya kuma kai kanshi fuskarta, a hankali yake yawon da hannun shi cikin jikinta, tare da kai kunnen ta, tare da faɗin. "Kina da kyau!" Wani irin ajiyar zuciya ya sauke, domin kuwa ta shiga cikin wani irin yanayi, tare da rike shi. Wato Mehran wani irin mutum ne da ya san kan tafiyar da mace, domin cikin siyasa da hikima yake birkita mata lissafi,kafin ya bata aikin da zata mishi bayan ya kai goshinsa kan gefen fusakarta. Yana goga hancin shi har zuwa wuyarta, rike rigar shi tayi tare da sauke wata irin ajiyar zuciya. "Sultan!" Ta kira sunan shi, tare da shigewa jikin shi. "Kinji abinda nace miki" "Eh Sultan naji kuma Insha Allah zan yi yadda kake so." Shafa fuskarta yayi tare da cewa. "Maza yarinyar kirki, jeki maza." Jikinta na rawa ta mik'e, kamar zata fadi, fisgo ta yayi tare da cewa. "Zo nan!" Kafaffunta ne taji kamar ba zata iya daukarta ba, shimfid'a ta yayi tare da gyara mata kwanciya, a jikinshi. Wani irin yanayi yake ji, tabbas idan yayi haka kamar yaci amanar zuciyar shi ce, dan haka ya mata masauki a jikin shi, tare da shafa bayanta, har ta fara sauke ajiyar zuciya, kafin ya d'ago kanta. Ganin yadda idanunta tana juyawa, shafa fuskarta yayi tare, da shafa bakinta tare da kallon yadda take kuma tsima, da mugun sha'awar shi. "Ikrammmmmm!" Ya ja sunan kasar makoshinsa, kafin ya d'agota yace mata. "Maza ki tafi inda na Turai" A hankali ta sauka daga gadon, tabbas tana bukatar shi, amma anya jin koda wasa ba zai bata wannan damar ba. Domin wallahi mace daya zai iya bata kanshi da ruhin shi, gangan jikin shi ta da ruhin shi mallakin Ikram ce, dan haka yake jin ba zai iya sake ya bawa wata mace ba. Ita daya ce nata ne kuma baya jin zai bata kuma. --- Gyara zaman igiyar da na zarga hannun a cikin shi nayi ina rintsa idanuna, ga wani uban zufar da nake kamar na had'iye gaushi. Kallon hannun nayi tare da kallon yadda hannun yayi fushi, tabbas sai na mishi illa. Domin bazan tab'a daukar wannan kasadar ba. Kallon juna muka yi da Izmah, murmushi tayi sannan tace min. "Gaskiya Sultan Mehran ya iya mu'amala, kan Uba yadda ya daki hannun nan bana jin zai kuma moruwa." Kwalla ne ya cika min idanu, na miki ina huci. "Kinga Mehran bafa banza Allah ya bashi duniya ba, wallahi baki isa ba, ba irin sakarkarrun da kike musu kisar gilla bane, dan haka karki kuma barin kuyi gamo na biyu, dan na rantse zaki sha mamaki!" Zuɓewa nayi kasar d'akin, kwalla naso zuba min nace. "Billahi azim! Idan na kuma zuwa gare shi sai na karshi!" "Me yasa baki karshi ba? Hmm! Ki daina zafaffawa fa" "Fitar min a daki bana son ganin ku!" Me fada da karfi ina me juyar da kaina, kwalla na zuba min. Domin ban tab'a faduwa irin na yau ba, Mehran ya hanani samun galaba akan shi, goge kwallar nayi dan nan da kwana uku zan koma mishi. ..... A hankali muka sami kwana uku babu wani abinda zan kira na jin zafin Mehran, sai ma tsanar shi da yake kuma samun zama a raina. A ɓangaren Mahlika kuwa wani irin haukacewa tayi da kaunar Mehran, domin idan ta zauna ji take kamar zata gigice. Kamshin turaren shi ya rike kayanta, har yau tana jin hancin shi da yake gogawa a wuyarta, wani irin shauki take ji, bata san lokacin da kuka ya kwace mata ba, domin yau kwana uku tana zaga cikin gari domin nima mishi labarin bakin da suka shigo babu labarin dan kullum SAMAIND bai rabuwa da baki, dan haka ta koma yau zata gaya mishi babu bakin da suka shigo garin. Sai dai ko zata mutu zai ta haɗa shimfid'a da matar da zai kira tashi, kamar yadda zai yi da Kwarkwarorin shi haka itama zata bashi damar yayi da ita, ba zata iya barin ya subuce mata ba, dan haka ta kulla iniyar haka a ranta, tare da zuba idanunta akan shi da kuma matan da zasu zo gare shi. Wannan shine alkawarin Mahlika, kamar yadda mahaifiyar ta, taso yi da Sultan Abdus Samad, yau itama tana kuma alkawarin zata gwada sa'ar ta akan Mehran. (Inda ba kasa nan ake gardaman kokuwa 🤔) ~~~ Ba haka yaso ji daga gare ta ba, kauda kanshi yayi daga kallonta, sannan ya mike tare da cewa. "Jeki!" A hankali ta juya tare da barin d'akin da sauri, tana jin kamar tayi kuka, amma kuma bata da halin haka, domin ita bata ki yace tazo ta kwana dashi ba. A falon kasa ya sami Sultana, "Akwai abinda ya shiga tsakanin ku ne?" Cikin girmamawa, ta sunkuyar da kanta sannan tace mata. "A'a!" Sai dai kuma ba haka taso cewa a'a ba, domin taso ace tace eh domin kuwa bata ki, tayi karya akan wani abu ya haɗa su ba, toh amma sanin cewa ba yarima bane sarki ne guda wanda haka zai iya janyo mata rasa rayuwarta yasa ta amsawa da babu. Domin wallahi ba a Samaind zaka yi wasa da rayuwarka ba, ai ko kura yasan gidan me babban sanda. Safa da marwa yake yana jinjina qarfin halin wanda ya kawo mishi hadi matukar ba ikram bane, toh tabbas babu aikawa yayi biyar cutar shi. Wato yayi niyyar mishi kisar gilla ne fa, domin yayi imani da wukar da za a caka mishi, daukar yayi yana murmushi, sannan ya ajiye wukar tare da kura mishi ido, yayi tare da cewa. "Koma waye zai kuma dawowa!" Dan haka ya dage kirjin shi da yake mishi zafi kadan, sabida damuwar da ya saka na kwana biyu, sakamakon binciken da ya tura Mahlika. Wasa wasa sai da hannun yakai sati daya sannan na iya juya takobi, dan haka wannan karon ina jin sauki na sake murmushin mugunta, sannan na nufi inda kayana suke na ware su. Sai da na bari dare yayi tare da rabawa sannan na nufi SAMAIND. Tafiyar minti arba'in ya kai ni cikin Alharami, ban tsaya bin wancan salon ba, na bi ta bayan gidan, sannan na hango shi tsaye a jikin tagar dakin shi, dan haka na shiga ta babbar kofar da yake sama, sannan na ciro gatarin da nazo dashi. Jin karar cire karfe kawai yayi bai juya ba. A yadda na kai farmaki ya bani mamaki domin kuwa kai min duka yayi tare da dukar kafana ma zube, sake kai min duka yayi a cikina, na hantsila can bakin kofar, kafin na sami Arzikin fita yayi nasarar dukar bayana, na zube a gurin,. Dakyar na mike dan ya tsaya tare da raba kafar shi a kaina,.kwashe shi ya fadi a kaina. Kokarin kwace kaina nake shi kuma yana ƙoƙarin gano fuskana, ganin haka yasani kaiwa abin shi duka, ya tintsira can, yana nishi. Sake mik'ewa nayi ya finciko ni, aikuwa na sake kawai maranshi duka, sai da ya sake wata irin gurnani, wanda ya sani razana. Kamar zan tsaya sai kuma na fita cikin farin ciki, finciko Ni yayi tare da matse ni da kasa, ina ƙoƙarin mik'ewa. "Waye kai?" Ya faɗa tare fisgar numfashin, sake kai mishi duka nayi a cikin shi, wani irin gurnani ya kuma sake min, tare da da cewa. "Meye nayi miki?" Da sauri na kwace kaina. "Ikram!" Tsigar jikina ne ya mike sakamakon jin yadda ya ambaci sunan, da sauri na kwace kaina baki daya bayan na kai mishi duka, a gefen cikin shi. Na fita na barshi dan nasan tabbas sai dai gawan shi ba dai wani ba, na gama da babin Mehran, tunda na samu na bar gidan, haka kawai naji zuciyata ta rabu cikin wasi-wasi, lumshe idanu nayi lokacin da naga tuno abinda yayi min, na tarkato na dawo gida. Duk lokacin da na tuna halin da na barshi sai naji kamar baka kyautattawa kai na ba, taya ya fahimci nice? Taya na san nice? Me yasa ya gane Ni? Babu wani dalilin da na bari da zai fahimtar da nice, domin ko turaren na daina shafawa, gudun kar ja fada cikin matsala, sai gashi ya gane ni. *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 26 Tunda na shiga cikin gidan, na zauna dab'as a kasa tare da cire bakin mayafin fuskana, ban tab'a jin nayi kuka ba, bayan daukar fansa sai yau, zuciyata tayi rauni ainun, naji a karan kai na ban kyauta ba,. amma kuma yadda nake jin zan amshi kuskurena ne bana jin zan amsa cikin sauki domin nasan nayi laifi babba. Amma kuma ya cancanci haka ne, ya cancanci haka daga gare ni, haka da nayi mishi shine hukuncin da ya karb'a amma kuma na kashe shi. Na kashe Mehran. Wani irin bugun zuciya ta take yi, tare da jin kamar zata fadi kasa, kuka nake wanda ya farka dasu daga barci suka tawo kai na, zuba min suka yi bayan sun ga jini a bakina. "A ina kika ji ciwo haka?" "Izmah! Nimrah na kashe shi!" Bakin su a haɗe suka tambaye ni. "Waye kika kashe?" Cikin mugun kuka nace musu, "Mehran!" "Au shine kike mana kuka? Toh an kin kyautawa kanki" kamar hadin baki suka barni zaune ina kuka. Dan tausayi sun ji amma bakin cikin taurin kaina ya saka suka juya min baya. Nayi kukan da tun bayan rasuwar Iyayena ban yi shi ba, kai ko mutuwar Airan banyi kukan ba kamar yadda nake kuka akan na kashe Mehran, ina zaune a gurin har kusan tsakiyar dare, ga garin yayi wani irin sanyi. Kwanciya nayi, ina sauke ajiyar zuciya kuma idanuna basu fasa zubda kwalla ba. Ina tuno lokacin da muke tare kafin mu zama abokan gaba. Duk da bana jin dadin shi, amma kuma yaki barin koda wani abu ya cutar dani, yana tsare lafiyata da rayuwata, Yau shi na kashe sarki guda, wanda ba a tab'a yin matashin sarki irin shi na, shine yazo a karnin na baya baya, me cike da ban mamaki. Matashin da ya haɗa kome ma rayuwa na kashe shi, me yasa nake da bakar zuciya ne? Me yasa ban Nime mutanen da suka kashe Airan ba? Amma nazo.. _Kashe miki miji yayi a daren ranar auren ku! Shin zaki yafe mishi? Idan da ace kun zama abu daya a wannan daren da yanzun kina dauke da Yaron ko yarinyar Noman, shin ke kina ganin ya cancanci a yafe mishi._ Wani irin kuka ne ya kuma dawowa min, dakyar na tashi nayi sallah asuba. Sannan na koma na kwanta, ina jin zuciyata bata min dad'i. Ba laifi bane dan na ɗauki fansa amma kuskure na aikata na kashe babban mutum irin Mehran. ... Bayan tafiyar ikram, Fudail yaga lokacin da aka sauka a katangar gidan, amma bai kawo kome a ranshi ba, dan haka yacewa dakarun. "Ku shirya an kawowa Sultan Mehran hari! Bari na shiga cikin gidan." Da gudu ya shiga cikin gidan, koda yazo ma, ya sami Mehran kwance cikin tashin hankali da gurnani, Kiran Sultana yayi suka kashi dakin shi aka shiga bashi taimakon gaggawa. Fita Fudail yayi tare da dauko likitan masarautan, aka zo dashi. Ya kusan kwana akan Sultan Mehran. Dan ana kiran sallah farko yana fitowa daga d'akin shi. "Ya jikin shi?" Inji Sultanah ta tambaye shi, ajiyar zuciya yayi sannan yace mata. "Alhamdulillahi! Da sauki sosai, sai dai ya sami barci? Taya aka yi Sultan MEHRAN ya fuskanci irin wannan harin? Anso kashe shi ne fa, domin dukar da aka mishi kan halittar shi na d'a namiji aka dake shi zuwa marar shi, sai dukar da aka mishi a kirjin shi don Allah ku kula" Shiru kowa yayi, ran Sultanah ya b'aci domin gani take a garin shegen bin mazan shine ya hadu da shu'umin da yayi mishi wannan dukar. Bayan tafiyar likitan kacokan ta dauki laifin ta daurawa Fudail, Domin gani take shi yake taimakawa Mehran yake sheke ayarshi idan ba haka ba, taya zai iya dauko namiji har zuwa sama, dan haka tayi tafiyarta dakin ta bata kuma zuwa gurin shi ba, sai da gari ya waye tangaran, sannan ta shigo dakin shi, yana ganinta ya sunkuyar da kan shi. "Meye amfanin dakarun da aka zuba su a kofar shigowa? Meye amfanin zamanka jarumi? Meye amfanin bibiyar maza yan uwan ka? Ka ga kenan babu, ba zan hana ka abinda ake so ba, amma matukar ina da iko akanka na kuma ganinka da namiji. Gawata zaka dauka, shine karshen biyan laifin da nayi maka tunda narasa da yadda zan biyaka." Daga haka ta fita daga dakin, lumshe idanun shi yayi tare da kallon Fudail da yake mika mishi abinci. A hankali ya karb'a yana ci bai koma d'ago kanshi ba yacewa Fudail. "Tana raye"ya faɗa tare da d'ago kai, yana kallon bakin kofar shigowa dakin, da sauri Fudail ya rufe kofar, sannan ya dawo gare shi ya d'an sunkuya yana fadin "wacece take raye?" "Yarinyar da tabi SAURAYINTA!" Cikin wani irin azama ya d'ago kanshi, yana me jin ina zai kyaleta ta rayu, juyawa yayi zai fita yace mishi. "Ina zaka?" "Zanje na sare kanta!" "Zata dawo, sai dai bana son Anne ta ji labarin, domin zata iya tsaneta domin idan ta tsane ta, ba zanji dadin ganinta a tare dani ba, kuma itama Anne ba zata ji dadin ganin mu a tare ba. Tunanin ta ya bata cewa ni nasaka a kashe shi, ita kuma tazo daukar fansa, domin irin yadda take niman hanyar da zata kashe ni ba na kananun makasa bane, nasan na koya mata kare kanta, amma ban zata a kaina zata kare ba, na zata zata iya tsayawa kanta ne. Alhamdulillahi tunda yana cikin koshin lafiya, babu abinda ya same ta,. mahaukaciya ta kara girma da taurin kai" ya faɗa yana dafe kanshi sakamakon yawan maganar da yayi, sannan ya lumshe idanun shi, yana jin wani irin abu a ranshi, murmushi yayi sannan kalli Fudail da yake kallon shi cike da mamaki. "Na zare ko?" Girgiza mishi kai yayi sannan ya maida kanshi yana cewa. "Anya itace kuwa!" Murmushi yayi sannan yaja bakin shi kamar ba zai magana na,sanan ya d'ago kai yana kallon shi..yace mishi. "Na tab'a maka karya ne? Na tab'a maka musu ne? Toh ka saka ido nan da kwanaki zata dawo, kuma zaka sha mamaki." Kasa magana yayi yana kallon Mehran, dan gani yake kamar na gaskiya bane, shi yasa ya dauke maganar a matsayin mara muhimmanci. Shi kuwa Mehran, murmushi yake lokaci zuwa lokaci, yana me kallon kofar yadda suka tukwaikuye kan su, sai ya sake murmushi. Yana jin babu wani ciwo da yake damun zuciyar shi sai ta begen ya kuma ganin ta,.da gefen fuskarta ya sani yanzun kuma zai ganta baki ɗaya. Gabaki daya ya nemi ciwon zuciyar shi ya rasa, dan haka Yacewa Fudail. "Ka taya ni rike sirrin ta, don Allah karka sake wani yasan meye ya faru, idan ba haka ba zan dauki mataki mara dadi akan kowa, dan haka ka kyaleta zata kuma dawowa haka da tayi ta nuna min ita jaruma ce, amma zan mata wani abu da zata cigaba da farin cikin har karshen rayuwar ta." Kasa jure wannan yanayin yayi ya juya ya fita, bai kuma bin takan Mehran ba, bai tsaya ba, sai wajen masarautan, ya gama yawon duniyar nan bai gansu ba. Sannan ya dawo gida. ~~~ Ranar zazzabi ne ya rufe ni me mugun zafi, haka suka yi ta fama dani, tare da bani magani. Wajen karfe ɗaya na rana, na ji dadin jikina har na tashi na gabatar da sallah bayan nayi wanka, abinci suka kawo min na tab'a kadan sannan na koma na kwanta. "Gaskiya irin zuciyarki ko a tarihi b'an taba ji ba, kiyi kokarin koyan hakuri ko dan gudun aikin dana sani, Allah kadai yasan abinda kika mishi da Yasaka ki kuka haka," inji Izmah, kasa magana nayi ina kallonta kafin nace mata. "Kin sami labarin ya mutu ne?" "Kai ina bana tunanin ya mutu domin da kinji gaba-daya Samaind ta dauka, kuma Kinga" "Izmah barci nake ji" na fada mata a fusace, domin nayi mamakin da yake raye, wani sabon bakin ciki ne ya kamani, tare da kara jin lallai sai na fille mishi kai zan sami nutsuwa a raina, koda kuwa ranshi na karfe ne, dan haka na d'aga kafa na kwana biyu. Ina sauraron naji ance ya mutu, amma shiru kake ji. .... A can kuwa tara dakarun yayi tare da basu hutu kwanaki biyar zuwa bakwai, domin yana son ya kare mata kallo ne yadda zata shigo gidan, babu masu tsaro, Sultanah kan fushi take dashi, tare da dauke kanta akan shi, duk da yana jin jiki amma haka ta cire tausayin shi ta daina shiga harkan shi, a cikin kwana biyar yaji babu dad'i, amma Alhamdulillahi, dan yaji sauki sosai. Har kwana uku. A ranar na biyar na shirya na dauki karamin wukar yanka tuffa, na tafi dashi ba tare da tsoro ko fargaba ba, koda za a kamani ban damu ba, kawai kaina na sani. Lokacin da na isa gidan naga babu kowa a bakin kofar dan haka na haura katangar kamar yadda na saba, bayan na gama hawa kawai na hango shi a bakin kofar yana zaune tare da kallona, har na isa inda yake. Duk da a tsorace nake, amma haka bai sani na juya ba, sai ma kara kusantarshi nake. "Me kike bukata! Shayi ko Ruwa?" "Ranka!" "Toh Ikram zoki dauka idan har haka zai baki damar samun farin cikin ki har abada, amma da sharadi. Kinsan ba zan tsaya na barki ki kashe ni ba, zan yi kokarin kare kaina, san haka idan kika yi nasarar kashe ni ina miki fatan Alkhairi." Ya faɗa a sanyayye, kallon shi nayi sai kuma naji ban yarda da abinda yake nufi ba dan haka, na kasa aiwatar da kome, takowa yayi har gabana. Sannan ya saka hannun shi dukka biyu a k'ugun shi yana kallona. Cikin zafin nama na kai mishi wukar kirjin shi. Da bayan hannun ya kare, yana murmushi me sauti, a hankali na kuma juyawa zan kai mishi duka ya kare, tare da taka kafana, sai da na sake yar kara cikin wahala, gyara tsayuwar shi yayi sanan ya kalle ni. . Yadda yaja ya tsaya da nasan ma'anar haka da na gudu abina z amma shegen taurin kai da ya addabi rayuwata, ya sani kai mishi duka, tare da kai wukar zan soka mishi, daukata yayi, cikin wani irin yanayi, sannan ya juyar dani yana me hada ni da bango, kamar wacce aka sani na makale mishi da kafaffuna, yadda ya jingina ni, kirjin mu yana gogan juna ya sani kai mishi duka a fuska. Damtse na ya daka. Yake naji kamar an kwashe min da wani kuzarina, daya gefen ya daka shima haka, kifa kaina nayi da goshinsa. "Ina kika shiga?" Ya tambaye ni bayan ya kai ni dakin shi ya rufe, ajiye ni yayi a gadon, sannan ya juya tare da dauko min ruwa, sannan ya mika min kasa karb'a nayi shi da kanshi ya shayar dani, kallon juna musu yi bayan na kumshe ruwan a bakina, yana ajiye kofin ina fesa mishi ruwan a fuska, saka hannun shi yayi tare da cire abinda nake rufe sauran fuskana. Yana murmushin mugunta, tare da kallon fuskana, ajiyar zuciya yayi ta saukewa, bai kuma min magana ba, har sai da yaga na fara ƙoƙarin mik'ewa sannan, yace min. "Toh yanzun meye laifina? Da ake kawo min wannan harin?" Kasa magana nayi domin dai yada yake natsuwa jikina ya soma razana ni, a hankali yake balle rigar shi. Kallona yake har cikin idanuna, had'iye yawu nayi tare da cewa. "Karka kuskura kace zaka tab'a ni, karka yarda kace zaka min abinda ban.." Hannun shi naji akan cinyata, duka na kaiwa hannun ya janye tare da ture ni, yana murmushi yace. "Ki koma ki shirya Mehran kainuwa ne dashen Allah, babu wanda ya dasani sai Allah, Ikram indai har zan baki damar ki huce haushinki ai kin san ba karamin dalili bane, dan haka bana son na kuma ganinki, a cikin Samaind. Idan kuma na kuma ganin ki, zan ajiye kome zan baki kyautar da bai riske ki ba " "Kai waye da zaka ce min na bar Samaind? Ai nazo Samaind kenan sai na kashe ka zan bar kasar nan idan yaso kun kama ni karku min ta dad'i....." *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 27 "Mhh!" Yayi murmushi me sauti sannan ya kuma ware idanun shi akai na, kafin yace min. "Har yanzun ke baiwa tace, dan haka na baki damar barin SAMAIND" "Ni kuma har yanzun niman ranka nake na baka damar kayi rayuwa kafin na dawo gare ka!" Amadadin naga fushi ko fusata haɗe da b'acin rai, sai naga kamar babu abinda ya dame shi. Hannun shi ya kai wuyana, tare da kallon yadda nake kokarin kwace kaina. Matse ni yayi da bango, yana kallon cikin idanuna kurawa juna ido muka yi, ya sake murmushin da zaka Fahimci farin ciki ne zalla a ranshi, a hankali ya cigaba da kallon cikin idanuna. Ban san lokacin da kasala tare da kaifin idanun shi suka saukar min ba, tsintar kai na nayi da lumshe idanuna, na kifa kai na a kirjin shi, ina me rintsa idanuna kamar zan fashe da kuka. Hannun shi ya kai haɓɓa na, tare da d'ago kai na, had'a fuskar mu yayi yana sauke ajiyar zuciya. "Bana son rashin da'a." "Idan nayi maka zaka yanka ni ne?" Janyewa yayi daga jikina, tare da cewa. "Ina lafiya, bazan iya aikin masu hankali biyu ba," da gaske Mehran Magana ya gaya min, dan haka na juyar da kaina, tare da kokarin kwace kaina. "Me yasa kike kokarin gudu?"yadda yayi maganar muryan shi can ƙasar makoshi sai da ya kara jefani cikin wani irin kasala, domin yayi maganar ne tare da fesar da iskar bakin shi, a wuyana. Kokarin kwace kai na nake , amma na kasa domin kuwa matse ni yayi sosai, numfashina yana fita sama sama. Shafa fuska na yayi tare da kallon fuskana sa nake kokarin b'oyewa a kirjin shi.domin wasa gaske Mehran sai da ya kashe min jiki murus. Da sauri na d'ago kai nayi cikin wani irin rawan jiki. "Hmmm! A da kina amfani da miski, me yasa baki amfani da shi yanzun?" Yayi maganar kama wanda yasha abin maye. Hannun shi ya kai fuskana tare da tallabo fuskar. Hada bakin mu yayi tare da lumshe kaifaffun idanun shi. Kasa motsi nayi domin ji nake numfashina yana niman barin jikina, hankalina yayi mugun tashi. Idanuna sun gaza fidda kwalla, rike rigar shi nayi ina sauke ajiyar zuciya. Tunda Uwata ta haife ni ban tab'a sanin akwai irin wannan abun ba. Sannan banda Abrad ban tab'a ganin wanda yayi min irin wannan abun ba, cikin hikima da dabara, sai da ya min masauki a gadon shi sannan ya shiga sumbatar ko ina a jikina, tare da rawan jiki, kamar zan gudu daga gare shi, goga kanshi yake daga wuyana zuwa kirjina, ban san lokacin da na birkice mishi ba, kuka ne ya kwace min, tare da rike hannun shi. "S...." Hada bakin mu yayi, babu duka babu zagi sai da naji kamar bakina da harshe na, rike hannun shi nayi. Ya bude idanun shi fess a kaina, tare da sumbatar wuyana. "Karki kuma yunkurin zaki." "Ka cuce ni! Allah sai ya saka min." "Ai haba? Toh bari mu karasa bidirin a gadon." Zaro idanu nayi tare da fashewa da kuka, ya kuma cigaba da jefani cikin tashin hankali, dakyar ya kyale ni, lokacin aka kiran sallah farko, har ban daki ya kai ni, wai zai min wanka bayan na san ba zan iya ganin kato a tube ba. Sai da ma bari ya shiga kwarin wankar na juyo tare da ɗaukar kayana, tare da barin gidan baki daya. Murmushi yayi domin ko babu kome ya cusa mata tsoro ko ba dukkan ba, wanka yayi wanda rabon shi da yayi hakan tun kafin ya kwanta jinya, ga wani irin iska da yake shigan shi ta ko ina, kaya ya saka tare da gabatar da sallar nafilla, sannan ya fita zuwa masallacin, suka yi sallah. Anan ya koma gefe suka shiga karatun, dan gari ya waye. Duk wanda ya san Mehran sai ya gane yana cikin farin ciki da nutsuwa. Har ya gama karatun, sannan ya nufi gida, koda ya shiga ya sami Sultana tana ta famar nuna yadda za a jera abincin, fuskar shi a sake ya gaishe ta, sannan ya juya ya nufi sama. "Yau ba zaka karya bane?" "Anne kina kirana ne" ya tambaye ta cikin fara'a, yayinda Narjis take kallon shi sosai, nuna mushi tabirin tayi da ido, da sauri ya dauko tare da zama, sai dai duk abinda yake idanun su yana kanshi domin ya kasa boye farin cikin shi. Da yadda yake ciki. Duk wanda ya kalle shi dai ya fahimci, yana cikin farin ciki ainun, duk da ba hira yake ba, amma baya minti biyar bai tsaya ya kalli abincin sannan ya kuma sake murmushi, gabaki daya ranar sun kasa fahimtar kome akan shi babu fushin nan da dakewa, babu dogon miskilancin, sai ma wani irin yanayi na ban mamaki, wanda babu wanda ya sanshi da ita, magana akan aure tare da bawa Fudail labarin ai tazo, kuma sun kusan raba dare suna tare, da farko Fudail bai yarda ba, sai da ya hade rai sannan ya kuma dawowa ya nuna amincewar shi. ~~~ Da bakin ciki da kuka tare da nufar gidan, a hankali naji ina son ganin Uwaisul Qarni, har na isa gida, na sami Izma zaune. Zama nayi tare da dauke kai na, dan gani nake kamar zasu karanci Iskancin da wancan sikagon yayi dani, dan haka na shiga ban daki nayi wanka tare da rage kazamtar jikina,ina fitowa na gabatar da sallah nafilla da sallah asuba, sannan na kwanta wani barci me cike da gajiya suka dauke ni, sai dai ban yi nisa ba, na farka sakamakon ganin Uwaisul Qarni. "Bilqisul Ikram! Ba zaki ajiye kayan yakinki da Mehran ba? Ko kin fi son kullum kina ganin shi cikin damuwa ne?" "Kashe min miji yayi fa?kuma na yafe mishi?" Kura mata ido yayi, da zata ga halin da rayuwarta yake ba zata so d'aga hankalin ta akan Mehran ba, sam bata cikin nutsuwa baki daya, matsalar jinin da ta zubda ya fara bibiyarta, bai ce mata kome ba, sai Addu'o'in da ta tofa mata a cikin ruwan sha, ya mika mata. "Karki sake yunkurin cutar dashi! Idan kika Kuskura kika d'aga hannu domin cutar da shi,, ina me baki tausayin abinda zai biyo bayan, domin kina gab da zama mara amfani." Murmushi nayi tare da bude baki zan ce mishi. Wani abu kawai ya kalle ni tare da shafa fuskana,. Komawa nayi na kwanta, ban farka ba sai kusan azhar, nayi wanka da alola, nayi sallah azhar. Ina idarwa na juya tare da kallon Izmah da Nimra, suna musu. "Yawwa Ikram, nace ba kin hadu da sarakunan larabawa babu iyaka wani sarki ne yafi burge ki da mulkin shi? Ni dai nace ina ga Sultan Mehran yafi sauran," "Ni kuma nace mata na tab'a ganin Amir Rahil, sau daya a wani tafiyar mu aikin hajji." "Duk cikin su babu wanda ya kai Mehran d'an Abdus Samad kyau da jarumta, sai dai mugu ne na gaban kwantaccen" yadda nake gaya musu halin Mehran da haduwar shi. Yasa su sake baki tare da cewa. "Amma taya kika iya rike dabi'ar shi haka? Sannan kuma karki manta da cewa makiyinki ne fa?" Wayo kunya ne ya kama ni, wato jiya inda Mehran ya kai ni ya sani kasa Fahimtar kome sai halin shi da nagartan shi. Na kasa fadar laifin shi, dan haka na juya na kwanta ina cewa. "Ba shi nake magana akan shi ba, Ni akan Amir Rahil nake magana," na fada. "Wai daga baya kenan, yarinya kin amayar da abinda yake ranki." "Bana son shashancin, ki fita bana son ganinku." Dariya suka saka min, sannan suka fita ni kuma na shiga jin babu dadi meye zanyi da mugu, haka na wuni cikin daki da dacin rai. .....Bayan kwana biyu. Ga baki daya Sultan Mehran ya kasa samun nutsuwa, burin shi dai ya fito gari ya ga Ikram, dan haka ya shirya cikin shigar badda kama, shida Fudail suka fito garin. Haka suka yi ta bin gidajen baki da suke wajen gari, har Allah ya kawo shi gidan da Ikram take, suna can wani gidan da babu alamar akwai mutane a gidan, daga bakin kofar shiga gidan ya hangota zaune tayi tagumi. A hankali ya shiga cikin gidan bata sani ba. Dai dai fitowar Izmah. "Kana niman wani ne?" Ta tambaye shi. Cire rigar jikin shi yayi da badda kamar da yayi ya kalle ta, sannan ya juya ga Ikram da bata san dashi ba ma. "Yallabai kai ne Sultan Aamaan Abdus Samad Mehran?" Ta faɗa bakinta da muryan ta yana rawa, kamar zata fashe da kuka,karamin murmushi yayi mata sannan ya kalli Ikram da bata san suna yi ba. "Barka da zuwa Yallabai ka shigo gidan mana" "Hmm! Nan ma ya isa" "Ke! Tunanin me kike? Ga Sultan nan" kamar wacce take mafarki hana na farka ina kallon su, shigowa Fudail yayi ya zuba min ido. Kallon shi nayi tare da sake mishi murmushin jin dadin ganin shi. "Yan uwan Fudail" "Ikram kece a Samaind?" Yayi kamar bai san abinda ya faru ba, murmushi tayi sannan tace mishi. "Gani nan Fudail" nan hira ya kwace a bakin su, tare da Mantawa da Mehran a gurin, wani irin hade fuska Mehran yayi tare da zabgawa Fudail harara,ya juya ya wabi b'ata rai. Yana kallon gidan, tare da cewa. "Hmm!" Ya faɗa tare da fidda wani irin nishi, da sauri Fudail ya koma waje. Ita kuma makira tace mishi. "A'a ka shigo gidan kaci abinci da ruwa!" "Kai basamuden mutum! Jeka abunka bari muzo tare domin Sultan yana son hutawa a cikin gidan." Izmah taja hannun shi suka fito daga cikin gidan, suka barsu a tsaye. Takowa yayi gabanta, tare da jan kumatunta yana fadin. "Karki kuma mun abinda kika yi" "Toh Ubana!" Buge min baƙi yayi, tare da kallon cikin idanuna, kasa nayi da kaina, tare da wasa da yatsuna, *Duk ranar da na sami dama sai na aikaka garin da ba a dawowa* D'ago kai na yayi tare da kallon cikin idanuna, sannan ya hura min iskar bakin shi me dauke da kanshi y'ay'an itacce. *Me yasa ba zaki Fahimci abinda nake tare da shi ba? Me yasa ba zaki gane girman ki a zuciyata ba? Me yasa kike wahalar da zuciyar da bata dauke da sharri sai Alkhairi?* Janye hannuna nayi daga gare shi sannan na dauke kaina zan fita, yayi maza ya riko hannuna, ya juyar dani, bayana yana kwance a kirjin shi, hannun shi ya sarkafe da hannuna ya manna akan cikina, tare da riko daya hannun ya saka akan cikina ya zarge ni a kirjin shi. Kanshi a bisa wuyana, yana sauke ajiyar zuciya akai akai. _Na tsane ka! Bana son ganinka? Akan idanuna kace bani da daraja! Sannan ka kashe min Mijina! Mehran nice ajalinka, mutuwarka a tafin hannuna yake_ Na karshe da shashekar kuka, tare da kokarin fita a jikin shi. "Ki gaya min meye laifina?" Cikin fushi na kwace kaina, tare da juyawa ina kallon shi. "Karka kuma takowa inda nake! Me yasa ba zaka gane bana son ganinka a rayuwata ba? Kai abin so ne? Waye ya gaya maka zan tab'a kaunar ka? Toh ko maza sun kare gwara na koma ga Allah babu mijin aure ka fita a rayuwata nace!!!" Na daka mishi tsawa, ina kuka tare da zuɓewa akan gwiwata, ina kuka. Shiru yayi sannan ya durkusa a gabana, ya riko hannuna..sannan ya kalle ni cikin damuwa kafin yace min. "Gashi kiyi yadda kike so dani! Zanyi alfahari idan na mutu a hannun ki, zanyi farin ciki idan mutuwa ta ya zame miki karshen matsalarki! Amma ban miki alƙawarin koda ina raye zan daina bibiyarki ba, wannan shine alkawari na dake" Kura Mishi ido nayi, na rasa gane wani irin mutum ne shi da bai damu da kanshi ba, sai dai ya kuntatta maka, banda kuntattawa me yasa zai kore Fudail ya kuma ce min na kashe shi salon yaja min magana.. *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 28 Kasa jure idanun shi nayi a cikin nawa, na kai mishi duka a kirjin shi, muryana yana rawa. "Me yasa?" Murmushi yayi sannan yace kai bakin shi saman kunne na, ya d'an kama da hakorin shi, rike rigar shi nayi tare da sauke ajiyar zuciya. Sake lasar kasan kunnen yayi na k'amk'ame shi tare da jin wani irin abu yana yawo a jikina kamar an watsa min tsutsa, kark'ada min harshen shi yayi a cikin kunne na, ji nayi kamar zan zube ƙasa, ya kuma rike ni sosai, Mehran Mugu ne, ba fada dashi bane matsalar. Kwana mita, domin a iya haka ya labtar da gangan jikina, ya kuma sani kuka babu fada babu zagi, hancin shi ya shiga gogawa wuyana, yana magana kasar makoshinsa. "Ba fada zanyi dake ba, kuma ba zan hana ki faɗa dani ba, sai dai ki sani a shirye nake na bawa zuciyarki horon yaki akai na, a shirye nake nayi ta sanya ki kuka akan abinda ba zaki iya bujirewa ba. Tsaf na shirya yaki da zuciyarki har sai ta nutsu akan Abu daya, sannan zan kyale ki. Mara jin magana kawai." Ya fadi haka tare da hura min iskar bakin shi, wani irin kuka ne ya kwace min domin kafaffuna rawa suke, a hankali ya juya ni tare da saka harshen shi akan fuskana, Yana lashe hawayen da suke zuba, tare da cewa. "Ni zan saka ki kuka! Kuma ni zan lashe kukan nawa, duk abinda zai fito daga gare ki nawa ne!" "Kyale ni, wallahi babu abinda zai zama naka ,Ni ba kara bace nice ajalin ka" na fada ina kuka. "Bakin ki yana yawan magana, kuma ina tsoron maganar karta zame miki matsala, harshen ki kamaninki, don Allah ki rage yawan fadar haka. Domin ke baiwa tace." Ture hannun shi nayi tare da kallon shi, kuka nake sosai tare da niman guri na zauna, murmushi yake, cikin jin Dadi. Allah ya gani yana son mace me jarumta, yana kuma son ganin mace tana kuka, cikin damuwa kara mata kyau yake balle Ikram da suka shekara uku basu hadu ba, zama yayi a kusa da ita, tare da matse ta a a jikin itaccen da aka yi gwafa da gidan. Hannun shi ya saka tare da riko hannun na, yana kallon yadda nake kuka. Tare da kallon yadda nake shashekar kuka. Ita take kukan amma jin hawayen ta yake kamar narkakken dalma ake diga mishi akan zuciyar shi. Kai hannu na ya kai kan kirjin shi, yana kallon yadda na sunkuyar da kaina, tare da kokarin zare hannun daga kirjin shi. Matso dani yayi jikin shi. Tare da d'ago kai na, yana goge min kwallar fuskana. "Me kike so?" Kallon shi nayi tare da kasa cewa kome. Bana iya kallon cikin idanun shi na tsawon mintina, lumshe idanun nayi kwalla suka kuma zubowa. "Qurratulain!" Ya ambaci sunan daga kasar makoshinsa, yana ji kamar za a kwace mishi ita, gani yake kamar duk wani dakika na duniya kara nesanta shi ake da ita. "Me kike bukata?" "So nake na kashe ka" na bashi amsa ina kallon cikin idanun shi. Murmushi me zubin dariya yake yana kallo na, yana shafa fuska ta, tare da kai kanshi saman hancina. "Har yanzun baki gaya min me kike bukata ba?" "Na tsane ka" "Anya kuwa?" "Bana son ganinka" "Da gaske?" Kokarin ture fuskar shi nayi tare da sake mishi wata irin siririn kuka.. "Yau nayi nasarar saka Jarumar mata kuka ko?" Mikewa yayi tare da kallon yadda take kuka, murmushi yayi sannan yace mata. "Ban miki alqawarin zan rabu dake ba, domin zanta bibiyar ƙi" daga haka ya juya barni a gurin ina kuka, wanda idan da zaka tambaye ni me yayi min wallahi ban sani ba, kawai dai ina tare dashi kuma ban san lokacin da nake kuka ba. Hannun shi suna zuba cikin rigar shi. Fidda su yayi tare da shafa fuskar shi zuwa kan shi yana lashe bakin shi, sannan ya juya bai kuma magana ba, ya bar gidan. Sai da ya fita na sami kaina da yin shiru, ina sauke ajiyar zuciya. Wato idan kana niman karfen kafa, ka sami Mehran ka gama kome domin lokaci guda ya zuba min wasu irin matakan tsaro, tare da sawa aka bibiyar kome na, bana fita Izmah da Nimra suke kome, ni ya hanani fita, domin da zaran na fito masu tsaron zasu taso min na koma cikin gidan. Akwai wani bikin da ake a garin SAMAIND wato bikin fitilar wuta, dan haka naso na shiga kasuwa na sayi abinda ake hada abin, amma wad'ancan masu kama da bishiyar su, hana ni fita. Kura musu ido nayi tare da cewa. "Zan karya kasusuwan ku! Dan haka ku barni nayi tafiya na" "Idan zaki shekara kina karya kasusuwan mu, ba zamu karya dokar Sultan Mehran ba, mu an kan mishi biyayya bamu damu da rayuwar mu ba" Jikina ne yayi masifar sanyi, dan haka na juya tare da zama a kofar dakin mu. "Ikram!" Juyawa nayi na kalli Izmah, Tasowa tayi tare da zama a kusadani. "Ban tab'a ganin mutum me kirki irinki ba, zuciyarki me kyau ne." "Bar min kewaye kewaye, fadi abin da yake ranki" "Sultan MEHRAN!" "Ai dama nasani" na bude baki zan yi magana kenan Fudail ya shigo da kayan a hannun shi, ya mika mata. Tare da juya kai yana niman Nimrah. "Wannan fa?" Murmushi yayi sannan ya kalle ni yace. "Inji Sultan Mehran!, Wai ku saka kayan zai zo an jima da dare." Yana raba idanun shi, akan kofar mu. "Ina Nimrah?" "Tana ciki kuma ai taji ka,, ka mikawa SULTAN Mehran godiya kace mishi Ikram ta amsa cikin mutuntawa. Mun gode" Murmushi yayi yana kallon yadda na b'ata rai, kamar bani ba. "Ikram" "Me zan maka? Ka dauki kayan tsiyar shi ka maida mishi, jinin mijina ya fi karfin tunanin shi, kar ya kuma kawo min kayan haukar s...." Had'iye maganar nayi tare da dauke kai na, sabida yadda yake kallona kasa kasa. "Sultan MEHRAN. Mun gode Allah ya kara maka bud'i da nisan kwana, Ubangiji yayi maka jagoranci akan duk wani abinda ka saka a gaba, Allah ya baka mace ta gari!" Kamar wacce aka watsa min ruwan zafi haka naji Addu'ar Nimrah. Tsaki naja musu sannan na mike zan bar gurin. Ban san ya akayi ba sai ji nayi kamar an ja kafana. Na tafi zan fad'i. Cikin abinda bai kai dakika biyu ba, naji ni a jikin shi tare da d'ago kai muka kalli juna, wani irin tsume fuska yayi wanda ya saka duk suka bar gida, janye jikina nayi tare da b'ata rai. "Me yasa kake son shige min?" Tab'e baki yayi tare da kauda kanshi yana wani shan kamshi, kamar wani wanda ya ga abin da baya so. "Me yasa ba zaka kyale Ni ba?" Na fada da karfi, kauda kanshi yayi tare da kallon kofar shiga gidan, yaga babu kowa. A hankali ya sake ni sannan ya ture ni har jikin kofar shiga dakin. "Mehran!" Na fada muryana yana rawa, na kira sunan shi. Bakina ya kama, tare da mishi wani irin azazzaben sumbatar da tasani jin kwalla ya zubo min, sabida yadda yake abin wallahi babu tsoron Allah a ranshi. Jin baki na kamar ba ajikina yake ba. Domin kuka tsotsar shi yake yana kuma taune bakina, bai kuma ji a ranshi haka da yake min kuskure ba, domin har harshe na zafi yake min da rad'ad'i, hannun shi kuwa bai fasa yawo dashi a jikina ba, domin jan rigana yake har zuwa sama. Ban tab'a ganin shi a irin wannan yanayin ba, domin da ban mamaki abun yake, Mehran ya tsotse bakina lebbe na kuwa har wani yaji yaji yake min, hannun shi da ya tura cikin rigana, yana kokarin cusa hannun shi cikin daurin kirjina, rike hannun shi nayi, ina girgiza kai na, tare da zubda kwalla. Sai da yaji ina wani irin gurnanin kuka ta cikin wuyana da bakina ya janye bakin shi daga nawa, yana murmushin mugunta da jin dadi a ranshi. Lashe lebben shi yayi kamar wanda aka lasa mishi zuma a bakin. Ya kuma kallona sannan ya juya tare da ɗaukar kayan a inda Izmah ta ajiye, ya mika min. "A cikin kasata, a da'irar birnina a cikin garina a cikin farfajiyar mulkina ke har kin isa ki kirani kayan tsiyata?" Murmushi yayi sannan ya juya har ya isa bakin kofar. "Bayan sallah isha, zan zo kuma idan." Cizon lebben shi yayi sannan ya sake murmushi, sannan yace. "Kina sanya Ni magantuwa" sannan ya juya abin shi yabar gidan. Zamewa nayi daga tsaye na zauna a kasa, duk zaratan da nake haduwa dasu. Ban tab'a haduwa da makiri, miskili irin Mehran ba, dan mugunta ya gama cinye min bakina, tare da sakani kuka kamar zan shiɗe. Shigowar su Izmah suka kalli bakina da yayi ja tare da d'an kumbura. "Laaa! Amma Sultan Mehran ya iya soyayya, dubi yadda ya cinye miki baki, kai jama'a nima ina tausayin kaina, domin ina kewar Firooz." Ta faɗa tana sake wata irin iska. Murmushi Nimrah tayi tare da gyara zaman gashinta sannan ta shige dakin. Kamar zan sake ihu tare da zuba kwalla, ina kallon Izmah sai dariya take, tana kallona tare da cewa. "Wallahi Sultan Mehran ya miki kankati, domin kuwa shi daya ne yake iya saki kuka tare da ya zane ki ko ya miki kome ba, gashi nan kina kuka wiwi." Haka ta gama min wulaqanci, sannan ta shiga magana irinta masu hankali. "Bilqisul Ikram! Maganar gaskiya ki rage kaifin kalaman ki, domin kuwa zata kai ki ta baro ku, kina gaya mishi maganar da yayi miki, karki manta shugaba ne fa idan ya tsaya a filin yaki dakaru kimananin miliyoyin mutane suke take mishi baya. Ikram Mehran ba kashin yarwa bane, Mehran ba haka kawai yake gabanki ba, Ikram baki da kome a kirjin ki, babu nono baki da abinda lafiyayyen namiji zai ganki yaji a ranshi yaga mace. Ikram ki duba yadda rayuwa take tafiya dake, kuma a cikin haka kika yi ta kai mishi farmaki bai tsaya ya duba meye ke tafe dake, ya kalle ki da kyakyawan niyya yana barin fadar shi ya fito sabida ke meye illar shi? Meye laifin shi? Wallahi na rasa gane miki na rasa fahimtar meke damun ki, Ikram idan rayuwar Mehran ne fansar jinin Noman ki tafi ki kashe shi ki huta, wannan wani irin k'iyayya kike mishi? Wani irin k'iyayya ne haka ya shiga tsakanin ku? Me yasa baki tuna abinda yayi miki abaya ba kike nuna mishi gundarin k'iyayyar ko dan ganin ya tura a kashe noman ne? Ni kuwa dan Sultan Mehran yace min kar nabi wani wanda nake so zan hakura domin shi din Shugabana ne, kuma Uban gidana ne shi. Bana jin dan ya kashe shi tsane shi, idan duniya da gaskiya kamata yayi ki bincike waye Mehran meye Mehran yake yi, me ya faru dashi bayan rabuwar ku baki yi ba, shine faidar dawowarki, kina tsanar Mehran ne kawai Amma duk halin da yake ciki sabida ke ce, Ya hakura da mulkin shi sabida ke, domin da suka ce zasu dakatar da shi idan wani ne kin amincewa zai yi kuma ya nuna musu karfin mulki. Amma sai ya juyawa mulki baya, a tsawon shekarun shi kamata yayi ace yana da matar da zata dauke mishi bukatar shi da kewar shi, sai gashi yayi fatali da matan da ake kawo mishi, duk shekara watsi yake da mutane haka kawai ba dan kome ba sai dan yana jiranki ki dawo gare shi." Kasa da murya tayi tare da rarrafawa gabana ta riƙe hannuna tana kallon fuskana sanan tace min. "Zunzurutun yana da muradinki ya hana a fitar da kin auri wani namiji. Meye kike bukata yayi miki? Meye kike so yayi miki? Meye nufinki akan shi? Mehran mutum ne guda ba b'ari ba, mutum ne da ya amsa sunan shi. A shekarun shi kamata yayi ace yana da Kwarkwarorin babu adadi amma yana zaune domin ra'ayin kanshi meye nufin shi da kawo wancan kayan? Saboda macen da take da daraja ake bawa, amma gabaki daya tunanin ki baya baki lissafin da ya dace kin tsane shi Allah ya baki sa'a da lafiya ki ta tsanar shi. Ba zaki gane illar abinda kike ba sai ranar da kika yanke shawarar da har ki koma ga Allah ba zaki daina kuka ba shine idanunki zai bude.." *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 29 "Kyaleta Izmah! Bata ga ni'imar da Allah yayi mata bane, shi yasa take butulce mishi da tasan tarin baiwar da Allah yayi mata da hikimar da ya tsara ba zata tsaya tana musguna mishi ba. Domin na gama nazarin abinda yake tsakanin su ban ga laifin shi ba, sai ma tarin girmama al'amarin ta da yake yi amma baiwar Allah nan ta rintsa idanun ta. Meye kike bukata a duniya? Mehran yayi ya kuma amshi hukuncin da kika aikata laifukan da ya dace naki ne amma shi ya amshi laifin akanki, Ikram meye matsalar ki da k'iyayyar da kike mishi, na rasa gane meye ya miki da zafi haka, wallahi ko ni da Mahaifiyata ta miki laifi baki min tsanar da kikewa Mehran. QpAmma kin rufe idanunki a madadin amshi kiran shi kin zauna kina juya halin ki a yadda shi kanshi dole wata rana ya gundura da halinki tir da ma ace Mahaifiyata ce ta haife ki sai nace kin sha mugun hali a nono ne ba a gurin kowa ba, amma abun ai jini yake bi, shi yasa kika dauki kad'an a halin ta." Ina jin su ina kuma jin yadda suka sani a gaba da gaya min magana, sabon tsanar shi nake ji a raina. Mehran ya saba kwace min farin ciki na, yau ma ya kwace min kawayena Insha Allah yau zamu yita ya kare ya rabu dani yayi tafiyar shi nagaji da halin shi, duk abinda na samu na farin ciki sai Mehran ya rabani dashi ya saka Ni kuka ya saka zuciyata kunci bai ishe shi ba, yau kawayena da na rabo su da ahalin su. Sune suka juya min baya. Kura musu ido nayi tare da sauke kai na kasa, kwalla ne ya zuba min daga idanuna. A hankali na d'ago kai na, zan yi magana kuka ne ya kwace min tare da shashekar kuka, ina jin kamar na had'iye zuciyata na huta. "Ku koma gurin Mehran!" Na fada musu a tsawa ce, ina share kwalla da take sauka min, ma tsani mutumin nan iya karshen rayuwata. Kuma wallahi ba zan tab'a kyale shi ba sai na ga bayan shi. Haka na shige dakin ba kyale su baki hangame da mamakina. ~~~ Merocco. Ga baki daya tun da aka nime Ikram aka rasa ya koma kamar karamin mahaukaci, yanzun ma a gabanta Sultan Mu'allim yake. Tare da narke Mishi. "Rahil har yanzun bamu da labarin ta dan ko har aika Sultanah Amrah tayi daga Askandariya, amma babu wani labarin da aka samu. Kayi hakuri ka kara hakuri insha Allah tana bayyana zan aura maka ita." Tun bayan tafiyar ta Sultanah Amrah tazo har masarautan tare da tambayar bayanin Ikram, suma suka tabbatar tabbas tazo amma kuma ai nata zauna Kamar yadda suka so ba, dan basu sami labarin ta ba sai bayan tafiyar ta, dan haka suma suke nimanta. Sannan suka daukarwa juna alkawarin matukar aka sami labarin ta, daga kowacce gefe su tabbatar da an tuntube juna. Toh har yanzun dai haka ake ta bincike akanta kuma babu labarin ta. Takai har niman masana kuma gogaggun masu iya zanen aka yi tare da zama hotonta ko za a dace. Dan haka aka yi ta rabawa kasuwanni da wasu guraren domin niman ta. Idanun shi cike da kwalla yacewa SULTAN Mu'allim. "Don Allah ka taimaki rayuwata, duk duniya bani son wata mace sai Ikram, don ALLAH Sultan ka taimake ni akanta kar na rasa rayuwata" Tausayin jikan nashi da kuma abinda yaron yake ji yasa shi rike hannun shi, cikin tabbatar da abinda yake nufi yace mishi. "Ni nake da iko da kai, haka itama ina da iko da ita, dukkan ku a karkashina kuke, don haka babu wanda zai shure dokana da sanin shi, iyayen ku basu shure doka na ba, ku y'ay'an su baku isa ku shure abinda na kafa ba." Sake karya wuyar shi yayi tare da kallon shi yace mishi. "Allah ya taimake ka, nasan ni ina jin tsoron kar ta haɗu da wani namijin ne, ina gudun karta hadu da wani da zai yi nasarar nisanta ta dani ne, Sultan don Allah idan aka ji labarin inda take a barni na wakilce ku, domin na dawo da ita, anan nake son kafa kai na, domin bana son tazo ana dolanta mata ni." Ya faɗa tare da zubda kwalla, sabida Allah ya gani yana mugun kaunar Ikram, kuma duk rintsi duk wuya sai ya mallake ta, nasiha Sultan Mu'allim yayi mishi sannan ya shafa kanshi ya tabbatar mishi da cewa, yana taya shi da addu'a, sannan Insha Allah Ikram tashi ce. ~~~ A wannan lokacin Sultan Abrad ya nime wata yar gwamnar yankin shi me suna Aseelah, kyakkyawar mace ce. Na gaban kwantancen, tunda ya hadu da ita yaji ya manta da Ikram. Dan haka suka baje amarcin su na wani lokaci. Yanzun ya manta da wata Ikram,.sai ma hidimar gaban shi yake da cusa Kanwar shi izuwa Daular su Mehran. Dan yaci alwashin ko bai sami damar kashe Mehran ba, sai ya shiga cikin mulkin kasar yayi kane kane, yadda zai ji dadin kuntattawa Mehran tare da takalar shi rigima idan yayi magana ya tinzara, sauran yankunan jazziratul Arab su yaki Mehran. Domin yayi alƙawarin sai ya dagula al'amurran Mehran. Dan haka a sauran kwanakin da suka rage zab'en matan sarki ya fara shirya Kanwar shi tare da nuna mata hikimar da zata yi na girki, tare da kiran manyan masu girki na kasan ana koya mata, duk wani nau'in girki da nuna mata yadda ake girmama al'amarin sarautar SAMAIND. "Sultanah!" Murmushi tayi domin tana jin dadin yadda suka fara kiranta da Sultana. Dan gani take dole itace zata lashe gasar. Kuma tayi tafiyar bazata da zuciyar shi. Murmushi tayi sannan tace musu. "Ina jinki Rubina!" Cikin jin dadi baiwarta Rubina tace. "Sultanah a yadda zab'en yake matukar kika samu nasarar zama matar da zai aura za a killace ki na wasu kwanaki a gama niman bayanin asalinki, sannan zaki kasance me lura da al'amuran Sultan har kwanakin da zaki yi a killace su cika. Sannan ba a son a wannan tsakanin ki kasance dashi ta shamfida, sabida idan kika kasance matar shi ba zai yi daukin ki ba, an fison ki hakura da shi wa Kwarkwarorin da zasu shiga zab'en. Sannan a cikin wannan yanayin babu ruwanki da shiga al'amuran gidan, babu ruwanki da shiga al'amuran Kwarkwarorin shi, babu ruwan ki da duk abinda zai yi da Kwarkwarorin shi, har ranar bikin ku ya kama a dawo dake masarautan shi." "Wannan dokar fa? Tab haka zan hakura da mijin da zan aura gaskiya babu wanda ya isa ya shiga tsakanin mu, domin wallahi ba zan yarda ba." Ta faɗa cikin fada da gatsine, sunkuyar da kai duk bayin suka yi tare da zare idanu. "Allah ya gani ba zan iya ba, wallahi ba zan iya ganin shi da mace na kasa hakuri ba." "Sultanah daga ranar da kika zama matar da zai aura, toh zaki iya sauya kundin tarihin masarautan, sannan zaki iya tafiya da ra'ayin kowa ko kuma yi fatali da ra'ayin su, ki kafa naki ra'ayin." "Kai Rubina idan na zama Sultanah uwar magajin sarauta zan yantaki har na baki me bani shawara na hannun dama na," ta faɗa tare da sake murmushin jin dadi. "Kai Nagode Sultanah Uwar Magajin sarauta." Murmushi tayi sannan tace mata. "Karki damu daga yau kuna da damar yin abinda kuke so, har mu tafi SAMAIND." "Sultanah mun gode! Azizatul Nissah mun gode ainun." Haka tayi ta murna sannan tace mata. "Toh bayan nan dole zaki daura damara da sauran matan, domin zasu ta kawo miki hari, tare da makirci kala kala, da munafunci. Idan har haka ne toh ba makawa zaki zama me, juyawa tayi tare da kallon sauran bayin sannan tace mata, Sultanah bani kunnen ki" nan suka rad'a munafuncin su , sannan suka kalli juna. Murmushi suka yi wanda zai nuna maka akwai wata a ƙasa, kafin suka ci-gaba da tattaunawa. ~~~ Ina kwance suka gama shiryawa, tare da dauke kaina akan su, dan naga ba karamin dukiya bane a jikin kayan, musamman rigunan aka dinke su da duwatsu lu'lu'u, sai azurfa da aka makala a wuyar hannun rigar, tare da saka musu digon karfe zinari. Sunyi kyau. Lumshe idanuna nayi amma kayan ne akan idanuna. Tsaki naja, sannan na juya baya abuna. "Ikram! Ki tashi ki shirya mana." Inji Izmah, "Kar wata ta min magana." Na fada a fusace, murmushi suka yi kafin suka shirya dan tunda nayi sallah isha nake zaune a gurin, kuma babban damuwar su na tashi na shirya. Amma fir naki. Juya baya nayi abinda daga kallon da suke min na rashin mutunci. Ya jima a bakin kofar shiga cikin dakin, murmushi sukayi tare da d'an dukawa suka gaishe shi, sannan suka daga d'akin. Kamshin turaren shi ne ya fahimtar dani yana cikin ɗakin. A hankali ya zare alkyabar shi ya ajiye a jikin kofar d'akin, sannan yayi zaman raƙumi a bayana, yana kallona, fuskar shi babu walwala. "Ki tashi" Banza nayi dashi tare da kin motsi. Gyara zaman shi yayi tare da rungume gwiwar shi, yana kallon yadda nake kwance. "Bana son gardama." Banza nayi dashi a karo na biyu, iskar bakin shi ya furza. Sannan yayi shiru. Ina jin idanun shi a kai na, ji nake kamar zane ni yake yi, kasa jure idanun shi nayi na tashi tare da kallon shi ina murguda mishi baki. "A daina cinye ni da ido!" "Hmm!" Ya faɗa a kasar makoshinsa, tare da lashe bakin shi, alamar haka a jikin shi yake. "Ni dai ka fita min a d'akin" Kamar da dutse nake magana yaki ko motsi, tare da sake murmushin jin dadi. "Don Allah ka fitar min a daki." Wani irin mayyen kallo yake bina dashi, kamar kura taga d'anyen nama, tare da lasar leben shi ba kasa,wanda nake hango yadda take rawa, tsoro ne ya sani mik'ewa da sauri tare da shiga ban ɗakin, bai damu ba sai ma sake murmushin da yake alamar yarinyar ta fara laushi daga horon idanu. Wanka na fito, yana inda na barshi bai matsa ba. Tura baki nayi tare da hararan inda yake, sannan na fara gyara jikina, haka na gama shiryawa fuskana ban yi mishi kome ba, ina gamawa ya kalli inda kayan yake sannan ya kalle ni. "Ni bazan saka ba!" Na fada kamar zanyi kuka, murmushi yayi sannan ya gyara zama. Shi yana kallon ta, ai maganin biri karen maguzawa, dan haka ba zai tab'ata ba balle tayi tunanin dan jikinta yake tab'ata ko daya, shi kawai dole ne ayi yadda yake so, idan mutum yaki zai ji a jikin shi. Yadda ya zuba min ido ya sani kwashe kayan daga cikin dakin zuwa ban daki. Ban fito ba sai da na shirya, sannan na fito ina yatsina fuska. Murmushi yayi sannan ya janyo alkyabar shi ya saka, tare da kallona. Nufin shi na daure mishi igiyar, kallon shi nayi baki sake ban san lokacin da na kwashe da dariya ba. Ina kallon shi. "Nice zan zo na daure maka zaren alkyabar?" Murmushin gefen baki yayi tare da nad'e hannun shi a kirjin shi yana me kallona da ido. _Yau duk abinda zaki yi sai kin daure min shi domin nafiki rigima dan mulki nake ji yau_ ya faɗa a ranshi. *Ni ba zan daurewa makashina alkyabar ba, matukar zan daure maka toh ba makawa sai na shake ka* Na fada a raina ina murmushi, takowa nayi tare da kallon fuskar shi, domin nasan matukar na isa gurin sai wuyar shi ya gaya mishi. _Bilqisul Ikram! Kome zaki yi ina shirye dake! Ina jiranki_ ya faɗa yana murmushin mugunta. Takowa nayi na isa gaban shi na saka hannuna da niyyar daure mishi igiyar, yadda na sarkafe tare da zarga mishi zaren, sai da ya matse ni da kirjin shi har ina jin yadda numfashina yana wani irin kamar zai fasa Kirjina. "Mehran!"""" [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 30 A razane na kira sunan shi, tare da jan numfashina dakyar, kan shi ya kai wuyana tare da sake min wani irin numfashi me hade da nishi, k'asa k'asa yace min. "Hmm! Na iya nima" d'ago kai nayi tare da kallon shi. "Hmmm!" Ya kuma cewa, alamun dai ma mishi abinda ya sani, kamar zan fashe da kuka haka na daura mishi sannan ya sake ni, muka fito daga cikin ɗakin. A hankali muka fito daga gidan, muna tafiya bai damu da yadda ake kallon mu ba, tare da kallon yadda mutane suke hidimar su na bikin ranar, duk da tafiyar kurame muke haka bai hanani jin wani irin nutsuwa ba, duk inda muka wuce shagali ake, ashe ni ce ma nake damuwa dasu domin kuwa jama'a kowa hidimar gaban shi yake, har muka isa inda ake ta soya kayan ciye ciye, kallon shi nayi ina son tambayar shi su Izmah, amma ganin yadda bai bani fuska ba ya sani jan bakina nayi shiru. Tsayawa yayi tare da kallon inda ake sayar da wani, wani abu kamar panke, abin yayi min kyau, muna tsayawa a gurin wasu matasa suka kalle mu. Tare da cewa. "Keeee! Kyakkyawa, idan zaki ci gashi." Satar kallon shi nayi da wutsiyar ido, mika min panken matasan suka yi. Ni kuma dake ina son na b'ata mishi rai kawai na amshi panken tare da sake murmushin mugunta. Faucewa yayi tare da wurga da abin a kasa yana hararar Matasan. Cikin isgilanci suka ce mishi. "Dalla malam mun ga kayan aiki kace zaka hanamu, yan mata kinyi mana! Kuma gaskiya muna sonki." Cikin murmushin jin dadi na bude bakina zanyi magana, ya cire hular alkyabar da ta hana mutane fahimtar shi, kamar wanda ake jiran ya cire gabaki daya mutanen gurin suka sauke wuta, kallon su yayi tare da girgiza kanshi yana fadin. "Ku watsa!" Jikin su yana rawa suka shiga watsawa, baki daya gurin ya zama babu kowa sai shi da dakarun shi. Shi kanshi me sayar da panken jikin shi rawa yake, dan kamar zai sake fitsari. "Darda bashi jakar tsaba nan!" Ajiyewa mutumin jakar kudin sannan ya koma gefe yana faɗin. "Ka zubawa Amirah Ikram abinda take bukata" "Ba zanci ba, baba ka rike amadadin kashe maka kasuwa da aka yi" murmushi mutumin yayi tare da cewa. "A'a Amirah wannan dukiyar ta isheni, koda zan shekarar goma banyi sana'a ba wannan zai ishe ni, nagode sosai Sultan Ubangiji ya kare rayuwar ka." Ya zuba min abin tare da mika min. Ganin yadda yake damun sai naci ya sani karb'a ina kallon Sultan. Dauke kanshi yayi tare da hango Jasrah tare da wasu bayinta, dan ta hango mu. D'ago kai nayi dan mishi magana naga hankalin shi yana kan ta, ajiye tasar nayi tare da mik'ewa na tsaya a gefen shi. Har Jasrah ta iso gurin. "Sultan MEHRAN kai ma kafito kallon wasan ne, Barka da kasancewa da kai a wannan lokacin." Murmushi yayi sannan ya kalle ni, tare da kallonta. Nad'e hannun nayi a kirji ina kallon su. "Ikrammmmm! Bake bace aka ce kin bi saurayi ba." Satar kallon shi nayi naga fuskar shi babu wani abu na sauyi, murmushi nayi tare da cewa. "Eh laifi ne?" Dariya tayi sannan tace. "A'a ba laifi bane, amma shi Sultan Mehran ya san cewa kuskure ne babba macen da take kasar ikon Sultan Mehran ta bijire mishi, duk da kuwa Sultanah Fazilatul nisa, tayi kokarin d'aga miki daraja kika zab'i bin saurayi koda yake ba laifi bane tunda matsayinki na bawa ce." Murmushi nayi tare da matsawa jikin shi sosai, sannan nace mata. "Eh Toh wannan ra'ayinku ne, ra'ayin shi ya gaya min, ban sani ba ko akwai wani abu bayan haka Mehran." Yadda na shiga jikin shi tare da manne mishi. Kura min ido tayi tare da kasa cewa kome, murmushi nayi mata tare da janyo hannun shi ka makala a k'uguna, ina murmushin jin dadi. Kasa jure ganin mu a haka tayi kawai, kamar wacce aka ingizo ta zata fadi a jikin shi itama, kayi maza na ture shi baya ita kuma ta fadi a jikina, murmushi nayi mata sannan nace mata. "Sannun karki ji kome, zan tare ki, Mehran ne dai baki isa ya tare ki ba." Ya ture ta, bayinta suka tawo da sauri suna ce mata. "Sannun Amirah," Kallon mu yake cikin jin dad'i, a ranshi, amma kuma ba zaka tab'a ganin wannan abun akan fuskar shi. Tasowa tayi tare da d'aga hannun ta zata mare ni, rike hannunta nayi tare da cewa. "Ki duba kwayar idanuna baki isa ba, Amir Zuhair bai isa ba balle kakan ku Amir Hood, ni dince ban sauya ba." Na wurgar da hannunta tare da jan hannun shi muka bar gurin, ina murmushi, muna karawa gaba na kalle shi cikin jin haushi na ja alkyabar shi na rufe kan shi, duk da kuwa ya fini tsayi. "Wallahi ni ba dan kai kayi fada na ba, nayi ne dan ra'ayina, kuma ka mayarda hulan kanka." Na fada ina tura mishi baki. Share ni yayi tare da wuccewa abin shi, a ranshi yana faɗin. *Magulmaciya zaki gama gulmarki! Amma tabbas yau naga abinda kike boyewa ina jiranki,* Haka muka yi ta zaga garin har kusan tsakiyar dare sannan ya dawo dani gida, tun muka iso yaga ina hamma, zama yayi tare da kallon yadda nake kokarin shiga daki yayi, ganin zan gudu na barshi ya sashi finciko ni. "Ni barci nake ji!" Zaunar dani yayi tare da saka kaina gefen kafadar shi, bai ce min kome ba, bai kuma nemi nayi magana ba, hannun shi a cikin nawa, yana murza yatsuna. a hankali har barci ya dauke ni me karfi. Yana zaune a gurin, har aka fara kiran sallah farko, kafin ya dauke ni zuwa cikin ɗakin ya kwantar dani, ya ja min bargo. Tare da shafa fuskana, sannan ya juya ya fita daga dakin. Dake na gaji sosai ban ma san har ya kawo ni dakin ba, sai da Nimrah ta tashe ni daga barcin sannan na mike a hankali na nufi ban daki nayi alola, bayan na idar da sallah ne na kalle su. Sun sayi abinci, tare da zama suna hirar yadda suka sha yawo da Fudail, ban saka baki a maganar su ba, sai da naji suna cewa. "Amma naji ance kamar an samu yar karamar rikici, tsakanin Amirah Jasrah da tawagar Sultan Mehran, wai da gaske ne?". Bude idanuna da yake cike da barci nayi sannan nace. "Ki tambayi Aamaan Mehran,!" "Kai Ikram amma baki da kunya kowa Sultan Mehran yake kiran shi ke kuma Aamaan Mehran, sai kace sa'arki!" Tab'e baki nayi sannan nace mata. "Aamaan Abdus Samad kike magana akan shi." Na fada tare da dauke kaina ina murmushin mugunta, dan naga yadda suka gwalallo idanu waje, na kuma sake samun damar na kwafta rashin mutunci a silalle. "Wai Aamaan Abdus Samar kuke faɗa?' kasa amsa min magana ta suka yi suna kallona, tare da cewa. "Dama haka kike baki da mutunci?" "Gado nayi a gurin Wancan d'an bakirin" na fada ina murmushi, Watsewar zabi sukain tare da min fatar shiriya, dan ganin mahaukaciya suke min. ~~~ Karyawa Mehran yake bini bini yana sake murmushi, gyara zama Sultanah tayi sannan tace. "Sultan dina anya baka fara soyayya ba?" Ya kuma sake murmushi a karo na babu adadi, yana daukar soyayen kwai ya saka a bakin shi yana me sake murmushi me sauti. "Fudail meye gaskiyar magana yau kimanin kwanaki masu yawa bana ganin shi da maraici,idan ya dawo kuma zai ta sake murmushi wacce barauniyar ce tayi sa'ar sace zuciyarshi?" Kallon juna suka yi tare da dauke kai. "Nifa kamar uwace! Idan baku gaya min wacece ita ba waye zai gaya min?" Ta tambaye su. Sake kallon juna suka yi kafin suka shiga kallonta an rasa wanda zai gaya mata gaskiyar maganar. Murmushi tayi sannan ta cigaba da cin abincin ta, tana me cewa. "Ikram itace mafarkinka, ba zanyi mamaki idan nace maka nasan tana cikin lardin nan ba, amma kuma ban san me ya dawo da ita ba, dan nasan dai haka kawai ba zata zo ba sai dan daukar...." Zuba mata ido yayi tare da rike cokalin hannun shi da mugun karfi har sai da ta lankwashe. "Karka damu! Ni ba a zalimar mutum bace, ina bawa kowa ra'ayin shi." Matsanancin kunya ce ta kama shi, tare da kasa kallon kallonta. "Toh Fudail idan Shugabanka yayi aure kai waye zaka aura?" Diriricewa yayi ya kasa tsayuwar guri guda, sai kallon gefe da gefe. "Nimrah" Mehran ya faɗa a sanyayye, kamar bashi yayi maganar ba, da sauri Fudail ya bar falon. "Dawo nan! Kayi min bayani daga ina take." "Sultanah tare suke da Ikram!" Inji Darda, "Hmm!" Ta faɗa tana murmushi, Mehran kan kasa cin abincin yayi, duk ya takure guri guda. "Bari na baka guri" ta faɗa tana murmushi, "hmm" yace mata, tana jinjina wannan karfin halin shi, toh ya yake yi da Ikram dan hira tsakanin mafadaciya da Miskili irin Ikram akwai matsala, dan kowanen su gwani ne akan halin shi, zafi da sanyi zasu haɗu guri daya, murmushi tayi a karo na biyu. Sannan ta shiga d'akinta. Tana zama tana son ganin Uwaisul Qarni, dan haka ta shiga addu'a kafin can tayi imani da Allah sannan ta ambaci sunan shi. Cikin hukuncin Ubangiji ya bayyana a gaban ta, a saman fatar damisa. Yana murmushi. "Ikram!" Cikin girmamawa tace mishi. "Barka da warhaka Baba na, eh itace!" Kallon tausayin yayi mata tare da girgiza kai, tare da cewa. "Kiyi ta addu'a, Allah ya taikaita tashin hankalin da yake tare da alaƙar su." A hanzarce tace mishi." Akwai damuwa ne?" "Idan Ubangiji ya so al'amarin shi, babu makawa sai ya faru, duk abinda yazo muku, ku amshe shi da hannun bibiyu, a duk inda ƙaddara take, toh yana da kyau bawa ya amshe shi hannun bibiyu, Wani al'amarin dole sai Ubangiji kadai zai warware miki shi, SOYAYYA ce me tattare da kalubalen rayuwa, soyayya ce da kema idan baki yarda da Allah zaki iya shiga al'amarin Ubangiji, soyayya ce me cike da raunin zukatan al'umma. Soyayya ce da zata kashe masoya ta kuma raya makiya, ban tab'a ganin irin wannan al'amarin ba, duniya cike take da kalubale, rayuwa cike take da tashin hankali. Wallahi babu wanda ya isa goge zanen ƙaddarar da ya zana. Dan haka karki yarda ki shiga wannan lamarin." Hawaye ne ya zubo mata, tana faɗin. "Yanzun babu hanyar da zan dakatar da wasu abubuwan?" Murmushi yayi sannan yace mata. "Eh mana! Kin isa ki aikata abinda Allah ya ƙaddara? Baki isa ba? Baki da ikon tafiyar da rayuwar wasu, kiyi addu'a, kiyi hakuri karki yarda wani abu ya shiga tsakanin wutar da zata kono a tsakanin wasu, karki yarda wasu su fahimci cewa akwai wutar da ya kama a cikin gidan ki." Ya faɗa tana tsare ta da idanu, kasa tayi da kai. "Nasan kina kaunar Ikram, dole wata rana zaki iya Mantawa da wannan tunanin, nasan zaki iya juyawa kome baya domin wani dalili, ina tausayawa lokacin da wasu abubuwan zasu juyawa wasu dalilai baya, na tausayawa tafiyar da za ayi ta a cikin tsananin zafin sahara, babu ruwa babu Uzuri, rayuka zasu koka zuciya zata kasa jure kome, tunani zai tsaya cak. Mafita zata yi ƙaranci, ba lallai bane na riski wannan yanayin, bai zama tilas na san lokacin ba. Domin lokacin tafiya na ya kusa, zan tafi baki daya." Ya faɗa a sanyayye, yana me juya kanshi ya ce mata. "Idan irin wannan lokacin ya riske ki, kiyi kokarin maida alamarinki ga Ubangiji, Insha Allah Ubangijin zai amsa miki kuma zai kawo miki ɗauki, karki yarda a juya miki nazarin ki. Insha Allah zaki yi farin cikin samun Ikram a rayuwarki." Gaba daya ta rasa abin cewa, ita kanta tausayin kanta da kanta take ji, dan haka har ya tafi bata iya fahimtar kome ba, sai hawayen da take zubdawa..... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 31 Ita kanta bata san iya adadin lokacin da ta dauka tana kukan tashin hankali da damuwa wanda bata san daga inda zai ɓullo mata ba, alola ta mike tayi tare da gabatar da sallah nafilla, ta jima tana kaiwa Allah kukanta, kafin ta fito daga dakin. Sam bata jin dadin ranta, tana fitowa ta sami Shairah da Narjis suna magana akan zab'en da za ayi, da yadda ake shirya bikin domin Fudail ya gabatar musu da wasu abubuwan da za ayi. Suna ganin Sultanah suka yi shiru. "Meye Mehran ya sauya a cikin tsarin?" Shiru suka yi tare da kallon shi. "Sultanah dama ya ce a cire maganar lallai sai anyi gwajin budurci ne?" Shiru tayi sannan tace musu, "babu wanda zai goge abinda aka kafa, dole yabi tsarin masarautan" ta faɗa musu, "amma Sultanah!" Suka fadi haka lokaci guda. D'aga musu hannu tayi sannan tace musu. "Dokar masarautan ce,bai isa ya take ta ba, ko Ni da na haife shi ban da ikon karya dokan balle shi din banza, doka ce babu wanda zai karya ta" "Toh Sultanah" haka ta zauna bata ce musu kome ba, ita dai wallahi da ana sauya ƙaddara tabbas da ta sauyawa Ikram da Mehran, sam ta rasa mafita lumshe idanu tayi tana nazarin me ya dace tayi ba tare da ya shafi rayuwar su ba. Sannan taya Ikram zata kashe masoya ta raya makiya. Ga baki daya ta rasa tunaninta. Dafe goshin ta tayi kamar wacce take fama da ciwon kai. Nan kuwa ƙwaƙwalwar ta ne yake aikin hargitsa mata lissafi. ~~~ Shiru suka yi tare da kallon Mehran, kafin suka shiga kallon shi an rasa wanda zai gaya mishi dalilin kiran shi fadar, asalima duk sun razana da yadda yake muxurai. "Sultan MEHRAN yana da uzuri fa!" Fudail ya gaya musu, "kai d'an mashawarta waye yayi dakai?" Murmushi Fudail yayi sannan yace mishi. "Darakshan! Bani da abinda zance maka, amma wata rana zaka biya ladan aikin ka" sannan ya kuma duban mutanen fadar yace musu. "Wani dalili kuke niman Sultan Mehran?" "Shi Sultan Mehran bai da bakin Magana ne inji Sultanah Hoyam?" Ta kalli Mehran, wanda kanshi yake sunkuye yana matsa hannun shi, kamar baya fadar. Kuma har ila yau sun kasa fadar abinda yasa suka nime shi, kasancewar ya zabga musu gargadi tun lokacin yakin da yankunan jazziratul Arab suka nemi shiga musu, ya dakatar. Dayawan su dattijai ne, da suka manyanta amma kasuguman munafukai ne. Dan haka da gayya yaki magana kuma dole sune zasu fadi dalilin da yasa suka kira shi, amma kuma babu wanda yake da zarrar bude baki yayi magana. Abin dariya sai wannan ya zunguri wannan, shi kuma ya zunguri na kusa dashi haka sukai tayi, karshe Amir Hood ne yayi shahadar kuda ya mike tare da cewa. "Jiya Jasrah ta gaya min cewa taga Sultan Aamaan Mehran da wata mace wacce taci mutuncin shi a cikin masarautan nan, sannan ta keta Alfarmar masarautan nan akan idanun kowa bayan ta kasance daya daga cikin fadar nan, shin Sultan Aamaan Mehran ya yarda da ita ne har ya iya yafe mata, ko ba saurayi ta bi ba? Sannan kuma ba girman SULTAN Mehran bane yana yawo cikin gari da kaskantacciyar baiwa a cikin jama'arsa, kar Sultan Mehran ya manta yana cikin dokar hana fita ne me yasa zai karya doka ko ya manta akwai Amirorin da suke jiran ya bada kayan bikin fitilar al'ada a kai musu, amma anga kaya masu daraja a jikin Ikram da kawayenta shin wata irin matsayi take dashi haka? Sannan abisa al'ada ba a yarda wani sarki ya auri macen da tayi mu'amalanci wani namijin ba, kuma ta bayyana ƙarara Ikram namiji tabi, sannan kuma dokar masarautan nan ne, babu batun auren bazawara ko karuwa mafi munin lalacewa ace Sultan Aamaan Mehran ya kwana a gidan ƙaruwai, wannan Zubewar mutuncin masarautan nan ne, mafi munin abu ace Sarki Guda ya kwana a gidan Ƙaruwai? Don Allah ku duba wannan lamarin" Lumshe idanun shi yayi yana jin kalmar karuwa da ya danganta Ikram dashi, jin yadda kalmar take dukar shi kamar ana saka bulalar k'aya karfe. Idanun shi yayi jajjur. Mikewa yayi tare da sauka akan kujeran shi dake fadar,.Yasaka kai zai fita daga fadan."kai waye da zamu yi magana ka mana shiru?" Suka daka mishi tsawa, wannan shine girman kuskuren da suka aikata mishi, dan haka ai ance shiru ma magana ne, dan haka ya fice daga fadan. Tunda yake babu wanda ya tab'a gaya mishi abinda ya saka shi bakin ciki sama da kowa ba, dan haka koda ya koma gida, Daki ya wuce ba tare da kalli inda Sultanah take, tunda ya shiga dakin bai kuma fitowa ba, domin kuwa baya son magana, fahimtar haka da Sultanah tayi yasa ta hana kowa yayi wani abun da zai saka ayi hayaniya ko wani magana me karfi. A bakin Fudail suka ji labarin abinda ya faru, tashi tayi tare da shiryawa tayi zata fadar Fudail ya ce mata. "Sultanah a halin da yake ciki baya son karin damu, matukar zaki nufi fadar toh ba makawa kin lalata kome, dan haka ki zuba ido kiga abinda ya shirya. Yakin masarautan nan Sultan Aamaan Mehran ba zai iya shi daya ba, sannan kuma ke idan kika shiga mishi zasu iya aikata wani abu kuma su makala miki, ni tsorona daya karsu kaiwa Ikram hari domin kuwa zasu aikata haka kuskuren da zasu damu da kansu." Ya fadi haka a raunane, domin yasan haka ce zata faru. Idan ba wani ikon Allah bane ya hana faruwan haka. Numfashi ta sauke tare da kallon shi tace mishi. "Ina Ikram din take?" "Tana wajen garin SAMAIND!" "Toh ka kai mata dauki mana, ko a tura mata dakarun da zasu kula da lafiyarta ". "Karku fara haka!" Ya fadi hakan lokacin da ya fito daga dakin, yana me shirin barin gidan. "Akan me?" "Ba mace kawai bace ita!" Yana gaya musu haka ya ficce daga gidan baki daya, can wajen gidan ya nufa, dan baya son abinda zai tinzira zuciyar shi. Cikin yanayin bakin ciki yake kallon dajin, da yadda kome yake zaune cikin tsarin Ubangiji da ikon shi, yau yayi danasanin kasancewar shi daya daga cikin gidan sarautar ƙasar shi. Damuwa tayi mishi yawa, bai san ta lokacin da ya b'ata a gurin ba, kuma ba zaka tab'a tsammanin yana gurin ba, dan ya saje da gurin baki daya, ya rasa inda zai cusa kanshi. Dan haka da ya gaji da zama ya mike zai dawo gida ne ya hadu da Fudail yana niman shi, kallon juna suka yi sannan yace mishi. "Sun kaiwa Ikram hari" Rab'a gefen shi yayi tare da barin guri a hanzarce ya isa gidan, kayan shi ya sauya sannan ya dauki gatarin shi ya nufi wajen gari. Gani yake dokin da yake kai bata gudu, duk da kuwa saurin da yake yi bai hana shi ganin nisan gidan da Ikram take ba, jike kamar ya cire zuciyar shi ya gulla tsabar tashin hankalin, koda ya isa ya sami dakarun da suke kula da lafiyar ta, duk an kashe su, yana shiga ya same ta zaune akan saman gawarwakin mutanen da ta kashe, jini na d'iga daga gefen cikinta. Ajiyar zuciya ya sauke sannan ya tako a hankali,yana murmushi ganin yadda take rike da takobin salon shi ta dauka, wato tayi kujera da mutanen. Ganin su Izmah da Nimra a gefe bakin su a fashe ne ya sashi kallon su da son karin bayani. "Muna zaune suka shigo, wai ance su kashe Ikram, shine tace inji waye? Sai suka ce mata Sultan Aamaan Mehran, ya umarce su, suka kasheta.mu kuma muka ce karya ne ba zaka tab'a sakawa a kashe ta ba, shine suka rufe mu da duka, daga nan ne ta ce su kyale mu ita ta yarda a kashe ta. Shine kawai suka juya kanta da dukka. Har da janya, bayanta ma jini na zuba. Ganin sun kama mu zasu shigar da mu d'akin ne domin kudirin su, shine ta fara kashe su, wallahi bana son naga tana kashe mutane haka, dabi'ar tai mata yawa, mace ce kuma hakkin jini ba zai tab'a barinta ta huta na." Izmah ta karshe maganar cikin kuka da tashin hankali. "Ikram bani takobin" ya mika mata hannu, bata d'ago kai ba, balle ya saka rai zata amsa mishi, a hankali ya taka har gaban ta, ya saka hannu ya tab'a kafad'arta, biyo shi tayi tare da zubewa a jikin shi. A kidime ya d'ago kanshi, tare da kai hannun shi bayanta, yaji wuka a suke a bayan ta, a hankali ya zare wukar. Kallon Fudail yayi sannan yace mishi. "Maza ka koma ka dauko keken dokin" da gudu ya fita, tare da kallon su Izmah da suke kuka. Kamar me, gani yake kamar Fudail baya dawowa, kamar yayi kuka haka yake ganin ta, dan ma ya tab'a wuyarta yaji tana raye, amma zubar jinin yana d'aga mishi hankali. Dan haka ya kalli Izmah da itace zata iya bashi amsa Nimrah kan tsoro ya cinye ta baki daya. "Basu kira sunan wani ba?" Shiru tayi tana nazarin abinda suka fada tare da kallon shi, girgiza kai tai tare da cewa. "A'a" shiru yayi tare da sake wata tsaki sabida ganin har yanzun Fudail bai iso ba ji yaƙe kamar ya kurma ihu, dan haka ya dauke ta cak zai fita da ita sai ga Fudail nan. "Afwa Sultan Mehran, dakyar suka barni na fito!" Ya kalli Izmah sannan yace musu. "Ku fito!" Ya juya tare da bin bayan Mehran, yana fita aka bude kofar keken ya sakata a kujeran sannan ya juya tare da riko hannun Izmah ta shiga sannan ya kalli Fudail da yake rike da Hannun Nimrah da take kuka. "Ina da abin yi!" Ya gaya musu a gaggaucce, da sauri sauri itama ta shiga cikin keken, hawa dokin shi yayi, Fudail ya hau gaban dokin. Basu B'ata lokaci ba suka nufi masarautar, inda dakarun suka nemi hana Keken shi kasancewar Sultan Mehran yana baya, ganin shi ya dawo gaba duk suka zube akan gwiwar su. Tare da niman afwa. Nufar gidan Mehran yayi da ita, shi kuma Mehran ya nufi gidan likitan masarautar yana shiga yayi karo da Amir Hood. "Zo muje ka duba min mara lafiya!" Ya faɗa a sanyayye, ko kallon Amir Hood bai yi ba,shima likitan haka, bai kalli inda Amir Hood yake ba, zasu fita yace. "Aamaan ba dai akan karuwar na bace kake damuwa?" Murmushi yayi sannan yace mishi. "Bani da lokacin ka!" Suka fita a fusace, Amir shima ya fita daga gidan yana jin lallai dole ya kashe Ikram, wannan itace bakar kaddarar da aka ce zata shigo masarautan. Kuma ya fahimci haka ne tun daga ranar da Sultan Aamaan ya saka aka hukunta Zuhair, sannan bayan an konata Aamaan ya dauke ta suka yi balagoron har Madinatul Mah, wannan yasa shi kara fahimtar haka akanta. Amma baya fatan abubuwan da ya aikata su biyayya har yarinyar ta sani. ~~~ Tunda likitan ya isa gidan yake famar bata kulawa har ya dinke ciwon jikinta, Mehran yana tsaye akanta tare da sintiri, idan kana gidan sai ka fahimci yadda Mehran ya dawo, bayan wani lokaci likitan ya fito yana faɗin. "Insha ALLAH zata samu sauki, sannan a kula da bayanta da kuma cikin ta." "Zata ji sauki nan da sati biyu?" Mehran ya tambaya a dame, "Eh Toh ya danganta da yanayin jikinta ne" rike bakin shi yayi sannan ya kalle shi, yace. "Babu wani matsala bayan Ciwon jikinta?' "Babu gaskiya" "Mun gode!" Inji Sultanah, Yana fita ta shiga dakin tare da kallon ikram, zucuyarta a raunane yake akan Yarinyar, amma tsoron goben D'anta take, tana gudun abinda zai je ya dawo mishi. Ikram itace ta dace da Mehran, amma idan ta duba yadda rayuwar su take, zai yi wuya kome bai faru ba, tana jin ciwon yadda kome ya cab'e mishi . Shigowar shi da yayi ne ya sata dauke kanta daga Ikram. "Naji kama tambayar zata sami lafiya nan da sati biyu. Meye kike nufi?" "So nake ta shiga cikin zab'en matan da za ayi." "Akan me?" Zuba mata ido yayi sannan ya sake murmushi. "Sabida ta zauna a matsayin shugaban Kwarkwarorin na!" "Yarinyar da take da sa'ar ce zata zauna a kwarkwarah? Hmm!..... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 32 Ta tambaye shi tare da kallon shi,bakin shi ya gaza furta kome, sai zare ido yake. "Mehran ba zan hanaka abinda kake so ba, amma ya girman hatsarin shi a rayuwarka, iya yanzun ma an fara samun matsala ina kuma ta shiga harkokin cikin masarautan? Ka duba abinda nake nufi akan Ikram kayi hakuri ka rabu da ita, bata da Sa'a a rayuwarka. Idan so ne a duniyar nan babu wanda ya kai ni sonka da kuma kaunarka da Ikram, amma dole ce Kanwar naki zata sani na iya dauke kai na daga Ikram, don Allah ka rabu da ita" Girgiza mata kai yayi, sannan ya juya tare da barin d'akin, numfashi ta sauke sannan ta kalli yadda ikram take barci cikin wahala, kafin ta juya ta fita. A gaskiya bata kin Ikram amma halin da zata jefa rayuwar shi ce take jin tsoron Allah akan haka, kuma tasan zai yi wuya ya rabu da ita, shi yasa take jin kamar ta kori ikram idan taji sauki ko kuma ta saka a a lalata mata jarabawar da zasu yi. Amma kuma idan ta tuna yadda yarinyar ta b'ata lokaci tana zaune da Mehran sai taji jikinta yayi mugu mugun sanyi, taji bata da wani hanyar da zata iya cutar da ikram, sai dai kuma ba zata iya daukar kasadar barin shi ya zauna da ikram ba, Allah ya gani ba zata yarda da wannan tunanin ba, gwara duk abinda zai faru ya faru, amma tabbas zata raba su Insha Allah. Dan haka ita zata zauna da ikram har ta warke ta kuma maida ita garin su ta gaji yanzun son D'anta take bata jin zata bar shi ga kowa. *** Kura musu ido yayi tare da cewa. "Akan me zaku ce min Sultanah ta hana a cire al'adar duba al'urar mace? Gaskiya ba zai yiwu ba a cire shi ko kuma." "Indai akan ikram ce kake wannan zakewar ba dai kai ka ba, domin haka da zaka aikata shi zai sanya kowa ya zargi wani abu daga gare ta, dan haka ka ɗauke kanka akan Ikram ko kuma na sanya a fidda ita daga Masarautan nan baki daya." Inji Sultanah, shafa kanshi yayi tare da kallon kasa, tabbas yana tinzira ta, domin bata tab'a juyawa muradin shi baya ba, sai wannan karon. "Shi kenan, amma ba zan lamunci kasawa ba, dan wallahi idan aka min kuskure za a ga mugun tashin hankali.".ya fadi haka a zuciye, sannan ya bar gurin su.... ..~~~ a cikin wannan yanayin aka fara shirya abubuwan da za ayi, duk da kuwa an fara tarb'an baki daga yankunan kasar. Musamman y'ay'an gwamnonin shi, Sakeenatu binti Abu Waqqas da Azizatul Nissah, sune kawai suka rage basu iso ba. Gefe guda kuwa zamu iya cewa Alhamdulillahi domin jikin Ikram ya d'an samu sauki, sai dai bata iya jure tsayuwa ko kuma wani abun da zai sanya ta zauna na wani lokaci. Sannan wani karin tashin hankali yadda take wasu abubuwan kamar tab'abb'iya, domin zata iya daukar wasu lokuta bata yi magana ba, idan kuma ka bata abinci zata na kallon shi kamar taga dodo, dan haka wannan yanayin ya sanya shi shiga tashin hankalin da ya kasa fahimtar kome. Itace dai yake sakawa a gaba da tunanin halin da zata kasance. Ganin haka yasa Sultanah ta kuma niman Uwaisul Qarni, sunyi magana sosai har ya gaya mata cewa. "Ku godewa Allah da iya haka ne ya same ta, domin ban da Allah ya taimaka na bata addu'o'in kwanaki ba da wallahi sai abin yafi haka, dan haka ku kai mata wannan, sannan karki zata abinda kike bukata zaki samu, karki kuma yunkurin rabasu, hakan kuskuren ne babba, karki nunawa Ubangiji wayonki, shi da ya had'a su shi yasan yadda zai yi da kowannen su. Dan haka kar na kuma jin kin ce zaki raba su, domin wani tunanin dake ranki." Da wannan yayi mata sallama, tare da barin gurinta, haka ta kai wannan ruwan addu'o'in dakin Ikram ta bata, sai da ta shanye sannan ta fita. "Anne meke damun tane?" Ya tambaye ta ranshi a jagule, ajiyar zuciya ta sauke sannan tace mishi. "Jini yake bibiyarta, amma Insha Allah idan tayi barci ta farka zata ji sauki wasu abubuwan." Kasa jure bayanin da Sultanah tayi mishi, dan haka ya juya ya bar gidan. Bai tsaya ba sai shashin da Su Izmah suke ya shiga ya same su a tsaye Mahlika tana cin kaniyar su. "Waye ya baki damar hukunta wasu?" "Afuwa Sultan ba zan kuma ba!" Dauke kanshi yayi sannan yace musu. "Muje" haka suka bishi, cikin jin dadi ya kawo musu dauki. Bayan sun bar gidan ya kai su lambun da yake cikin gidan, suka nufa. Tun da suka zauna yayi shiru kafin ya tambaye su. "Izmah meye faru da Ikram domin na Fahimci kun jima tare," gyada mishi kai tayi sannan ta fara bashi labarin abinda ya faru, lumshe idanun shi yayi sannan yace musu. "Lallai biri yayi kama da mutum, sai yanzun na fahimci dalilin da yasa take saurin fushi, dalilai na rayuwa sun sauya ta, Ikram din da na sani ba ita bace wannan,wancan Yarinyar bace da nasani, halin wannan ya banbanta na wancan." A hankali yake gaya musu abinda ya faru, da yadda aka kashe Noman ba tare da sanin shi ba. Amma yasan koda yayi mata bayani ba kula shi zata yi ba, dan ranta yana kan fansa, dan haka ya kyale ta tayi yadda take so. ~~~ Sintiri take hannun shi goye a bayan shi, tun sati biyu ya sami labarin Ikram tana cikin Samaind bai yarda ba, sai da ya tura amintattun bayin shi mutane biyu, suka je har can suka binciko mishi ita, dan haka ba zai iya kyale ta ba, dan wallahi sai ya kuma dawowa da ita rayuwar shi. Shigowar Nawwas ne ya katse mishi shirun shi. "Sultan Abrad!" "Hmm!" Ya faɗa kamar zai zunduma ihu, kafin yace mishi.. "Ikram tana raye!". Cike da mamaki ya d'ago kanshi tare da kallon shi sannan yace mishi.."waye ya gaya maka?" "Na tura har mutane biyu sun duba min ita, amma tana cikin masarautar bata da lafiya, ka tabbatar sunyi aure da Noman?" Ya tambayi Nawwas yana me kallon shi. "Eh na tabbatar sunyi aure aka kashe shi." Murmushi Abrad yayi sannan yace mishi. "Kace min a daren amarcin su ko?"ya tambaya tare da kallon Nawwas, had'iye yawun yayi sannan yace mishi."eh Sultan Abrad" wani irin murmushin mugunta yayi tare da kallon Nawwas sannan yace mishi. "Dole Mehran ya bar min ita, domin an ce min zai gabatar da ita a zab'en da zai yi, ya ka gani idan na fasa cewa ta tab'a aure?" "Amma wannan kuskure ne babba, karka yi amfani da abinda kake ji akanta ka cutar da ita mana! Kayi mata adalci idan." "Kayi min shiru! Ikram tawa ce!" Ya faɗa da karfi, kafin ya shiga wasu zautattun bayanai kamar tab'abbe, yana gaya mishi abinda yake ji akanta, tare da yadda yake ji duk wanda ya shiga tsakanin su, sai uwar shi ta haifi wani amma tabbas sai ya kashe shi. "Sultan MEHRAN kuma sai na tsaya da karfin tsiya na raba su, ko kuma na raba mishi hankalin shi akan mulkin shi." "Gaskiya kana sonka ka da yawa, da yarinyar nan tana da ra'ayinka dangane da zama da kai da Nan zata dawo, amma dake bata da ra'ayin ka, gurin shi ta nufa, don Allah karka shiga abinda zai dame ka har karshen rayuwar ka" ya fadi haka a sanyayye. "Shawara kake bani ko gargadi na kake?" Murmushi yayi sannan yace mishi. "Abrad bani da ikon baka umarni sai dai shawara idan zaka dauka idan na zaka dauka ba kabarshi Allah ya kyauta, an jima zamu bar garin!" "Ka kira Samim! Zamu bar mishi garin zan biku!" D'ago kai yayi yana kallon Abrad cikin mamaki me tattare da damuwa. "Shi kenan!" Ya faɗa mishi, sannan ya bar d'akin. Wani irin murmushi yake irin na samun nasara akan abokin gaban ka. Yau zai je ya sami Ikram. ~~~> Yau saura kwana uku, A hankali na kalli Sultanah Fazilatul nisa, sannan na maida kai ma ga maganin gaba na, ina sha. "Yau ma gani a gabanki kamar can baya, nazo domin Mehran yana bukatar ki shiga cikin zab'en." "Tab" na fada tare da tab'e baki, "Me yasa kike son ganin sai na sami kusanci da shi? Wato dan d'anki ne ko? Toh gaskiya ni ba zan shiga dan shi ba, zan shiga ne dan biyan buƙatar kai na, dan haka ki kyale ni ba zan shiga dan shi ba sai dan rad'in kaina." Kallonta Sultanah tayi tare da jin babu dadi. "Amma me yasa baki jin Magana? Me yasa kike wahalar da mutanen da suka damu dake? Shi kenan, kiyi yadda kike so, amma ki sani, Allah ba zai tab'a barin hakkin shi ba, wallahi matukar kika jagoranci wulakanta shi, Allah sai ya saka mishi." Kasa nayi da kaina sannan nace mata. "Lokacin da ya kashe min mijina baki tausaya min ba, baki san yadda naji a lokacin b.." Bamu san shigowar shi ba sai ji nayi ya shake wuyata ranshi a jagule. Huci yake kawai dan bai iya magana ba, sai ɓari jikin shi yake ya bani tsoro sosai. "Sake ta nace" ta daka mishi tsawa, cikin fushi ya fita daga dakin bayan ya sake ta. Itama fita tayi daga d'akin, Izmah da Nimra da suke bakin kofa suka shiga d'akin. "Amma baki mutunci ko daya? Wallahi ba haka Mahaifiyar ki take ba, duk da sanin yarinta nayi mata Wallahi bata da rashin da'a, ke wacce irin shaidaniyar yarinya ce? Me kike bukata a rayuwarki? Kin san halin da Sultan Aamaan yake ciki? Ko damuwa da mutanen da suka kashe miki Mahaifiyarki baki yi ba, kin zo kin Buwayi rayuwar shi? Sabida ke yake rayuwa a nan,.sabida ke ya zabi ya xauka babu mulki wallahi Allah sai ya saka mishi, mutumin da bai ji ba bai gani ba kika tsana akan mutumin da bai kai iyayenki daraja ba,.na zata zaki tafi daukar fansan kanwarki ashe ke gurin bawan Allah zaki tsaya, jahilar banza jaka dabba, idan kin so karki shiga dan Mehran ki shiga dan ki kashe shi wawuya doluwa wacce jahilci da rashin kunya ya cika mata kai,Mahaifiyarki koda ta kasance Sarkin yaki bata yi aiki da hauka irin taki ba, idan kin so karki bar Mehran a raye. Ban da shima da damuwa meye zai tsaya samun damun kanshi da yarinyar da babu mamora a jikinta. Dube ki har zaki kira kanki da mace, banziya kawai." Sake baki nayi ina kallon yadda ake tijara, domin tsakani da Allah suka zage ni tass, sannan kuma suka rabu dani. Ban kuma ganin su ba, sai ma suka daina shigo min, har ana gobe za ayi abun lokacin Sultanah Fazilatul nisa, ya ajiye ranar zata bayyana kanta. Sai dai bata da kwarin gwiwar haka,.ina zaune Fudail ya zagayo bayan gidan da nake zaune, zama yayi sannan yace min. "Gobe Insha Allah za a gabatar da abubuwa da yawa,. Sannan Mehran zai so ki lashe zaben baki daya, Ikram Mehran yana raye cikin makiya ne, duk yadda nake son ki fahimta ba zaki gane ba, dan haka iya yau kike dashi tare da saka ido idan an gama zaben abinda sakamakon ya bada kina da karfin iko kashi talatin da biyar cikin dari, dan haka wannan damar da kike dashi ya isa ya tabbatar da cewa zamu sami sabon sauyi a Samaind, sannan don Allah karki saka idanu akan sauran matan, ki zuba musu ido idan suka tab'a ki ne zaki tab'a su karki yarda su miki tambarin da zai kai ki har fada domin matukar kika shiga makiyan Mehran da wasu zasu bayyana a rayuwarki..... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 33 "Sannan karki yarda wani yasan batun kinyi aure, idan ya fito daga cikin masarautan nan zamu dakatar idan ya fito daga wajen masarautan nan zamu kashe koma waye, Ikram Mehran ya shirya tsaf domin baki rayuwar shi, don Allah karki bari wannan damar ta subuce miki domin na rantse da Allah, mutane dayawa suna niman kusancin su da Mehran amma Allah bai nufa ba, ke da kika samu kina mishi rikon sakainar kashi, Mehran yana da kirki kuma yana da hakuri, rayuwa da kika ga yayi tsara mishi aka yi wanda Allah ya tsara mishi kuma aka ruguje shi don Allah karki juya mishi baya lokacin da yake bukatar ki, don Allah ki taimaka mishi wallahi yana cikin damuwa ainun." "Yana ina ne?" Na tambaye shi.. "Yana dakin shi da yake sama" ya faɗa tare da barin gurin, a hankali na mike tare da nufar cikin gidan, dakin shi na wuce. Samun shi nayi a dakin shi. A hankali na bude kofar d'akin shi. Karatu yake dan naji muryan shi yana tashi, da sallama na shiga d'akin. Ajiye Alqur'anin yayi tare da amsa mata, daga haka ya cigaba da abinda yake, tun da na shiga tare da niman guri na zauna. Ganin ya cigaba da karatun shi ya sani kallon dakin da yadda yake cikin. Kome a shirye yake sai kamshin turaren shi yake, ga wani sanyin dad'i da dakin yayi. Ya bada wani irin yanayi, me wiyar fassaruwa. Lumshe idanu nayi tare da ware su akan wani loka, haka kawai naji ina son ganin abinda yake cikin shi. Dan haka na kai hannuna zan bude naji yace min. "Kinyi min ajiye ne?" Juyawa nayi tare da barin bude kofar, kallon shi nayi yadda ya tara kasumba, idanu shi sunyi zuru, faffarar kirjin shi me cike da gargasa, ya kara cikowa sakamakon tarin kwanjin da suka cika kirjin. Sunkuyar da kaina tare da cewa. "Kayi hakuri da abinda na aikata" juya bayan shi yayi tare da Cigaba da abinda yake, domin idan ya cigaba da kallonta, ran shin ba zai so yadda take nuna nadamarta ba, dan haka ya juya abin shi zai bar dakin. Shan gaban shi nayi tare da cewa. "Ya ina magana ka share ni?" Na tambaye shi, "Me kika ce?" Ya tambaye ni cikin gajiya da gani na, eh mana ya gaji da gani na, idan na gajiya ba meye zai wani ce bai ji me nace ba. "Kenan baki ji me nace ba?" Na kuma kuma tambayar shi a karo na biyu. Tab'e baki yayi sannan ya girgiza min kai, da naga da gaske shiga ban daki zai yi nayi maza na tare kofar, zuba min ido yayi sannan ya bude baki zai min magana na riga shi. "Kayi hakuri mana" "Toh bani hanya na shiga wanka," matsawa nayi daga jikin kofar, da yazo shiga cikin banɗakin. Tsayawa yayi tare da bude kofar zai shiga. Riko hannuna yayi muka shiga tare, tunda muka shiga na fara hada mishi ruwan wanka, bayan na gama, na kalle shi. "Zoki goge min baya!" Ya faɗa min haka yana shiga ruwan wankan, zama nayi a saman gurin wankan na shiga wanke mishi kanshi tare da taimaka mishi har na gama na fito shima ya karasa, ina gamawa na fito daga dakin shi. Sannan na sami tawada da alkalami na rubuta musu karamar wasika, sannan na bar gidan tare da su Izmah basu so haka ba, amma babu yadda suka iya dani. Lokacin da ya fito yaga Anne da sakon ta karanta, murmushi tayi sannan tace mishi. "Yarinyar nan tana da kaifin basira, zata shiga amma bada ikon ka ba, zata shiga da ikon Aabis Bin Ansar, Sarkin sahara. Kenan idan ya shigo da tambarin wata masarautan." "Amma lallai Ikram mahaukaciya ce, kinsan daga Masarautun da tafito? Daga Askandariya da kuma Merocco ne fa, taya ba zata shiga da ahalin ba? Me yasa ba zata iya tsayawa danginta ba,.idan tayi kyau sahara za a kira idan ta ɓaci kuma wa za'a kira?" Ya faɗa a zafaffe, yau da Ikram tana gaban shi babu abinda zai hana shi ya mare ta, domin ya tsani renin hankali. "Ba zata so tab'awa daularta suna ba, sannan idan ta tsayawa danginta ta fadi abin kunya ce a gare ta,.idan kuma tayi nasara Cigaban su ce, dan haka ka kyale ta,.muga tsarinta tunda gobe za'ayi abin." Ajiyar zuciya ya sauke tare da kallon Sultanah, "Ni yanzun ban," "gidan Mahaifiyar Fudail ne zasu zauna domin ina ganin yau sahara zasu tawo da wakilar su." Haka suka shiga tattaunawa da yadda abin zai tafi yadda ya dace. --- Tunda na shiga dakin mahaifiyar Fudail,nake murmushi sabida dattijuwar tana da kirki da addini, tana yawan ganin yadda Nimrah ta takure guri guda, ni da Izmah kuwa hiran mu tayi da ita. shigowar Fudail ya kura mata ido, sunkuyar da kai tayi tana murmushi, murmushi mahaifiyar shi tayi tare da cewa. "Fudail itace Nimrah ko?" Kunyar Maman shi ce a kama shi yace min. "Ikram Sultan Mehran yana farfajiya." Fuskar damuwa nayi sannan na mike tare da yafa alkyabar ta, ina fita ha hango shi hannun shi cikin aljuhun wando shi, ya jingina da bishiya, tare da juya min baya. Tausayi ya bani a karo na farko bayan na dawo da niyyar sai na kashe shi. A hankali na taki bayan shi, na tsaya. "Amincin Allah ya tabbata a gare ka" "Kema haka ya tabbatar a gare mu baki daya, sarauniyar yan taurin kai, wallahi Ikram ina tausaya miki ranar da zaki shiga hannuna, Kinga kwana biyu ban saka ki kuka ba ko? Shine kike min yadda kika so? Sama kin bani hakuri zaki bar cikin Harami ne? Me yasa kike son nunawa duniya baki da daraja ne?" D'ago kai nayi sannan nace mishi. "Na sani mana, taya zan kai kaina cikin dangina nace musu nima daya ce daga cikin su? A'a kawai dai na zab'i muradun zuci ne nayi nisan da zasu nime ni ban sha'awa ace na kai kaina suyi tsammanin nazo yaudarar su ce!" Ta fadi haka a matukar sanyayye, rike hannun ta yayi cikin nashi yana kallon yadda take sunkuya da kai kasa, "Kina da hankali amma ba me yawwa ba, domin haukarki tafi yawa" murmushi nayi, bance mishi kome ba. Kuma ai bani da abinda zan ce, kawai dai na cigaba da zama kafada da kafada da shi, duk da hiran ta kurame ce amma kuma yana matukar muhimmanci. "Ashe kin iya fada haka ranar da nazo ma zata zan samu an yi gunduwa gunduwa da yar kwailata sai naga ashe kwaila jaruma ce har ta iya salon Mehran?" Kallon mamaki nayi mishi domin mutum ne da baida yawan magana, amma yadda yake surutun sai abin yazo min wani sabon a gurina. "Ki daina irin wannan dabi'ar mazan, ke mace ce bana son ki gaji mahaifanki. Sultanah nake so ki zama ba wata bardiya ba." "Kana sona ne?" Na tsinci bakina da tambayar shi, kallon juna muke tare da kasa furta kome, "kiyi hakuri! Ban tab'a sonki ba, kawai ina bukatar kine a rayuwata, kuma nasan kema kina bukata na a rayuwar ki!" Sunkuyar da kai nayi ban kuma cewa kome ba, kawai dai nasan nayi kuskuren tambayar shi, amma kuma me yasa kowa yake ganin kamar yana sona ne! Bayan shi ba sona yake ba, kawai ra'ayina yake. "Ki daina abubuwa dayawa ki zama mace sosai, na bawa Fudail sako yabawa Umman shi zata miki bayani," juya fuskana yayi tare da hura min iskar bakin shi yana me kallon kwayar idanu na, d'ago kai nayi tare son zan mishi magana, ya zira min harshen shi cikin bakina, zaro idanu nayi cikin wani irin tsoro da shaƙar shi. Iska ta hancina hannun shi yakai keya na, ban san lokacin da na cusa hannuna cikin rigar shi ba, tare da shigewa jikin shi. Ban tab'a jin yanayin da nake ji ba, mun jima a haka kafin na janye jikina daga cikin nashi, riko hannuna yayi tare da cewa. "Don Allah ki tuna da wannan gobe karki bani kunya,!" A hankali ya mike tare da mikar dani, hannun shi ya kai k'uguna. "Ina bukatar ki daina wannan dabi'ar mazan ki koma mace, duk cikin su kin fisu yarinta, so nake ki zama yarinya kamar yadda nake so." Kallon shi nayi tare da jin tausayin shi, sam bana jin dadin kusancinsa dani, an haka dai na daure muka shiga cikin gidan, har cikin gidan, nan aka kuma buɗe sabon hira, duk idanun shi yana kai na, tare da kasa cewa kome. A hankali muke satar kallon juna, sabida yadda muke da d'an tazara a tsakanin mu, murmushi nayi sannan na kalle shi, shima murmushi yayi tare da kallon na, yana min magana da idanu. Girgiza kai yayi tare da nuna min Izmah, lumshe idanuna nayi tare da gyada mishi kai. A hankali muke tare da kallon Izmah da take kallon mu, mik'ewa yayi tare da kallon Umma yace.. "Zamu tafi umma!" "Toh mun gode Sultan Mehran!" Murmushi tayi sannan ta bishi da addu'a, haka ya fita tare da kallon inda nake, dauke kai nayi tare da cewa. "Allah ya kai mu lafiya" Haka suka tafi,ina jin a raina tausayin shi yana rinyana, sunkuyar da kai nayi, wato tunda suka fita yaja tunga ya tsaya, duk ya rasa me zai ce, can kuwa yacewa Fudail. "Hmm, baka yi mantuwan ba?" Dake shima ya harbo jirgin shi, sai yace mishi. "Ban manta kome ba, sai dai ko kai?" "Hmm! Ina jin kam nayi mantuwa a cikin gidan." "Toh na kira maka Ikram sai ka saka ta ta dauko maka abin." "Hmm! Manta kawai mu tafi dare yayi" haka suka suka bar gidan babu wani armashi a fuskarshi. ---- Tunda suka tafi muke hira da Umma take min bayanin abubuwan da zanyi amfani dashi a cikin daren zuwa gobe da safe, sai kuma yadda take buƙatar nayi wasu abubuwan, kama daga tafiya na, kasa magana nayi ina kallon ta, har ta gama. ~~~ Da asuba su Abrad suka iso, garin SAMAIND ta jirgin ruwa, babban masauki aka tanadar musu, sannan suka kwanta Huce gajiyar su. Amma Allah ya gani baya ta matar shi,.Ikram ce yake bukata a lokacin. Dan haka ya kwanta da mafarkai akanta, washi gari suka shirya tsaf sannan aka ɗauki Azizatul Nissah aka tafi da ita su kuma suka take mata baya, A hankali ya'yan shuwagabannin yankunan da suka yi ta wucewa, wurin hatsi Sakeenatu binti Abu Waqqas ta iso, itama ta wuce sannan. Nima banyi tsammanin zan sami tawaga ba, aka turo na fito. Haka na fita sanye da wata rigar da aka kawo mintin daga Masarautan Sahara, tare da shigar alfarma wanda idan ka ganin zaka Fahimci lallai tabbas na fito daga babban masarautan,haka muka nufi cikin masarautan. *** Cikin shigar alfarma yake kallon yan matan da suke zuwa, har ya cire rai da zata shigo, domin ya kalli Fudail ya kai sau bakwai, kafin aka sanar cewa ga Amirah Bilqisul Ikram daga Masarautan Sahara. Yadda aka kawo ni tare da fitowa na, Yasaka zukatar mutane dayawa ya girgiza, dan haka na sunkuyar da kaina, tare da nufar inda aka ajiye mana kujerun mu, su Izmah da Nimra suna kallona, Idanun Abrad kuwa ya kur akan Ikram, yarinyar ta kuma girma da kyau, sai wani sheki take, ga wani shegen annurin da take fitarwa, a gurin dai ta zame mishi fitilar shi. Haka yayi ta kallonta tare da jin cewa tabbas ya mallake ta, kowa kuwa haka zai kuma tinzira zuciyar su ga yaki ne sai ya amshi abin shi, dan haka ya sauke ajiyar zuciya, tare da yarda da cewa, dole ya kawo karshen Labarin. Domin koda taci kome bazata zama matar sarki ba sai Kanwar shi. A ɓangaren Mehran kuwa hankalin shi a tare yake. A ranshi kuwa tambayar kanshi yake. _Wani irin Girma kike dashi ne a zuciyata Ikram?_ Ya kasa samun amsar domin kuwa, ya gama lallubar kome.... *Ana dara ga dare yayi.....* [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 34 MEROCCO Da sauri wani Bafade ya shigo tare da zuɓewa a gaban Sultan Mu'allim, tare da sadda da kanshi, jikin shi yana rawa. "Huzaif lafiya?" Amir Sulaiman ya tambaye shi, "Allah ya taimaki Sultan, An sami inda Ikram take." Jikin Rahil na rawa ya taso kamar zai fada kan Huzaif yace mishi. "A ina? Tana ina ne? Waye ya bada labarin ganinta? Ina yaƙe?" Yayi tambayar jikin shi yana rawa, "Tana SAMAIND!" Ya faɗa a sanyayye, kallon kallo aka shiga yi da dattawan fadan, bakin shi na rawa yace mishi. "Me ta jeyi a can?" "Ta shiga cikin zab'en matan sarki da..." Wani irin duhu ya gani tare da jin faduwar gaba, kaman zai zube kasa, haka ya kasance dashi. Idanun shi da suke cike da kwalla, yake lumshe su. Rike shi aka yi tare da shafa kanshi. Amir Sulaiman yake yana kallon shi. Tausayin Amir Rahil suke gabaki daya ya sussuce musu. "Nifa kawai ku tashi muje, kar mukara dan wallahi ba zan barwa kowa ita ba. Don Allah ku tashi mu tafi." Haka suka wuce dashi cikin gidan, nan suka shiga tattaunawa daga nan suka ajiye maganar yadda zasu tinkari SAMAIND ba tare da sun sami matsala ba. Duk da sun so ba zasu tafi da Amir Rahil ba, amma suka hakura domin matukar suka ce ba zasu tafi da shi ba, zasu iya samun labarin ya mutu. A yanzu ma ya aka kare dashi. Dan haka zasu tafi dashi. Sai dai sun san ba tafiyar yau bane dole su hakura sai gobe. A ranar aka kuma tura wani bafade har askandariya. Domin kuwa idan ba haka ba babu wanda zai kaiwa Sultanah Amrah labarin. ~~~ SAMAIND. Shiru gurin taron yayi kafin Fudail ya fara musu bayani kamar yadda ake yi, tare da nuna musu inda kayan abincin yake zasu diba. Sannan aka saka musu lokacin da zasu fara aikin. Haka kowa yaje ya dauki nashi cikin ladabi. Sai dai yaran shuwagabannin yankunan ne basu da dad'i. Domin magana suke gaya min, dan haka ban damu ba. Na nufi inda zan dauki nawa kayan aikin ne na samu sun kwashe kome. Juyawa nayi tare da kallon su, sannan na tafi na dauki ruwan da duka bari, haka na dauka tare da dawowa na rufe shi. Sai dariya suke min tare da kallona, ban damu ba ban kuma ji a raina zan fadi ba. Fitowar Sultanah ya saka mutane dayawa mik'ewa cikin tashin hankali da dimuwa, cikin su har da Amir Hood, tare da Sultanah Hoyam. Zama tayi a inda Fudail ya ajiye mata kujeran domin kallon yadda ake gabatar da abubuwan. Awa daya ya wuce sannan aka kuma samun awa biyu yazo. A lokacin kowa ya fara alaman ya gama abincin, ina kallon su. Mik'ewa suka yi nima haka, sannan Fudail yazo ya fara kwashe abincin yana kaiwa ana jerawa, tare da saka tambarin gidajen su. Da aka zo kaina suka dauki ruwan,. "Me yasa haka?" "Bani da zab'i." "Baki tunanin zaki fadi!" Murmushi nayi mishi sannan nace. " Allah zai tsaya min,Nasara a jini na take." Na fada mishi. Juyawa yayi gurin sauran ya musu magana sannan ya wuce. An fara gabatar da abincin da kuma tambayar kowa yadda suka hada, babu laifi wannan karon sunyi bazata, domin idan kaci abincin wannan ,.ka kuma cin na wannan sai kaji na wannan yafi na wancan. Haka ayi ta jingina musu musamman iyayen su. Ruwa ka gabatar mishi , kallona yayi cikin tuhuma. Sunkuyar da kai nayi, sabida yadda ake dariya daga manyan gurin har zuwa yaran su, sai Sultanah Fazilatul nisa ce ta kalle ni, Fudail yace min. "Ikram muna jin hujjar ki na kawo ruwa a madadin abinci." Mikewa nayi tare da rike hannuna, sannan nace Mishi. "Mulki ba iya abinci yake bukata ba ga talakawa, suna bukatar tsaro da kula da hakkokin su, sannan dole duk wacce zata kasance matar sarki ta kasance me tunanin rayuwar al'umma, babu wanda zai fito daga sahara ka dauki abinci ka bashi, sannan kayi tunanin zai yi rayuwa cikin nutsuwa. Ruwa yake bukata, kana bashi ruwa tamkar ka warware mishi duk wani abinda ya dauko ne daga can. Sannan muhimmanci ruwa Yasaka ake mishi kirarin ruwa abokin aiki, duk abinda zaka yi dole sai ka bukaci ruwa a cikin shi. Hatta masana kiwon lafiya su tabbatar da cewa. Kaso mafi yawa a jikin mutum ruwa ne, sai jini dan adam ba zai iya rayuwa babu ruwa ba, kamar yadda zai iya rayuwa babu abinci matukar akwai ruwa zai iya samar da abinci. Ba zaka gane baiwar da Ni'imar da Allah yayiwa Ruwa ba sai ka shiga sahara babu ruwa dai abinci nan zaka ga mutane da yawa suna mutuwa, amma idan da akwai ruwa zaka samu zasu kai labari duk lokacin da zaka ci abinci dole ka bukaci ruwa, dukda dashi ake sarrafa abincin, wannan shine dalilina na amfani da ruwa a cikin tsarina." Shiru kowa yayi musamman yan matan da suke ganin kamar sun lashe zab'en, sai juyawa suke suna kallona, wato nayi abinda basu iya ba, bayan an gama wannan sai aka bukaci mu dafa shayi. A tare muka tashi. Da haka iya ganyen shayin ne sai zuma. Tashi nayi tare da nufar Lambun da yake gurin na tsinko ganyayyekin masu kyau da kamshi, sannan na fara dakawa a hankali ina maida hankalina akan abinda nake, a cikin ganye akwai janye minnan nas, akwai ciyawar lemo,.akwai ganyen citta, da ganyen kanumfari, sai ganyen na'ana dan haka duk na dake su, sai ganyen ciyawar lemo ne ban saka ba, na barshi sai da shayin na dauko dafuwa na saka, a hankali kamshin ya cika gurin su kansu yan matan kallona suke kamar zasu yi ihu. Dan haka ina gamawa na zuzzuba a cikin kofunan sannan kuma na d'iga musu zuman,a hankali aka yi ya kai na sauran kafin aka zo kaina, suna zuwa Fudail yace. "Sannun da ƙoƙari." Murmushi nayi mishi sannan suka wuce da shayin, kai na a sunkuye na zauna,.ina jiran sakamakon. Kamar yadda aka raba na kowa haka aka kai nawa ya dauka a hankali yana kallon yadda na sunkuyar da kaina. A hankali ya kurb'a, dadda'ar d'and'ano da kamshi me gamsar da zuciya Yasaka shi d'ago kai yana kallona, kurb'an shayin yayi sanan ya kuma kallon yadda kowa yake shan shayin cikin gamsuwa, musamman Abrad da yake jifar Ikram da kallon duk da bata san yana yi ba. A hankali suka tashi suka fara bayanin su,.duk kusan abu daya suka yi dan haka ina mik'ewa nace musu. "Gabaki daya ganyayyekin da nayi amfani dashi yana magani. Domin dukkan su, ana mana abinci da shi. Sannan ita kanta wannan shayin idan mura ta dame ka, aka hada maka kana sha da Yardan Ubangiji zaka ji sauki sosai, shi yasa na hada shi sabida nasan dayawa ana fama da ciwon mura. Kasancewar muna yankin da take da yawan dusar ƙanƙara. Ita kanta maganin sanyi ce." Zama nayi domin sun yarda da abinda na faɗa, can aka kuma zuwa da wani bayani. Inda Darakshan ya kawo bayanin kamar haka. "Kasancewar kina matsayin Sultanah sai sarki ya tafi yaki, kuma bai talakawa babu abinci a tare dasu, kayan abincin su ya kare, gashi Sultan bai bada Umarnin a raba ba, sabida haka ke a baki tunanin me zaki iyawa talakawa? Sai manomin da yayi noma tare da saka tsammanin abincin shi zai kai labari, sai aka wayi gari d'an shi bai baida lafiya kuma yana da saniyar shi na hud'a, dan haka sai ya saka.saniyar shi da abincin shi a gaba wane zai sayar? Sai na uku, mutane uku sunyi laifi kuma ba a san waye mai laifin ba, dan haka sarki ya basu wasika akan su tafi can wajen gari su bawa dakarun. Sai kafin su isa sai aka fara ruwan sama, dan haka sai fada ta kama su. Har takai sun sake wasikar su a sunyi musayan wasikar, daya kuma yana rike da wasikar shi. Dan haka da suka isa gurin dakarun sai suka maida abinda ya kawo su, sannan aka amshi wasikar dayan su, aka duba..su kuma aka yanke musu hukuncin kisa? Bayan kuma daya ne mai lafiyan shin taya zaku gano me laifin?" A hankali Sakeenatu binti Abu Waqqas ta mike sannan tace. "Idan Sultan bayan ba zan tab'a dukiyar masarauta ba, sabida babu hurumina a cikin wannan yanayin. Na biyu kuma manomi zai sayar da saniyar shine domin lafiyar d'an shi. Na uku kuma a kashe su dukkan su biyu, domin koda za a tsananta binciken ba za a gane ne gaskiya ba. Wannan shine hujjata." Azizatul Nissah ta mike sannan tace. "Bazan yi katsalandan ga shiga harkan tallafawa talakawa ba, ai daman tun kafin a fara yaki dole zasu bukaci su tanadar da kayan abincin su. Na biyu manomi zai iya sayar da saniyar shi domin idan ya sayar da abinci bai da abinda zai ci,saniyar kuma ba zata isha shi ba. Na uku, wanda za a kashe shine wanda yazo da wasikar."dafe kai Abrad yayi. Sabida sam amsar ba haka ban. A hankali akayi ta tafiya har aka zo kaina. "Idan muka duba dalilin da yasan manomi zai fidda kayan abincin shi da saniyar shi ba ƙaramin lalura bane, domin abincin nan idan yayi tattalin shi zata kai shi har kafin faduwar damina me zuwa, dan haka babu hujjar sayar da saniya, abincin zai raba gida biyu ya sayar da rabi tunda yayi noman a wadacce, saniyar kuma da ita yake aikin nomar idan ya sayar da ita bai da wanda zai miki kwaftu, saboda dan shi bai kai wanda zai iya noma ba, shi kuma karfin shi ya kare. Kuyi min hakuri na fara da amsar manomi ne.. A matsayina na Sultanah, aka wayi gari Sultan Mehran ya tafi yaki kuma bai ce min kome ba dangane da al'ummar shi, gashi akwai kayan abinci a cikin Baitul Malin masarautan! Zan duba soyayyar su da kaunar su ga Sultan Mehran,.zan saka ayi ta diban abinci cikin dare ana kai musu kofar gidajen su, domin ya rage musu zaman dar-dar da suke yi. Bayan nan idan suka gani washi gari addu'o'in su itace kashin bayan dukkanin mulkin shi da nasarar shi. Sai batun masu laifi, akwai wani dabi'a na mai laifi ban sani ba ko wasu sun fahimci haka, amma idan mutum ya aikata laifi yana iya fin kowa firgice, sannan da zaka saka kanka a kirjin shi bugun zuciyar shi yafi na kowa, sannan abinda na Fahimta shine Mai laifin da ya fahimci shi za'a kashe shine ya dauke wasikar wancan, badan kome ba yasa ni fadar haka sai dan hujjar da nake da ita. Duk yadda akayi mutane biyu da suke jajjayan nan sun bude wasikar su..shi na ukun su bai san meke faruwa ba, dan haka su biyu sun san meye a cikin wasikar su.daya ne za a kashe ba dukkansu ba." "Shin ko Ikram zata gaya mana taya zata iya gane mara gaskiya, duk da, sun kafe akan cewa wasikar su ne?" Amir Hood ya min tambayar. Dan mik'ewa nayi tare da gaishe shi, sannan nace mishi. " Bayyana nayi bayanin domin mara gaskiya duk inda yake zaka iya d'ago shi, idanun shi yana yawan budewa, sannan shi kansa baya iya tsayawa guri guda ba, jikin shi kuwa rawa yake yi, tsoro takan zame mishi shimfid'a akan fuskar shi. Bayan haka yafi kowa zakewa da rantsuwa." Na fada sannan na zauna sai lokacin na kalli Mehran da ya haɗa ya dunkule hannun shi, yana kallona, fuskar shi ta bayyana farin cikin shi. Dayawan dattawan gurin magana daya suke, yarinyar yayi kokari tana da basira. Murmushi nayi ina me jin dadin nasarar da na samu, a hankali.suka yi ta bayyana mana sakamakon mu, karshe dai aka bankad'o tafiya na da nayi shi ya saka ban samun damar tsayawa a.matan shi sai suka barni a shugaban Kwarkwarorin shi. Mikewa Fazilatul nisa tayi sannan tace musu. "Wannan sakamakon bai yi ba, dan haka Ikram itace matar Mehran, ko kuma allura ta tono garma.., *Toh fa wata sabuwa....* [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 35 Cikin fusata Sultanah Hoyam ta mike tare da kallon ta, cikin fushi mara iyakata tace mata. "Wacece ke da zaki saka mana ,doka Mu kuma mu bi?" Murmushi tayi tare da gyara zama sannan ta kalli Ikram tace mata. "Kin cika duk wata sharudan da ake bukata, dan haka kece yau zaki gana da Mehran! A matsayina na mahaifiyar shi, na baki shi gudan shi ba b'ari ba." Kallonta gabaki daya Emiraters councilors din, suka yi domin abinda suke gudu kenan shigar Fazilatul nisa cikin harkokin Masarautab,. Tunda da suka ji labarin bata mutu ba suka san cewa tabbas tana raye ne domin fansar ta, dan haka suka mike tare da kallon ta, kafin suka ce. "Mun amince Yaran mu zasu zama Kwarkwarorin shi, sanan muna rokon Sultanah arzikin karta bawa Ikram karfin da zata juya a kalar masarautan." "Karya ne, Mehran d'ana ne dan." "Bani da lokacin ki, Ita wancan Yarinyar nake da Muradin a bata matsayinta! Ko kuma hmm!" Fazilatul ta sake murmushin mugunta. Cike da mamaki nake kallon ta, domin dai nasan tana da nata Muradin idan ba haka ba, me zai saka ta kafe akai na. "Toh an bar mata matsayinta a bisa sharadi guda uku! Sharadi na farko dole ta kasance budurwan! Sharadi na biyu dole ta kasance yar da tafito daga Masarautan? Sharadi na uku karmu kama ta da wani kuskure ko muji labarin wani mugun abu yafito idan ba haka ba. Hmm!" Yayi wani irin murmushi hade da kumshe bakin shi, yana kallon ta. Murmushi yayi sannan yace mishi. "Insha Allah! Na yarda da Allah kuma na yarda da ita, kuma Allah zai bamu sa'a." Ta faɗa tana murmushi. "Shin wai ince wannan kika tsayawa? Wannan kika tsayawa? Lallai kina bukatar nazari. Amma lokaci zai nuna mana." Takowa tayi daga sama, inda take zaune ta tawo har inda yaƙe, sannan tace mishi. "Mir Umdatuddawla ko kana da matsala da ita ne? Dan naga Yarka Yasmin kake taya kishi! Duk wanda yayi magana tabbas yayi magana ina da yakinin Yar shi yake tsayawa kishi, dan haka kowa ya zuba ido." Shiru duk suka yi tare da sunkuyar da kai, sannan ta juya kai ta kalle ni. "Daga ranar da kika amshi matsayinki na Sultanah ina son ki shiga binciken sanadin mutuwar Abdus Samad, idan kika amshi ragamar Sultanah ina son ki bincika mike faruwa a cikin masarautan nan! Idan kika yi haka zaki taimakawa mijinki gurin bincike! Kina da damar tuhumar me yasa aka dakatar da mijinki akan muqamin sa? Bayan nan kuma ina rokon adalci daga gare ki na bi min hakkina akan kazafin da aka min. Ina tayaki murna." Daga haka ta juya daga gurin taron, tana me jin dadin ta wanke abinda yake ranta, tabbas tasan ba zasu iya dakatar da matsayin Ikram ba, kodan tsira da mutuncin su. Sannan ba zasu so asirin da suke aikatawa ya fito fili ba, dan haka ta barsu da tashin hankali. Domin kuwa matukar suka barta tayi magana. Zata iya fadar abinda zai daure su har karshen rayuwar su, dan haka suka yi farin ciki barin ta gurin dan tana magana da yawa, duk yan matan an kira su tare da karrama su.. sannan aka kirani daga karfe aka bani kyautar da yafi nasu, bayan na amsa ni dasu Izmah da Nimra muka bar gurin. Takawa Abrad yayi har gurin Mehran, ya kura mishi ido sannan ya mika mishi hannun, cikin girmamawa yace mishi. "Kana ta farin ciki zaka auri budurwa ko? Koda yake naji an cire gwajin budurci. Domin wasu yan matan zawarawa ne, idan kuma dattawan masarautan ka suka ji labarin Sarki Abrad ya tab'a kwanciya da ita fa? Hhhh koda yake shima wancan ai sauran Abrad ya samu. Ka tambaye ta, tun bata kai haka ba, na saka mata girmana jikinta kuma ta dauke ni cif. Dan haka kasan dole sai ta cika sharadin budurci ko kuma hukuncin kisa ya haura kanta. Itama zata so na rufa mata asiri dan haka ka ajiye a ranka zaka fara jin kararrawan tashin hankali. Matukar ina raye Ikram tawa ce ni daya." Kura mishi ido Mehran yayi tare da sunkuyar da kan shi kasa, yana jin kamar ya dauki takobin shi ya dauke mishi kai cikin tashin hankali yake murza hannun shi, kafin ya d'ago kanshi yana murmushi yace mishi. "Zan iya cewa haushin ka rasata yasa ake gaya min magana haka ba. Dan haka babu damuwa koda a gidan ƙaruwai na samo ta, tabbas zan zauna da ita." Cikin fusata ya kalli Mehran sannan yace mishi. "Tabbas zaka yi kuskuren da ba zaka manta ba, domin zan kashe duk wanda yake tare da ikram, domin ita mallaka ta ce" "Ina ga baka tab'a kowa Askandariya ka tambayi ina Yar uwan matanka take ba ko? Zanga yadda zaka iya hada kazamtar da kake shirin aikatawa." Daga haka ya juya tare da barin gurin, domin jin kirjin shi yake kamar zata fashe, yana shiga ya hango ikram daga nesa, wani irin tausayin kan shine ya kama shi. Meye laifin shi da kaddarar ta yake walagigi dashi? Me yasa ba za'a barshi ya huta da ita ba, sai tashin hankali da damuwa. Kura mata ido yayi yaga yadda take dariya da farin ciki. Ji yayi wani kamar zai fashe da kuka domin kuwa yana hango yadda Abrad ya kwanta da ita, tare da hango Yadda Numan yayi ta juya ta a shimfid'ar shi. Wato maza biyu sun keta mishi alfarman shi, sunci mutuncin shi sama da yadda ake cin mutuncin wani a duniya, da takalmi suka dauka suka dake shi da shi ba zai mishi ciwo irin wannan da Abrad yayi mishi ba, ji yayi duk wata alfarmar da yake dashi ya tsinke gani yake kamar duk wata mutuncin shi sun tsinka mishi. Duk da yasan tayi aure baya jin haka yayi mishi ciwo kamar yadda Abrad ya nuna mishi ya kwanta da ita..mafi kololuwar ɓaci rai da ya tab'a ji a ranshi kenan. Dan haka ya bar abin a ranshi kafin yasan mafita. *** Had'iye yawun Abrad yayi tare da juyawa yana kallon taron jama'a da suke watsewa. Ba dai Ikram Yar Joindah bace? . tabbas idan yarta ce ta haramta mishi, innalillahi wa'inna ilaihi rajioun me yasa haka ya faru dashi. Lallai dole ya dakatar da kome ya tsaya Domin rusa Mehran da ya ikram, idan ba haka ba tabbas zai yi biyu babu, ya kwadaitu da jikin Ikram, dan haka koda zai mutu ya dawo wallahi sai ya shiga ya mata faca faca da ruwan jikin shi. Wannan shine tunanin da ya tsaya a ranshi, dan haka yayi wucewar shi zuciyar shi daya..yana haduwa da Nawwas ya gaya mishi abinda ya faru. Ba karamin kaduwa Nawwas yayi na, tare da cewa. "Wallahi baka da kirki! Me kake shirin aikatawa? Yarinyar da babu aure a tsakanin ku shine zaka shirya mata mugun makirci haka..toh wallahi zan gaya mata gaskiyar abinda kake shirin aikata mata domin ta farga daga abinda kake shirin aikata mata ai wannan rashin imani ne idan kanwarka aka yiwa haka ba zaka ji dadi ba, dan haka wallahi dai na gaya mata idan ban sami ganinta ba zan gayawa Mehran dan yaji abinda kake shirya musu.. son kan ka yayi yawa toh wallahi ba zan tab'a barin ka, ka lalata musu rayuwa ba, tunda kai kana da naka rayuwar!" "Nawwas ni kake gayawa Magana? Toh naga wanda ya isa ya dakatar da ni." Ya faɗa da karfi, nan fada yaso kaurewa a tsakanin su, dakyar wasu daga cikin dakarun suka raba su. Cikin fushi Nawwas yace mishi. "Wallahi ina sane da kome da ka aikata, kyale ka nayi kawai amma wannan karon zaka sha mamakin abinda zai faru." Cikin mugu mugun fargaba ya kalli Nawwas, sannan ta danne abinda yake ranshi. "Na gina ka da hannuna, sannan Ni zaka kashe. Tabbas kai butulu amma zan baka lokaci ka nime yafiyana kafin na fusata akan ka." Inji Abrad. Dariya Nawwas yayi cikin takaici da haushi yace. "Wato kai har dama ake bani na nemi yafiyarka? Toh karka yafe min, ka zauna a gurin na kyale ka ne, amma tabbas idan akwai wanda ya dace da Ikram ni ne ba kai ba, domin ni na fara sonta lokacin da na sayo ta." Hannun shi ya saka a cikin aljuhun shi sanan ya ciro jakar kudin da Abrad ya bashi lokacin da ya tura ya sayo mishi ikram. "Wannan Shi ne, jakar kudin da ka bani, ita kuma da kudina na sayo ta, dan haka karka kuma alakanta kanka da ita, domin ni na barwa Mehran ita." .ihu Abrad yayi tare da kaiwa kasa duka, yana fadin. "Wallahi baka isa ba, Ikram tawa ce wallahi sai na kashe ku dukkan ku, akan Ikram sai kashe kowa domin ita tawa ce. Kai ma ka fara gudu domin na kyale ka zanyi ba." Wannan rigimar bata yi musu dad'i ba, domin karfi da yaji suka zama abokan gaba, kuma Abrad yayi alƙawarin sai ya kashe Nawwas shima kuma yayi alƙawarin sai ya fadi gaskiya kafin ya kashe Abrad. Da kyar aka fidda Nawwas daga cikin gidan, domin fadar sun tayi ƙamari Sosai. ~~~ Yana zaune yayi shiru tun da ya idaar da sallah, yake kallon waje yana son ganinta amma idan ya tuna zantuntukarka Abrad sai yaji kirjin shi yayi zafi, shigowar Fudail a karo na biyu ya sashi d'ago kanshi yana kallon shi. "Sultan MEHRAN! Ikram tana son ganawa da kai." "Kace mata ba yanzun ba." Ya faɗa fuskar shi a daure, "Toh sai yaushe Mehran?" Na tambaye shi lokacin da na shigo d'akin, juyar da kai yayi tare da cewa. "Ka fitar min da ita bana son ganinta." Ya faɗa tare da juya min baya. "Akan me baka son gani na? Meye nayi maka da zafi da kak'i kallona, ko baka so na zama abinda kake bukata bane?" Na tambaye shi muryana yana rawa, Mikewa yayi tare da nufo ni, bai yi wata wata ba, ya riko damtsen hannuna ya turo ni waje, sannan ta kalli Fudail shima ya fita dan baya son magana. Kasakai nayi ina kallon kofar Mehran, na rasa gane abinda Mehran yake nufi dani, kallon Fudail nayi domin shi daya ne kawai zai fidda Ni cikin duhun da nake ciki. "Karki ga laifin shi. Sultan Abrad yayi mishi wasu maganarki wanda ban san me ya gaya mishi ba." Bakina yana rawa na kura mishi ido, sannan na juya tare da barin shashin sa, na nufi inda nake da zama, a hanyar wucewa ta naji Kwarkwarah shi wato Sakeenatu binti Abu Waqqas tana faɗin. "Idan mace ta isa bata bin namiji shi yake binta" halin da nake ciki bana jin zai barni nayi magana kawai na kad'a kai nayi gaba abuna, sabida ba zan iya daukar tashin hankali biyu ba, ga nashi ga na wad'anda ban san kansu ba. .... Tunda na zauna nake kallon madubi, abisa ka'idar zan kai mishi abinda da kuma zama dashi dan hira, sai dai shigowar Sultanah ta zuba min ido. "Me yasa Mehran ya bukaci Jasrah bake ba." Murmushi nayi sannan nace mata. "Eh naje d'azun nan kuma gaskiya ni bana son na amshi ragamar shi sai ranar da aka daura min igiyar shi a kaina, su kuma suna da damar shiga gare shi. Tunda matar da zai aura ce ni kamata yayi nabi tsarin addini da na Ubangijin." Takowa tayi gabana, sannan ta zauna kamar yadda na zauna..kafin tace min. "Addinin ki da Ibadar ki yasani mishi kwadayin ki, idan ba wani abu me karfi ba,.nayi imani da Allah ba zaki juya mishi baya ba, domin kuwa babu kwaɗayin duniya a ranki don Allah ga Mehran nan ki tsaya mishi Insha Allah zaki yi nasara." Murmushi nayi domin kuwa ban san me zance mata ba, amma kuma ina tunanin zan mata yadda ta bukace ni. *Ana dara ga dare yayi....* [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 36 Kasa gane kan MEHRAN nayi kowa yana jin dadin mu'amala dashi ban dani, tun Fudail yana ƙoƙarin gano yadda zai magance matsalar mu ya kuma sassanta mu, abin yaci tura. A cikin kwana uku kacal Mehran ya nunawa kowa baya tare dani, domin kuwa Zanyi kokarin tinkarar shi domin magana yana gani na zai mike ya nemi hanyar barin gurin. Ko kuma yana gani na zai tsira fushi da b'ata rai. Bana jin dadin haka ko babu kome bai dace sabida Abrad ya gaya mishi magana ya nemi juya min baya, ranar da ya nime jasrah. Dan sai da tayi kwana uku a cikin turakar shi, kafin hudun ta fito, nan ne tana fitowa aka bata matsayin (Lady royal) tafi kwarkwarah ta kuma fi karfin a kirata da kuyanga, matsayi ne wanda yafi na kwarkwarah. Shi yasa tana fitowa ta fara gudanar da aikinta yadda ya dace. Abinda ta fara shine ta turo da wasikar lallai sai dai ina fitowa cikin su ina cin abincin. Sannan ta zab'a min bayi mata guda biyu, sannan ta turo min su. Ajiye takardan nayi sannan na kalle su, a tsanake kafin nace musu. "Nagode! Sannan ku gaya mata bana bukatar kowa, ina da yan uwana na jikina bana bukatar masu taimakona. Batun cin abinci kuwa kice mata shima na gode ni mace ce kamar zinariya baka cin abinci a gaban kowa sai wanda ya ajiye ni da kuma yan uwana." Haka suka fita abinsu, ban san me ya faru ba, sai gata tare da Mahlika. Suna zuwa basu yi wata wata ba, tasa aka rufe Izmah da Nimra da duka. _Dole zasu biyo ki! Musamman yadda suka fahimci kina da matsala da Mehran, kiyi kokarin dauke Kanki kansu_ inji Fudail. Dauke kai nayi haka suka musu lillis, kafin suka juyo kai. Tare da takowa har gabana, sauran matan suna bayan ta. "Na saka doka kuma dole kibi yadda nake son domin nice budurwan masarautan. Idan zaki ga Mehran dole sai kin biyo ta hannuna." Ban kalli inda suke ba, dan haka suka juya suka fita. Da sauri na isa gurin su Izmah zanyi magana tace min. "Karki damu, ai Sultanah ta gaya mana. Dole zaki fuskanci wannan yanayin, ta bamu hakurin mu tayaki jurewa, Babban matsalar ki kama Mehran a hannunki, idan kika kama shi har abada ba zaki kuma fuskarta matsala ba." Hawaye ne ya zubo min tare cewa. "Dole na nimo Abrad, naji meye ya gayawa Mehran haka?" Kallona suka yi sannan suka ce. "Babu Matsala a fitar ki? Don Allah Karki kuma yin abinda zai jefa ki cikin matsala." "Babu kome zanje ba zan jima ba. Kayanki zaki bani Nimrah." Had'iye yawun tayi sannan ta mike ta cire, sakawa nayi sannan na fita a saɗaɗɗe. Ina samun na bar harami na sauke ajiyar zuciya. Ban tsaya ba, sai masaukin su. Ina zuwa na sami Nawwas yana tare da wasu dakarun. Ka rasawa nayi gurin shi. Sannan nayi mishi magana. "Ikram!" Ya ambaci sunana da mamaki. "Ina Abrad?" "Yana cikin gidan!" Nufar hanyar cikin gidan nayi, ban tsaya ba sai da na dangana da cikin dakin da yake. Tun a bakin kofar shiga, na dauki takobin shi. Ina shiga na same shi da mace shi banyi wata wata ba, na saka mishi tsinin takobin a kirjin shi. "Meye ka gaya mishi?" "Dama nasan zaki zo aiki, abinda na gaya mishi kike son sani?" "Maganar banza nake son ji?" "Wannan kuma duk ke ta shafa, dan haka ina tayaki murna domin tarko na d'ana miki kuma yanzun haka Mehran yana bayanki! Zai zo ya same ki a cikin gidan nan." Cikin fushi na yanke shi da kaifin takobin, cike da mamaki yake kallona idanun shi waje. "Ko zaki kashe ni ba zan fasa gaya mishi magana ba, kuma zaki gani da idanun ki idan ya karaso!" Cikin mugun b'acin rai na kuma dukar shi da kasar takobin, abinda ya bashi damar riko hannuna, daidai lokacin da Mehran ya bude kofar dakin kenan.. shi kuma ya fisgoni na fada kanshi. Ya kuma yi amfani da karfin ya juyar dani akan idanun Mehran. Juyawa yayi tare da barin kofar d'akin, ina mik'ewa na kai mishi duka a gaban shi dai da ya suma..sannan na fita na damu yana tafi ko dokin shi yaki dauka haka Fudail shima ya kasa hawa kan dokin Nawwas yana bin shi tare da mishi magana. Amma bai kula shi ba. Da sauri na sha gaban shi. "Aamaan ka saurarre Ni, wallahi yadda kake tsammani ba haka bane." Dariya ya saka wanda tunda nake dashi ban tab'a ganin shi yana dariya ba, sai murmushi. Sosai yake dariya har da dafe bishiya. "Aamaan don Allah ka saurarre ni, wallahi nayi kuskuren zuwa amma kayi alakari da abinda ya baro ya kawo ni gurin shi." Kura min ido yayi sannan yace min. "Kiyi yadda kike so! Gashi nan nan da sati daya zaki koma inda ake bukatar ki." "Mehran me yasa kake son tilasta zuciyarka ganin laifin da ba nawa ba?" "Akan me ba Zanga laifin ballagaza karuwa makashiya, sha-sha-sha me kwanciya da mijin Kanwar mahaifiyarta? Akan me zan yiwa kaina adalci bayan ta sani kawo datti cikin masarautan da babu dad'i a cikin shi. Ke kazama ce. Wallahi da iya auren Numan kika yi zan yarda na zauna dake akan kwanciya da wancan kazamin, zaki iya tafiya. Amma karki yarda ki bar min kome da yafito daga hannunki." Ban tab'a ganin abinda ya sani kuka har na kasa hawaye ba, sai kalaman Mehran, yayi min zafi da ciwo. Ina kallon shi ya bar ni a gurin kuka nake sosai. Kamar raina zai bar jikina Mehran ya min mugun zato. Haka suka tafi Nawwas kadai ya zauna a kusadani yayi ta bani hakurin. Karshe haka na mike tare da barin gurin. *** Tunda na shiga cikin gidan ban kuma sha'awan fita ko kofar gidan ba, sai da naji labarin ana bikin maidawa Mehran kujeran shi, ban ko leko ba Kwarkwarorin shi suka yi ta bidiri, a lokacin Fazilatul nisa ta Fahimci akwai tashin hankalin a tsakanin mu, ta same shi ayi magana yaki bata lokacin shi sai uzirin da yayi ta kawo mata, ni kuma na kasa cewa kome. Ranar da akayi bikin da yamma Baƙi daga Merocco da Askandariya suka zo. Kukan da nake sabida farin ciki ya kasa misaltawa. Tunda suka shiga falon shi. Yake juye- juye, yana niman ta inda zata fito. Cikin shigar alfarma nayi sallama a katon falon shi. Suna zaune. Da sauri ya mike tare da nufar inda nake yana faɗin. "Salsabilah na." Rungume ni yayi tare da sauke ajiyar zuciya. Kuka ne ya kwace min tare da kai hannuna na rungume shi..ina kuka sosai. "Kiyi hakuri, gani nan nazo gare ki babu wanda zai kuma saka ki kuka kinji.". Jinjina mishi kai nayi tare da rike rigar shi. Kokarin danne tashin hankalin da yake ciki yake amma tabbas da ace mutanen gurin zasu Fahimci halin da yake ciki da su da kansu zasu bukaci Amir Rahil ya sake Ikram dan ji yake kamar kirjin shi zai fashe da tashin hankali. Zafin da yake ji ya hana shi sakat, dan haka ya dauki ruwa ya shanye tass, sannan ya dauke kanshi daga gare su. Janye jikin nayi tare da kallon yan uwa da dangin mu, zama nayi a kusa da sultanah Amrah,. Wacce kamar ta daya da Ummyn mu, zama nayi ina me jin kuka yazo min tunda na kifa kaina a kafad'arta nake kuka, domin nayi imani da Allah idan na tafi ba zan kuma dawowa SAMAIND ba. "Ya isa haka?" Ta faɗa min a sanyayye, Wazir din Merocco ne ya fara bayani a hankali tare da girmama juna, sannan ya kuma faɗa mana makasudin zuwan su. "Alhamdulillahi mun gode Sultan Mehran, gashi zamu dauke maka ita, sannan muna me baka hakuri abisa abinda zamu gaya maka. Mun yiwa Ikram Miji Amir Rahil. Wanda shine Sarkin mu na gaba, dan haka zaka yi hakuri da yadda muka zo a makare." A razane na d'ago kai na, ina kallon Rahil da yake ta zabga min murmushi. Sannan na maida kai na, ga Mehran wanda ko a jikin shi babu abinda ya dame shi. Cikin dakewa ya kalli inda nake amma kuma zuciyar shi sai girgiza take, sannan ya fesar da iskar bakin shi kafin tace musu. "Babu damuwa! Allah ya bata zaman lafiya..Insha Allah nima zan so zuwa bikin" Kura mishi ido nayi hawaye na zuba daga cikin idanuna. Ina kuma kallon shi. Dani zai yi Yakana??? A kaina zai saukar da YAKANA?? Wato sabida rashin adalci ya gwammace ya hakura da aurena saboda na tab'a mu'amalantar wani da namiji, rike hannun na, Sultanah Amratu tayi tare da cewa. "A duk lokacin da muka ga hawaye a kan idanun jama'ar muna da yakinin suna cutuwa ne da mulkin mu. Amma idan aka wayi gari munga wahale akan sarauniyar mu, tabbas muna da yakinin abu biyu ya sata kuka. Farin ciki da bakin ciki,. imma soyayya mara iyaka,.indai akwai daya cikin biyun da nayi magana akai toh wajibi ne Ikram tayi hakuri tare da YAKANA!" Yadda take maganar babu wanda zai fahimci magana take sabida yadda take yi a sanyayye, share kwalla nayi sannan.. na sake mata murmushi, kafin muka nufi cikin gidan. Muka shiga hada kayana,. Ita kuma Sultanah Amrah ta nufi Shashin Sultanah Fazilatul nisa, anan suka shiga hira, mazan kuma aka kai su masaukin su. Banda Rahil da yace babu inda zai je, ina zaune ya turo naje. Tunda na isa gurin a bakin wani tafkin da agwagi suke wanka, muna zauna dashi. "Tun bayan tafiyar ki nayi ta jinya." "Toh Sannun;" Rau-rau yayi da fuska, kamar zai fasa ihu. "Na zata zaki tambaye ni akan me nayi jinyar?" "Toh kayi hakuri, ?gaya min akan me kayi jinyar." Dariya yayi sannan yace min. "Akan sonki mana" kallon shi nayi domin banyi mamaki ba, amma kuma ni bana jin wannan yanayin a tare dashi, ji nayi kamar ana kallon mu na juya. A hankali, sake labulen tagar shi yayi. Nima a sanyayye nake kallon ruwan gabana. Ina me jin zafi da ciwon abinda ya faru. --- Kallon yake tun da suka fito yake kallon su, bai tab'a ganin mutanen da suka dace da juna kamar Rahil da Ikram, a hankali ya sauke ajiyar zuciya bayan ta juyo tana kallon shi, sake labulen yayi.sannan ya kalli Fudail ya ya jima da shigowa. "Me yasa kayi shiru ba tare da ka gaya musu yadda kake kaunar ta ba? Me yasa ka xabi'a YAKANA akan kaunar da kake mata? Wannan babu adalci.". "Ya isa haka. Karka manta na ce maka na rabu da ita, na rabu da ita har karshen rayuwata, dan haka karka kuma kawo min batun wata Ikram." Ya dakawa Fudail tsawa, ka rabu da ita kake leken ta? Ka rabu da ita ka gaza rike hawayen Soyayya! Dubi Cikin idanunka zaka Fahimci itace muradinka don Allah karka kashe abinda ba zaka iya raya shi ba. Zaka iya kashe so amma raya shi nada matukar wahala, don Allah karka rabu da ita, ka koma ka gaya musu ita ce zab'inka zasu Fahimce ka." Kamar ya daki Fudail yake ta huci, shi dai bai fasa ba kuma bai daina gaya mishi gaskiya ba, har dai da ya kore shi daga dakin sannan yace mishi. "Kaje ka aure ta, na yafe maka ita." Dariya Fudail yayi sannan yace mishi. "Tun duniya na kwance naso aurenta Allah bai nufa ba dai yanzun da nasan tana cikin zuciyar Mehran. Kawai kayi wani abu a gyarota." "Ba zanyi ba! Ba zan iya ba. Ba zan tab'a yarda na zubda kimata ba dan haka ka barta ta tafi. Ni dai na yafe Ikram har karshen rayuwata. Ta zalunci rayuwa ta, ta lalata min rayuwa,tayi nasarar jefani .... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 37 "Wani irin rayuwa ta lalata maka? Wannan ni banga wani laifin da kake danganta da shi ba, sabida ai a baiwa tazo masarautan nan, kai kana da tabbacin." Kasa fadar abinda yake son ya faɗa yayi tare da kallon Mehran dan yasan maganar ya yi mishi girma. "Ba budurcin ta nakewa hidima ba, itace nakewa hidima. Idan har zan iya hakura da shugabanci na, domin laifinta an kansa bata da abinda zan iya samun a gare ta fansan abinda na rasa, kawai na hakura da ita ne." Ya faɗa a sanyayye. Sannan ya juya, yabar gurin baki daya. ~~~ "Sultanah ga koshi ga kwanan yunwa, domin kuwa nasan Ikram na barin SAMAIND Za'a daurawa Sultan Mehran Jasrah abinda ake gudu zai faru." Inji Narjis. Cikin dakewa tare da ɓoye tashin hankalin ta, ta sake murmushi sannan tace mata. "Allah yana tare da Mehran, shi yasa koda an ɓullo mishi ta wani gurin ,zai kauce ta wani gurin. Ita kuma Jasrah karki damu da ita." Ta faɗi haka tare da ɗauke kanta. Wato kuka take son yi, amma bata son Narjis da Shairah su karaya,. Balle shima Uban garin yaji labarin. Kasa dannewa tayi ta mike zuwa ban daki ta zauna tare da fashewa da kuka. Kuka irin me tab'a zuciya da ruhi, kuka take tare da jin ina wannan ranar bata zo ba,.me yasa Ƙaddarar su take da zafi ne haka? Ga baki daya bata da inda zata kama tace gashi shine mafita a gare ta. Tana ji tana gani zata kuma rasa Ikram, a hankali ta wanke fuskarta tare da fitowa d'akinta, ta same su. Suma kuka suke, cikin juriya ta zauna tana kallon su. "Idan Allah ya baka lafiya sai kai ta jin dadi da farin ciki, idan kuma ya baka Arziki baka da kwanciyar hankali, idan ya baka mulki kai da farin ciki har abada. Gashi ya bashi kome amma ya hana shi farin cikin rayuwar shi, soyayyar da yake riritawa itama ta subuce mishi. Mulkin da yake kai ya rasa, dukiyar da yake da ita bata amfane shi da kome ba, sai tarin tashin hankalin da damuwa. Ita da nake ganin itace kwarin gwiwar shi ashe ba haka bane.." ta karshe maganar cikin rawan murya alamar zata yi kuka. Duk wanda yake dakin sai da ya zubda kwalla. Dan haka suka zube gwiwar su a kasa suna kuka. Murmushin tausayin MEHRAN tayi sannan ta juya tare da cewa. "Ku kira min Ikram" Da sauri Narjis ta fita. ...“Mace idan ta isa mace ta zauna a daularta ba sai ta biyo namiji ba, amma ayi mace mara daraja da kima, don Allah ku hada kaya ku koma can." Kallon Yesmin nayi sannan na sake murmushi kafin nace mata. "Zan bar muku Aamaan Abdus Samad Mehran na biyu, zan tafi na barshi kamar yadda nazo na same shi." Dariya ne ya kwace min sannan na cigaba da cewa. "Idan na tafi kunyi ban kwana da farin ciki, kun daina ganin dariyar shi da murmushin sa. Kuma ai dama ba ma'abocin yi bane dan haka sai kinyi danasanin mara amfani." Shigowar Narjis ya sani kallonta, kafin na juya zan tafi tace min. "Amirah Ikram!" Juyawa nayi tare da amsa mata. "Sultanah tana mahaifiyar Sultan Aamaan Mehran, tana son ganawa dake. Sirikae mafi soyuwa a zuciyar Sultanah Fazilatul nisa" .kallon Jasrah nayi sannan na juya kai na, kafin nace musu. "Mulki ya haife ni, amma yadda nake jin shi ko kuda aka haifa cikin masarauta ba zaku nuna min mulki ba. Uwar Mehran! Mahaifiyar Aamaan Mehran take don ganawa dani. Daga mahaifiyar shi sai ni kaf daular nan babu wanda ya isa ya kira shi da Mehran! Dan haka kadangarun bariki bani da lokacin da zan b'ata akan shi ina kishi. Duk macen da bata had'a zakuna a gabanta suna yaƙi akanta ba. Sunanta lusara jakar mata macen da ta isa da kanta take haɗa zaratan maza! Ko yau Mehran bai isa yace na biyo shi dan soyayyar shi ce, kudirina ya kawo ni gare shi bayan haka bani da wani abin da zan ce nazo daukar daga gare shi." Ina gama gaya musu haka, na fita tare da barin su a gurin suna mamaki na, nauyin da yake raina na sauke tare da jin nutsuwa a raina, sannan na Barsu da kallona. Har muka b'ace. "Ne yarinyar nan take nufi? Wato duk cikin mu babu wacce zata iya kiran shi da Mehran." Inji Sawda, "Ga alamu nan, dukda nasan na tab'a haduwa dashi amma ban sami zarrar kiran shi da Mehran ko Aamaan ba, amma kiga ita yadda take kiran sunan shi gaskiya Sultan Mehran ya bata dama dayawa." Inji Yasmin. Jasrah bata ce musu kome ba, amma kuma a hankali take fuskarta abinda suke tattaunawa, ita dai tasan ko kwanakin da tayi a dakin shi bata iya d'aga kai ta kira sunan shi ba, a iya kwanakin da tayi bata da wani sabon abu da zata iya nunawa nacewa yana tare da ita, domin duk zamanta a dakin babu abinda ya haɗa su. . Sai tausa da bashi ruwa da wasu labarai har ta cika kwanakin babu abinda zata ce gashi ya faru a tsakanin su. Shi kuma dan ya tuzira Ikram ya bawa Jasrah damar zama wani abu a jikin shi sannan yace ta iya da bakinta ta nuna cewa kome a tsakanin su ya faru, sannan ya tara mata manyan gwala-gwalai ya sallame ta dashi tare da bata wani babban daki wanda ya kusan kai na Ikram girma. Duk yayi haka ne dan ya tinzira ikram, kuma ya yi nasarar haka, domin kuwa ranar da tafito take farin ciki tare da habaici. Kasa barci Ikram tayi, kuka kuwa dannewa tayi tayi, a cikin daren sau uku tana zuwa turakar shi yana cewa ace yana aiki ne ta tafi sai ya sami lokaci zai kirata. Har yanzun yau da yaki sauraronta, tana jin zafin haka balle kuma da ya kamata da laifin zuwa gidan Abrad. Shi yasa yaji ta bashi haushi baki daya, yaji ya tsane ta baki daya, baya kaunar ganinta koda wasa, amma kuma haka bai hana shi jin tashin hankali da damuwa ba, domin kuwa yana jin ba zai iya hakuri ya rabu da ita ba,.idan ya tuna abinda take aikatawa sai yaji kamar ya cire zuciyar shi ya huta domin kuwa yana zaune kalau ta haɗa mishi tashin hankalin da bai taɓa kawowa a rayuwar shi ba. ...... Koda muka isa dakin Sultanah, Narjis ta gaya mata abinda matan suka min. Murmushi tayi sannan tace mana. "Ita ikram kallon su tayi bata ce musu kala ba?" Sunkuyar da kai kasa tayi tare da rike hannunta tace mata. "A'a ai tana da kaifin basira ta gaya musu abinda ba zasu iya ba koda zasu shekara dubu da Sultan Aamaan Mehran" "Hmm!" Tace tare da kallona ta nuna min guri na zauna, shayi ta mika min. Na amsa cikin nutsuwa tare da cewa. "Nagode!" Kurb'a tayi tare da kallona. Ina juya kofin a hannuna, nakasa sha. Kallon fuskana tayi tayi. Ganin yadda damuwa da firgici ya cika kanshi tam. Murmushi tayi sannan tace min. "Baki son komawa gida ne?" Da sauri na d'ago kai tare da kallonta, sannan na maida kaina kan kofin nace mata. "Ina son komawa!" Shiru nayi nakasa koda furta kalama daya ne. "Gaya min meke faruwa?"ta kuma tambayana, "Laifi na mishi wanda har ta kai ya tsane ni a duniyar shi!" Na faɗi haka ina jin kamar na fashe da kuka. "Kina son shi ne?" Da wani irin sauri na d'ago kaina, girgiza mata kai nayi sannan nace mata. "Kallon Ɗan uwana nake mishi ban tab'a jin son shi ko kaunar shi a rai na ba." Na fadi haka kamar zanyi kuka. "Wato keda shi kuna kokarin kashe junar ku, wannan lafazin zai iya tab'a darajar ku keda shi. Amma babu damuwa, Allah yasa hakan itace mafi alkhairi. Amma ki sani zamu yi kewar ki ni da sauran mutanen cikin gidan nan!" A hankali na mike tare da mata godiya sannan na fice daga dakin. A hanyar d'akinta muna hadu ni zan fita shi kuma zai shigo. Kallon juna muke tare da kasa furtawa juna koda da kalmar sannun ce, karshe sai gashi mun tsincin kan mu da kasa bawa juna hanya idan ya kuma gefe nima zan koma gefe,. .idan ya tsaya zan tsaya karshe ture ni yayi gefe ya shige abin shi ina kallon shi. Wannan wacce irin rayuwa ce haka? Meye nayiwa Mehran da ba zai yafe min ba yake bani wahala har haka? Zan tafi zan yi nesa dashi yadda zai gane bani da laifin da yake zargina, amma tabbas Mehran ya zalince ni sosai. Babu kome Allah zai bayyana gaskiya koda bana tare dashi. Duk tsawon lokacin da na dauka, da fansar da nace zan dauka na ƙasa daukar haka sabida Mehran yau gashi sabida abin da yake da yakinin bai faru ba, ya kirani mazinaciya, karuwa, datti,shara, bolar kowa. Share kwalla nayi tare da barin kofar d'akin, na nufi hanyar da zai fitar dani, Fudail muka ci karo. "Ikram yanzun ɗan uwanki yake ta niman ki kamar wani karamin Yaro." Murmushi nayi sannan nace mishi. "Rahil rigima!" Har zan wuce yace min. "Kiyi hakuri! Kishi yake damun Sultan Mehran, amma kece rayuwar shi." Ganin shi muka yi a gaban mu, jikin shi yana kerma. "Waye kake magana akan shi? Ni Allah yayi min tsari indai ni ne, wannan itace rayuwata? Kishinta nake?" Riko hannuna ya yi tare da jana zai kai ni cikin Kwarkwarorin shi ya tozartani. Sai ji nayi an rike hannuna, tare da fisgo ni. Dukkan mu a tunanin mu Fudail ne. Amma abinda mamaki Amir Rahil ne. Cikin b'acin rai,.wanda tunda nake ban tab'a ganin shi ita ba. Fuskar shi har wani jajja jjaa tayi. Ya karasa takowa gaban Mehran ya. ya janyo ne jikin shi tare da sakala hannun sa a kafadana, yana kallon Mehran. "Ba zaka wulakantatta ba, matukar ina raye. Muje Salsabila ke kadara ce me tsada baki yi wannan arahan nan da za a tozartaki ba. Dan haka muje cikin Zuri'ar mu kiga yadda ake kaunarki. Mulki yake yawo a jininka shi yake yawo a jininta. Ya zaka ji idan na gaya maka ita kanta Sultanah ce a kasar Masar! Ya zamani idan mace maka ita Sultanah ce a Merocco. Dan haka karka tozarta ta, domin zan iya sare hannunka." Ya faɗa mishi yana kallon cikin idanun sa, juyawa muka yi tare da fita daga gidan baki daya. Kukan da nake rikewa ne yazo min, sosai nayi tare da kifa kai na a kirjin shi. Har muka isa masaukin su, anan ya ajiye Ni a dakin shi, yayi ta min hira tare da bani labarin abinda zai sani da dariya. Nayi kokarin koran b'acin rai da damuwa, akan fuskana amma a zuciyata kawai ina jin babu dadi. Dan haka nayi ta biye mishi muna ta hira har ya ga nasake ina dariya. Tausayi ya bani sabida yadda yake nuna min so ba karya bane, kaunar da yake min yana shimfiɗe akan fuskar shi. Dan haka yake kokarin sai ya sani dariya kota halin k'ak'a. ~~~ Har suka bar gidan yana tsaye kamar gumki, idanun shi jajjur. Dan ji yaƙe kamar an tafi mishi da zuciyar shi, niman faduwa yake. Fudail ya rike shi. Kallon shi yayi sannan yace mishi. "Sultan MEHRAN! Kayi kuskure babba. Duk abinda za a gaya maka akan Ikram bai dace ka dauka ba, sannan itama kanta taje taji meye ya faru har ka tsane ta haka. Mehran ko yanzun haka Nawwas yana jiranka zai maka bayanin abinda ya faru, amma ka sani sai ka cire wannan tsanar da kake mata, tare da fahimtar wacece ita. Sai ka haɗa abinda ya gaya maka da mahaunin hankali matukar kace ba zaka yi haka ba, tabbas yanzun ka fara nadama, domin zaka yi ta kuka har karshen rayuwar ka...... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 38 Kallon Fudail yayi cikin damuwa, amma kuma idan ka kalli yadda ya ɓoye haka zaka iya rantsewa har da Allah babu kome a ranshi, Mehran yana cikin mutanen da Allah yayi musu baiwar ɓoye damuwar su, zai yi wuya ka zauna dasu su ka gane akwai damuwa a tare dasu dan yana da irin zurfin cikin nan ne wanda idan ba shi yayi magana ba ba, ba zaka yi yarda ba. Sannan yana iya ɓoye abin a ranshi ba tare da ya gayawa kowa ba, yayi ta cin shi ba tare da kowa ya fahimci haka. Ko Fudail yana saurin d'ago shi ne ta hanyar tsananta binciken motsin shi. Wannan d'anyen halin nashi ba karamin damun Sultanah FAZILATUL gani take kamar da gayya yake k'in faɗa mata, ita bata damu da kanta ba, koda wani zai iya gaya mishi. Amma fir yaki nuna damuwar shi sai dai ya rufe kanshi a daki yayi ta zaman kunci. Duk lokacin da ya shiga wannan yanayin, kowa yana shiga damuwa. Shi yasa basu son Ikram tayi nesa da shi. Kuma da alamu haka ce zata faru, tunda ya kasa furta kalmomin da ya dace, gashi nan danginta zasu tafi da ita. Juyawa yayi yana kallon waje. Kalmomin Abrad ne yake yawo a kunnen shi. _Ko mijin da ta aura ba zai iya cewa shi ya dauke abinda kake hari ba! Ka tambaye ta ni na fara kwanciya da ita! Ni na bude idanun ta. Ni na nuna mata yadda namiji yaƙe_ Rintsa idanun shi yayi tare da jin bakin ciki dama da kullum, ji yaƙe kamar ya cire zuciyar shi ya huta, ga baki daya ya tsani kanshi da Abrad ina ma da yana da damar kashe Abrad tabbas sai ya kashe shi. "Sultan!" D'aga mishi hannu yayi tare da cewa. "Bana son ganin shi." "Amma wannan kuskure ne kake tafkawa, kana kuskure ne babba. Me yasa ba zaka Fahimci yarinyar nan ba? Me yasa ba zaka gane meke faruwa ba, Idan abinda kake zargi haka ne me yasa ba zaka ajiye shi a wani guri na daban ba, kake kuntatta mata da hanyar da bai dace ba! Gaskiya baka mata adalci ba. Shi kenan Allah yasa haka shine mafi alkhairi ga sakon daga Fada Amir Hood ya baka auren jikar shi. Amma sai nan da wata uku zuwa huɗu. Tunda sun sami labarin Ikram an mata bai ko da Amir Rahil. Allah ya tabbatar da alkhairi." Daga haka ya juya tare da barin d'akin, tunda ya fara magana bai juya ba, har sai da ya bar dakin sannan ya juya yana kallon kofar tabbas yana son ganinta. Yana son jin meye ta sauke shi. Yana son ganinta kome dare ba zai ya fita da rana tsaka ba, dole ya fita cikin dare ya isa gare ta. Amma kuma meye makomar shi. Ajiyar zuciya ya sauke tare da dauke kanshi kasa. Yana shafa kan shi tare da murmushi. ~~~ Kasa magana nayi ina kallon yadda Sultanah Amrah take kallon Nimrah, mayar da Nimrah baya nayi. Sannan na tsaya a gaban ta, nace. "Kiyi hakuri Ummyn, bata da laifi. Kuma nasan ke me adalci ne." Dakatar da ita tayi ta hanyar d'aga mata Hannun, tare da kura mata ido. "Ban ce zan mata kome ba, amma ina tsoron abinda Mahaifiyarta tayi mana ne, domin ba lallai bane ta fahimci abinda ta aikata." "Insha Allah, Nimrah ba zata aikata kome ba, wallahi ki yarda dani bata da wannan tunanin a ranta ban dai sani ba, amma babu wannan karsashin a ranta." Haka nayi ta lallab'a Sultanah Amrah kafin ta sake jiki, tana kallona daga lokaci zuwa lokaci. Musamman idan ta fahimci na shiga yanayin damuwa,.sai ta ce min. "Kina son zama da Mehran ne?" "A'a nafi son zama daku." "A'a Ikram bamu shiga hakkin ki ba?" "A'a" nace tare da mik'ewa zan bar dakin domin na tsani hirar da zata kawo min zancen Mehran. Shi yasa bana son zama koda su Izmah ne domin rabin hiran su akan shi suke min. A waje na hadu da Rahil ya kawo Abrad, dan haka ban yi mamaki ba, dan nasan yazo gaida Ummyn ne, har cikin gidan ya shiga suka gaisa, sannan suka shiga tattaunawa akai na, wanda duk hiran akan yadda ake shirya min tarb'a da bikin da za ayi mun ni da Rahli. Bai ce komai ba, amma daga yadda ya rasa nutsuwar shi har ya gama hiran da ita, muna zaune a harabar masaukin. Zama yayi a kusa dani tare da zuba min ido. Dauke kai na nayi daga gare shi sannan na cewa Rahil. "Ina son zan sha madara! Amma bana son bayi su kawo min" na fada cikin sakakkiyar murya. Mikewa yayi tare da cewa. "Zauna ki huta mata na, ba zata tab'a wahala ba. Domin ita din sarauniya ce zan kawo miki." Ya faɗa tare da nufar hanyar cikin gidan. Gyara zama nayi sannan na kalle shi. "Kayi ƙoƙarin raba ni da Mehran, ka dasa mishi k'iyayyana. Sai dai kayi kuskuren mafi girma domin kuwa kayi abinda ba zai tab'a barin ka ba, daga yanzun daga wannan lokacin ka fara boya, kayi ta gudu karka tsaya. Domin tsinin takobin shi sai ya huda kirjin ka. Ka fara gudu karka tsaya inda zai same ka. Nayi danasanin fadawa hannunka, domin babu wanda ya kashe ni da rayuwata sama da kai. Babu wanda ya lalata min rayuwa sama da kai. Sannan sauran da yarage kazo zaka lalata min su! Meye nayi maka da zafi? Meye na tsare maka da zafi haka? A sanina ka auri Kanwar Mahaifiyata toh meye kake son daga gare Ni? Amma masu iya magana since idan ajali yayi kira ko ba'a ciwo za aje." Daga haka na mike , rike hannuna yayi cikin zafin rai na tsinka mishi mari sannan na wuce abuna, duk akan idanun Amir Rahil ne, ina shiga ya zuba min ido. "Meye ya haɗa ki dashi? Meye Matsalarki dashi? Yau zan dakatar da shi." Gudun kar a kuma aikata abinda Ya faru yasani rike shi tare da kallon shi nace. "Karka damu. Ya wuce na koya mishi yadda ake mutuntawa." Murmushi yayi tare da mika min madaran muka shiga zaga gidan, wai duk sabida kar na saka damuwa a raina. "Wai dama an miki baiko da wancan basamuden ne?" Kallon shi nayi tare da murmushi kafin nace mishi.o "Eh amma kuma sawun giwa ya badda na Raƙumi ba" shima kallona yayi sannan yace. "Ban gane ba?" Murmushi nayi a karo na biyu, sannan nace mishi. "Zaka gane mana." Dariya yayi sannan yace min. "Amma kuma" "Amma kuma me?" Na tambaye shi, "Amma kamar kuna son juna da wancan basamuden?" "Me ka gani?" "Kin dawo min da tambayana" "Kamar ya?" "Kamar yadda na gani da idona" "Lallai kayi kuskuren" "Banyi kuskuren ba sai gaskiyar da na hango." Kasakai nayi ina kallon shi.kafin nace mishi. "Babu wata soyayya a tsakanin mu, kawai kana ganin haka ne amma ban ga!" "Da gaske baki son shi?" Ya tambaye ni, tsayawa nayi ina kallon shi. Tambayar da yayi min iya gaskiyar shi ce, amma kuma bana jin zan bashi amsar wannan tambayar dan haka na juya tare da barin shi a gurin, bakin ruwan da yake gudana a gurin na isa sannan na zauna tare da saka kafana ina nazarin maganar da muka yi da Rahil. Zama yayi kusa dani, sannan yace min. "Kiyi hakuri da sakaki surutu da nayi, sai dai kowani mutum me hankali da sanin ya kamata zai so ya ajiye irinki a gefen shi ko badan mu'amalar aure ba, ana bukatar mutum ya ajiye mace irinki na farko zaki bashi garkuwa, na biyu zaki bashi farin ciki a rayuwar shi, na uku kuma..." Murmushi yayi sannan ya cigaba da cewa. "Sai nan gaba zaki Fahimci abinda nake nufi" Girgiza kai nayi sannan na juya tare da kallon cikin ruwan, ina jin babu dad'i domin Allah ya gani son Ƴan uwantaka nake mishi ba son kauna na aure ba, kuma ba zan iya bijirewa iyayen mu ba, tunda abinda suka yanke kenan. Amma ko ya ya bai kamata su zartas da hukuncin haka ba, idan suka yi dubi da ni bakuwa ce a cikin su. "Ikram ko na takura miki ne?" Ya tambaye ni cikin damuwa, "A'a baka takura min ba, sai dai kana da hawa kai" na fada ina kallon shi, "Toh kiyi hakuri! Ban san yadda zan nuna miki farin cikin da yake raina bane, amma kuma ina jin nutsuwa a zaman mu nan."ya faɗa cikin sanyin murya, duk sai ya bani tausayi, tabbas akwai matsala domin nasan dai ba zan hada maza biyu ba, amma kuma yadda Mehran yayi min ban ji dadi ba, dan haka na juya ina wasa da ruwan. Kasa hakuri yayi tare da zama kusadani kamar zai shige jikina, kallon shi nayi kafin nayi magana ya jingina kan shi akan kafadana, tare da riko hannun na, yana me matsawa a hankali. ...... Ya saba da ganinta tana sintiri dan haka yau da bai ganta ba, duk sai ya damu dukda ya ganta lokacin da ta fito dakin Sultanah, amma kuma zuciyar shi da ruhin shi suna begen ganinta, ƙwaƙwalwar shi tana yawan hango mishi.wasu abubuwan akanta, dan haka ya mike tare da sauya shiga izuwa kayan dakarun kasar ya fita daga gidan. Gidan bakin dake cikin masarautan ya nufa, tunda ya shigo ya hango yadda suke zaune da Abrad, sai yaji kamar ya koma, amma kuma ya fasa bayan ta gama gayawa Abrad magana yana mamakin yadda take iya sarrafa maza, dan yasan haka kawai ba magana me dad'i ta gayawa Abrad ba. Bayan fitar Abrad, ya hango suna magana da Rahil. Sam Mehran bai dauki Rahil a wani namiji can ba, amma ganin yadda Rahil din yake ta damunta da surutu sai yaji tsoron kar abinda ta rasa a gare shi ta samu a gurin Rahil tunda soyayya ta tasa kuma idan ta samu a gurin Rahil shi bai da wani abun da zai gwada mata. Suna tafiya yana bin bayan su har gurin ruwan. Duk da bai san meye suke fada ba. Amma kuma tabbas abinda suke fada akwai muhimmanci dan haka ya nace sai yaji abinda suke fadi. Bayan ya matso ne yaji lokacin da Rahil yake gaya mata kowani namiji zai so samunta a rayuwar shi. Take hankalin shi ya tashi domin shi ya dace ya fahimci haka, amma baƙin kishin sa Ya saka shi kasa fahimtar kome akan haka. Yana kallon su har ya daura kanshi a kafad'ar ta, a lokacin sai da yaji kamar zuciyar shi zata dirko daga kirjin shi domin babu abinda ya tsana kamar yaga namiji a jikin ta. Yau gashi akan idanun shi wani yake jingina kanshi a kafad'arta. Ji yayi kwallar bakin ciki ya cika mishi ido. Dan haka ya juya tare. Da barin su a gurin tabbas bai da sa'a shi yasa ya rasata a karo na biyu,a da yana tunanin ya sami kanta ko bai gaya mata yana sonta ba, zata iya furta mishi ashe hasashen shi ce, ba tunaninta bane. Bai yarda da abinda Sultanah ta gaya mishi ba sai yanzun da ya gani da idon shi lallai yayi sake d'an zaki ya girma yayi kuskuren barinta ta rayu da wani, da tun lokacin ya kafa gwamnatin shi babu wanda ya isa ya rab'e ta, amma ya zauna sai tsanarta mata amfani da yake ji. Da wannan tunanin ya bar masaukin.. Haka kawai naji kamar Mehran ya zo har inda nake dan haka ba juya tare da kallon wani badakare yana tafiya. Haka kawai nake mishi kallon kamar Mehran ne, har na juya zan cigaba da wasa da ruwan sai kuma naji bari na kuma juyawa dan kamar yana kallona, koda na juya yana nan a tsaye. Sannan ya kasa tafiyar shi. [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 39 Juyawa nayi sabida idanuna da suke min gizo, a hankali kwalla suka cika min ido. Tabbas Matsayin Mehran Babba ce a zuciyata ya, shi yasa na kasa Mantawa dashi. Saka hannun shi yayi tare da tare kwallar da take sauka akan fuskana. "Waye ya tab'a min ke?" Murmushi nayi tare da goge kwallar nace mishi. "Ina kewar Airan ce, kuma kaga dole nayi kuka domin itace kawai ta rage min gashi ba rasata ga kuma Allah ya bayyana min dangin mu." "Ikram!" Ya ambaci sunana a hankali yana kallona, sannan yace min. "Bana raba daya biyun kina tunanin Mehran ne" Kura mishi ido nayi, da gaske haka ne amma kuma ɗan na karya ta abinda yake tunani a kaina yasani faɗin. "Tir wannan wacce irin magana ce? Na rasa wanda zanyi tunanin shi sai mutumin da bai da wani amfani a rayuwa ta, kawai dai kana zargina ne, amma idan ba haka ba me zai sani tunanin Mehran." Cikin fushi na mike zan bar gurin, riko hannuna yayi tare da zaunar dani. "Kiyi hakuri!" Ya faɗa min a sanyayye, sannan yace min. "Dole naji babu dad'i, babu namijin da zai so yana yana tare da mace amma zuciyar ta yana ga wani mutum na daban, Kinga kuwa zai cigaba da ganin haka kamar rashin adalci ne." Tabbas ya bani haushi amma kuma yana da kyau na tausaya mishi domin gabaki daya ya addabi rayuwata da naci, dan haka na sassauta fushina nayi sannan na zauna ina kallon shi. "Ke kamar Uwace a gare ni, kin bani kwarin gwiwar da na rasa akan me zaki yi fushi da Ni? Bayan ke bani da wanda zan ƙalla nace shi Masoyina ne. Amma ke kuma na ambace ki da kalmar me tsada da girma,don Allah karki yi fushi da d'an uwan ki." Na rasa me zance domin duk wata kalmar da zai yi amfani da ita,rudurduga min zuciya take, duk wata harafin da zai ambata kamar kunawa zuciyata huta yake, gabaki daya sai naji ba zan iya ganin shi cikin rashin nutsuwa ba, zan amshi auren shi duk da ina da zab'i amma kuma shi din zab'in kakanni na ne, hannuna yakai fuskar shi sannan yana faɗin.. "Ki dube ni da idanun rahama, karki juyawa tayina baya" Hawayen da nake b'oyewa ne suna sauko a hankali tare da kura mishi ido, tabbas kome ya kare min dan haka na rike hannun shi tare da cewa. "Ba zan tab'a juyawa tayin ka baya ba, ina tare da kai kuma zan zauna da kai." Ina gama fadar haka na mike zan bar gurin. Shima mikewa yayi sannan ya saka hannun shi dukka biyu ya rungume ni. Yana shafa bayana. Mehran yana kallon mu. Juyawa yayi tare da barin gidan baki daya. Idan ka ganshi zaka dauka bai da lafiya ne. Hamas shiga Harami ya nemi faduwa, tare da jin wani mugun sanyi ya shige tare da zazzaɓi me mugun zafi. Fudail da yaga fitar shi, shine ya fara ganin shi san yana harabar gidan. Ya rike shi zuwa cikin gidan. "Fudail kirjina zai fashe." "Sannun Sultan! Ina kaje haka? Ko kamanta kana da ciwon zuciya ne? Gashi a karon farko zaka kashe kanka." Ina kasa magana yayi sai juya kai yake, yana jin kamar kirjin zata fashe, a dakin shi aka kwantar dashi. "Fudail, Ikram" ya faɗa a sanyayye dukda idanun shi a rufe suke amma bai hana shi. Kiran sunan Ikram ba, gabaki daya ya zauce baya gane kome sai sunan Ikram,har akayi sallah magarib da isha Mehran baya cikin hankalin shi. Matan da aka zab'e mishi kuwa kasa hakuri suka yi. Sai da suka magantu. Amma haka bai hana Mehran kiran Ikram ba, tun ana zata zafin zazzaɓi ne har suka gane cewa ita din yake bukata, gashi dare yayi sosai. Dan haka suka yi ta fama dashi, daga karshe dai Sultanah da Fudail suka fita har gidan bakin. ...... Ina kwance banyi barci ba amma kuma zuciyata babu dad'i dan haka na tashi zaune, naja labulen gadon ina kallon su Nimrah da Izmah, da suke kwance can gefe guda. Kallon su nayi naga suna barcin su. Wato sai kana da nutsuwa kake samun damar barci idan baka da shi kuwa. Kai da barci har abada. Buga kofar dakin mu akayi na sauka a gadon sannan na bude tare da kallon Ummyn da Sultanah Fazilatul nisa. "Ikram! Don Allah zoki taimake mu. Mehran zai mutu." Ban tab'a sanin akwai rudewar da zata sani niman fita daga cikin gidan babu suturar Arziki a jikina ba sai da aka gaya min Mehran zai mutu. Riko hannuna Rahil yayi cikin dakewa sannan yace min. "Baki da lafiya ne? Dubi yadda zaki fita? Koma ki shirya ina jiranki!" Haka nayi kamar yadda yace min, tare muka tafi har da wasu dakarun. Tunda muka shiga cikin harabar gidan, Rahil ya riko hannuna. "Karki manta akwai alkawarina akanki. Dan haka kiyi kokarin kare girman alkawari." Kallon shi nayi domin na kasa Fahimtar me yake nufi, a lokaci guda naji ya fice min a raina. Hawayen da ban san yaushe ya sauko min ba. "Kasan girman shi a cikin idanuna? Kasan yadda nake jin shi a raina? Da kasan yadda nake kokarin kyautata mishi ba zaka tab'a sanya min sharadi dan zan ganshi. Ka tsaya a matsayin ka na wanda aka mana alkawari karka tinzira zuciyata izuwa aikata abinda ba zan iya daukar shi ba. Sultan MEHRAN wani shashine na rayuwata. Don Allah karka raba abinda yake a haɗe." Ina gaya mishi haka na shige cikin gidan. Na sami Kwarkwarorin shi a bakin kofar, suka gani na suka shiga matsa min a hanyar. Shiga dakin nayi na same shi rike da kirjin shi. "Ikram! Ku kawo min ita" ina shiga matan shi suna shigowa. Tsayawa nayi a bakin gadon ina kallon yadda yake dafe kirjin shi. A hankali na zauna a bakin gadon. Na kai hannuna tare da riko hannun shi. Ajiyar zuciya ya sauke tare da ƙamƙame ni. "Ikram!" Ya kira suna na idanun shi a rufe. "Na'am Sultan Mehran!" Bude idanun shi yayi sannan yace min. "Mehran zaki ce, ki ce min Mehran." "Meke damun ka?" Hannu na yakai bakin shi ya sumbata, sannan yace min. "Kece ciwo na. Kece magani na" ya fadi haka, kallon sauran matan Fudail da Sultanah suka yi tare da musu alamar su fita. Fuuuu suka fita daga dakin, ina rike da hannun Mehran, tashi yayi tare da dawowa kan cinya ta, yana sauke ajiyar zuciya. "Karki tafi! Kunne na yana min kai-kayi, ko zaki susa min" Shafa kan shi nayi tare da jin saukar kwalla daga idanun shi akan cinyata. "Kayi hakuri! Ni zan tafi gobe Insha Allah..sannan ka rungumi matan da aka baka, Insha Allah zaka sami wacce zata fini tsayin daka." "A wani matsayi kika ajiye Ni?" Ya tambaye ni tare da damke hannuna. Shafa kanshi nayi a hankali tare da jin tashin hankalin a raina. "Mehran! Kai kamar Uba ne a gare ni, bana son na ganka cikin tashin hankali da damuwa, Mehran ina zaune ne domin kai bayan haka bani da hurumin zama a cikin Masarautan SAMAIND, amma kuma sai naji kunyar abinda ka aikata min. Mehran na tawo da niyyar daukar fansa akan abinda kasa aka aikawa Numan." D'ago kai yayi tare da kallona. _Me yasa ba zaki gane bani da hannun cikin kisar gilla da aka yiwa Mijinki? Me yasa ba zaki gane ban san kome akan kashe shi ba! Nayi kuskuren furta sai na kashe shi amma bani na aikata ba_ Shiru nayi tare da janye idanuna daga cikin na shi, sannan na cigaba da cewa. "Haka bai sani ajiye makamina ba, na amshi aikin da ka sani ba. Mehran sai da na gama tsalleke duk wani mataki da iyaka, amma ka juya min baya, alhalin kasan ba zan yi abinda kake zargi na ba, Mehran ko daga cikin gidan ƙaruwai la dauko ni,.zaka min uzuri balle kuma kai da kanka kasan ba haka nake ba. Ka kira Ni da sunaye masu kazamta da muni. Kayi hakuri Mehran amma iya yau nayi domin Mahaifiyarka ce da Aminin ka, bayan haka Akwai alqawarin auren D'an Uwana, don Allah kayi hakuri. Kai Ubane a gare Ni bayan haka bana jin akwai bukatar na kara maka wani matsayin." Na fada mishi haka ina had'iye kukan da ya taso min, sannan na cusa hannuna cikin gashin kanshi ina wasa dashi. Hawaye na yana zuba akan gashin kanshi. "Ban yi laifin da kake zargina ba. Amma ka kasa fahimtar kome a kaina, kayi hakuri nasan nayi laifi da kuskuren fita daga harami zuwa gidan da Abrad yaƙe, amma yadda kasame mu da shi babu wani abinda kake tunanin ya faru, nasan bai zama dole ka yarda dani ba, amma iya gaskiyar kenan." Tashi yayi zaune tare da kallona, idanun shi jajjur bakin shi yayi fari sol kamar wanda ya jima yana jinya. Mikewa nayi sannan na dauko mishi ruwan na mika mishi. Riko hannuna yayi tare da haɗawa da nashi ya kai ruwan bakin shi ya sha, sannan ya janyo ni jikin shi yana kallon fiskana da take jike da kwalla. Tari ya fara tare da daidaita tsayi na da fuskar shi. "Meye matsayina?" Kallon shi nayi sannan na fara ƙoƙarin mik'ewa, sake murmushi yayi tare da cewa. "Meye matsayina?" Kwalla ne suka shiga tuttukowa daga cikin idanuna, bakina yana rawa na bude zan bashi amsa, sai jin harshen shi nayi cikin bakina, tare da lumshe idanun shi, ya rike kai na gam. Wani irin kuka naja tare da ajiyar zuciya. Ina kallon shi har cikin idanuna. Abinda nake hangowa ba abin wasa bane, ba kuma karamin abu bane. Amma zurfin cikin da YAKANA sanya shi b'oyewa. Gani yake idan ya fitar duniya zata iya zage shi. Shi yasa yake kokarin ganin ya adana abin a idanun shi da zuciyar shi. Amma abin yaki ajiyuawa, dan ba gama garin sirri bane da ake iya boye suka zauna lafiya. Da kanshi ya sake min bakina da yasha tauna a gurin shi, haka ba sabon abu bane a gare ni amma kuma kuma tambayar anan shine meye yasa Mehran yayi min haka? Me yasa ya kasa yarda dani? Meye yake kokarin b'oye min? Kasa nayi da kaina, domin bani da amsar da zan bawa kaina, amma daya biyun ina kara fahimtar kaunar da yake lullube da kishi na akan idanun shi. Hannun shi naji cikin rigar jikina. Da sauri na rike tare da kallon shi. "Me ye matsayina?" Bakina yana rawa na kalle shi tare da cewa. "Shugaba na!" "Hmm! Ban yarda ba" "Allah da gaske nake gaya maka" sake tura hannun yayi zai kuma tab'a min jikina nayi maza na mike ina gyara zaman rigar jikina. "Ina zaki?" "Na bar Rahil a waje kuma nasan yanzun dare yayi." Tab'e baki yayi sannan ya dauke kanshi. "Baki gaya mishi gurina zaki zo ba?" "Ya sani rakoni yayi!" "Toh gaskiya babu inda zaki a daren nan, a nan zaki kwana." Ya nuna min gefen shi. "Amma Mehran!" "Na gama magana idan kuma ban isa ba zaki iya tafiya dama ai bani da daraja da matsayin da zaki zauna dani ko ance miki ban san labarin zaman za kuka yi dashi a cikin gida daya bane, wato ni aka maida sakarai, ayita zagawa ana cin amana Na, idan nayi magana ace na cika zargi bayan kowa ya sani Salsabilah yake kiran ki, wato koramar shi. Ni kuma d'an iska ban san me zance ba." Matse hannuna nayi a cikin juna, ina jin wani irin takaicin Mehran da haushin sa, kafin na d'ago kai nace mishi. "Kai ma ai kana da naka sunan da kasa min kamanta ne?" .wani dauke kai yayi cikin jan aji irin ya manta dole na tuna mishi. A hankali na dan sunkuya ina kallon shi.. "Sultan MEHRAN!" Da sauri ya juyo yana harara ta, sannan yace min. "Qurratulain!" Murmushi nayi sannan nace mishi..... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: *200₦ ta bank GTBNK Ramlat Abdulrahman 0472282105 ki katin mtn 300 ta wannan Number +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat ko ta wannan Number 08130269641..* Mai_Dambu... _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 40 Karshen book 2 "Me yasa kake son tilasta min zama da kai bayan kai baka yarda da ni ba? Kasan girman kuskuren da ka aikata? Da a ciwo a.." Yatsar shi ya saka akan bakina, yana kallon yadda nake kokarin cire idanuna a cikin nashi. "Kamar yadda kike zargina da kashe Nu'man haka nayi domin." Jan iskar bakin shi yayi tare da mik'ewa yana me kai hannun shi kan fuskana ya d'ago ni tsaye. Dukka hannu bibbiyu ya zuba a k'uguna, yana me ben fuskana da kallon me cike da sanyin yanayi. "Duk yadda naso kare kai na, baki bani damar haka ba, sai ma kuma tinzara da kike. Ikram na baki damar shiga rayuwata ce a karo na biyu dan ki zama alkali a rayuwar mu, don Karki hukunta ni da laifin da ban aikata ba" ya faɗa muryan shi can kasa tare da saka kanshi a kafadana. D'ago shanyayyun idanun shi yayi a karo na biyu, yana kallon yadda nake kokarin janye jikina daga gare shi. Juyar dani yayi tare da daura kanshi a kafadana. "Na san na fada a kashe shi! Amma kuma ban ba da damar kashe shi ba. Ki dube ni da idanun rahama karki nisanta kanki da ni" ya faɗa yana me kai hannun shi dukka biyu kan cikina. Ina jin yadda zuciyar shi take bugawa, kan shi kuwa wani irin zufa yake fiddawa, narkewa nayi a jikin shi tare da lumshe idanuna, ina kuma jin kamar nacewa Sultanah Amrah ni kawai su tafi ba zan bisu ba. Juyawa nayi zan fita ya kuma tare kofar. "Me yasa kike saurin tafiya gurin shi?" Sunkuyar da kai nayi tare da maida gashin kai na baya, sannan na d'ago kai na, kafin nace mishi."Mehran kayi hakuri akwai alqawarin auren shi a kaina..." Wurgi yayi da kayan abincin shi. "Alqawarin banza, ko Ni bani da zuciya ne da ba zaki fahimci halin da nake ciki ba? Ce miki akayi dadin Kowa nake ji bayan ke? Toh jeki kawai jeki Allah ya baki zaman lafiya. Kije ki aure shi." Cikin jin haushi ya turo ni waje daga dakin shi ya rufe kofar d'akin shi. Yana cikin dakin sai barna yake kamar yaro karami. Juyawa nayi tare da barin gurin, har na sauko kasa Kwarkwarorin shi suna kallona, ganin yadda suke b'ata rai ya sani dauke kai na abuna, sabida duk cikin babu wacce ta taki sa'ar da na samu, dan haka babu wacce zata min iyayi ko kankanba. Ina fita na hango Rahil zaune shi dasu Shairah da Fudail sai Darda. A hankali na isa gare su, sannan nayi musu bankwana. Ina lura da yadda jikin shi yayi sanyi musamman yadda na same su, suna hirar Mehran. A hankali muke tafiya yana me sauke ajiyar zuciya a kai a kai, ba zaka tab'a jin bai sauke tare da fitar numfashin sa ba, kuma yaki kallona, abinda na fahimta matsanancin kishi yake. Domin ina lura da yadda yake naushin hannun shi har muka isa gidan. Saka kai nayi zan wuce masaukin mu naji ya riko hannuna, juyawa nayi tare da kallon shi. "Me yasa baki da tausayi da jin kai? Me yasa ba zaki gane yadda nake kokarin kyautata miki ba? Kin fi son bare a kaina? Tun da kika shiga cikin gidan kika manta da batu na, sai yanzun kika tuna dani, gaskiya ina da zafin kishi da zafin rai idan na kuma ganin haka zan aikata abinda ba zai miki dadi ba." Kasakai nayi ina kallon bawan Allah nan, wato sun mai dani sha tara, kowannen su buga ni yake kamar tamola, meye nayi musu haka da kowannen su yake jin zafi na? Nima cikin fushi na bar shi a tsaye,ban saurare shi ba,balle yayi tunanin zan bashi hakuri ko wani abu makamancin haka. ... A wannan daren mutane uku basu rintsa ba, gabaki dayan su kowanne da abinda yake ji, dan haka gari na wayewa. Mehran ya fara fitowa yana kallon masaukin da suke ciki. Har zuwa lokacin da aka fara fidda kayan Ikram, a lokacin Abrad ya shigo gidan. Babu shiri Mehran shima ya fita tare da nufar hanyar gidan. Tare da wasu manyan dakarun shi suna dauke da manyan akwatin karfe, sai bayi mata da suke bin bayan Fudail dauke da tire a lullube da jan kyale. Tun safe Izmah da Nimra suke kallona, "Toh wai meye suke nufi dake ne? Domin ga Abrad da Mehran suna Wajen sai Amir Rahil." Zare tagumi nayi tare da cewa. "Wallahi sun addabi rayuwata, musamman Abrad ya hana rayuwata sakat, Mehran kuwa bani da damuwa dashi. Sabida na gama zama dashi." Shiru nayi ina kallon su, kafin na cigaba da cewa. "Amir nake tsoron kar Abrad yayi mishi renin hankalin da." "Amirah ana jiran ki!" A hankali na mike tare da hada abinda zan iya, sauran kuma su Izmah suka hada min, fitowa nayi na sami Sultanah Amrah, tana karyawa,zama nayi dan sam ban lura da falon dauke yake da mutane ba, sai da na zuba ruwan shayi, na tsinkayo Muryan Mehran. "Ko zaki hada dani dan ban karya ba." Caaaa suka min da ido, shi kuma yadda ya zauna tare da saka hannun shi ya kishingida kamar yana falon shi, d'ago kai nayi ina kallon shi. Kafin na mike tare da hada mishi jikina yana rawa, tasowa yayi tare da nufar inda nake hada shayin ya kai hannun shi zai rike ni. "Har yanzun tana karkashin kulawata ce, idan ta fita daga Cikin SAMAIND ta shiga da'iran kulawar kowa, anan babu wanda ya isa ya tab'a ta a gaban D'an Abdus Samad." Had'iye yawun nayi ina kallon Amir Rahil da yazo rike ni, sosai na kadu da yadda Fuskar Mehran ya sauya, dan haka kafin Amir Rahil ya rike ni, na kauce sannan na nufi inda Mehran da kofin ruwan zafin. Duk abinda yake faruwa Sultanah Amrah da Abrad suna kallon mu, sake shan kaina Amir Rahil yayi, ture shi Mehran yayi tare da kallon inda nake, ya mika min hannuna. A sanyayye na isa gare shi, rike hannuna Rahil yayi. "Akwai baiko na akanta dan haka na fika iko akanta." "Ni kuma baiwata ce, naga wanda ya isa ya min iko akanta." "Wai kai waye ne? Meye nufinka da ita? Bilqisul Ikram Mustapha matar da zan aura ce! Dan haka baka isa ka tab'a min matar da zan aura ba." Karb'an ruwan shayin yayi tare da ajiyewa, ya fisgo jikin shi. "Aamaan ka sake min mata na" Amir Rahil ya daka mishi tsawa, Tsakiyar su Abrad ya shiga tsakanin su, kallon Mehran yayi cikin nutsuwa da jin dadi, muryan shi kasa kasa, yace mishi. "Fanko ce kake harzuka akanta, shima idan yasan wacece ita. Fasa auren ta zai yi. Karshe dai Ni ne dai zan karasa ab...." Tass Mehran ya dauke shi da mari, tare da shake wuyar shi. Kamar mahaukaci ya rufe shi da duka, abun sai ya bamu tsoro da mamaki. Domin kuwa Amir Rahil ya kamata ya daka, amma ya bige da dukar Abrad dama yana cike dashi, kokarin shiga tsakanin su nayi amma Abrad ya riko ni, dai-dai Mehran yaja hannun shi zai naushe shi. Ganin yadda ya rungume ni yasa shi tsayawa cak. " Sarkin Karfi gata a kirjina dake mu, nace ka dake mu. Ga Ikram din ta faɗa da bakin ta" da sauri na juya ina kallon shi tare da girgiza mishi kai. "Karka tozarta ta! Na yarda kayi min kome amma karka wulakantatta a gaban jama'ar ta." Ya faɗa tare da sauke hannun shi. Kallon su nayi na ma kasa magana, hawaye Masu zafi suke zuba a cikin idanuna. "Abrad meye nayi maka da zafi haƙa?" Na tambaye shi bayan na kwace kai na, kallona yayi sannan ya fashe da dariya, bude baki yayi zai magana na kifa mishi mari, hawaye na zuba. "Meye nayi maka da zafi? Meye na tsare maka da kake niman hanyar da zaka wulakantani? Ka gaya min meye nayi maka!" "Zaki biya abinda kika aikata." Takowa yayi gaba na, tare da kallon fuskana yace min. "Kina jin kunyar Kakarki ce? Ko kina tsoron kar kashe gimbiyar da tayi mu'amalanci wani namijin? Ko zaki iya tuna abinda wannan hannun yayi miki shekarun baya, da na tura shi." Ji nayi kamar zan fadi,.dan wani irin jiri ne yake niman kayar dani, Lokaci guda Mehran da Rahil suka kawo min dauki, murmushi yayi sannan yace min. "Sai na hanaki sukuni." "Abrad wannan wani irin wawanci ne? Ikram din ce kake mata irin wannan haukar ka manta matsayinta ta ne a gurin Sariya? Yar Yayar matar ka ce fa. Wannan wacce irin hauka ce mara to ..." "Kul! Idan kika yi wasa abinda zan fada sai ya saka yan majalisar ki sun sauke ki a kan mulkin ki, sannan kuma itama Ikram din Askandariya sai tayi mata wahalar shi, kai kuma Mehran kamar yadda na gaya mata haka kai ma. Kai sha-sha-sha bani da lokacin ka, sabida mutanen da suke da iko nake yi dasu. Abinda na sani baka isa ka auri Ikram ba. Amma zan baka damar niman taimako na yadda zaka aure ta. Idan ka shirya." Yana gama abinda zai yi ya fita yana dariya wai shi yayi nasara. Sai da ya fita na sami damar fashewa da kuka. Kamar yadda naso yi. Mikewa Mehran yayi tare da barin gidan, Rahil kuwa kasa magana yayi. Kawai sai damke hannuna yayi tare da cewa. "Ba zan tab'a barin ki cikin matsala ba matukar ina raye." Sultanah kuwa kasa d'gowa tayi domin kuwa tana me jin kunya da bakin cikin abinda ya faru, ita da kanta ta kashe Zuri'ar ta, yau tayi abinda zai kaita ya baro ta. Rike rigar shi nayi tare da fashewa da kuka, Abrad ya wulakantani, Mehran ya juya min baya, bani da zabin da ya wuce Rahil ko naki ko naso Rahil shine ya dace da rayuwata, ba zai tab'a bari na cikin kuncin rayuwa ba. Dan haka ya taimaka min na mike tare da kai ni har waje inda aka jibe mana kayan da Mehran ya kawo min yayi tafiyar shi. Haka su Izmah da Nimra suka kwashe kayan aka zuba a saman rakumai, sannan na shiga keken dokin shi, su kuma suka shiga cikin na Sultanah Amratu. Muka bar masaukin bayan an hada mu da rakiyar dakarun Samaind kimanin dubu goma sha biyar, har Askandariya zasu rakani inji Sultan Mehran. Tunda na shiga cikin keken nake kuka, wanda nasan ba na abinda Abrad yayi min bane, a'a zunzurutun rabuwa da Mehran ne da zanyi. Ji nake kamar na sauka nace musu bani tafiya ko ina zan zauna da Mehran. Tun kafin mu bar da'iran SAMAIND. Naji jikina yana bani tare dashi muke tafiya, dan haka na bude labulen jikin keken. Kurawa juna ido muka yi, sanya yake da kayan dakarun ƙasar. Hannun shi ya kai tare da riko hannuna. Sannan ya sake linzamin dokin shi ya saka min zoben da ya ciro daga aljuhun shi. Tare da sumbatar hannun. "Ina tare dake har karshen rayuwata." Daga haka ya sake min hannuna. Ina gani muka yi ta tafiya muka bar shi a can baya. Hawayen da nake dannewa ne ya zubo min. A hankali nace. "Ina sonka!" Haka muka bar shi a gurin. ....... Hawayen da bai tab'a zaton zai zubda akan So ba yau ya zubda su. Rike d'an kunnenta yayi tare da kallon shi, ya tuna ranar da tazo amsar tayin shi take zata bude inda d'an kunnen yake ya hanata, kwallar shi ce ta sauka akan d'an kunnen. Ya damke a hankali. Tare da sumbatar shi, yace. "Ina Sonki! Mara iyaka. Kece fitilar rayuwata." Ya fada a hankali, kamar wani na jin shi. Tabbas sai yanzun ya kuma fahimtar shakuwar da take tsakanin su, bata wasa bane. "Abrad!" Da sauri ya juya linzamin dokin shi ya nufi SAMAIND a guje tare da tuna ranar da ya fara ganin Ikram...... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ Littafi na uku 01 Tunda ya bar masaukin su Ikram ya sa aka hada musu nasu kayan suka bar gidan da suke, sai da suka kusan barin cikin garin SAMAIND. Yasa aka kama Nawwas. Kallon juna suka yi kafin yacewa. "Na sami labarin ka gayawa Fudail duk abinda ya faru, sai dai kayi kuskuren domin ba zan barka a raye ba, shi yasa nayi gaggawan barin SAMAIND domin wancan mahaukacin idan ya ritsani sai ta Allah." Dariya Nawwas ya saka yana kallon Abrad, tare da nuna shi da yatsa kafin yace mishi. "Kai tsaye ka mu'amalancin Ikram, Ni kuma a ruwan sanyi Mu'amalanci kanwarka tare da dauke abinda yake jikinta. Bamu bar SAMAIND ba sai da na tabbatar da na kuma buɗe tsakanin kafarta na jefa linzamina. Yadda koda na mutu dole na bar baya da kura." Dariya ya kuma fashewa da shi, yana mai maita abinda ya faru,, yana kuma gaya mishi abinda ya aikata da Kanwar shi. Babu abinda ya kai wannan abin tashin hankali. Idanun shi ne suka cika da kwalla. Wanda ya kasa jurewa har ya kai da ya zuba masa. "Meye nayi maka Nawwas? Da kayi min yankan baya haka? Nawwas meye na tsare maka hakan da ka zab'i cilla rayuwar kanwata cikin tashin hankali? Nawwas me yasa baka yi a kaina ba." "Hahaha... Hmmm, ka zata zan zuba ido ne ka tozarta Ikram? Ko ka zata zan zuba ido ne ka cigaba da abinda ranka yake so? Wannan shi ne kishi a tsakanin zubda jini. Idan kana tunanin ka zubda jinin Nu'man dan jin dadin ka da kuma cusgunawa Mehran dan Ikram ta tsane shi wannan kuskure ne babba karka manta kamar yadda ka mayarda da Ikram a shimfid'ar ka, hakan na mayar da Amirah Azizatul Nissah. Na maida ta kamar matar da na biya sadaki me daraja dan haka karka yi tunanin Mehran zai yarda da wata mace bayan Ikram! Kamar yadda kake da kwarin gwiwar rubutawa yan majalisar Masarautan SAMAIND haka nima na gayawa Mehran alakata da Kanwar ka, dan haka sai ka jira abinda zai biyo baya domin dai SAMAIND ba kanwan lasa bane. Kayi kuskuren hadamme kome, Ni kuma nayi ƙoƙarin bayyanawa duniya waye kai, Ikram yanzun tayi maka nisa kanwarka zaka yi kokarin ganin ka fito da ita daga SAMAIND idan ba haka ba". Cikin wani irin fusata Abrad yaja takobi bai yi wata wata ba, ya sokawa Nawwas a kirjin shi sai da ya hudo bayan shi. Zuɓewa yayi akan gwiwar shi, ya kuma sake jan takobin ya soka mishi sai da jini ya fito ta bakin Nawwas. A lokacin ya tuna da Abinda Nu'man ya gaya mishi. *Ban san meye muka yi ba kuka raba mana rayuwar mu! Sai dai nasan wata rana kai ma haka ce zata mamaye ka! Yadda kayi min haka kai ba za a maka* Hawaye ne ya zubo mishi tare da kallon Abrad cikin tsannanin azaba. "Ni nayi haka ne domin al'ummar Daular Umayyad! Nayi wannan aikin ne saboda Banu Umayyad. Sai dai kuma nayi imanin yadda na zubda jinin bawan Allah haka nima rawa jinin ya salwanta. Kai kuma Banu Umayyad za a shafe baki daya. Sai kayi gudun da babu macecin ka. Abrad ni abokinka ne tun yaranta ka kashe ni da hannunka. Ba iya ni ne matsalar ba, rayuwar Kanwar ka anan zaka Fahimci muhimmancin rayuwar wanda kake so yaƙe" Kasa magana yayi sakamakon jinin da ya cika mishi baki, mika mishi hannu yayi amma fir yaƙi amsar hannun. Juya baya Abrad yayi kwalla na zuba mishi. Bai san ta yadda zai taimakawa Azizah ba, babban tashin hankalin shi Azizatul Nissah. Juyawa yayi cikin tsannanin fushi ya sare kan Nawwas, ya fadi can jini yana zuba kamar da bakin kwarya. Zama yayi tare da sake takobin ya fashe da kuka. Domin Nawwas ba kashin yarwa bane, ba kasafai ake samun irin shi ba. Nawwas abokin tarayya ne na kwarai. Mutum ne da ba a cika samun irin shi ba. Shi yasa yake kuka, sai kuma yadda Nawwas yaci Amanar shi yayi ta tarayya da Kanwar shi. Sannan ya kwashi sirrin shi ya gayawa Mehran, "Me yasa Nawwas yaci amanata?" Ya tambaya da karfi cikin tsorata da yanayin shi duk suka ja baya, sai daga can asalin amintaccen bawan Nawwas yace mishi. "Sabida shi ya fara son Ikram! Ya kaunace ta sama da kaunar da yakewa rayuwar shi! Ya bada rayuwar shi ne domin ita? Ya kuma saka duk wani matakin da zai bawa rayuwar ta taimako koda baya raye. Sultan kayi hakuri amma kaunar Nawwas ga Ikram gaskiya ce. Soyayyar shi ga Ikram gaskiya ce, tabbas yaso ta tun daga ranar da muka sayo ta, har zuwa yau. Ya gaya maka gaskiya kamar yadda kowa ya kasa fahimtar da kai haka ne. Amma tabbas bayi kuskuren ba, samun masoyi irin shi ma sai an tuna." Yana fadar haka ya shiga tattara gangan jikin Nawwas da kanshi yana zubda hawayen bakin ciki, da tausayin abinda ya faru. Ya tuna abinda Nawwas ya gaya mishi jiya. "Karka sake ka gaya mishi gaskiya akan alakata da Azizatul Nissah! Zan gaya mishi abinda zai fusata shi. Domin ya bar Ikram ta rayu da Mehran, naso Mehran ya tsaya muyi tsayayya magana dashi amma fir yaki. Dan haka zan gayawa Fudail Insha Allah zai saurare ni. Amma kasan me? Hmm idan Abrad yaga zai rasa Ikram zai sauya tsarin gudanar da abinshi ka saka ido kayi kallo. Don Allah Rab ka kula min da Azizatul Nissah da abinda zata haifa." A kidime ya kalle shi sannan yace mishi. "Shugabana ka manta matsayinta ne a yanzun? Har kake batun abinda zata haifa" Murmushi yayi sannan yace mishi. "Ba da ita ga Mehran ba shi yake nufin ita din mallakar shi bace, ita da abin cikin ta nawa ne, kuma mallakina ce, don Allah karka sake wani abu ya shiga cikin rayuwar su, fatana idan ka bar Oman kayi ƙoƙarin tsayawa Ikram, ka same ta da batun kome, kuma na roke ka don Allah ka tsaya a bayanta karka bari wani ya tab'ata. Ita kuma zata tsaya a gaban Azizatul Nissah." Wani irin kuka ne ya kwace mishi me ƙarfi yana me kuma rungume kan Nawwas, tare da jin tashin hankali sama da farkon faruwan kome, kara rungume kan yayi yana faɗin. "Me yasa kayi haka? Me yasa ka bada rayuwar ka domin wasu. Baka tuna bayanka ne? Me yasa kika zab'i zubda jini sama da kome ne?" Ya faɗa da karfi, yana kuka tare da k'amk'ame kan Nawwas, juyawa Abrad yayi tare da zuba mishi ido, tabbas sun zabi zubda jini sama da kome akan mace! Akan Ikram, koma waye za a kashe! Akan Ikram koda kuwa rayuwar shi ce zai iya badawa, wani irin kwalla yake zubdawa tare da kallon gawan Nawwas, mutum na farko da ya fara ankarar dashi kuskuren abinda yake aikatawa ya kashe mutumin da bai hada shi da kome ba ya kashe mutumin da zunzurutun kaunar shi da shi ko barci yake sai ya tashi idan ya tura a kira shi ya kashe. Ya kashe mutumin da yaso shi da gaskiya, ihu ya takarkara a cikin jirgin ruwan, sai da duk suka toshe kunnen su, ya kuma fashe da kuka yana faɗin. "Jininki fansa ce ga jinin Aminina" ya faɗa yana kuka da bakin cikin abinda ya aikata , Rab yana jin shi, tabbas ya fara dauko haske akan abin da Nawwas ya gaya mishi. Shiru cikin gurin yayi babu wanda ya kuma magana, mik'ewa yayi tare da cewa. "Ku dauki gawan shi ku wurga a ruwa!" "Sultan Abrad!" A fusace ya juya ga Rab, had'iye yawun yayi sannan ya sunkuyar da kanshi,bai kuma cewa kome ba. Amma tabbas wannan shine abinda ba zai iya dauka ba, dan haka yana ganin an dauki gawar Nawwas, aka fito dashi shima yabi bayan su da gudu, kafin yayi wani yunkuri an wurga cikin teku bayan dakaru sun rike shi. Ihu yake tare da kokarin kwacewa a hannun su, amma suka kara rike shi, yana ji yana gani gawan Nawwas ya nutse cikin ruwan, kuka yake tare da ihun. Buga mishi kasa takobi Abrad yayi. Bai kuma fahimtar inda kan shi yake ba. *** Wurgi yayi da takobin hannun shi, tare da fasa kara yana huci. "Tabbas Abrad yasan zan dawo na bi takan shi, wato shine ya gudu. Fudail Darda ina Nawwas din?" "Sultan MEHRAN! Tun jiya muke binka akan Nawwas, amma baka tsaya munyi magana ba, shi yasa da ya gaji yayi tafiyar shi bai..." Yadda ya kafe Fudail da ido ne, yasa shi sunkuyar da kai kasa, yana had'iye yawu. "Sultan MEHRAN!" "Ina jinka, meye yace?" Ya tambaye shi, tare da kallon gefe. Fita suka yi daga cikin gidan..sai da suka yi tafiya me nisa, sannan yace mishi. "Sultan MEHRAN! Nawwas bai gaya min kome ba!" Cakume wuyar shi yayi tare da fidda huci. "Ni zaka mara da takalmin kafarka? Ko zaka samu damar boye min abinda yake ranka? Gaya min meye laifina da kuke boye min abinda ya dace na sani." "Kayi hakuri bai gaya min kome ba, amma yace na nime bawan shi Rab." Wani dirkeken naushi ya kasake a jikin bishiyar da Bayan Nawwas yake jingine. Sai da hannun shi ya farfashe. Sannan ya takarkare ya fasa ihu. Sai da dajin ya amsa. Zafi biyu yake ciki, babu wanda zai gaya mishi gaskiya kenan? Ya rasa Ikram ya rasa wanda zai gaya mishi abinda ya faru kenan, dan haka ya tashi cikin tashin hankali ya juya zai tafi. Ya kuma juyawa ya kalli Fudail, sannan ya saka kai zai bar gurin. Ajiyar zuciya Fudail yayi sannan a ranshi ya ayyana cewa. *_Ba zan tab'a yarda na gaya maka gaskiya ba! Sai har na gama gabatar da abinda yake gaba na, ba zan tab'a yarda na kyale wanda ya cutar da ikram koda da bakar magana ce balle da farar magana! Kayi hakuri Sultan Mehran_* Ya faɗa a sanyayye, yana me jin tausayin Sultan Mehran. Domin a yanzun gaskiya yake nima idanu a rufe, kuma baya jin zai gaya mishi koda kuwa zai rasa rayuwar shi, Dole kuwa Azizatul Nissah taji a jikinta itama. Abin kunyar da suke amfani dashi ga rayuwar Ikram itama taji yadda tozarci yake. Amma kuma idan ya tuna rokon da Nawwas yayi mishi sai yaji tsoron kar haka kuma ya tab'a kimarta. Dafe goshin da yayi tare da bin bayan Mehran, yana tafiya yana zancen Zuci. Har ya isa inda dokin shi yake, dan yanzun kan yasan Mehran yayi mishi nisa, koda ya cilla dokin shi ya hango su, dab da Masarautan. Amma kuma koda ya isa Fir dakarun suka hana shi shiga. Wannan shine karon farko da Mehran ya mishi hukunci me tsauri ta hanyar amfani da hana shi, shiga SAMAIND! Dan haka bai yi fushi ba, ya zauna a gurin gashi garin da alamun shigowar damina. Duk sai yaji babu dad'i a ranshi, yau shine Mehran yayiwa wannan hukuncin, dan haka duk dai yake gani kamar tozartawa ne, ga wani muzancin da yake ji a ranshi. Kanshi a sunkuye har aka fara yayyafi. Bayan wani lokaci ruwa ya fara me mugun karfi da yawa. Yana tsaye a bakin kofar shiga masarautan.. ---- Tunda ya shiga cikin gidan, ake mishi magana kome ya gani fatali yake dashi, har ya shiga cikin dakin shi. Huci yake ya rasa yadda zai yi da Fudail idan kowa zai ci amanar shi yana tunanin ai Fudail ba zai tab'a yarda a cutar dashi ba. Kuma yayi imani da Allah akwai da yake boye shi, kuma ba zai tab'a yarda da munafunci ba, domin idan ba munafunci ba akan me zai boye mishi maganar da yake bukatar yaji, dan haka babu abinda zai hana shi bai hukunta shi ba, sai ya hukunshi sosai domin kuwa ba zai yarda da wannan wulakancin ba, tsaki yayi tare da kutufal da kayan shayin gaban shi, yana jin ana buga kofar shi amma fir yaki buɗe sabida yayi fushi anci amanar shi... (See me see trouble😹😂😹🤣 ta ina aka ci amanar ka Yau ga D'an Uwan Jamal🤔) +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 02 Kaiwa yake yana komowa, tsabar yaji haushin abinda ya faru. Jin cidan hadari tare da rugugi ya sashi zare ido cikin takaici da bakin ciki. "Duk irin zaman da muka yi da.". Bude kofar shi da aka yi yasa shi had'iye sauran maganar da da zai yi, ya zubawa kofar ido. Shigowa tayi tare da ajiye mishi ruwa. Sunkuyar da kai tayi cikin girmamawa tace mishi. "Sultan MEHRAN gashi." Kallon ta yayi tare da tuna abinda Abrad yayi mishi dan haka ya a nufi ruwan bai ce mata kome ba, ya dauka ya shanye tass. Ya ajiye kofin kafin ya zauna yana kallon ta. "Me yasa yayi min haka?" Kallon shi tayi a razane tare da ja da baya, tana girgiza mishi kai. "Ni." "Tambayar ki nake zaki dawo min da tambaya na" wani shegen tsoro ne ya lullube ta, tare da zaro idanu waje, jikinta yana rawa. Tabbas duk rayuwarta da tayi bata tab'a ganin wanda iya tsawar shi abar firgita ce kamar Mehran. Shin dan ya kasance Shugaba ne? Koko dan ya kasance Zaki ne kisabo, wallahi ita har tsoron had'a idanu take dashi. Ganin taki fita ya sashi fahimtar akwai abinda take buƙata, bai tsaya da tunanin shi ba, yaji marar shi kamar an daure mishi. Wani azazzaben sha'awar kasancewa da mace ya taso mishi. Kura mata ido yayi ganin yadda take kallon shi. Komawa yayi saman kujeran ya zube yana sauke numfashin sa. A hankali ta tako gaban shi, tare da tsayawa tana kallon yadda yake lumshe idanun shi, wato shi ba zai kira mace ta taimaka mishi ba, ya gwammace koda zai mutu ne gwara ya mutum, zare kayan jikinta tayi suka zube a kasa. Sannan ya taimaka mishi suka shiga d'akin. A wannan lokacin shi kanshi idan ka tambaye shi wani hali yake ciki bai sani ba, amma tabbas yaji a ranshi yana kwance da mace. Sai dai har yau kamar can baya da yaki matan dan kanshi ya kyamaci haka a ranshi. Duk da kyamar bai hana shi buga mata isa ba. Ya kasance ta da iya karfin shi da lafiyarta, tun tana kallon haka a matsayin abin da bai kai ya kawo ba, har ita da kanta ta fara dukar shi tana kuka. Shi kuma wai yayi haka bane dan lafiyar shi, haka ya faru ne dan abinda ta bashi ya sha, shi yasa ya rasa tunanin shi ya hake mata Sosai. Komawa gefe yayi tare da kwanciya rub da ciki. A hankali barci me nauyi ya dauke shi. Kallon shi tayi sannan ta mike a hankali. Bata tsaya wanka a dakin shi ba, ta saka kayanta tare da fita daga d'akin bayan ta ajiye mishi wani tambarin da zai iya wargaza mishi kome har karshen rayuwar shi. ~~~ Sai da ruwan nan ya kare tsaf akan Fudail ya shigo Masarautan, koda ya shiga shashin sa ya nufa yayi wanka da ruwan zafi sannan yana wankan tare da murmushin abinda Mehran yayi mishi bai wani damu can ba, sabida ko shi aka yiwa haka iya hukuncin da zai yanke kenan. Dan haka babban abinda yake shirin akan Azizatul Nissah ce. ~~~ Munyi tafiya me nisa wanda muka bar yankin Farisa sannan muka nufi kuduncin jazziratul Arab, anan muka yada Zango. Tunda muka tsaya aka gama shirya mana tantin mu. Na shiga gurin Sultanah Amrah, na zauna duk da ba hira muke ba, amma kuma haka yana sani jin kamar ina tare da Ammyn na ne, dan haka bayan munyi sallah na kwanta a gurin, ita kuma ta cigaba da abinda take, lokaci zuwa lokaci tana kallon yadda nake barci. Hawaye ne ya zubo mata, ta girgiza kai sannan ta cigaba da aikinta, tana tuna abubuwa dayawa akan yaranta da mulki yasa ta manta da su. Tabbas mulki matukar baka nemi Izni Allah akan shi ba, zai iya kai ka ya baro ta, Kamar yadda ya kaita ya baro ta, sai dai ta wani gefen zata iya godewa Allah tunda akwai Ikram da Ilham, Yar gidan Abrad. Murmushi tayi bayan ta shafa kanta, tana me jin kewar Yaran ta. ... Zan iya cewa barcin da nayi me cike da gajiya da mafarkai marasa kyau da dad'i, karshe dai haka na farka da sunan Mehran. Da gudu Rahil ya shigo tantin. Da sauri ya iso gabana, fadawa jikin shi nayi ina haki. "Me ya faru?" "Mehran!" Na fada kamar zanyi kuka. Juyar da kan shi yayi. "Ba zaki daina kwadayin ganin shi ba?" "Karka raba ni da shi, zuciyata halittar shi ce." Matse bakina yayi idanun shi cike da kwalla. "Ni kuma sabida ke aka halicce ni, ina sonki Ikram. Nasan idan ba zama daya muka yi ba, ba zaki daina kwadayin shi ba" ya faɗa bayan ya cire hannunsa a bakina, kokarin hada bakin mu yake na kawar da kaina. "Meye kike nufi? Ba zaki." Ture shi nayi tare da mik'ewa, ya kuma tasowa yana kallona. Kamar zai yi kuka yace. "Meye yafi Ni dashi? Meye na rasa da ba zaki amshi tayi na ba, wallahi yau sai na dasa miki kaunata a ranki." Fada sosai muka yi da Rahil domin ya kafe sai ya fahimtar dani yadda yake sona. Ni kuma na rantse ba zan yarda da wannan tunanin na shi ba haka muka gama dakyar na kwaci kai na. Sam na kasa nutsuwa a raina, domin kuwa, haushina yake ji kamar ya kashe ni, bayan fitar shi Sultanah Amratu ta shigo, fadawa nayi jikinta ina kuka. Tare da cusa kai na a jikinta. "Zuwa yanzun ya kamata ki cire Sultan Aamaan Abdus Samad Mehran, a ranki domin kwanaki ƙalilan zaki kasance matar Rahil. Don ki daina tunawa da sultan Aamaan." Kallonta nayi baki sake, kafin na sauke idanuna kasa, ina kuka. "Ummyn!" Yatsar hannunta ta saka min akan bakina, tare da girgiza min kai. "Kowa yasan cewa kece kwarin gwiwar shi, ki taimaka ki sauko ayi kome cikin ruwan sanyi." Hawayen da nake tarewa suka daga cikin idanuna, na kasa magana baki daya sai kallonta nake. "Tsarin masarautar mu, cike yake da kawaici da YAKANA karki yarda ahalin Mahaifinki su fahimci kin sayar da zuciyarki ga wanin su. Domin haka tilin abin kunya ce gare mu!" "Toh dole ne sai na rayu cikin mulki? Me yasa ba zaku gan.." d'aga min hannun tayi tare da kallon, yadda bakina yake rawa. Kifa kai nayi a tafin hannuna, na fashe da kuka. Ina girgiza kai, Tashi tayi tare da bar min tantin kuma ta hana kowa shigo min, domin tana ganin matukar suka shigo min zan iya tsarewa. Gurin yan uwan Baba na, ta nufa suka tattauna. Anan suka ajiye shawara ita zata wuce Asakandariya su kuma su wuce dani can Merocco. Idan ita mace ce mai rauni tausayina zai iya sakawa ta bani abinda nake so. Su kuma ahalin mahaifina babu wannan yanayin a tare dasu, dan haka su tafi dani. Bayan ta dawo ne, take kallon yadda na kifa kai ka a saman gwiwar kafana. "Zaku wuce Merocco." Da sauri na d'ago kai na, zanyi magana ya juya min baya bata bani damar ma tambayarta ba, ta cigaba da abinda take, ni kai na nasan ba zan iya tababa da ita ba, amma kuma ya kamata su fahimci abinda nake so. Bayan mun huta aka kuma tadda tafiyar. Ina ji ina gani ta tafi da Nimrah. Ni kuma muka tafi da Izmah, bayan mun sha kuka. Tunda muka dauki hanya, banzan can yake wani shige min. Ko kallon shi banyi ba, har muka wuni a hanyar, dab Magarib muka shiga garin, wanda tun kafin mu iso labari ya iso musu muna kan hanyar mu, sakamakon wani mahayi da aka turo shi. Dan haka garin ya kasance kamar ana bikin sallah, wani irin biki ake me cike da shagali. Haka muka isa har fadan, inda aka muka yada zango a falon Sultan Mu'allim. Mika min hannun yyi. Da sauri na isa gare shi. Ina isa na zube gwiwata a kasa, kai na a bisa kafadar shi, na sake kuka me cin rai. Takaici yasa Rahil fita a gidan. Kuka nake wanda idan ka tambaye ni ba zance maka ga abinda aka min ba, amma kuma a cikin raina, ina kuka ne domin na rasa Mehran. Yadda nake kukan ya sashi sake murmushin jin dadin. Sannan ya shafa kai na, yace. "Kiyi hakuri! Haka muke tsara miki baki rayuwar. Da karen layi gwara Zakin gidanka koda kuwa zaka zane shi da bulala ne, kiyi dan mahaifanki da kanwarki. Ba akan ki da soyayyar ki ba. Mun rigada mun yanke kuma al'adunmu sun sha banban da kowane, mukan iya binne abinda muke so! Mukan iya boye abinda muke kauna, matukar hakan zai bamu damar fuskantar matsalar. A tsarin mu, bai zama dole mace ta samu abinda take so ba, matukar zata bawa Mulkin mu. Gudunmawa dan haka na zab'i ra'ayin shi sabida ki bashi gudunmawa. Yanayin ku yayi daidai da mulkin, abinda ake bukata domin mulki kin hada, dan haka ki amshi Rahil a matsayin abokin rayuwar ki." Hawaye ne ya shiga zuba min, na kasa magana tare da sunkuyar da kaina, domin yayi min kwarjini. Haka aka fitar dani har dakin Bilqisul Ikram, tankwarata. Shafa kaina tayi sannan ta kira amintattun bayin ta, suka shiga dani ban daki. Aka hada min wani irin ruwan wanka tare da turaruka masu dadi. Sai furen kamshi da wanka aka watsa a ruwan, sannan suka shiga cudani. Hawaye na zuba a idanuna. Shi kenan na rasa Mehran. Na rasa Jarumina, me yasa tun tuni ban amsa mishi ba. D'ago kai nayi sannan nace a raina. _Toh amma ai bai ce yana sona Ba? Toh amma kuma ai duk abinda yake min duk na soyayya ce! Kishi da zafin rai akai na duk abinda masoyi ne kaɗai yake yin shi! Toh Ni me yasa na shiga zab'en? Kenan bawai na shiga dan shi bane sai dan ina son shi?_ Kwalla ne ya zubo min, ban san lokacin da na fashe da kuka ba, haka suka taimaka min nayi wanka na fito bayan sun bani wani yadi na lullube jikina, tare da fitowa daga ban ɗakin, tunda na fito suka shiga shafa min wani abu kamar mai kamar sabulu, ina zaune ina kallon su. Kwallar da nake sharewa a kai a kai, yasa Bayin suka shiga rarrashina, kamar dama jiran su nake na fashe da kuka. Hannun daya daga cikin su ta saka min a bakina. "Abin kunya ne babba ga Sultanah Balkisu Ikram aji cewa babbar Yar D'anta na farko tana kuka akan SO kinsan yadda muke boye kalmar a ran mu kuwa? Toh koda kuwa zaka rasa ranka akan sone yana da kau kayi hakuri da shi, idan baso kike mulkin kasar nan ta gagari Amir Rahil ba. Don Allah ki hakura da Sultan Aamaan Mehran. Mun san yadda kike son shi, amma duk wanda zaki gani a cikin masarautan nan yana da tab'on soyayya, dan haka karki sake a Fahimci zuciyarki tana ga wani da namijin domin abin kunya ce ga Kakarki." Haka suka kashe ni da magana tare da nuna min illar abinda nake aikatawa, nayi kuka da sunan Allah kuma nayi bakin cikin zamowa ta, daya daga cikin ahalin babban gida. Ina ji ina gani ranar aka mai dani kamar wata yar tsana, zunzurutun wanke nan shafe ne. Ana gyara min jikina. Har kusan tsakiyar dare a sannan nayi wankar karshe tare da sallah na kwanta,. Ranar barci na zance kacokan mafarkin Mehran nayi tayi. Ina kuka ina kome haka zan farka naga bayin nan suna rarrashina. ..... Washi gari ina farkawa kafin nayi sallah asuba, suka bani madara dafaffiya,, sai da na wanke baki na shanye tass, sannan na shiga wanka tare da Alola ina idarwa, aka kuma kawo min yankanken y'ay'an itacce, wanda aka zuba madara da zuma na shanye shi, ina ji suna faɗin. "Kirjinta muke son ya cika kafin zuwa bikin su." Shiru nayi domin bani da bakin magana sai yadda suka yi dani... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 03 Wato ma'ana bani magani suke tare da abinci me gina jiki, duk abinda suke idanuna a rufe suke, bana budewa wani lokaci haka zasu yi ta magana ina jin su, bana tanka musu, idan suka gama min kuwa a gurin nake kwanciya. Ina kuka duk taurin zuciya ta da taurin kai na, sai da ya kai komi kashin b'acin rai kuka yake sani. Rabona da Izmah kuwa sai dai na shafe kwanaki goma kafin aka barta ta shigo min dakina, lokacin da ta ganin sai da ta firgita, tana mamaki. "Ikram! Baki da lafiya ne? Kinyi kyau amma kuma kinyi mugun rama, meye yake damunki? Me aka miki? Don Allah gaya min" Zama tayi a jiki na, ban san lokacin da na fashe da kuka ba, nace mata. "Izmah Mehran nake son gani" kamar wacce aka dasata, haka take kallona. Bakinta yana rawa tace min. "Sultan MEHRAN?" Ta kuma tambayana, gyada mata kai nayi tare da rushewa da kuka, rike hannuna tayi tare da kwantar da kaina a kirjinta. "Ikram!" "Don Allah Mehran;" na katse mata abinda zata fada, duk sai ta rasa abinda zata ce min, ta kuma bude baki zata yi magana, Amir Rahil ya shigo cikin ɗakin, yan mata na biye dashi. Mikewa tayi zata fita na rike hannun ta. "Kiyi hakuri zan jira idan ya fita zan shigo muyi Magana." "Wacce magana zaku yi? Ai akan wancan Jahilin da ya kasa miki uzuri ko? Ko akan Abrad da ya gama da budurcin ki? Kinga Ikram. Ina Sonki shi yasa zan dauki duk abinda ya same ki, amma kika Kuskura kika shigo da Mehran yake ko Aman yake? Wallahi Billahi azim, zan kashe wannan abin" ya nuna min Izmah, sauka nayi daga gadon na zube gwiwata a kasa, tare da rungumo Izmah, ina kuka nace mishi. "Kayi hakuri! Ba zan kuma maganar shi ba, amma karka tab'a lafiyarta. Idan nice na amince." Na fada cikin kuka, murmushi yayi tare da nunawa Izmah kofa ta fita, tunda ya shigo inda nake ya d'ago ni. Kallon kayan jikina yayi yadda ya fitar da surar jiki na. Nayi kyau na fitar hankali. Duhun fatar da nake dashi ya washe nayi wani irin haske me ban mamaki. Matsalar kawai rashin nutsuwar da bani da shi ne ya janyo min rama. D'ago kai na yayi tare da kallon fuskana. Kan shi ya kawo da sunan zai hada bakin mu na kauda kaina, murmushi yayi tare da cizon kunne na, rike rigar shi nayi tare da jin saukar kwalla daga idanuna. Na bakin ciki dan Allah ya gani bana son shi a mijin aurena, a dan uwan na dauke shi amma bai Fahimci haka ba, yayi ta shige min. "Ai da wancan banzan ne ba zaki na kuka kamar karamar yarinya ba, dake baki kaunata shi yasa kike kuka. Ikram me yasa baki sona? Ni dan uwanki ne kuma zan iya bada rayuwata domin." "Ba zaka iya, shi daya ya bada rayuwar shi domin ni, don Allah." Dama abinda yake nima kenan, kuma ya samu. Dan haka banyi wani abun da zai nuna mishi jin dadi ko bakin ciki ba, na dai rufe idanuna. Ya gama sumbatar bakina, sannan ya janye daga jiki na, ganin har lokacin idanuna a rufe suke, ya sashi fita daga d'akin yana murmushin jin dadi. Haka rayuwar mu yayi ta tafiya, ina zuwa shashin Sultan Mu'allim, yana bani wasu abubuwan da ya zama mallakar mahaifina, tare da wasu kyautattakar, haka zan dawo shashin Sultanah Balkisu Ikram, na zauna, shima sabida wancan wahalallen nake haka, idan a d'akin ta, domin yana shigowa zata kore shi. Haka ya sani tarewa a d'akinta, duk da kuwa d'akina na kallon nata ne, haka akayi ta gabatar min da y'ay'an gwamnonin nahiyar, tare da manyan mutanen ƙasar. Har zuwa lokacin Mehran shi yake da kaso mafi girma a zuciyata, na kasa cire shi a raina. Na sha tambayar kaina me yasa lokacin da nake tare dashi ban ji haka ba, sai da bamu tare? Wannan amsar har yau na kasa bawa kaina amsa. Kullum da wannan nake kwana nake tashi. "Ciki abincin mana!" Kallon Sultan Mu'allim nayi tare, sunkuyar da kaina, na tsakuri abincin na kai bakina. "Rahil yace min har yanzun baku fahimci juna ba?" Sunkuyar da kai nayi tare da kasa kai abincin bakina. Ajiyewa nayi zan mike yace min. "Zauna." Komawa nayi ka zauna, tare da damke hannuna, jikina yana rawa. "Kar na kuma jin labarin kinyi magana akan SULTAN Mehran! Idan kuma hakan ya faru, zamu kashe baiwar da kike kauna, domin idan bamu fito miki a asalin mutane ba zaki kunyata mu. Bamu son muyi miki dole shi yasa muka baki damar ku fahimci juna. Nan da wata biyu muka baki ki fahimci waye shi idan ba haka ba." "Taya zan Fahimci abinda kuke so? Bayan ni din ba mallakarku bace, ni bana son lusari." Dukar tabirin yayi tare da kallon Sultan Mu'allim. "Atta kana jin abinda harshenta yake faɗa." Kallona yayi sannan ya kuma maida kanshi ga Ikram. "Haka zaki zauna dashi domin baki da mijin da ya wuce shi." Mikewa nayi zan bar gurin Rahil ya taka rigar jikina, karar yagewar jikina, naji kallon shi nayi ban san lokacin da na wanke shi da mari ba, sai da ya firgice. Tabbas yayi kuskuren babba, amma kuma marin da tayi mishi shine mafi girman wulakanci da aka tab'a mishi. Shafa fuskar shi yayi sannan yace. "Atta! Marina tayi." "Me yasa ka taka mata rigarta? Matar da zaka aura bata bukatar tilastawa, kasan tana da wanda zuciyarta yake so kai kuma ka same ta ne a sama. Karka sake haka ya kuma had'aku." Juyawa yayi sannan ya cigaba da cewa. "Ke kuma za aka kaiki gidan horo." "Atta!" Ya kira sunan Sultan Mu'allim, murmushi yayi sannan ya d mishi. "Idan na yanke hukunci ko kaina bana saurarra dan haka, Bhaiq kazo ka tafi da ita." Ban yi gardama ba dan haka na amince aka tafi dani. "Atta don Allah." "Matar da zaka zauna da ita ta mare ka, me kake tunanin nan gaba zata aikata? Dan haka ka bari a nuna mata girmanka da darajarka." Jikin shi a matukar sanyayye ya bar gurin cin abincin, bai tsaya ko ina ba, sai gidan kakan shi na gurin Uwa wazir. Zama yayi cikin nutsuwa sannan ya gaishe shi, tare da yin shiru. Kasa magana yayi yana kallon yadda Rahil din ya nutsu, kafin ya ce mishi. "Ina jinka!" "Dama dama dama.." "Ka nutsu kayi min magana!"inji kakan shi, nutsuwa yayi kafin ya fadi abin da ya kawo shi. Da kuma dalilin da yasa aka rufe Ikram. Kallon son kai yayi mishi, tsantsan domin kuwa banda son kai babu abinda ya hango a maganar Rahil. "Tun lokacin da ka bayyana soyayyarta a ranka na gaya maka cewa ka rabu da ita, amma fir ka kiya, sai ma goyan bayan da kasamu daga danginka, ba wai Ikram nace bata sonka kai ne baka dace da rayuwarta ba, ai duk wanda yaga yadda ta bar kasar nan bayan ta gama maka aiki har ta kai da ta nuna ita ta mutu zaka fahimci akwai soyayya a cikin tafiyarta, amma zuciyarka dake a rufe take kaki yarda akan lallai ita kake buƙata " "Amma kuma taya gida bai koshi ba za a dauka akai waje? Taya ina sonta zan kyaleta ta tafi yanki mafi hatsari da ganganci da rayuwa? SAMAIND cike take da rayuwa da mutuwa! Kuskure daya idan mutum yayi mutuwa tafi kome sauki a rayuwar shi. Uwa uba zunzurutun makircin da yake cikin masarautan. Kaka nazo ne domin niman hanyar da Ka fidda ikram, idan ba zan samu ba na hakura nayi tafiya ta" Kallon shi yayi na tsawon lokaci kafin yace mishi. "Ta yaro kyau take bata karko, Ba zan daina gaya maka ba Ikram bata dace da rayuwar ka ba, Ka barta tayi rayuwarta da wanda take SO Ni dan taimaka maka, amma ba zan tab'a tilasta mata ba,.kuma ba zan mata dole kamar yadda kuka mata ba, zan bata goyan baya ta auri wanda take so." Mikewa yayi cikin fushi zai fita, har ya isa bakin kofar kakan Yace. "Kai ake bukatar ka zama sarki, idan har baka san yadda ake sadaukarwa ba yaushe zaka yiwa Al'ummar ka adalci? Ita saboda jarumtarta ake bukatar ta a jikinka, me yasa ba zaka zama jarumi ba kamar ita? Amma karka tilastawa zuciyarta yake cike da kaunar wani. Domin kana ji kana gani zaka yi danasanin rayuwa." Fita yayi daga cikin gidan, ya nufi can babban shashin. Inda ta zube a gaban Sultanah Balkisu Ikram. "Me yasa bani da Sa'a? Me yasa kowa yake min kallon mahaddami? Ni ne ban dace da Ikram ba ko ƙaddara ta ce bata dace da ita bane? Sultanah a tunanina ni Maraya ne, samun Ikram ne ya sani fahimtar ni me galihu ne, me yasa Ikram ta sani nake jin ni ba kome bane? Me yasa a kullum nake jin nayi son kai? A duk lokacin da na kalli Ikram sai na dinga jin a raina nayi son kai sama da kome a rayuwar mu, tunda ta dawo cikin gidan nan ban tab'a ganin ta dauki takobin domin kare kanta ba, me yasa?" "Sabida zuciyarta tana wani guri na daban, kaunar da take mishi ba boyayya bace, yadda take kuka akan shi ya tabbatar min ita din ba kowa bace a fagen SOYAYYA! Zai yi wuya ka hada soyayyar da Jarumta, amma kuma ana ana iya hada soyayya da yaki koda kuwa haka zai bada damar a shafe alkarya guda! Akan soyayya tana iya haifar da juyin juya halin a cikin masarautan! Akan soyayya akan iya shayar da sarki guba domin cimma manufar Soyayya! Irin soyayyar Ikram da Mehran! Idan ba ayi takatsantsar gurin nuna musu bambanci rayuwa ba, dole dayan su yayi rayuwa dayan su ya mutu? Soyayya ce ta shiga tsakanin zubda jini! Kasancewar dukkan su sun kasance, a cikin lambu. Ba zance shine ƙayar ba amma tabbas haka ya nuna min cewa soyayyar su kamar fure ne cikin ƙaya. Gashi da kyau amma kuma haka za a hakura da shi,.idan kuma ka nace kana so. Ba makawa kayar zata illata ka. Idan kuma ka hakura dole haka zaka ji ranka ya raya maka soyayyar furen da take ciki ƙaya. A halin yanzun..Ikram ta kasance fure cikin ƙaya ce. Duk inda Mehran yaƙe yana faffutikar ganin ya iso gare ta, idan ma shi bai isa gareta ba, ita tana kokarin isa gare shi" "Taya bayan tana gidan bada horo? Haka ba zai yiwu ba " Ya faɗa tare da kallon kakan shi. "Zai yiwu mana, kai abinda ka sani kenan. Ita kuma abinda ta sani zata aikata. Kayi hakuri da Ikram domin ita zuciyarta tana ga Mehran..kai ma ai akwai shukrah da take sonka me yasa ba zaka hakura da Ikram ba?" Ka sake yayi yana kallon kakar su, kafin yace mata. "Me yasa kika ce haka?" Gyara zama tayi sannan tace mishi. " Kai anan gabaki daya cikin masoya da dangi kake, Mehran kuma cikin makiya yake rayuwa, da ace yana cikin dangin shine da suke kaunar shi ba zata tab'a komawa gare shi ba" " Amma kuma ai dan daukar fansa ta koma gare shi. Domin rama abinda yayiwa Nu'man." Dariya tayi sannan tace mishi. "Waye ya gaya maka k'iyayya ce ta kaita gare shi? Duk wanda ya gaya maka ta koma ne domin rama abinda yayi mata toh yayi karya, soyayya ce ta maida ita da ɗaukar fansa ne ba zata tab'a amsar tayin shi ba, da ɗaukar fansa ne ba zata tab'a yarda ta amshi ragamar auren shi ba, kasan inda ake kurman Kaunar! Toh ka zuba ido zaka ce na gaya maka Allah ya bamu nisan kwana" "Yanzun Nanna duk soyayyar da na mata ya tashi a banza Kenan? Na sota iya so babu algus me yasa na rasa ta? Soyayyar ta nake mata babu cutarwa a cikin shi amma me yasa ba zan same ta ba? Don Allah Nannah ki taimaka min na same ta. Dan itace abokiyar rayuwa ta...." [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 04 Murmushi tayi tare da ɗaukar ruwan da yake gabanta ta kurb'a, sannan ta dauke kanta kana ta cigaba da cewa. "Ba zan ce ka hakura da ita ba, domin ba a san maci tuwo ba sai miya ta kare, wayallah kayi nasara wayallah kuma ka fadi wannan shine abinda zan gaya maka." "Amir SULTAN yana niman ka" a hankali ya juya tare da kallon Bhaiq, sannan ya tashi tare da bin bayan shi. Suna shiga ya zauna a gaban Sultan Mu'allim da Wazir. Shiru duk suka yi sannan Sultan yayi gyaran murya yana faɗin. "Kaje ka tawo da ita" "Toh Atta mun gode." Daga haka ya juya ya bar gurin su, yana kara godiya. Bayan fitar shi Wazir ya kalli Sultan."ina ganin me zai hana ka hakura da wannan hadin da zaka yi ka barta ta akan zab'in ranta, tunda shi Rahil yana da masoya babu amfanin a tirsasata yin abinda bai dace ba." D'ago kai yayi sannan ya sake wata wadatacciyar murmushi kafin yace mishi. " Koda Rahil bai ce yana sonta ba, bana jin zan barta ta auri wani bayan shi, tunda kuma yace yana sonta sai naji faduwa tayi daidai da zama, abinda nake buƙata ne Allah ya kuma biya min bukatar, dukkan su mallakina ne!" "Allah ya huci zuciyar ka, ba wai ina nufin wani abu bane, sai dai idan har aka bata wanda take bukata haka kamar karin daraja ce ga masarautan mu, Yar mu tana auren Sarkin Samaind ka duba abinda idanun basira mana." Lashe bakin shi yayi tare da sunkuyar da kanshi yana wasa da furfuran kanshi, sannan ya kalli Waxir ya sake wata ƙaramar murmushi yace mishi. "Eh na hango katin ci-gaba amma bana jin a raina haka wata masalaha ce, babu cigaban da zata kawo ma, sannan babu wani abinda zai bayyana mana na cigaba dan tana auren Sultan Aamaan Abdus Samad Mehran! Kawai haka ba wani abun azo a gani bane dan babu wani Cigaba da za a ce an samu dan kawai tana auren Sarkin Samaind!" Shiru Wazir yayi yana kallon yadda Sultan Mu'allim, kasa yayi da kan shi ya kuma cigaba da cewa. "Sultan akwai matsala domin Ikram bata son shi da Aure a matsayin d'an uwan ta dauke shi, kuma haka ba zai tab'a kawo zaman lafiya, ido da ido kuke wariya akan ta, kuna nuna mata dan ita mace ce, ba zata zab'i abinda take so ba, sai shi? Haka zai sanya tayi ta mishi kallon ya fita daraja a gaban ku, sannan haka zai sanya tayi ta jin ina ma bata dawo gare ku ba, ban san yadda zan gaya maka kuna cusa k'iyayyar ku a zuciyar ta ba, amma tabbas babu adalci a tsarin ku." Shiru yayi sannan yana nazarin abinda Wazir ya faɗa. ... Ina zaune sai gashi ya shigo, kallona yayi sannan ya sake murmushi yana faɗin. "Bilqisul Ikram!" Dauke kai na nayi ina murmushin bakin ciki, takowa yayi har ina nake zaune. Durkusawa yayi tare da kifa min mari, sannan ya d'ago kai na, tare da yana kallona. Murmushi yayi sannan yace min. "Baki isa ba! Kinyi kaɗan Ikram marina kika yi? Idan da kin dake ni, yanzun baki isa ba." Tofa mishi yawu nayi tare da kallon shi har cikin idanun shi. Share fuskar shi yayi tare da wani irin murmushin takaici. Mikewa yayi sannan tare da cewa. "Ku kunce hannun ta, tare da kawo min ita shashina." Ya faɗa tare da ficewa daga dakin, tunda suka kunce hannun, suka tasa keyana har shashin shi, tunda nake da Mehran bai tab'a nuna min karfi ba, bai tab'a kawo min farmaki ba, yau sabida soyayyar shi Rahil yake nuna min karfi. Tunda na shiga ya saka ni a gaba da bala'i, domin karfi da yaji ya fara kokarin keta min rigana. Dakyar na kwaci kaina, yana ganin haka ya kuma shake ni tare da matse min nonuwa na, kuka ne ya kwace min tare da kallon shi. "Me yasa kake son lalata min rayuwa? Tunda nake da Mehran bai tab'a kawo min hari ba, kullum mutuntani yake tare da girmamani, na kwana a daki daya da Mehran na kwana a jikin Mehran hannun shi bai tab'a isa cinyata ko kirjina ba, bai tab'a kawowa a ranshi zai iya amfani da karfi ba. Yau d'an uwana yake son keta min mutuncina sabida nace bana son shi!" Murmushi yayi sannan ya mike tare da ture ni, ya nufi ban dakin shi yana ji kamar zuciyar shi zata fita, bai dan me yasa yake jin babu dadi akan Ikram ba, kuma ba kome ya janyo haka ba, sai dan yadda take nuna soyayyar Mehran a sama da kome. bata tausayin shi kamar yadda take nuna mishi da, yanzun ga baki daya ta tsane shi sabida Mehran, da zai ga Mehran tabbas sai ya kashe shi. Ya tsani Mehran ya tsani rayuwar shi. Kuma Insha Allah sai ya raba ta da kimarta koda kuwa ba zai same ta ba. Kafin ya fita na tashi tare da ɗaukar alkyabar shi na saka, sannan na nufi shashin mu. Tunda na shiga na zube a tsakar dakin na sake wani irin kuka me mugun cin rai, ina tuna Mehran. Ga baki daya naji na tsani kai na, me yasa a daren da nake duba shi ban bashi kai na ba, koda kuwa ace haka zai janyo min jifa ranar Amarcina. Kuka ne ya kuma kwace min, shigowar Ruwaida da Izmah ya sani juyawa ina kallon su, zama suka yi sannan suka ce min. "Abinda kike babban Abin kunya ne, ace yau kina kuka akan SO, WALLAHI ABIN GORI KIKE AIKATAWA UWAR DAKINA DON ALLAH KARKI KUMA ZUBDA HAWAYEN KI SABIDA SO" Dafa kafana Izmah tayi sannan tace min. "Kiyi hakuri Ikram!" Rintsa idanuna nayi.tare kifa kaina akan cinyar Izmah tana shafa min gashina, sallamar Ruwaida tayi tana kallon yadda nake zubda kwalla. "Ikram ki daina kukan nan, kiyi hakuri Insha Allah idan Mehran ne rabonki zaki mallake shi idan kuma ba rabonki bane shi Allah ya sassauta miki halin da kike ciki." Haka tayi ya rarrashina, har barci ya dauke ni. Gyara min kwanciya tayi tare da jera min matashin a kaina. Kallon Ikram tayi cikin damuwa, tana tuno abubuwan da suka faru, a baya tabbas wannan kadai ya ishi me hankali fahimtar hikimar Ubangiji, duk wannan zafin yanzun duk babu. Sai sanyin da tayi gabaki daya ta zama wata iri mara amfani. Bata iya fada bata iya rigima babu zafin rai babu kome sabida so tayi watsi da kome. ~~~ SAMAIND Kimanin wata daya kenan, kallon juna Jasrah da Mahlika suka yi cike da mamaki, jin likitan masarautan yana tabbatar musu da cikin da Azizatul Nissah take dashi. Saka su mutuwar tsaye. Shi kan shi Mehran kura mata ido yayi. Tabbas ya kwanta da ita tun daga lokacin da ya sha maganin ba sau daya ba ba sau biyu ba. Yasha Narjis ta kawo mishi ita, amma kuma bai tab'a kawowa a ranshi zai mata cikin ba. Domin idan ya tuna duk abinda yake da ita bawai yana mata yadda zata ji dadi bane yana mata yadda zata wahala ta gudu ne ya sami abinda zai kafa hujja dashi sai ga cikin shi ya isa kafa hujja. Wani irin yanayi yake ji na gamayyar damuwa ko tashin hankali. Kallon Azizatul Nissah Fudail yayi domin ya fara gajiya da tashin hankalin da yarinyar ta Kunno mishi wanda shima yasan laifin shine da ya gayawa Mehran wancan lokacin da yaci Ubanta amma yanzun ko ya faɗa zasu kira shi da d'an dakin Ikram ne, shi yasa ya zuba mata ido, yana kallon yadda take kokarin daurawa Mehran cikin da bana shi ba. Babu babban wawa sai shi. Yayi kuskuren barinta da cikin bai gayawa Mehran ba, da ya gayawa Mehran da kome bai faru ba, kuma dan kayan haushi ko Sultanah Fazilatul nisa bai gayawa,.yaja bakin shi yayi shiru dan wauta. "Sultan MEHRAN! Muna taya ka murnan samun Magaji Allah ya sauki Amirah Azizatul Nissah lafiya ta haifa mana Yarima." Cikin karfin iko da mulki tace musu.. "Insha Allah sai dai Na haifi Sultan Abdus Samad Aamaan Mehran, na biyu." Kallonta suka yi tare da kauda kansu, idan. Suka ci-gaba da tsayuwa zata iya saka su fidda abinda yake ransu. Dan haka suka juya tare da barin d'akin, suna mata fatan Alkhairi. Zama yayi a kusa da ita yana kallonta. "Ya jikin naki?" Murmushi tayi sannan tace mishi. "Da sauki, ina son cin abinci amma ina tsoron kar a bani guba sabida kishin rashin samun damar daukar cikin ka." Mikewa yayi tare da barin d'akin, murmushi tayi sannan ta shafa cikin Jikinta, kallon Fudail tayi da ya kura mata ido, tabbas badan kar yayi abinda zai sanya Mehran ya kullace shi ba, da yayi ta dukar cikin jikinta, har dai ta mutu. Amma a halin yanzun kana tab'a cikin kamar ka sayi mutuwa je da hannunka,domin Mehran ba zai tab'a barin ka a raye ba. Amma kuma taya haka ya faru? Cikin a sanin shi na Nawwas ne, kuma sai gashi ya juye tare da komawa na Mehran,.kuma babban damuwar shine meye ya faru ranar da ta fara kwana da Mehran. ---- Kallon ta Sultanah Hoyam tayi sannan tace mata. "Kamar Ya Azizatul Nissah tana da ciki? Kina nufin yayi tarayya da ita ne! Ko kina nufin." Zuɓewa Mahlika tayi tare da rike hannunta cikin juna jikinta yana rawa tace mata. "Sultanah! Duk abinda kike tsammani haka ne". Ture kayan gabanta tayi tare da cewa. "Na aike ki ne ki zo ki gaya min matar da suke kewayen shi.tana da ciki ne? Meye amfanin abinda na baki kina saka musu a shayin su? Wato ga sakarya nan bata san me take yi ba, Yanzun meke tafiya a harem?" "Kiyi hakuri abinda ke faruwa babu dad'i domin dai ta kwace duk abinda ake yi, sannan kuma ta hana kowa shigowa shashinta. A takaice dai hatta abincin da zasu ci sauran matan daga gare ta yaƙe.". Sake wurgi tayi da kayan marmarin gabanta. "Wani irin hauka kika yi ne? Me kika aikata min haka? Baki da hankali da zaki bari kome ya koma hannunta, ni kuma nawa aikin fa?" Sake damke hannunta tayi iyaka razana ta razana, amma bata iya ko tari ba, domin Sultanah Hoyam ta isheta riga da wando, dan haka ta sunkuyar da kanta, sannan tace mata. "Ki gafarce ni!" "Tashi ki fita!" Ta daka mata tsawa. Da sauri ta mike tare da barin d'akin, ta nufi harem. Ajiyar zuciya ta sauke yafi sau uku. Sannan ya nufi Harem, tunda ta nufi hanyar gidan, take jin kamar zuciyarta zata buga, tana shiga tayi karo da Rubina babban baiwar Azizatul Nissah. "Ina kika tafi? Toh muje zaki yabawa aya zakinta, tunda da zaki fita baki gayawa Sultanah Azizatul Nissah ba. Wato anje kitsa munafunci ko?" Bata ce mata kome ba, har ta shiga gurin Azizatul Nissah, kanta a sunkuye. Tana shiga ta tsaya daga bakin kofar shiga d'akin. "Da izinin waye kika fita daga Harem?" Shiru tayi tare da wasa da warwaron hannunta. "Kinawa Ikram Aiki ne?" Da sauri Mahlika ta d'ago kanta, tare da girgiza kai tana faɗin. "Me kuma zanyi mata bayan bata nan!" "Ki min shiru! Koda yake ba mamaki kinawa Jasrah aiki ne ko? Toh zo nan." Durkusawa tayi a gabanta, tare da matsawa kusa da ita. Babu tausayi ta shiga marin Mahlika, sosai fa tun yarinyar tana jurewa har ta kasa jurewa, bata fasa ba, shigowar Mehran ya sata sauke hannunta da ta d'aga, zata kuma marin Mahlika. "Meye haka?" "Sultan MEHRAN! Abu ta kawo min da guba, wai ikram ce ta bata sakon duk lokacin da ta sami labarin ina da ciki ta zuba min nasha." Ta faɗa tare da sake kuka. Wangale baki yayi tare da kallon su, kara kallon Mahlika yayi yasan yace mata. "A sanina baki shiri da Ikram meye gaskiyar abin da ta faɗa?" ... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 5 Jikinta ne ya dauki rawa, tana kallon sharri kiri kiri. Amma bata da ikon kare kanta, kallon ta yayi a karo na biyu fuska babu alamar wasa yace mata. "Ba dake nake ba?" Ya faɗa da dan karfi, haka ya sanya ta kuma rud'ewa tana zaro idanu. "Sultan!" Ta kira sunan shi jikinta yana wani irin rawa."Fudail!" Ya kira sunan Fudail ko rufe baki bai yi ba, sai gashi shigo d'akin. "Yawwa bawa Fudail ka tafi da ita,.ka kuma tabbatar ka hukuntatta, domin tayi yunkurin zubda min cikin jikina ko Sultan Mehran" ta ambaci sunan Mehran tana kallon shi. Dauke kan shi yayi tare da zama ya kasa cewa kome. "Zaku iya tafiya!" Ta kuma fada, tana murmushi. Matsowa tayi kusa dashi, ta zauna tana me sake mishi murmushin jin dadi. "Sultan MEHRAN! Kaga ikon Allah baka ta samu haihuwa ba sai a kaina, kuma." Juyawa yayi yana kallonta,.kafin ya dauke kanshi yana me jin b'acin rai akan yanayin da yake ciki. Haka tayi ta damun shi da magana, ganin yaki kulata yasa ta mike tare da barin d'akin, bin bayanta yayi da ido, ita kuwa tana fita bata tsaya ko ina ba, sai Shashin Sultanah Fazilatul nisa, tana tare da Shairah da Narjis, suna tattaunawa ta shigo. Murmushi tayi sannan ta nemi guri kusa da Sultanah tace mata. "Nazo ne ki albarkaci jikanki da yake cikin mahaifana" A matukar mamaki suka kalle ta, bakin su sake. "Sultan MEHRAN bai gaya miki bane? Ai wata biyu da suka wuce ya..." "Toh ya isa!" Inji Shairah, ya daka mata tsawa. Gyara zaman tayi cikin fusata tace mishi. "Kai waye? Bawa dan daudu, ni zaka dakawa tsawa? Lallai kana son na saka a maka koran kare." "Ya isa haka, me kike bukata?" Inji Sultanah Fazilatul nisa. Tana kallonta, Dariya tayi sannan tace mata, "Bana son a kuma barin Mehran yayi mu'amala da wata mace! Sannan bana son ana shiga shirgin shi. Idan da hali a fita hanyar shi. Domin nice Magajiyar sarauta nan gaba, Uwar Yaron shi da yake kwance mahaifana!" Ta mike tare da zaga dakin tana murmushin mugunta, tana faɗin . "Mugun hukunci zai tabbata a kan wanda ya Kuskura ya shiga lamarin Mehran. Zan gyara mishi tunanin shi da nazarin shi, kar na kuskura naji mugun labarin akan haka, a sanar da matan da suke dakon ya kwana dasu." Tana gama fadar haka ta bar dakin cikin jin dadi tare da jin ta isa domin ta kaftawa Sultanah Fazilatul nisa kashedi kuma hakan zai taimaka mata, domin idan ba haka ba tana ji tana gani sauran matan da suke hareem zasu iya daukar cikin Mehran. Koda ta fita, kallon matan da suke hutawa tayi, sannan ta zauna tana gyara gashin kanta, tana murmushi. Baiwarta Rubina ta kalle matan gurin ta shiga musu bayanin cikin Azizatul Nissah, take Jasrah ta mike tana faɗin. "Karya ne, baki isa ki" "Kawo min ita nan" inji Azizatul Nissah, babu musu aka kawo ta, jefata aka yi a gabanta, mik'ewa tayi a hankali, tare da kallon ta. Murmushi tayi sannan tace mata. "Kika ce me?" "Kar..." Kifa mata marin da tayi yasa ta had'iye maganar da zata yi. "Rubina, ki zane min ita." Inji Azizatul Nissah wai a zane Jasrah. Duk sauran matan hatta Sakeenatu binti Abu Waqqas, sai da jikinta yayi sanyi, domin tunda take rayuwa bata tab'a tsintar kanta cikin mugun yanayi ba, sai da ta shigo cikin Samaind. Akan idanun su, aka zabe Amirah Jasrah irin mugun dukar nan da babu wanda ya isa yayi maka ita sai mugu. Shafa Jelar gashin kanta tayi tana faɗin. "Ya isa haka, ba ita ba hatta ku idan kuka kuskura kuka d'aga min murya zan ba kowa kyautar hukuncina, ku dauke ta ku kaita shashinta." Cikin wani irin tsoro da fargaba tabbas Azizatul Nissah ta shirya fuskarta kowa kuma a cikin wannan yanayin, ta gaya musu ciki ne da ita, dan haka kar kowa ya taka shashin Sultan Mehran sai da izinin ta. Gyada mata kai suka yi. Domin babu wata hanya da zasu mata bori. ---- "Meye ya hadaki da ita har ta sako Ikram a maganar ta." Fudail ya tambayi Mahlika. "Kawai sharri take son yi mata, kuma tasan a halin da Mehran yake ciki na kewar Ikram zai iya tsanar." Rike bakinta tayi tana kallon shi. Murmushi yayi sannan yace mata. "Karki damu. Yanzun me kike ganin zaki yi?" Shiru tayi sannan ta sunkuyar da kanta kasa, tana me jin kamar tace mishi zata koma Madinatul Mah, sai kuma ta d'ago kai tana faɗin. "Babu abinda zanyi." "Ni kuma zan sakaki aiki" ya faɗa mata yana leka hanyar, a hankali ya matsa tare da gaya mata abinda yake son tayi mishi, zaro idanu tayi sannan tace mishi. "Zanyi amma da sharadin. Zaka hada ni da sultan Aamaan! Murmushi yayi sannan yace mata. "Ba zan iya hadaki dashi ba, mutum ne me ra'ayin kanshi, idan kika sami damar ya gayyace ki toh idan kuma baki samu wannan damar ba, ina me tuna miki aikina da na baki. Sultan MEHRAN yana cikin kewar Ikram ne ko yayya aka tunzura shi zai iya aikata wani abu bayan haka." Yana gama gaya mata haka ya juya abin shi ya barta a gurin. Shiru tayi na wani lokaci kafin ta bar gurin tana jin itama zata tsayawa kan. ...... A can cikin gidan kuwa, kallon Juna ake tsakanin Sultanah Fazilatul nisa dasu Shairah. Kura musu ido tayi kamar tana son gano gaskiyar abinda Azizatul Nissah ta faɗa, sai kallon su take kamar tana hango abinda. "Ina Mehran? Maza ku nimo min shi." Ta faɗa da karfi. Kallonta suka yi kafin suka ce mata. "Yanzun lokacin hutawar shi ce, idan muka." "Nace ku nimo min shi ko?" Babu musu suka fita, shashinta suka nufa, inda Shairah yayi karo da Sultanah Hoyam, itama tana kokarin shiga shashin Sultan Mehran. "Dama kana raye?" Murmushi yayi sannan yace mata. "Ina nan daram." Ya bata amsa. "Toh haka ma yayi, sai dai har yanzun baka gaji da bautawa matar da bata san ƙaruwar ku bane." Murmushi yayi sannan yace mata. "Gaskiya labarin da nake ji bai kai adadin abinda zaki bani ba, koda yake ai girman jiki gare ki bana shekaru ba, idan kika sake mummunar alaƙar da kike da Darakshan ya fito tabbas." A firgice take kallon shi. "Karka min Sharri!" Sassauta muryan shi yayi sannan yace mata. "Karki damu, babu wanda ya fahimci haka sai ni, kuma babu wanda zai fahimci abinda kike aikatawa sai har kin tonawa kanki asiri." Daga haka ya wuce ta bai kuma mata magana ba, karshe bata shiga gurin Mehran ba, ta koma da baya. .... Yana shiga ya same shi zaune ya faɗa cikin mugun tunani me shegen zurfi, dan ya jima akan shi kafin ya mishi magana ya farka. Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya kalli Shairah. "Sultanah tana son ganin ka!" Kurawa Shairah idanu kamar wanda yayi mantuwa, a hankali ya janye daga kallon shi tare da gyada mishi kai, fita yayi cikin tausayin MEHRAN, domin baki daya yayi laushi. Tausayin yadda soyayya ta maida shi yake. Ya jima yana nazarin abinda yake damun shi wanda yayi itifakin Babu shakka Ikram itace rayuwar shi, sannan bayi da wani kuzari sai idan tana tare da shi. Ya san a wannan lokacin tana tare da Rahil. Suna soyayyar su. Haka kawai idanun shi ya shiga hango su, suna hira a lambun suna soyayya. Watsi yayi da kayan gaban shi,yana haki. Kwalla ne ya cika mishi ido, a hankali ya kai hannun shi kirjin shi yana jin kamar zuciyar shi zata buga. "Innalillahi wa'inna ilaihi rajioun Ubangiji ka yayye min, ka kuma kara min hakurin rashin ta. Ya Allah ka jarabce ni ta inda ba zan iya cinyewa ba. Ya Allah na tuba ka yafe min." Ya faɗa tare da jin kwalla nason zuba daga idanun shi mai dasu yayi, tabbas yana cikin wani hali, Ikram ta shiga rayuwar shi. Ya jima sosai a gurin kafin ya daidaita nutsuwar shi yayi sannan ya fita daga dakin. --- tunda ya isa shashin Sultanah, bai ce kome ba sai dai duk tambayar da tayi mishi baya ko motsi balle ta saka ran zata sami amsar tambayoyinta. "Aamaan" ta kira sunan shi kamar ,zata fashe da kuka tana cewa. "Meye gaskiyar abinda." "Anneh bana son kina shiga cikin al'amarin gidana." Daga haka ya mike zai bar d'akin tace mishi. "Amma me yasa ba zaka gaya min abinda yake damun ka ba?" Juyawa yayi tare da sake murmushin takaici, sannan ya bar dakin yana ji kamar ya had'iye zuciyar shi ya huta, ranshi ya kai kololuwar ɓaci, baya ganin gabansa. Yana shiga cikin d'akinta ya tokari kofar shi, kallon shi tayi a razane. Amma ta dake, juyawa tayi tare da kallon bayin d'akinta. Da sauri suka fita, Da sassarfa ya isa gabanta, zai kamo wuyar ta, tayi baya tana girgiza mishi kai. "Duk abinda aka gaya maka karya ne, tunda suka ji labarin samuwar cikin jikina suke kokarin ganin bayan shi, sabida." "Na tambaye ki ne? Nace kiyi min magana ne? Meye ya kai ki shashin Mahaifiyata." Ya tambaya ta a tsawace. Diriri cewa tayi kafin ta saka mishi kuka, tana faɗin. "Ita Fazilatul nisa ce Mahaifiyar ka?" "Tauuu!" Ya kifa mata mari, wanda yasa ta ganin taurari, a hargitse ta d'ago kanta, wani shegen tsoro ne ya kamata bata san lokacin da ta sunkuyar da kanta ba, gwiwarta zube a gaban shi. "Na kuma jin labarin haukarki ta kwashe ki har kofar shashin ta, sai na karya ki na maida ke yankin ku, kije can kuyi ta haukar ku sakarya." Yana gama fadar haka ya juya tare da barin d'akin, tunda ya fita yake jin kamar ya tattara ya bar SAMAIND ko zai sami sauƙin damuwar da yake ciki, amma ina. ---- Dan haka ya tattara ya koma can gidan shi da ya tab'a zama, dan anan yake jin zai iya samun nutsuwar da ya rasa. Tare da Fudail suka koma sai masu kula da abinda zai ci, sam baya son magana ko da kuwa a cikin mutane ne, yafi son ya keb'e kanshi yayi shiru. ---- Merocco. Da wani zai gaya min yadda rayuwata zata koma ba zan yarda ba, dawowar Nimrah bai kara min kome ba, sai damuwa domin tunda tazo bata da wani aiki sai kukan halin da ta sami Mahaifiyarta, ga kuma soyayyar Fudail da ya kamata, kwanciya tayi a jikina. Tana zubda kwalla, tare da gaya min halin da take ciki. Shafa kanta nayi domin ita kukan dad'i take, kuma nasan zata sami abinda take so ni kuma fa? Waye zai bani abinda nake so? Sam mulki da nasabarta bata dace da rayuwata ba, ni rayuwar Yanci nake so. Bana bukatar kome bayan Yanci, shi yasa da zan mallaki Mehran tabbas zamu bar SAMAIND har karshen rayuwar mu, mu shiga inda ba za a kuma ganin mu ba, muyi rayu daga mu sai Yaran mu. Wannan shine tsarin da nake shirya mana,.kamar Yadda iyayena suka bar gidajensu, haka mu ma zamu bar cikin daular mu. Muje mu kafa kanmu tare da boye asalin mu. "Assalamun Alaikum!" Sallamar Rahil ya katse min nazarin da nake. Lumshe idanuna nayi kamar ina barci, shigowa yayi tare da zama yana kallon yadda na sunkuyar da kaina, murmushi yayi tare da cewa. "Toh meye laifin sallamar da ba za a amsa min ba?" Ya tambaye ne ni, tare da tsare Ni da ido. Mikewa Nimrah tayi tare da kallon shi tace mishi. "Barka da shigowa Amir Rahil," d'aga mata hannun yayi yana murmushi, a hankali ta bar d'akin. Dawowa gabana yayi tare da zama ya zuba hannun shi akan cinyata. "Me yasa kika fi son shi akan Ni? Meye bani dashi? Dame ya fini da kike zubda hawayen ki sabida shi?" D'ago kai nayi ina kallon shi sannan nace mishi. "Kai zab'in kakannin mu ne, shi kuma wani shashi ne na rayuwa ta, zan amshi aurenka ne...[5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat Book3 _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 6.. Cike da mamaki yake kallon yadda nake kokarin gaya mishi gaskiyar da ya kasa Fahimta, so nake lallai ya gane babu dole a soyayya. Kura min ido yayi tare da sake murmushi yace min. "Koda zaki na yankan namar jikina kina ɗona min gishiri zan zauna da ke haka kuma zan kare rayuwata dake!" Murmushi nayi mishi tare da shafa kanshi nace mishi. "So bai maka adalci ba, kamar yadda ya ratsa tsakanin zukatar mutanen da basu shiryawa zanen ƙaddarar su ba, ba zan hana ka ba." Rike hannuna yayi cikin na shi sannan ya matse a hankali, yana murza yatsuna hannun. "Ikram ni na dace dake, karki manta zan zauna dake a duk yadda kike, Ikram ina tsananin kaunar ki" Rike hannun shi nayi cikin nawa tare da kura mishi ido, ina hango iyakar gaskiyar shi. Dauke kai nayi tare da cewa. " Nasan kana sona, amma ya aka ji idan ka taso daga sahara me matsanancin zafin rana, sannan kuma kana murnan zaka tsallake kana hango koramar ruwa, kana isa ka sami ruwan an hanaka sha. Ya zaka ji? Toh haka ka shiga tsakanin mu." Mikewa nayi zan shiga ban daki yace min. "Zan iya hakuri dake har zuwa lokacin da zaki soni amma Tabbas zan aure ki. Kuma zan zauna dake." Cak na tsaya sannan na juya ina kallon shi, kafin nace mishi. "Zaka zauna da ni Tabbas zaka ƙunshi bakin ciki, domin zan zame maka kamar ramin maciji ne, kowani motsi kayi da dafina zaka motsa, bana son mu kai ga haka shi yasa nake gaya maka illar haka." Na shige abuna. Shiru yayi tare da jin babu dadi a ran shi, amma kuma babu yadda ya iya, dole haka ya saka kai ya fice daga d'akin. Tunda na shiga ban daki na fashe da kuka, tare da zama a gurin ina kuka, Tabbas na san yana sona, amma haka bayana nufin zan iya rayuwa da shi bane, Mehran shine zab'i na, Rahil dan uwana ne shi. Ban shirya zama dashi a matsayin abokin rayuwata ba. A hankali na fito daga ban dakin ina sauke ajiyar zuciya, tare da zuɓewa a jikin gadon dakin ina jin kwalla na zuba min. Mehran shine zab'i na, shi din farin cikina ne..idan ana iya musayar so ba zan tab'a musayar Soyayyar shi ba, ina mugun son shi, a lokacin da ba zai min amfani ba. Lokacin ya gama kure mana, dan haka na had'iye kukan tare da kifa kai na a jikin gadon, ina jin wani irin kewar shi. *** Takowa yayi har gaban gawar da masunta suka dauko shi daga ruwa. Babu abinda ya sami gawar, kamar bai jima da mutuwa ba, sai hasken fatar da yayi irin fari fauu din nan. Kallon gawan Nawwas Fudail yayi sannan yaja mayafi ya rufe kafin yace. "Wannan gawar shugaban dakarun daular Umayyad ne, dan haka ba zamu binne shi ba, sai mun san ta yadda aka yi gawar ta wanzu a cikin yankin mu." "Toh shugaba!" Suka amsa mishi. "Kwanakin Baya mun ga lokacin da ya shiga wata jirgi, tare da a yarin daga nan ne na shiga jirgi na, na haura saman Teku, daga nesa na hango lokacin da ake jefa wani a cikin ruwan amma ban sani ba ko shine ba." Gyada kai Fudail yayi lokacin jin da yaji bayanin wani mutum da yaga lokacin da Abrad yasa a wurga gawan Nawwas a ruwa. Murmushi yayi sannan yace mishi. "Toh babu kome zamu bincika." Gaba yayi sannan dakarun suka ɗauki gawar a makara, suka nufi cikin garin SAMAIND da shi. ..... Kallon Mehran Azizatul Nissah tayi tare da toshe bakin ta, tana me fashewa da kuka, da gudu ta nufi hanyar da zai sadata waje, Bin bayanta yayi sabida karta tab'a lafiyar cikin jikinta, zuɓewa tayi a gaban gawar tana kuka da ihu, sabida yadda ta ga gawar shi bata kawo hakan ba a ranta, dakyar Mehran ya d'aga ta, ya koma da ita, sai da aka gama bai bincike sosai, kafin aka nad'e gawar aka mishi jana'iza. "Zan tafi gida, ina ganin babu wanda yasan da labarin mutuwar shi don Allah karka hanani." Shafa kanta yayi tare da maida gashin ta baya, yana me jin tausayinta a ranta, sannan yace mata. "Ba yanzun ba sai kin haihu." Wani irin kuka ne ya kwace mata, bata san lokacin da ta kuma sake kukan ba, ta rike hannun shi tana faɗin. "Toh taya zasu sami labarin mutuwar shi." "Zan aika da sako a gaya musu. Insha Allah" sake rungume ta yayi, ta kuma narke Mishi kamar wacce take cikin tashin hankali na gaske. Haka yayi ta rarrashinta, domin kuwa baki daya ta birkice mishi. Kwana biyu tsakani idan ka ganta zaka Dauka jinya tayi nan kuwa dauke hankalin shi tayi da makirci kamar mutuwar ya dake ta. Duk da kuwa ta kadu da mutuwar amma ba wani jijjiga ta ba, sabida cikin jikinta kar yace dai kwace abin shi, ko wani dalili da zai fito ya fadi gaskiyan cikin nashi ne, Tabbas akwai matsala domin haka zai iya janyo yakin da za a rasa rayukan al'umma, sannan itama bata tsira ba, kisar wulakancin za a mata a gaban jama'a. Dan haka mutuwar Nawwas yazo mata a gaɓɓar da ya dace, dan haka bata ga abinda zai wargaza mata lissafin ta ba. Shima Mehran duk ya damu, domin a tunanin shi da gaske take, dan haka duk ya shiga damuwa duk da yana cikin damuwa, amma sai ya tsinci kanshi da tausaya mata sosai, har yakan zauna yana b'ata lokacin shi akan ta, ita kuma haka sai ta narke tayi ta nuna alamar bata ita fa tana kewar gida, dan haka ya taimaka ya kaita ko da yayya ne yan uwanta sun san yadda take ji gashi babu wanda ya san da mutuwar sa ita. Dan kar ya samu damar da zai nufi gurin Sultanah Fazilatul, yasa ta baki daya ta kawo mishi yanayin da take ciki, yana fita sallah zata ware, ko kuma tayi ta kuka, asalima ta hana shi ko zuwa fada, domin yana fita zata saka rigima haka zai dawo matan da suke dakon shi kuwa haka suke jin babu dadi ga zafin kishinta da suke ji. Wata idan ka nutsu zaka Fahimci burin Azizatul Nissah, bukata take ta dauke hankalin Mehran baki daya, haka da sauran suka gani yasa su hade kan su, suka tsayar da shawara. Akan su shiga jikin Sultanah Fazilatul nisa, sai aka yi rashin Sa'a an sami munafukai a cikin su. Wato Sakeenatu binti Abu Waqqas, ta rubuta wasika ta bawa baiwarta mesuna Munirah ta kaiwa Azizatul Nissah. Ita kuma da ta tashi hada rigima sai ta sauya tsarin labarin tare da kwafe wani ta saka wani abu na daban. Sannan ta bawa Baiwarta me Suna Unaizah takai Fada. Inda Sultan Mehran yaƙe, tare da shaidawa duniya cewa tana dauke da juna biyun shi. Shiru Fadar yayi sannan magatakardan ya cigaba da karanta wasikar kamar haƙa. _Sultan Mehran a halin da nake ciki ina dab da rasa rayuwata, ba dan kome ba sai yadda Fazilatul nisa! Tasa Matan da suke Hareem su dake ni! Sultan MEHRAN ka kawo min a gaji domin zasu kashe ni da goyan bayan Matar da kake mata kallon Mahaifiyarka, tare da amintacciyar baiwar Ikram_ Wani irin lumshe idanun shi yayi tabbas, yana bukatar ya dakatar da Sultanah Fazilatul nisa, amma yana jin wani irin girma da darajar ta a ran shi, shi yasa yake kasa murza mata kome, dan haka ya mike ba tare da yayi musu magana ba, ya nufi cikin gidan. Kallon juna suka yi manyan Fadar. "Kanwar Abrad ce ta samu damar daukar cikin shi? Lallai akwai abinda yake shirin Faruwa, idan har muka dake wata daga wata daular ta haihu da Mehran har abada mulki ya fita hannun Daular Abbasiyyah! A barar da cikin" Dariya Sultanah Hoyam tayi sannan tace musu. "Cikin ba zai tab'a zuba ba! Sabida shi kanshi cikin zan bukaci na tsaya kan shi kamar yadda na tsaya akan uban dab haka babu batun zubda jinin Mehran" "Amma!" "Na yanke kuma ya yanku, babu wanda ya isa ya sauya min ra'ayina, ko kuma dole kubi abinda nace." Ta fadi haka tana mik'ewa daga kujeran ta. Bin bayanta suka yi da ido, Tabbas sun dibo ruwan dafa kansu dan haka su san abinyi domin kuwa har da hannun yaransu a cikin abinda aka turo, wani irin hukunci Mehran zai dauka akan Yaran su? Kuma me yasa ya ajiye FAZILATUL a gidan sarautar? Duk basu da amsar tambayoyinsu dole shi ne zai basu. "Toh ya zamu yi idan da hannun Yaran mu a ciki!" Inji Mir Umdatuddawla, "Sai mu maida laifin kan Fazilatul nisa, ai tafi su hankali, kuma sunanta ya fara fitowa kan nasu, dan haka karka damu sune zasu kwaci kan su." Daga haka suka watse daga fadan. ---- Lokacin da Mehran ya shiga cikin gidan, Ya samu Sultanah Fazilatul nisa tana kokarin shiga tsakanin su Jasrah da Azizatul Nissah, sakamakon fadar da suke yi, wanda dama can tana cike da ita akan zaneta da ta saka aka yi, dan haka ta same ta da bugu, a bangaren Azizatul Nissah itama abinda take bukata kenan Mehran yazo ya same su a wannan yanayin, sabida ta sami damar sharrin da ta kulla musu. Tana ganin shi ta yanki jiki ta fadi tare da rike cikin jikinta. "Wayyo Allah na, wayyo cikina, wayyo Mehran" Ga baki daya ta birkice mishi tare da murkusussu, kallon Sultanah Fazilatul nisa yayi, cikin matsanancin b'acin rai. "Anneh! Sad'akata ce kika sa Jasrah ta sake ta da cikina?" Zaro idanu tayi waje tana faɗin. "A'a Aamaan akan me zan saka su dake ta? Me tayi min da zafi haka da zan tab'a lafiyar ta." "Ya isa! Ki tattara ki bar cikin fadar nan ko kuma." "Sultan MEHRAN!" Fudail ya kira sunan shi da karfi. "Karka hana shi, bar shi ya kore ni barshi ya tura ni waje saboda Azizatul Nissah." Sanyayye ta juya zata bar falon, amma ba haka Azizatul Nissah taso ba, taso idan ya kore ta yasa a kaita gidan horo, b'ata fuska tayi sannan tace. "A haka zaka kyaleta, ba ka hukunta ta ba, bayan so take a kashe ni itama Jasrah hukuncin. Da ya dace da ita kenan, sannan a nuna musu matsayina." Kallonta yayi tare da kai hannun shi kan cikinta yace. "Fudail ka kama Anneh,. A kaita tsohon gida ta zauna a can kar a hada da masu kula da ita, a barta ita daya, Jasrah kuma a kaita gidan horo." Daga haka ya mike tare da Ɗaukar Azizatul Nissah, kura musu ido Fudail yayi, a ranshi yana cewa. *Ikram itace kawai zata iya dakatar da wannan wulakancin* sannan ya raka Sultanah Fazilatul nisa yana bata hakuri, murmushi tayi sannan tace mishi. "Karka damu, tunda Ikram ta bar gidan nan na fahimci babu me iya tankwara Mehran bayan ita, Azizatul Nissah kuma tayi amfani da cikin jikinta ta juya mishi tunani, amma nayi mishi Uzuri." "Yanzun babu abinda za ayi Ikram ta dawo?" Ya tambayi Sultanah Fazilatul, "Itama danginta suna kaunar ta, babu wanda zai so ta shigo wannan rayuwar." Ta faɗa tana share kwalla. Haka ya takata har gidan, sannan ya dawo ya tasa keyar Jasrah. Bayan Mehran ya kai Azizatul Nissah d'akinta, lallab'a ta ya shiga yi har tayi kamar ta fara barci, kallonta yayi sannan ya mike zai bar dakin ta rike hannun shi. "Sultan MEHRAN! Shin kana kaunata?" Kura mata ido yayi sannan ya zare hannun shi cikin nata, sannan yace. "Ina Sonki mana, koda abin cikin jikinki." "Me yasa ba zaka kaunace ba?" Murmushi yayi sannan ya shafa kanta, bayan ya mike zai fita. "Ko har yanzun wancan Yarinyar da maza suka gama hawa da sauka akan ta kake kauna? Amma kuma taya zaka gayawa Al'ummar ka Ikram ta tab'a aure har ta kwanta da wani namijin? Koda yake ai baka san yadda akayi kome ba, domin Yayana ya sha kwanciya da ita ni ganau ce ba juyau ba.... [5/19, 4:13 PM] Addah Ramla💃🏼: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat Book3 _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 7... "Ya isa haka!!!" Ya daka mata tsawar da sai da dan cikinta ya juya zunzurutun fusata, jikin shi yana kerma ya nufe ta kamar zai rufeta da duka. "Kika sake raina ya b'aci dake, ba zai miki kyau, wallahi sai na baki mamaki. Sai na wulakanta ki a cikin Masarautan nan, sakarya me kike son nayi miki? Ita nake kauna. Ita na fara sani, ban damu ba ko mazan duniyar nan zasu kwanta akanta abinda na sani kaunarta dani gaskiya ce, babu karya a cikin shi. Idan na kuma jin Kinyi irin wannan haukar zan baki mamaki." Daga haka ya fita ya barta, ita a tunaninta Mehran irin mazan nan ne da zaka. Sarrafa su cikin tsarin da ka gindayawa musu sai ya nuna mata shi baya cikin mutanen da zaka tanada domin bukatar kanka. Mehran da Ikram ba tasha ta da a tare da shi ba, duk da kuwa suna kaunar juna Kamar ya, murmushi da farin ciki ne suka rufe ta, kamar zata tashi sama. Ta jefe tsuntsun biyu da Dutse daya, ta sanya shi ya kori Mahaifiyar shi da Jasrah ta kuma cusa mishi jin haushin Ikram, kenan babu amfanin da ba zai mata ba,. Dan haka daga yau tayi ta sanya shi cikin wani yanayi kenan. Kiran Rubina da Unaiza tayi tare da basu silallar zinari akan suje su watsa a ko'ina na farkon da bayi mata suke zama. Tana murmushi, suma cikin farin ciki suka fita suna watsawa. Kallon juna Sawda da suka baiwar ta me suna Atika, cikin yanayin damuwa tace mata. "Uwar d'akina, kamar fa anyi haka ne dan a tinzira zuciyar ku." Murmushi tayi sannan tace mata. "Karki damuwa, dan haka saka ido ki ga yadda za ayi ta." Mik'ewa tayi tare da barin gurin, ta nufi waje, a hankali take tafiya har ta hango Sultan MEHRAN a can yana zaune. Fudail yana tsaye a gefen shi. haka ma Sarwat shima yana gefen shi. A nutse ta isa inda suke, kallon su tayi tare da musu alamar su basu guri. Zama tayi a daya daga cikin kujeran dake gurin na alfarma, a hankali ta zubawa fuskar shi idanu. Kallon ruwan da aka kawo mishi bai sha ba, ta mike da kanta ta zuba mishi tare da mika mishi. Amsa yayi tare da dauke kan shi, sai da ya sha sannan ya cigaba da rike kofin ruwan. "Uwa irin Fazilatul nisa, ba zata tab'a yunkurin abinda zai tab'a ɗanta ba, tunda mutanen duniya suka fahimci karfin Abbana yana tare da Ummina suka saka shi a gaba sai sun raba su, amma kasan me? Uwa irinta ake alfahari da ita, domin duk abinda aka yi domin a raba tsakanin su, Allah bai yarda ba sai da shida kanshi yayi ikon shi da ita. An yiwa mahaifiyar mu kome domin itace Kwarkwarah shi da yafi kauna, amma kuma lokacin zuwa lokacin ana batun matsayin irin na sarauta sai gashi an cilla rayuwarta cikin hatsari, Mahaifiyar mu, ta badda rayuwar ta ne ta hanyar da aka so ta kashe Abban mu, sai ta amshi gubar tasha, kafin ta rasu ta rubuta cewa. Ita bata yi haka dan kowa ba sai dan Ni da Abba na, don Allah kar ya tura rayuwata kamar yadda ita ta tura rayuwarta. Sultan MEHRAN ban baka labarina dan kayi ta kallona ba, na baka labarina ne sabida Sultanah Fazilatul nisa da kasa aka rufe ta a wani gurin. Duk wanda yake tare da kai yasan kana kewar Ikram, amma sabida zurfin ciki ka iya b'oyewa domin fusakarta Al'ummar ka, Sultan MEHRAN ban biyo ka ɗan na cusa maka b'acin rai ba, na biyo ka ne, dan na tuna maka mahaifiyar ka bazata tab'a ganin bayan ka ba. Amma kayi hakuri Insha ALLAH ba zan kuma maka shishigi ba." Daga haka ta mike zata wuce, riko hannun ta yayi tare da kallon yadda take kokarin barin gurin. "Zauna!" Zama tayi tana kallon shi, sake shanye ruwan yayi sannan ya mika mata tare da cewa. "Kara min!" Ta kuma zuba mishi ya shanye, sannan ta kuma zuba mishi ya shanye, kafin yace mata. "Ban taso da kowa ba, haka nayi rayuwa cikin kaɗaici da bani umarni nayi kaza nayi kaza." Shiru yayi tare da lumshe idanun shi kafin ya bude a kanta, yana faɗin. "Lokacin da ta shigo rayuwata ta sha wahala sosai, ta sha ukuba, ni kaina nasan na bata azaba da hannuna, amma kuma ta tafi ta barni da ciwon da ba zai tab'a warkewa ba, ya zaki ji idan aka ce miki abinda kake matukar kauna bai da inganci?" "Idan har kaunar nakewa abun taya zan damu da batun mutane, Sultan Mehran karka daka ta mutanen duniya haka suke su kashe kashe ka, da ranka ba abun damuwa bane." Tagwayen ajiyar zuciya ya sauke tare da kallon ta, sannan yace mata. "Anneh! Tasan ita ta haife ni ta cilla rayuwata cikin gararin? Laifin Anneh yana da yawa, domin Ikram ce ta sani fahimtar kome akanta, shin zan iya yafewa Anneh, ta kashe mahaifina sabida mulki ni kuma tana son ta kashe abin da za a haifa min taya zan iya dauke kai na akan abinda ta aikata? Hada baki tayi da ku zaku kashe abin cikin Azizatul Nissah fa, Kinga kuwa dole naji babu dad'i." Cike da mamaki take kallon shi sannan tace mishi. "Wallahi bana son zama a cikin wannan masarautan amma sanin cewa nan ne zaman lafiya na, ya sani amincewa na zauna da kai. Na rantse da Allah wanda babu wani sarki sai shi, Sultan Mehran, Anneh bata tab'a tunanin tayi maka haka ba, bari kaji abinda ya faru." " Bana son jin kome, tashi ki tafi kawai" ya faɗa mata, babu musu ta mike tare da mishi sallama. Cikin damuwa ta nufi hanyar barin gurin, kallon Fudail tayi sannan tace mishi. "Yaki saurarona, ban san me haka yake nufi ba, dama haka yake da kafiya?" "Rashin Ikram ce ya kuma mai dashi zuwa haka" "Tana ina ne yanzun?"ta tambaye shi. "Tana can Merocco, ana shirin bikinta da Amir Rahil, dan uwanta ne" ya bata amsa, "Toh amma haka zamu zuba ido muna kallon shi babu me iya tankwara shi akan abinda yake aikatawa? Ni yanzun idan nace zan tafi can, zai yi wuya ya barni na tafi amma don Allah kayi wani abu, sannan a kaiwa Anneh bayinta domin jikin girma da damuwa zai mata yawa, idan aka kai mata mutane tana jin motsin su zata rage damuwa." Gyada mata kai yayi sannan yace mata. "Toh ya zamu yi da Mehran idan ya fahimci mun kai mata bayi?" "Karka damu, zan gyara kome Insha Allah. Sannan ka sami lokaci ka bani labarin Ikram, tayu na dauki wani abu daga cikin halayyar ta." Gyada mata kai yayi sannan suka yi sakayi sallama, ta bar gurin. Cike da gamsuwa. Idan baka iya kuka ba aka ce uwarka ce bata mutu ba, dan haka Sawda tayi amfani da wasu dabi'a tare da bin bayan Mahaifiyarshi domin samun kusanci da ita. Tun daga ranar ta maida gurin shi gurin hirar ta, dukda tana yawan mishi shirme haka yasa shi jin zai iya sawa a dawo da Mahaifiyar shi, tunda itama Sawda tayi kokarin ganin ya fahimci gaskiya, sanan itama tana kokarin zuwa har inda Sultanah Fazilatul nisa take, tana zama da ita. ~~ Kallon kakan shi yayi wanda ya haifi Mahaifiyarshi, kafin ya shiga wasa da kofin shayin da aka bashi ya cigaba da cewa. "Insha Allah zan yi yadda kace, sai dai zuciyata ba zata ji dadi ba," "Ka gwada Rahil zaka sami nutsuwa, kuma itama zata girmama al'amarin ka, zata kuma gane kai mutum ne me nagarta, amma idan ka nuna mata kai Kanka kake so zayi wuya baka samu tangarda da ita ba! Amma kayi nazari da kai." Kai kofin shayin yayi sannan ya kurba, mik'ewa yayi tare da cewa. "Zan koma" A hankali ya mike tare da barin gidan kakan shi, wani irin tausayi ya bashi, yana son Ikram amma kuma shi a nashi tunanin ya hakura da ita, badan kome ba, sai dan yadda tazo jiya ta gaishe da kakan da ya kalle ta sannan tace mata. "Bilqisul Ikram! Ya batun shirye shiryen bikin ku, naga anata tura sakon gayyata" Matse hannun ta, tayi tare da sunkuyar da kanta sannan tace mishi. "Ana kan shirin." Murmushi yayi sannan yace mata. "Ke baki shirya bane" Matse hannunta tayi kamar zata karya shi. "Ina kai" Kura mata ido yayi sai ya fahimci bata son maganar auren ne baki daya, dan haka ya jefeta da tambayar da ta sata d'ago kai. "Shin ko kina da wanda kike so ne? Bamu sani ba" Da sauri ta d'ago kai tana kallon shi sannan ta kuma maida kanta kasa,.kwallar da take kokarin dannewa ne ya shiga sauko mata, a hankali ta saka bayan hannunta ta goge. Murmushi irinta manya yayi mata sannan yace mata. "Share hawayen ki, kinji kiyi hakuri da abinda muka zab'a miki,.Insha Allah zaki yi farin ciki." Gyada kai tayi tare da mik'ewa zata bar falon, duk sai yaji babu dad'i musamman yadda ta kasa rike kukanta, dan haka yake ji ba mata adalci ba, dan haka yake ganin koda anyi auren zasu ta azabtar da juna ne ta hanyar amfani da k'iyayyar juna, shafa gemun shi yayi, dan yasan auren kan babu fashi. Kamar anyi an gama ne ma. ....... Kallon sakon gayyatar Masarautan SAMAIND yayi, sannan ya ajiye shi a gefe kafin yace. "Zanje da kaina naga meye Mehran ya fini dashi" Dan haka ya mike tare da nufar cikin gidan, yana shiga ya wuce dakin kakan shi wato Sultan Mu'allim, zama yayi sannan yace mishi. "Ka tura na ko ina amma ni zan kai na SAMAIND tunda ta zauna a gurin Sarkin Daular, ka ga kenan zamu gayyace shi." Murmushi yayi sannan yace mishi. "Allah ya jikan Iyayen ka, ina son yadda kake nuna jarumtar nan,.dan haka ka shirya gobe Insha Allah ka kai mishi!" Gyada kai yayi sannan ya mike tare da yin sallamawa kakan, dakin Ikram ya nufa, ya same ta ta cusa kanta a tsakanin cinyoyinta, tayi wani mugun kyau da cika, shi kanshi sai da yaji a aran shi ya dauke ta ya boye ta shi dayan shi. Sai kace Yar tsana, birkitotta yayi yana sumbatar goshinta. A hankali ya saukar da kanshi zuwa wuyarta. "Ikram me zan gayawa Saurayin ki domin zan kai mishi sakon gayyata na bikin mu." Ban san lokacin da na d'ago da mugun sauri ba, nace. "Mehran? Gurin shi zaka?" Sharr hawaye ya fara zuba, kamar yadda nake tsammanin, kasa tabuka kome nayi, na lumshe idanuna..ina jin wani irin kuka yana zuwa min, shi kuwa abinda yake son gani kenan, dan haka ya zame ni cikin lumana ya fara jagwalgwala ni, rike hannun shi nayi tare da cewa. "Don Allah,.karka min haka duk tsawon lokacin da na kare kaina, bai isa ba sai lokacin da ya rage taki kadan kace zaka kutsa min." Janye jikin shi yayi sannan ya sauka a gadon, tare da fita zuwa dakin Sultanah Balkisu Ikram, sun jima suna hira kafin yayi mata sallama. Tunda ya fita nake kuka. Domin yau nake jin wani irin kewar Mehran, ban tab'a sanin cewa na haukace akan Mehran ba sai da yace min zai tafi gurin shi, naji kamar na cire zuciyata na bashi ya kai mishi, haka Izmah da Nimra suka shigo min itama kallona take, tare da cewa. "Naji wai Amir Rahil zai tafi SAMAIND, amma zan bashi sako ya kaiwa Fudail." Gyada mata kai nayi, sannan na juya musu baya na kwanta ina ajiyar zuciya, har barci ya dauke ni, ban farka ba sai da dare ya raba sannan na nufi ban daki nayi alola, sannan nazo na gabatar da sallar nafilla, na jima i a gayawa Allah kuka na, ina kuma niman a gaji a gare shi, kwallar da nake danne su, suka zuba min, tabbas so masifa [5/22, 7:48 PM] Mehkram1256: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 02 Kaiwa yake yana komowa, tsabar yaji haushin abinda ya faru. Jin cidan hadari tare da rugugi ya sashi zare ido cikin takaici da bakin ciki. "Duk irin zaman da muka yi da.". Bude kofar shi da aka yi yasa shi had'iye sauran maganar da da zai yi, ya zubawa kofar ido. Shigowa tayi tare da ajiye mishi ruwa. Sunkuyar da kai tayi cikin girmamawa tace mishi. "Sultan MEHRAN gashi." Kallon ta yayi tare da tuna abinda Abrad yayi mishi dan haka ya a nufi ruwan bai ce mata kome ba, ya dauka ya shanye tass. Ya ajiye kofin kafin ya zauna yana kallon ta. "Me yasa yayi min haka?" Kallon shi tayi a razane tare da ja da baya, tana girgiza mishi kai. "Ni." "Tambayar ki nake zaki dawo min da tambaya na" wani shegen tsoro ne ya lullube ta, tare da zaro idanu waje, jikinta yana rawa. Tabbas duk rayuwarta da tayi bata tab'a ganin wanda iya tsawar shi abar firgita ce kamar Mehran. Shin dan ya kasance Shugaba ne? Koko dan ya kasance Zaki ne kisabo, wallahi ita har tsoron had'a idanu take dashi. Ganin taki fita ya sashi fahimtar akwai abinda take buƙata, bai tsaya da tunanin shi ba, yaji marar shi kamar an daure mishi. Wani azazzaben sha'awar kasancewa da mace ya taso mishi. Kura mata ido yayi ganin yadda take kallon shi. Komawa yayi saman kujeran ya zube yana sauke numfashin sa. A hankali ta tako gaban shi, tare da tsayawa tana kallon yadda yake lumshe idanun shi, wato shi ba zai kira mace ta taimaka mishi ba, ya gwammace koda zai mutu ne gwara ya mutum, zare kayan jikinta tayi suka zube a kasa. Sannan ya taimaka mishi suka shiga d'akin. A wannan lokacin shi kanshi idan ka tambaye shi wani hali yake ciki bai sani ba, amma tabbas yaji a ranshi yana kwance da mace. Sai dai har yau kamar can baya da yaki matan dan kanshi ya kyamaci haka a ranshi. Duk da kyamar bai hana shi buga mata isa ba. Ya kasance ta da iya karfin shi da lafiyarta, tun tana kallon haka a matsayin abin da bai kai ya kawo ba, har ita da kanta ta fara dukar shi tana kuka. Shi kuma wai yayi haka bane dan lafiyar shi, haka ya faru ne dan abinda ta bashi ya sha, shi yasa ya rasa tunanin shi ya hake mata Sosai. Komawa gefe yayi tare da kwanciya rub da ciki. A hankali barci me nauyi ya dauke shi. Kallon shi tayi sannan ta mike a hankali. Bata tsaya wanka a dakin shi ba, ta saka kayanta tare da fita daga d'akin bayan ta ajiye mishi wani tambarin da zai iya wargaza mishi kome har karshen rayuwar shi. ~~~ Sai da ruwan nan ya kare tsaf akan Fudail ya shigo Masarautan, koda ya shiga shashin sa ya nufa yayi wanka da ruwan zafi sannan yana wankan tare da murmushin abinda Mehran yayi mishi bai wani damu can ba, sabida ko shi aka yiwa haka iya hukuncin da zai yanke kenan. Dan haka babban abinda yake shirin akan Azizatul Nissah ce. ~~~ Munyi tafiya me nisa wanda muka bar yankin Farisa sannan muka nufi kuduncin jazziratul Arab, anan muka yada Zango. Tunda muka tsaya aka gama shirya mana tantin mu. Na shiga gurin Sultanah Amrah, na zauna duk da ba hira muke ba, amma kuma haka yana sani jin kamar ina tare da Ammyn na ne, dan haka bayan munyi sallah na kwanta a gurin, ita kuma ta cigaba da abinda take, lokaci zuwa lokaci tana kallon yadda nake barci. Hawaye ne ya zubo mata, ta girgiza kai sannan ta cigaba da aikinta, tana tuna abubuwa dayawa akan yaranta da mulki yasa ta manta da su. Tabbas mulki matukar baka nemi Izni Allah akan shi ba, zai iya kai ka ya baro ta, Kamar yadda ya kaita ya baro ta, sai dai ta wani gefen zata iya godewa Allah tunda akwai Ikram da Ilham, Yar gidan Abrad. Murmushi tayi bayan ta shafa kanta, tana me jin kewar Yaran ta. ... Zan iya cewa barcin da nayi me cike da gajiya da mafarkai marasa kyau da dad'i, karshe dai haka na farka da sunan Mehran. Da gudu Rahil ya shigo tantin. Da sauri ya iso gabana, fadawa jikin shi nayi ina haki. "Me ya faru?" "Mehran!" Na fada kamar zanyi kuka. Juyar da kan shi yayi. "Ba zaki daina kwadayin ganin shi ba?" "Karka raba ni da shi, zuciyata halittar shi ce." Matse bakina yayi idanun shi cike da kwalla. "Ni kuma sabida ke aka halicce ni, ina sonki Ikram. Nasan idan ba zama daya muka yi ba, ba zaki daina kwadayin shi ba" ya faɗa bayan ya cire hannunsa a bakina, kokarin hada bakin mu yake na kawar da kaina. "Meye kike nufi? Ba zaki." Ture shi nayi tare da mik'ewa, ya kuma tasowa yana kallona. Kamar zai yi kuka yace. "Meye yafi Ni dashi? Meye na rasa da ba zaki amshi tayi na ba, wallahi yau sai na dasa miki kaunata a ranki." Fada sosai muka yi da Rahil domin ya kafe sai ya fahimtar dani yadda yake sona. Ni kuma na rantse ba zan yarda da wannan tunanin na shi ba haka muka gama dakyar na kwaci kai na. Sam na kasa nutsuwa a raina, domin kuwa, haushina yake ji kamar ya kashe ni, bayan fitar shi Sultanah Amratu ta shigo, fadawa nayi jikinta ina kuka. Tare da cusa kai na a jikinta. "Zuwa yanzun ya kamata ki cire Sultan Aamaan Abdus Samad Mehran, a ranki domin kwanaki ƙalilan zaki kasance matar Rahil. Don ki daina tunawa da sultan Aamaan." Kallonta nayi baki sake, kafin na sauke idanuna kasa, ina kuka. "Ummyn!" Yatsar hannunta ta saka min akan bakina, tare da girgiza min kai. "Kowa yasan cewa kece kwarin gwiwar shi, ki taimaka ki sauko ayi kome cikin ruwan sanyi." Hawayen da nake tarewa suka daga cikin idanuna, na kasa magana baki daya sai kallonta nake. "Tsarin masarautar mu, cike yake da kawaici da YAKANA karki yarda ahalin Mahaifinki su fahimci kin sayar da zuciyarki ga wanin su. Domin haka tilin abin kunya ce gare mu!" "Toh dole ne sai na rayu cikin mulki? Me yasa ba zaku gan.." d'aga min hannun tayi tare da kallon, yadda bakina yake rawa. Kifa kai nayi a tafin hannuna, na fashe da kuka. Ina girgiza kai, Tashi tayi tare da bar min tantin kuma ta hana kowa shigo min, domin tana ganin matukar suka shigo min zan iya tsarewa. Gurin yan uwan Baba na, ta nufa suka tattauna. Anan suka ajiye shawara ita zata wuce Asakandariya su kuma su wuce dani can Merocco. Idan ita mace ce mai rauni tausayina zai iya sakawa ta bani abinda nake so. Su kuma ahalin mahaifina babu wannan yanayin a tare dasu, dan haka su tafi dani. Bayan ta dawo ne, take kallon yadda na kifa kai ka a saman gwiwar kafana. "Zaku wuce Merocco." Da sauri na d'ago kai na, zanyi magana ya juya min baya bata bani damar ma tambayarta ba, ta cigaba da abinda take, ni kai na nasan ba zan iya tababa da ita ba, amma kuma ya kamata su fahimci abinda nake so. Bayan mun huta aka kuma tadda tafiyar. Ina ji ina gani ta tafi da Nimrah. Ni kuma muka tafi da Izmah, bayan mun sha kuka. Tunda muka dauki hanya, banzan can yake wani shige min. Ko kallon shi banyi ba, har muka wuni a hanyar, dab Magarib muka shiga garin, wanda tun kafin mu iso labari ya iso musu muna kan hanyar mu, sakamakon wani mahayi da aka turo shi. Dan haka garin ya kasance kamar ana bikin sallah, wani irin biki ake me cike da shagali. Haka muka isa har fadan, inda aka muka yada zango a falon Sultan Mu'allim. Mika min hannun yyi. Da sauri na isa gare shi. Ina isa na zube gwiwata a kasa, kai na a bisa kafadar shi, na sake kuka me cin rai. Takaici yasa Rahil fita a gidan. Kuka nake wanda idan ka tambaye ni ba zance maka ga abinda aka min ba, amma kuma a cikin raina, ina kuka ne domin na rasa Mehran. Yadda nake kukan ya sashi sake murmushin jin dadin. Sannan ya shafa kai na, yace. "Kiyi hakuri! Haka muke tsara miki baki rayuwar. Da karen layi gwara Zakin gidanka koda kuwa zaka zane shi da bulala ne, kiyi dan mahaifanki da kanwarki. Ba akan ki da soyayyar ki ba. Mun rigada mun yanke kuma al'adunmu sun sha banban da kowane, mukan iya binne abinda muke so! Mukan iya boye abinda muke kauna, matukar hakan zai bamu damar fuskantar matsalar. A tsarin mu, bai zama dole mace ta samu abinda take so ba, matukar zata bawa Mulkin mu. Gudunmawa dan haka na zab'i ra'ayin shi sabida ki bashi gudunmawa. Yanayin ku yayi daidai da mulkin, abinda ake bukata domin mulki kin hada, dan haka ki amshi Rahil a matsayin abokin rayuwar ki." Hawaye ne ya shiga zuba min, na kasa magana tare da sunkuyar da kaina, domin yayi min kwarjini. Haka aka fitar dani har dakin Bilqisul Ikram, tankwarata. Shafa kaina tayi sannan ta kira amintattun bayin ta, suka shiga dani ban daki. Aka hada min wani irin ruwan wanka tare da turaruka masu dadi. Sai furen kamshi da wanka aka watsa a ruwan, sannan suka shiga cudani. Hawaye na zuba a idanuna. Shi kenan na rasa Mehran. Na rasa Jarumina, me yasa tun tuni ban amsa mishi ba. D'ago kai nayi sannan nace a raina. _Toh amma ai bai ce yana sona Ba? Toh amma kuma ai duk abinda yake min duk na soyayya ce! Kishi da zafin rai akai na duk abinda masoyi ne kaɗai yake yin shi! Toh Ni me yasa na shiga zab'en? Kenan bawai na shiga dan shi bane sai dan ina son shi?_ Kwalla ne ya zubo min, ban san lokacin da na fashe da kuka ba, haka suka taimaka min nayi wanka na fito bayan sun bani wani yadi na lullube jikina, tare da fitowa daga ban ɗakin, tunda na fito suka shiga shafa min wani abu kamar mai kamar sabulu, ina zaune ina kallon su. Kwallar da nake sharewa a kai a kai, yasa Bayin suka shiga rarrashina, kamar dama jiran su nake na fashe da kuka. Hannun daya daga cikin su ta saka min a bakina. "Abin kunya ne babba ga Sultanah Balkisu Ikram aji cewa babbar Yar D'anta na farko tana kuka akan SO kinsan yadda muke boye kalmar a ran mu kuwa? Toh koda kuwa zaka rasa ranka akan sone yana da kau kayi hakuri da shi, idan baso kike mulkin kasar nan ta gagari Amir Rahil ba. Don Allah ki hakura da Sultan Aamaan Mehran. Mun san yadda kike son shi, amma duk wanda zaki gani a cikin masarautan nan yana da tab'on soyayya, dan haka karki sake a Fahimci zuciyarki tana ga wani da namijin domin abin kunya ce ga Kakarki." Haka suka kashe ni da magana tare da nuna min illar abinda nake aikatawa, nayi kuka da sunan Allah kuma nayi bakin cikin zamowa ta, daya daga cikin ahalin babban gida. Ina ji ina gani ranar aka mai dani kamar wata yar tsana, zunzurutun wanke nan shafe ne. Ana gyara min jikina. Har kusan tsakiyar dare a sannan nayi wankar karshe tare da sallah na kwanta,. Ranar barci na zance kacokan mafarkin Mehran nayi tayi. Ina kuka ina kome haka zan farka naga bayin nan suna rarrashina. ..... Washi gari ina farkawa kafin nayi sallah asuba, suka bani madara dafaffiya,, sai da na wanke baki na shanye tass, sannan na shiga wanka tare da Alola ina idarwa, aka kuma kawo min yankanken y'ay'an itacce, wanda aka zuba madara da zuma na shanye shi, ina ji suna faɗin. "Kirjinta muke son ya cika kafin zuwa bikin su." Shiru nayi domin bani da bakin magana sai yadda suka yi dani... [5/22, 7:48 PM] Mehkram1256: _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ Littafi na uku 01 Tunda ya bar masaukin su Ikram ya sa aka hada musu nasu kayan suka bar gidan da suke, sai da suka kusan barin cikin garin SAMAIND. Yasa aka kama Nawwas. Kallon juna suka yi kafin yacewa. "Na sami labarin ka gayawa Fudail duk abinda ya faru, sai dai kayi kuskuren domin ba zan barka a raye ba, shi yasa nayi gaggawan barin SAMAIND domin wancan mahaukacin idan ya ritsani sai ta Allah." Dariya Nawwas ya saka yana kallon Abrad, tare da nuna shi da yatsa kafin yace mishi. "Kai tsaye ka mu'amalancin Ikram, Ni kuma a ruwan sanyi Mu'amalanci kanwarka tare da dauke abinda yake jikinta. Bamu bar SAMAIND ba sai da na tabbatar da na kuma buɗe tsakanin kafarta na jefa linzamina. Yadda koda na mutu dole na bar baya da kura." Dariya ya kuma fashewa da shi, yana mai maita abinda ya faru,, yana kuma gaya mishi abinda ya aikata da Kanwar shi. Babu abinda ya kai wannan abin tashin hankali. Idanun shi ne suka cika da kwalla. Wanda ya kasa jurewa har ya kai da ya zuba masa. "Meye nayi maka Nawwas? Da kayi min yankan baya haka? Nawwas meye na tsare maka hakan da ka zab'i cilla rayuwar kanwata cikin tashin hankali? Nawwas me yasa baka yi a kaina ba." "Hahaha... Hmmm, ka zata zan zuba ido ne ka tozarta Ikram? Ko ka zata zan zuba ido ne ka cigaba da abinda ranka yake so? Wannan shi ne kishi a tsakanin zubda jini. Idan kana tunanin ka zubda jinin Nu'man dan jin dadin ka da kuma cusgunawa Mehran dan Ikram ta tsane shi wannan kuskure ne babba karka manta kamar yadda ka mayarda da Ikram a shimfid'ar ka, hakan na mayar da Amirah Azizatul Nissah. Na maida ta kamar matar da na biya sadaki me daraja dan haka karka yi tunanin Mehran zai yarda da wata mace bayan Ikram! Kamar yadda kake da kwarin gwiwar rubutawa yan majalisar Masarautan SAMAIND haka nima na gayawa Mehran alakata da Kanwar ka, dan haka sai ka jira abinda zai biyo baya domin dai SAMAIND ba kanwan lasa bane. Kayi kuskuren hadamme kome, Ni kuma nayi ƙoƙarin bayyanawa duniya waye kai, Ikram yanzun tayi maka nisa kanwarka zaka yi kokarin ganin ka fito da ita daga SAMAIND idan ba haka ba". Cikin wani irin fusata Abrad yaja takobi bai yi wata wata ba, ya sokawa Nawwas a kirjin shi sai da ya hudo bayan shi. Zuɓewa yayi akan gwiwar shi, ya kuma sake jan takobin ya soka mishi sai da jini ya fito ta bakin Nawwas. A lokacin ya tuna da Abinda Nu'man ya gaya mishi. *Ban san meye muka yi ba kuka raba mana rayuwar mu! Sai dai nasan wata rana kai ma haka ce zata mamaye ka! Yadda kayi min haka kai ba za a maka* Hawaye ne ya zubo mishi tare da kallon Abrad cikin tsannanin azaba. "Ni nayi haka ne domin al'ummar Daular Umayyad! Nayi wannan aikin ne saboda Banu Umayyad. Sai dai kuma nayi imanin yadda na zubda jinin bawan Allah haka nima rawa jinin ya salwanta. Kai kuma Banu Umayyad za a shafe baki daya. Sai kayi gudun da babu macecin ka. Abrad ni abokinka ne tun yaranta ka kashe ni da hannunka. Ba iya ni ne matsalar ba, rayuwar Kanwar ka anan zaka Fahimci muhimmancin rayuwar wanda kake so yaƙe" Kasa magana yayi sakamakon jinin da ya cika mishi baki, mika mishi hannu yayi amma fir yaƙi amsar hannun. Juya baya Abrad yayi kwalla na zuba mishi. Bai san ta yadda zai taimakawa Azizah ba, babban tashin hankalin shi Azizatul Nissah. Juyawa yayi cikin tsannanin fushi ya sare kan Nawwas, ya fadi can jini yana zuba kamar da bakin kwarya. Zama yayi tare da sake takobin ya fashe da kuka. Domin Nawwas ba kashin yarwa bane, ba kasafai ake samun irin shi ba. Nawwas abokin tarayya ne na kwarai. Mutum ne da ba a cika samun irin shi ba. Shi yasa yake kuka, sai kuma yadda Nawwas yaci Amanar shi yayi ta tarayya da Kanwar shi. Sannan ya kwashi sirrin shi ya gayawa Mehran, "Me yasa Nawwas yaci amanata?" Ya tambaya da karfi cikin tsorata da yanayin shi duk suka ja baya, sai daga can asalin amintaccen bawan Nawwas yace mishi. "Sabida shi ya fara son Ikram! Ya kaunace ta sama da kaunar da yakewa rayuwar shi! Ya bada rayuwar shi ne domin ita? Ya kuma saka duk wani matakin da zai bawa rayuwar ta taimako koda baya raye. Sultan kayi hakuri amma kaunar Nawwas ga Ikram gaskiya ce. Soyayyar shi ga Ikram gaskiya ce, tabbas yaso ta tun daga ranar da muka sayo ta, har zuwa yau. Ya gaya maka gaskiya kamar yadda kowa ya kasa fahimtar da kai haka ne. Amma tabbas bayi kuskuren ba, samun masoyi irin shi ma sai an tuna." Yana fadar haka ya shiga tattara gangan jikin Nawwas da kanshi yana zubda hawayen bakin ciki, da tausayin abinda ya faru. Ya tuna abinda Nawwas ya gaya mishi jiya. "Karka sake ka gaya mishi gaskiya akan alakata da Azizatul Nissah! Zan gaya mishi abinda zai fusata shi. Domin ya bar Ikram ta rayu da Mehran, naso Mehran ya tsaya muyi tsayayya magana dashi amma fir yaki. Dan haka zan gayawa Fudail Insha Allah zai saurare ni. Amma kasan me? Hmm idan Abrad yaga zai rasa Ikram zai sauya tsarin gudanar da abinshi ka saka ido kayi kallo. Don Allah Rab ka kula min da Azizatul Nissah da abinda zata haifa." A kidime ya kalle shi sannan yace mishi. "Shugabana ka manta matsayinta ne a yanzun? Har kake batun abinda zata haifa" Murmushi yayi sannan yace mishi. "Ba da ita ga Mehran ba shi yake nufin ita din mallakar shi bace, ita da abin cikin ta nawa ne, kuma mallakina ce, don Allah karka sake wani abu ya shiga cikin rayuwar su, fatana idan ka bar Oman kayi ƙoƙarin tsayawa Ikram, ka same ta da batun kome, kuma na roke ka don Allah ka tsaya a bayanta karka bari wani ya tab'ata. Ita kuma zata tsaya a gaban Azizatul Nissah." Wani irin kuka ne ya kwace mishi me ƙarfi yana me kuma rungume kan Nawwas, tare da jin tashin hankali sama da farkon faruwan kome, kara rungume kan yayi yana faɗin. "Me yasa kayi haka? Me yasa ka bada rayuwar ka domin wasu. Baka tuna bayanka ne? Me yasa kika zab'i zubda jini sama da kome ne?" Ya faɗa da karfi, yana kuka tare da k'amk'ame kan Nawwas, juyawa Abrad yayi tare da zuba mishi ido, tabbas sun zabi zubda jini sama da kome akan mace! Akan Ikram, koma waye za a kashe! Akan Ikram koda kuwa rayuwar shi ce zai iya badawa, wani irin kwalla yake zubdawa tare da kallon gawan Nawwas, mutum na farko da ya fara ankarar dashi kuskuren abinda yake aikatawa ya kashe mutumin da bai hada shi da kome ba ya kashe mutumin da zunzurutun kaunar shi da shi ko barci yake sai ya tashi idan ya tura a kira shi ya kashe. Ya kashe mutumin da yaso shi da gaskiya, ihu ya takarkara a cikin jirgin ruwan, sai da duk suka toshe kunnen su, ya kuma fashe da kuka yana faɗin. "Jininki fansa ce ga jinin Aminina" ya faɗa yana kuka da bakin cikin abinda ya aikata , Rab yana jin shi, tabbas ya fara dauko haske akan abin da Nawwas ya gaya mishi. Shiru cikin gurin yayi babu wanda ya kuma magana, mik'ewa yayi tare da cewa. "Ku dauki gawan shi ku wurga a ruwa!" "Sultan Abrad!" A fusace ya juya ga Rab, had'iye yawun yayi sannan ya sunkuyar da kanshi,bai kuma cewa kome ba. Amma tabbas wannan shine abinda ba zai iya dauka ba, dan haka yana ganin an dauki gawar Nawwas, aka fito dashi shima yabi bayan su da gudu, kafin yayi wani yunkuri an wurga cikin teku bayan dakaru sun rike shi. Ihu yake tare da kokarin kwacewa a hannun su, amma suka kara rike shi, yana ji yana gani gawan Nawwas ya nutse cikin ruwan, kuka yake tare da ihun. Buga mishi kasa takobi Abrad yayi. Bai kuma fahimtar inda kan shi yake ba. *** Wurgi yayi da takobin hannun shi, tare da fasa kara yana huci. "Tabbas Abrad yasan zan dawo na bi takan shi, wato shine ya gudu. Fudail Darda ina Nawwas din?" "Sultan MEHRAN! Tun jiya muke binka akan Nawwas, amma baka tsaya munyi magana ba, shi yasa da ya gaji yayi tafiyar shi bai..." Yadda ya kafe Fudail da ido ne, yasa shi sunkuyar da kai kasa, yana had'iye yawu. "Sultan MEHRAN!" "Ina jinka, meye yace?" Ya tambaye shi, tare da kallon gefe. Fita suka yi daga cikin gidan..sai da suka yi tafiya me nisa, sannan yace mishi. "Sultan MEHRAN! Nawwas bai gaya min kome ba!" Cakume wuyar shi yayi tare da fidda huci. "Ni zaka mara da takalmin kafarka? Ko zaka samu damar boye min abinda yake ranka? Gaya min meye laifina da kuke boye min abinda ya dace na sani." "Kayi hakuri bai gaya min kome ba, amma yace na nime bawan shi Rab." Wani dirkeken naushi ya kasake a jikin bishiyar da Bayan Nawwas yake jingine. Sai da hannun shi ya farfashe. Sannan ya takarkare ya fasa ihu. Sai da dajin ya amsa. Zafi biyu yake ciki, babu wanda zai gaya mishi gaskiya kenan? Ya rasa Ikram ya rasa wanda zai gaya mishi abinda ya faru kenan, dan haka ya tashi cikin tashin hankali ya juya zai tafi. Ya kuma juyawa ya kalli Fudail, sannan ya saka kai zai bar gurin. Ajiyar zuciya Fudail yayi sannan a ranshi ya ayyana cewa. *_Ba zan tab'a yarda na gaya maka gaskiya ba! Sai har na gama gabatar da abinda yake gaba na, ba zan tab'a yarda na kyale wanda ya cutar da ikram koda da bakar magana ce balle da farar magana! Kayi hakuri Sultan Mehran_* Ya faɗa a sanyayye, yana me jin tausayin Sultan Mehran. Domin a yanzun gaskiya yake nima idanu a rufe, kuma baya jin zai gaya mishi koda kuwa zai rasa rayuwar shi, Dole kuwa Azizatul Nissah taji a jikinta itama. Abin kunyar da suke amfani dashi ga rayuwar Ikram itama taji yadda tozarci yake. Amma kuma idan ya tuna rokon da Nawwas yayi mishi sai yaji tsoron kar haka kuma ya tab'a kimarta. Dafe goshin da yayi tare da bin bayan Mehran, yana tafiya yana zancen Zuci. Har ya isa inda dokin shi yake, dan yanzun kan yasan Mehran yayi mishi nisa, koda ya cilla dokin shi ya hango su, dab da Masarautan. Amma kuma koda ya isa Fir dakarun suka hana shi shiga. Wannan shine karon farko da Mehran ya mishi hukunci me tsauri ta hanyar amfani da hana shi, shiga SAMAIND! Dan haka bai yi fushi ba, ya zauna a gurin gashi garin da alamun shigowar damina. Duk sai yaji babu dad'i a ranshi, yau shine Mehran yayiwa wannan hukuncin, dan haka duk dai yake gani kamar tozartawa ne, ga wani muzancin da yake ji a ranshi. Kanshi a sunkuye har aka fara yayyafi. Bayan wani lokaci ruwa ya fara me mugun karfi da yawa. Yana tsaye a bakin kofar shiga masarautan.. ---- Tunda ya shiga cikin gidan, ake mishi magana kome ya gani fatali yake dashi, har ya shiga cikin dakin shi. Huci yake ya rasa yadda zai yi da Fudail idan kowa zai ci amanar shi yana tunanin ai Fudail ba zai tab'a yarda a cutar dashi ba. Kuma yayi imani da Allah akwai da yake boye shi, kuma ba zai tab'a yarda da munafunci ba, domin idan ba munafunci ba akan me zai boye mishi maganar da yake bukatar yaji, dan haka babu abinda zai hana shi bai hukunta shi ba, sai ya hukunshi sosai domin kuwa ba zai yarda da wannan wulakancin ba, tsaki yayi tare da kutufal da kayan shayin gaban shi, yana jin ana buga kofar shi amma fir yaki buɗe sabida yayi fushi anci amanar shi... (See me see trouble😹😂😹🤣 ta ina aka ci amanar ka Yau ga D'an Uwan Jamal🤔) +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat [5/22, 7:48 PM] Mehkram1256: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 03 Wato ma'ana bani magani suke tare da abinci me gina jiki, duk abinda suke idanuna a rufe suke, bana budewa wani lokaci haka zasu yi ta magana ina jin su, bana tanka musu, idan suka gama min kuwa a gurin nake kwanciya. Ina kuka duk taurin zuciya ta da taurin kai na, sai da ya kai komi kashin b'acin rai kuka yake sani. Rabona da Izmah kuwa sai dai na shafe kwanaki goma kafin aka barta ta shigo min dakina, lokacin da ta ganin sai da ta firgita, tana mamaki. "Ikram! Baki da lafiya ne? Kinyi kyau amma kuma kinyi mugun rama, meye yake damunki? Me aka miki? Don Allah gaya min" Zama tayi a jiki na, ban san lokacin da na fashe da kuka ba, nace mata. "Izmah Mehran nake son gani" kamar wacce aka dasata, haka take kallona. Bakinta yana rawa tace min. "Sultan MEHRAN?" Ta kuma tambayana, gyada mata kai nayi tare da rushewa da kuka, rike hannuna tayi tare da kwantar da kaina a kirjinta. "Ikram!" "Don Allah Mehran;" na katse mata abinda zata fada, duk sai ta rasa abinda zata ce min, ta kuma bude baki zata yi magana, Amir Rahil ya shigo cikin ɗakin, yan mata na biye dashi. Mikewa tayi zata fita na rike hannun ta. "Kiyi hakuri zan jira idan ya fita zan shigo muyi Magana." "Wacce magana zaku yi? Ai akan wancan Jahilin da ya kasa miki uzuri ko? Ko akan Abrad da ya gama da budurcin ki? Kinga Ikram. Ina Sonki shi yasa zan dauki duk abinda ya same ki, amma kika Kuskura kika shigo da Mehran yake ko Aman yake? Wallahi Billahi azim, zan kashe wannan abin" ya nuna min Izmah, sauka nayi daga gadon na zube gwiwata a kasa, tare da rungumo Izmah, ina kuka nace mishi. "Kayi hakuri! Ba zan kuma maganar shi ba, amma karka tab'a lafiyarta. Idan nice na amince." Na fada cikin kuka, murmushi yayi tare da nunawa Izmah kofa ta fita, tunda ya shigo inda nake ya d'ago ni. Kallon kayan jikina yayi yadda ya fitar da surar jiki na. Nayi kyau na fitar hankali. Duhun fatar da nake dashi ya washe nayi wani irin haske me ban mamaki. Matsalar kawai rashin nutsuwar da bani da shi ne ya janyo min rama. D'ago kai na yayi tare da kallon fuskana. Kan shi ya kawo da sunan zai hada bakin mu na kauda kaina, murmushi yayi tare da cizon kunne na, rike rigar shi nayi tare da jin saukar kwalla daga idanuna. Na bakin ciki dan Allah ya gani bana son shi a mijin aurena, a dan uwan na dauke shi amma bai Fahimci haka ba, yayi ta shige min. "Ai da wancan banzan ne ba zaki na kuka kamar karamar yarinya ba, dake baki kaunata shi yasa kike kuka. Ikram me yasa baki sona? Ni dan uwanki ne kuma zan iya bada rayuwata domin." "Ba zaka iya, shi daya ya bada rayuwar shi domin ni, don Allah." Dama abinda yake nima kenan, kuma ya samu. Dan haka banyi wani abun da zai nuna mishi jin dadi ko bakin ciki ba, na dai rufe idanuna. Ya gama sumbatar bakina, sannan ya janye daga jiki na, ganin har lokacin idanuna a rufe suke, ya sashi fita daga d'akin yana murmushin jin dadi. Haka rayuwar mu yayi ta tafiya, ina zuwa shashin Sultan Mu'allim, yana bani wasu abubuwan da ya zama mallakar mahaifina, tare da wasu kyautattakar, haka zan dawo shashin Sultanah Balkisu Ikram, na zauna, shima sabida wancan wahalallen nake haka, idan a d'akin ta, domin yana shigowa zata kore shi. Haka ya sani tarewa a d'akinta, duk da kuwa d'akina na kallon nata ne, haka akayi ta gabatar min da y'ay'an gwamnonin nahiyar, tare da manyan mutanen ƙasar. Har zuwa lokacin Mehran shi yake da kaso mafi girma a zuciyata, na kasa cire shi a raina. Na sha tambayar kaina me yasa lokacin da nake tare dashi ban ji haka ba, sai da bamu tare? Wannan amsar har yau na kasa bawa kaina amsa. Kullum da wannan nake kwana nake tashi. "Ciki abincin mana!" Kallon Sultan Mu'allim nayi tare, sunkuyar da kaina, na tsakuri abincin na kai bakina. "Rahil yace min har yanzun baku fahimci juna ba?" Sunkuyar da kai nayi tare da kasa kai abincin bakina. Ajiyewa nayi zan mike yace min. "Zauna." Komawa nayi ka zauna, tare da damke hannuna, jikina yana rawa. "Kar na kuma jin labarin kinyi magana akan SULTAN Mehran! Idan kuma hakan ya faru, zamu kashe baiwar da kike kauna, domin idan bamu fito miki a asalin mutane ba zaki kunyata mu. Bamu son muyi miki dole shi yasa muka baki damar ku fahimci juna. Nan da wata biyu muka baki ki fahimci waye shi idan ba haka ba." "Taya zan Fahimci abinda kuke so? Bayan ni din ba mallakarku bace, ni bana son lusari." Dukar tabirin yayi tare da kallon Sultan Mu'allim. "Atta kana jin abinda harshenta yake faɗa." Kallona yayi sannan ya kuma maida kanshi ga Ikram. "Haka zaki zauna dashi domin baki da mijin da ya wuce shi." Mikewa nayi zan bar gurin Rahil ya taka rigar jikina, karar yagewar jikina, naji kallon shi nayi ban san lokacin da na wanke shi da mari ba, sai da ya firgice. Tabbas yayi kuskuren babba, amma kuma marin da tayi mishi shine mafi girman wulakanci da aka tab'a mishi. Shafa fuskar shi yayi sannan yace. "Atta! Marina tayi." "Me yasa ka taka mata rigarta? Matar da zaka aura bata bukatar tilastawa, kasan tana da wanda zuciyarta yake so kai kuma ka same ta ne a sama. Karka sake haka ya kuma had'aku." Juyawa yayi sannan ya cigaba da cewa. "Ke kuma za aka kaiki gidan horo." "Atta!" Ya kira sunan Sultan Mu'allim, murmushi yayi sannan ya d mishi. "Idan na yanke hukunci ko kaina bana saurarra dan haka, Bhaiq kazo ka tafi da ita." Ban yi gardama ba dan haka na amince aka tafi dani. "Atta don Allah." "Matar da zaka zauna da ita ta mare ka, me kake tunanin nan gaba zata aikata? Dan haka ka bari a nuna mata girmanka da darajarka." Jikin shi a matukar sanyayye ya bar gurin cin abincin, bai tsaya ko ina ba, sai gidan kakan shi na gurin Uwa wazir. Zama yayi cikin nutsuwa sannan ya gaishe shi, tare da yin shiru. Kasa magana yayi yana kallon yadda Rahil din ya nutsu, kafin ya ce mishi. "Ina jinka!" "Dama dama dama.." "Ka nutsu kayi min magana!"inji kakan shi, nutsuwa yayi kafin ya fadi abin da ya kawo shi. Da kuma dalilin da yasa aka rufe Ikram. Kallon son kai yayi mishi, tsantsan domin kuwa banda son kai babu abinda ya hango a maganar Rahil. "Tun lokacin da ka bayyana soyayyarta a ranka na gaya maka cewa ka rabu da ita, amma fir ka kiya, sai ma goyan bayan da kasamu daga danginka, ba wai Ikram nace bata sonka kai ne baka dace da rayuwarta ba, ai duk wanda yaga yadda ta bar kasar nan bayan ta gama maka aiki har ta kai da ta nuna ita ta mutu zaka fahimci akwai soyayya a cikin tafiyarta, amma zuciyarka dake a rufe take kaki yarda akan lallai ita kake buƙata " "Amma kuma taya gida bai koshi ba za a dauka akai waje? Taya ina sonta zan kyaleta ta tafi yanki mafi hatsari da ganganci da rayuwa? SAMAIND cike take da rayuwa da mutuwa! Kuskure daya idan mutum yayi mutuwa tafi kome sauki a rayuwar shi. Uwa uba zunzurutun makircin da yake cikin masarautan. Kaka nazo ne domin niman hanyar da Ka fidda ikram, idan ba zan samu ba na hakura nayi tafiya ta" Kallon shi yayi na tsawon lokaci kafin yace mishi. "Ta yaro kyau take bata karko, Ba zan daina gaya maka ba Ikram bata dace da rayuwar ka ba, Ka barta tayi rayuwarta da wanda take SO Ni dan taimaka maka, amma ba zan tab'a tilasta mata ba,.kuma ba zan mata dole kamar yadda kuka mata ba, zan bata goyan baya ta auri wanda take so." Mikewa yayi cikin fushi zai fita, har ya isa bakin kofar kakan Yace. "Kai ake bukatar ka zama sarki, idan har baka san yadda ake sadaukarwa ba yaushe zaka yiwa Al'ummar ka adalci? Ita saboda jarumtarta ake bukatar ta a jikinka, me yasa ba zaka zama jarumi ba kamar ita? Amma karka tilastawa zuciyarta yake cike da kaunar wani. Domin kana ji kana gani zaka yi danasanin rayuwa." Fita yayi daga cikin gidan, ya nufi can babban shashin. Inda ta zube a gaban Sultanah Balkisu Ikram. "Me yasa bani da Sa'a? Me yasa kowa yake min kallon mahaddami? Ni ne ban dace da Ikram ba ko ƙaddara ta ce bata dace da ita bane? Sultanah a tunanina ni Maraya ne, samun Ikram ne ya sani fahimtar ni me galihu ne, me yasa Ikram ta sani nake jin ni ba kome bane? Me yasa a kullum nake jin nayi son kai? A duk lokacin da na kalli Ikram sai na dinga jin a raina nayi son kai sama da kome a rayuwar mu, tunda ta dawo cikin gidan nan ban tab'a ganin ta dauki takobin domin kare kanta ba, me yasa?" "Sabida zuciyarta tana wani guri na daban, kaunar da take mishi ba boyayya bace, yadda take kuka akan shi ya tabbatar min ita din ba kowa bace a fagen SOYAYYA! Zai yi wuya ka hada soyayyar da Jarumta, amma kuma ana ana iya hada soyayya da yaki koda kuwa haka zai bada damar a shafe alkarya guda! Akan soyayya tana iya haifar da juyin juya halin a cikin masarautan! Akan soyayya akan iya shayar da sarki guba domin cimma manufar Soyayya! Irin soyayyar Ikram da Mehran! Idan ba ayi takatsantsar gurin nuna musu bambanci rayuwa ba, dole dayan su yayi rayuwa dayan su ya mutu? Soyayya ce ta shiga tsakanin zubda jini! Kasancewar dukkan su sun kasance, a cikin lambu. Ba zance shine ƙayar ba amma tabbas haka ya nuna min cewa soyayyar su kamar fure ne cikin ƙaya. Gashi da kyau amma kuma haka za a hakura da shi,.idan kuma ka nace kana so. Ba makawa kayar zata illata ka. Idan kuma ka hakura dole haka zaka ji ranka ya raya maka soyayyar furen da take ciki ƙaya. A halin yanzun..Ikram ta kasance fure cikin ƙaya ce. Duk inda Mehran yaƙe yana faffutikar ganin ya iso gare ta, idan ma shi bai isa gareta ba, ita tana kokarin isa gare shi" "Taya bayan tana gidan bada horo? Haka ba zai yiwu ba " Ya faɗa tare da kallon kakan shi. "Zai yiwu mana, kai abinda ka sani kenan. Ita kuma abinda ta sani zata aikata. Kayi hakuri da Ikram domin ita zuciyarta tana ga Mehran..kai ma ai akwai shukrah da take sonka me yasa ba zaka hakura da Ikram ba?" Ka sake yayi yana kallon kakar su, kafin yace mata. "Me yasa kika ce haka?" Gyara zama tayi sannan tace mishi. " Kai anan gabaki daya cikin masoya da dangi kake, Mehran kuma cikin makiya yake rayuwa, da ace yana cikin dangin shine da suke kaunar shi ba zata tab'a komawa gare shi ba" " Amma kuma ai dan daukar fansa ta koma gare shi. Domin rama abinda yayiwa Nu'man." Dariya tayi sannan tace mishi. "Waye ya gaya maka k'iyayya ce ta kaita gare shi? Duk wanda ya gaya maka ta koma ne domin rama abinda yayi mata toh yayi karya, soyayya ce ta maida ita da ɗaukar fansa ne ba zata tab'a amsar tayin shi ba, da ɗaukar fansa ne ba zata tab'a yarda ta amshi ragamar auren shi ba, kasan inda ake kurman Kaunar! Toh ka zuba ido zaka ce na gaya maka Allah ya bamu nisan kwana" "Yanzun Nanna duk soyayyar da na mata ya tashi a banza Kenan? Na sota iya so babu algus me yasa na rasa ta? Soyayyar ta nake mata babu cutarwa a cikin shi amma me yasa ba zan same ta ba? Don Allah Nannah ki taimaka min na same ta. Dan itace abokiyar rayuwa ta...." [5/22, 7:48 PM] Mehkram1256: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 04 Murmushi tayi tare da ɗaukar ruwan da yake gabanta ta kurb'a, sannan ta dauke kanta kana ta cigaba da cewa. "Ba zan ce ka hakura da ita ba, domin ba a san maci tuwo ba sai miya ta kare, wayallah kayi nasara wayallah kuma ka fadi wannan shine abinda zan gaya maka." "Amir SULTAN yana niman ka" a hankali ya juya tare da kallon Bhaiq, sannan ya tashi tare da bin bayan shi. Suna shiga ya zauna a gaban Sultan Mu'allim da Wazir. Shiru duk suka yi sannan Sultan yayi gyaran murya yana faɗin. "Kaje ka tawo da ita" "Toh Atta mun gode." Daga haka ya juya ya bar gurin su, yana kara godiya. Bayan fitar shi Wazir ya kalli Sultan."ina ganin me zai hana ka hakura da wannan hadin da zaka yi ka barta ta akan zab'in ranta, tunda shi Rahil yana da masoya babu amfanin a tirsasata yin abinda bai dace ba." D'ago kai yayi sannan ya sake wata wadatacciyar murmushi kafin yace mishi. " Koda Rahil bai ce yana sonta ba, bana jin zan barta ta auri wani bayan shi, tunda kuma yace yana sonta sai naji faduwa tayi daidai da zama, abinda nake buƙata ne Allah ya kuma biya min bukatar, dukkan su mallakina ne!" "Allah ya huci zuciyar ka, ba wai ina nufin wani abu bane, sai dai idan har aka bata wanda take bukata haka kamar karin daraja ce ga masarautan mu, Yar mu tana auren Sarkin Samaind ka duba abinda idanun basira mana." Lashe bakin shi yayi tare da sunkuyar da kanshi yana wasa da furfuran kanshi, sannan ya kalli Waxir ya sake wata ƙaramar murmushi yace mishi. "Eh na hango katin ci-gaba amma bana jin a raina haka wata masalaha ce, babu cigaban da zata kawo ma, sannan babu wani abinda zai bayyana mana na cigaba dan tana auren Sultan Aamaan Abdus Samad Mehran! Kawai haka ba wani abun azo a gani bane dan babu wani Cigaba da za a ce an samu dan kawai tana auren Sarkin Samaind!" Shiru Wazir yayi yana kallon yadda Sultan Mu'allim, kasa yayi da kan shi ya kuma cigaba da cewa. "Sultan akwai matsala domin Ikram bata son shi da Aure a matsayin d'an uwan ta dauke shi, kuma haka ba zai tab'a kawo zaman lafiya, ido da ido kuke wariya akan ta, kuna nuna mata dan ita mace ce, ba zata zab'i abinda take so ba, sai shi? Haka zai sanya tayi ta mishi kallon ya fita daraja a gaban ku, sannan haka zai sanya tayi ta jin ina ma bata dawo gare ku ba, ban san yadda zan gaya maka kuna cusa k'iyayyar ku a zuciyar ta ba, amma tabbas babu adalci a tsarin ku." Shiru yayi sannan yana nazarin abinda Wazir ya faɗa. ... Ina zaune sai gashi ya shigo, kallona yayi sannan ya sake murmushi yana faɗin. "Bilqisul Ikram!" Dauke kai na nayi ina murmushin bakin ciki, takowa yayi har ina nake zaune. Durkusawa yayi tare da kifa min mari, sannan ya d'ago kai na, tare da yana kallona. Murmushi yayi sannan yace min. "Baki isa ba! Kinyi kaɗan Ikram marina kika yi? Idan da kin dake ni, yanzun baki isa ba." Tofa mishi yawu nayi tare da kallon shi har cikin idanun shi. Share fuskar shi yayi tare da wani irin murmushin takaici. Mikewa yayi sannan tare da cewa. "Ku kunce hannun ta, tare da kawo min ita shashina." Ya faɗa tare da ficewa daga dakin, tunda suka kunce hannun, suka tasa keyana har shashin shi, tunda nake da Mehran bai tab'a nuna min karfi ba, bai tab'a kawo min farmaki ba, yau sabida soyayyar shi Rahil yake nuna min karfi. Tunda na shiga ya saka ni a gaba da bala'i, domin karfi da yaji ya fara kokarin keta min rigana. Dakyar na kwaci kaina, yana ganin haka ya kuma shake ni tare da matse min nonuwa na, kuka ne ya kwace min tare da kallon shi. "Me yasa kake son lalata min rayuwa? Tunda nake da Mehran bai tab'a kawo min hari ba, kullum mutuntani yake tare da girmamani, na kwana a daki daya da Mehran na kwana a jikin Mehran hannun shi bai tab'a isa cinyata ko kirjina ba, bai tab'a kawowa a ranshi zai iya amfani da karfi ba. Yau d'an uwana yake son keta min mutuncina sabida nace bana son shi!" Murmushi yayi sannan ya mike tare da ture ni, ya nufi ban dakin shi yana ji kamar zuciyar shi zata fita, bai dan me yasa yake jin babu dadi akan Ikram ba, kuma ba kome ya janyo haka ba, sai dan yadda take nuna soyayyar Mehran a sama da kome. bata tausayin shi kamar yadda take nuna mishi da, yanzun ga baki daya ta tsane shi sabida Mehran, da zai ga Mehran tabbas sai ya kashe shi. Ya tsani Mehran ya tsani rayuwar shi. Kuma Insha Allah sai ya raba ta da kimarta koda kuwa ba zai same ta ba. Kafin ya fita na tashi tare da ɗaukar alkyabar shi na saka, sannan na nufi shashin mu. Tunda na shiga na zube a tsakar dakin na sake wani irin kuka me mugun cin rai, ina tuna Mehran. Ga baki daya naji na tsani kai na, me yasa a daren da nake duba shi ban bashi kai na ba, koda kuwa ace haka zai janyo min jifa ranar Amarcina. Kuka ne ya kuma kwace min, shigowar Ruwaida da Izmah ya sani juyawa ina kallon su, zama suka yi sannan suka ce min. "Abinda kike babban Abin kunya ne, ace yau kina kuka akan SO, WALLAHI ABIN GORI KIKE AIKATAWA UWAR DAKINA DON ALLAH KARKI KUMA ZUBDA HAWAYEN KI SABIDA SO" Dafa kafana Izmah tayi sannan tace min. "Kiyi hakuri Ikram!" Rintsa idanuna nayi.tare kifa kaina akan cinyar Izmah tana shafa min gashina, sallamar Ruwaida tayi tana kallon yadda nake zubda kwalla. "Ikram ki daina kukan nan, kiyi hakuri Insha Allah idan Mehran ne rabonki zaki mallake shi idan kuma ba rabonki bane shi Allah ya sassauta miki halin da kike ciki." Haka tayi ya rarrashina, har barci ya dauke ni. Gyara min kwanciya tayi tare da jera min matashin a kaina. Kallon Ikram tayi cikin damuwa, tana tuno abubuwan da suka faru, a baya tabbas wannan kadai ya ishi me hankali fahimtar hikimar Ubangiji, duk wannan zafin yanzun duk babu. Sai sanyin da tayi gabaki daya ta zama wata iri mara amfani. Bata iya fada bata iya rigima babu zafin rai babu kome sabida so tayi watsi da kome. ~~~ SAMAIND Kimanin wata daya kenan, kallon juna Jasrah da Mahlika suka yi cike da mamaki, jin likitan masarautan yana tabbatar musu da cikin da Azizatul Nissah take dashi. Saka su mutuwar tsaye. Shi kan shi Mehran kura mata ido yayi. Tabbas ya kwanta da ita tun daga lokacin da ya sha maganin ba sau daya ba ba sau biyu ba. Yasha Narjis ta kawo mishi ita, amma kuma bai tab'a kawowa a ranshi zai mata cikin ba. Domin idan ya tuna duk abinda yake da ita bawai yana mata yadda zata ji dadi bane yana mata yadda zata wahala ta gudu ne ya sami abinda zai kafa hujja dashi sai ga cikin shi ya isa kafa hujja. Wani irin yanayi yake ji na gamayyar damuwa ko tashin hankali. Kallon Azizatul Nissah Fudail yayi domin ya fara gajiya da tashin hankalin da yarinyar ta Kunno mishi wanda shima yasan laifin shine da ya gayawa Mehran wancan lokacin da yaci Ubanta amma yanzun ko ya faɗa zasu kira shi da d'an dakin Ikram ne, shi yasa ya zuba mata ido, yana kallon yadda take kokarin daurawa Mehran cikin da bana shi ba. Babu babban wawa sai shi. Yayi kuskuren barinta da cikin bai gayawa Mehran ba, da ya gayawa Mehran da kome bai faru ba, kuma dan kayan haushi ko Sultanah Fazilatul nisa bai gayawa,.yaja bakin shi yayi shiru dan wauta. "Sultan MEHRAN! Muna taya ka murnan samun Magaji Allah ya sauki Amirah Azizatul Nissah lafiya ta haifa mana Yarima." Cikin karfin iko da mulki tace musu.. "Insha Allah sai dai Na haifi Sultan Abdus Samad Aamaan Mehran, na biyu." Kallonta suka yi tare da kauda kansu, idan. Suka ci-gaba da tsayuwa zata iya saka su fidda abinda yake ransu. Dan haka suka juya tare da barin d'akin, suna mata fatan Alkhairi. Zama yayi a kusa da ita yana kallonta. "Ya jikin naki?" Murmushi tayi sannan tace mishi. "Da sauki, ina son cin abinci amma ina tsoron kar a bani guba sabida kishin rashin samun damar daukar cikin ka." Mikewa yayi tare da barin d'akin, murmushi tayi sannan ta shafa cikin Jikinta, kallon Fudail tayi da ya kura mata ido, tabbas badan kar yayi abinda zai sanya Mehran ya kullace shi ba, da yayi ta dukar cikin jikinta, har dai ta mutu. Amma a halin yanzun kana tab'a cikin kamar ka sayi mutuwa je da hannunka,domin Mehran ba zai tab'a barin ka a raye ba. Amma kuma taya haka ya faru? Cikin a sanin shi na Nawwas ne, kuma sai gashi ya juye tare da komawa na Mehran,.kuma babban damuwar shine meye ya faru ranar da ta fara kwana da Mehran. ---- Kallon ta Sultanah Hoyam tayi sannan tace mata. "Kamar Ya Azizatul Nissah tana da ciki? Kina nufin yayi tarayya da ita ne! Ko kina nufin." Zuɓewa Mahlika tayi tare da rike hannunta cikin juna jikinta yana rawa tace mata. "Sultanah! Duk abinda kike tsammani haka ne". Ture kayan gabanta tayi tare da cewa. "Na aike ki ne ki zo ki gaya min matar da suke kewayen shi.tana da ciki ne? Meye amfanin abinda na baki kina saka musu a shayin su? Wato ga sakarya nan bata san me take yi ba, Yanzun meke tafiya a harem?" "Kiyi hakuri abinda ke faruwa babu dad'i domin dai ta kwace duk abinda ake yi, sannan kuma ta hana kowa shigowa shashinta. A takaice dai hatta abincin da zasu ci sauran matan daga gare ta yaƙe.". Sake wurgi tayi da kayan marmarin gabanta. "Wani irin hauka kika yi ne? Me kika aikata min haka? Baki da hankali da zaki bari kome ya koma hannunta, ni kuma nawa aikin fa?" Sake damke hannunta tayi iyaka razana ta razana, amma bata iya ko tari ba, domin Sultanah Hoyam ta isheta riga da wando, dan haka ta sunkuyar da kanta, sannan tace mata. "Ki gafarce ni!" "Tashi ki fita!" Ta daka mata tsawa. Da sauri ta mike tare da barin d'akin, ta nufi harem. Ajiyar zuciya ta sauke yafi sau uku. Sannan ya nufi Harem, tunda ta nufi hanyar gidan, take jin kamar zuciyarta zata buga, tana shiga tayi karo da Rubina babban baiwar Azizatul Nissah. "Ina kika tafi? Toh muje zaki yabawa aya zakinta, tunda da zaki fita baki gayawa Sultanah Azizatul Nissah ba. Wato anje kitsa munafunci ko?" Bata ce mata kome ba, har ta shiga gurin Azizatul Nissah, kanta a sunkuye. Tana shiga ta tsaya daga bakin kofar shiga d'akin. "Da izinin waye kika fita daga Harem?" Shiru tayi tare da wasa da warwaron hannunta. "Kinawa Ikram Aiki ne?" Da sauri Mahlika ta d'ago kanta, tare da girgiza kai tana faɗin. "Me kuma zanyi mata bayan bata nan!" "Ki min shiru! Koda yake ba mamaki kinawa Jasrah aiki ne ko? Toh zo nan." Durkusawa tayi a gabanta, tare da matsawa kusa da ita. Babu tausayi ta shiga marin Mahlika, sosai fa tun yarinyar tana jurewa har ta kasa jurewa, bata fasa ba, shigowar Mehran ya sata sauke hannunta da ta d'aga, zata kuma marin Mahlika. "Meye haka?" "Sultan MEHRAN! Abu ta kawo min da guba, wai ikram ce ta bata sakon duk lokacin da ta sami labarin ina da ciki ta zuba min nasha." Ta faɗa tare da sake kuka. Wangale baki yayi tare da kallon su, kara kallon Mahlika yayi yasan yace mata. "A sanina baki shiri da Ikram meye gaskiyar abin da ta faɗa?" ... [5/22, 7:48 PM] Mehkram1256: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 5 Jikinta ne ya dauki rawa, tana kallon sharri kiri kiri. Amma bata da ikon kare kanta, kallon ta yayi a karo na biyu fuska babu alamar wasa yace mata. "Ba dake nake ba?" Ya faɗa da dan karfi, haka ya sanya ta kuma rud'ewa tana zaro idanu. "Sultan!" Ta kira sunan shi jikinta yana wani irin rawa."Fudail!" Ya kira sunan Fudail ko rufe baki bai yi ba, sai gashi shigo d'akin. "Yawwa bawa Fudail ka tafi da ita,.ka kuma tabbatar ka hukuntatta, domin tayi yunkurin zubda min cikin jikina ko Sultan Mehran" ta ambaci sunan Mehran tana kallon shi. Dauke kan shi yayi tare da zama ya kasa cewa kome. "Zaku iya tafiya!" Ta kuma fada, tana murmushi. Matsowa tayi kusa dashi, ta zauna tana me sake mishi murmushin jin dadi. "Sultan MEHRAN! Kaga ikon Allah baka ta samu haihuwa ba sai a kaina, kuma." Juyawa yayi yana kallonta,.kafin ya dauke kanshi yana me jin b'acin rai akan yanayin da yake ciki. Haka tayi ta damun shi da magana, ganin yaki kulata yasa ta mike tare da barin d'akin, bin bayanta yayi da ido, ita kuwa tana fita bata tsaya ko ina ba, sai Shashin Sultanah Fazilatul nisa, tana tare da Shairah da Narjis, suna tattaunawa ta shigo. Murmushi tayi sannan ta nemi guri kusa da Sultanah tace mata. "Nazo ne ki albarkaci jikanki da yake cikin mahaifana" A matukar mamaki suka kalle ta, bakin su sake. "Sultan MEHRAN bai gaya miki bane? Ai wata biyu da suka wuce ya..." "Toh ya isa!" Inji Shairah, ya daka mata tsawa. Gyara zaman tayi cikin fusata tace mishi. "Kai waye? Bawa dan daudu, ni zaka dakawa tsawa? Lallai kana son na saka a maka koran kare." "Ya isa haka, me kike bukata?" Inji Sultanah Fazilatul nisa. Tana kallonta, Dariya tayi sannan tace mata, "Bana son a kuma barin Mehran yayi mu'amala da wata mace! Sannan bana son ana shiga shirgin shi. Idan da hali a fita hanyar shi. Domin nice Magajiyar sarauta nan gaba, Uwar Yaron shi da yake kwance mahaifana!" Ta mike tare da zaga dakin tana murmushin mugunta, tana faɗin . "Mugun hukunci zai tabbata a kan wanda ya Kuskura ya shiga lamarin Mehran. Zan gyara mishi tunanin shi da nazarin shi, kar na kuskura naji mugun labarin akan haka, a sanar da matan da suke dakon ya kwana dasu." Tana gama fadar haka ta bar dakin cikin jin dadi tare da jin ta isa domin ta kaftawa Sultanah Fazilatul nisa kashedi kuma hakan zai taimaka mata, domin idan ba haka ba tana ji tana gani sauran matan da suke hareem zasu iya daukar cikin Mehran. Koda ta fita, kallon matan da suke hutawa tayi, sannan ta zauna tana gyara gashin kanta, tana murmushi. Baiwarta Rubina ta kalle matan gurin ta shiga musu bayanin cikin Azizatul Nissah, take Jasrah ta mike tana faɗin. "Karya ne, baki isa ki" "Kawo min ita nan" inji Azizatul Nissah, babu musu aka kawo ta, jefata aka yi a gabanta, mik'ewa tayi a hankali, tare da kallon ta. Murmushi tayi sannan tace mata. "Kika ce me?" "Kar..." Kifa mata marin da tayi yasa ta had'iye maganar da zata yi. "Rubina, ki zane min ita." Inji Azizatul Nissah wai a zane Jasrah. Duk sauran matan hatta Sakeenatu binti Abu Waqqas, sai da jikinta yayi sanyi, domin tunda take rayuwa bata tab'a tsintar kanta cikin mugun yanayi ba, sai da ta shigo cikin Samaind. Akan idanun su, aka zabe Amirah Jasrah irin mugun dukar nan da babu wanda ya isa yayi maka ita sai mugu. Shafa Jelar gashin kanta tayi tana faɗin. "Ya isa haka, ba ita ba hatta ku idan kuka kuskura kuka d'aga min murya zan ba kowa kyautar hukuncina, ku dauke ta ku kaita shashinta." Cikin wani irin tsoro da fargaba tabbas Azizatul Nissah ta shirya fuskarta kowa kuma a cikin wannan yanayin, ta gaya musu ciki ne da ita, dan haka kar kowa ya taka shashin Sultan Mehran sai da izinin ta. Gyada mata kai suka yi. Domin babu wata hanya da zasu mata bori. ---- "Meye ya hadaki da ita har ta sako Ikram a maganar ta." Fudail ya tambayi Mahlika. "Kawai sharri take son yi mata, kuma tasan a halin da Mehran yake ciki na kewar Ikram zai iya tsanar." Rike bakinta tayi tana kallon shi. Murmushi yayi sannan yace mata. "Karki damu. Yanzun me kike ganin zaki yi?" Shiru tayi sannan ta sunkuyar da kanta kasa, tana me jin kamar tace mishi zata koma Madinatul Mah, sai kuma ta d'ago kai tana faɗin. "Babu abinda zanyi." "Ni kuma zan sakaki aiki" ya faɗa mata yana leka hanyar, a hankali ya matsa tare da gaya mata abinda yake son tayi mishi, zaro idanu tayi sannan tace mishi. "Zanyi amma da sharadin. Zaka hada ni da sultan Aamaan! Murmushi yayi sannan yace mata. "Ba zan iya hadaki dashi ba, mutum ne me ra'ayin kanshi, idan kika sami damar ya gayyace ki toh idan kuma baki samu wannan damar ba, ina me tuna miki aikina da na baki. Sultan MEHRAN yana cikin kewar Ikram ne ko yayya aka tunzura shi zai iya aikata wani abu bayan haka." Yana gama gaya mata haka ya juya abin shi ya barta a gurin. Shiru tayi na wani lokaci kafin ta bar gurin tana jin itama zata tsayawa kan. ...... A can cikin gidan kuwa, kallon Juna ake tsakanin Sultanah Fazilatul nisa dasu Shairah. Kura musu ido tayi kamar tana son gano gaskiyar abinda Azizatul Nissah ta faɗa, sai kallon su take kamar tana hango abinda. "Ina Mehran? Maza ku nimo min shi." Ta faɗa da karfi. Kallonta suka yi kafin suka ce mata. "Yanzun lokacin hutawar shi ce, idan muka." "Nace ku nimo min shi ko?" Babu musu suka fita, shashinta suka nufa, inda Shairah yayi karo da Sultanah Hoyam, itama tana kokarin shiga shashin Sultan Mehran. "Dama kana raye?" Murmushi yayi sannan yace mata. "Ina nan daram." Ya bata amsa. "Toh haka ma yayi, sai dai har yanzun baka gaji da bautawa matar da bata san ƙaruwar ku bane." Murmushi yayi sannan yace mata. "Gaskiya labarin da nake ji bai kai adadin abinda zaki bani ba, koda yake ai girman jiki gare ki bana shekaru ba, idan kika sake mummunar alaƙar da kike da Darakshan ya fito tabbas." A firgice take kallon shi. "Karka min Sharri!" Sassauta muryan shi yayi sannan yace mata. "Karki damu, babu wanda ya fahimci haka sai ni, kuma babu wanda zai fahimci abinda kike aikatawa sai har kin tonawa kanki asiri." Daga haka ya wuce ta bai kuma mata magana ba, karshe bata shiga gurin Mehran ba, ta koma da baya. .... Yana shiga ya same shi zaune ya faɗa cikin mugun tunani me shegen zurfi, dan ya jima akan shi kafin ya mishi magana ya farka. Ajiyar zuciya ya sauke kafin ya kalli Shairah. "Sultanah tana son ganin ka!" Kurawa Shairah idanu kamar wanda yayi mantuwa, a hankali ya janye daga kallon shi tare da gyada mishi kai, fita yayi cikin tausayin MEHRAN, domin baki daya yayi laushi. Tausayin yadda soyayya ta maida shi yake. Ya jima yana nazarin abinda yake damun shi wanda yayi itifakin Babu shakka Ikram itace rayuwar shi, sannan bayi da wani kuzari sai idan tana tare da shi. Ya san a wannan lokacin tana tare da Rahil. Suna soyayyar su. Haka kawai idanun shi ya shiga hango su, suna hira a lambun suna soyayya. Watsi yayi da kayan gaban shi,yana haki. Kwalla ne ya cika mishi ido, a hankali ya kai hannun shi kirjin shi yana jin kamar zuciyar shi zata buga. "Innalillahi wa'inna ilaihi rajioun Ubangiji ka yayye min, ka kuma kara min hakurin rashin ta. Ya Allah ka jarabce ni ta inda ba zan iya cinyewa ba. Ya Allah na tuba ka yafe min." Ya faɗa tare da jin kwalla nason zuba daga idanun shi mai dasu yayi, tabbas yana cikin wani hali, Ikram ta shiga rayuwar shi. Ya jima sosai a gurin kafin ya daidaita nutsuwar shi yayi sannan ya fita daga dakin. --- tunda ya isa shashin Sultanah, bai ce kome ba sai dai duk tambayar da tayi mishi baya ko motsi balle ta saka ran zata sami amsar tambayoyinta. "Aamaan" ta kira sunan shi kamar ,zata fashe da kuka tana cewa. "Meye gaskiyar abinda." "Anneh bana son kina shiga cikin al'amarin gidana." Daga haka ya mike zai bar d'akin tace mishi. "Amma me yasa ba zaka gaya min abinda yake damun ka ba?" Juyawa yayi tare da sake murmushin takaici, sannan ya bar dakin yana ji kamar ya had'iye zuciyar shi ya huta, ranshi ya kai kololuwar ɓaci, baya ganin gabansa. Yana shiga cikin d'akinta ya tokari kofar shi, kallon shi tayi a razane. Amma ta dake, juyawa tayi tare da kallon bayin d'akinta. Da sauri suka fita, Da sassarfa ya isa gabanta, zai kamo wuyar ta, tayi baya tana girgiza mishi kai. "Duk abinda aka gaya maka karya ne, tunda suka ji labarin samuwar cikin jikina suke kokarin ganin bayan shi, sabida." "Na tambaye ki ne? Nace kiyi min magana ne? Meye ya kai ki shashin Mahaifiyata." Ya tambaya ta a tsawace. Diriri cewa tayi kafin ta saka mishi kuka, tana faɗin. "Ita Fazilatul nisa ce Mahaifiyar ka?" "Tauuu!" Ya kifa mata mari, wanda yasa ta ganin taurari, a hargitse ta d'ago kanta, wani shegen tsoro ne ya kamata bata san lokacin da ta sunkuyar da kanta ba, gwiwarta zube a gaban shi. "Na kuma jin labarin haukarki ta kwashe ki har kofar shashin ta, sai na karya ki na maida ke yankin ku, kije can kuyi ta haukar ku sakarya." Yana gama fadar haka ya juya tare da barin d'akin, tunda ya fita yake jin kamar ya tattara ya bar SAMAIND ko zai sami sauƙin damuwar da yake ciki, amma ina. ---- Dan haka ya tattara ya koma can gidan shi da ya tab'a zama, dan anan yake jin zai iya samun nutsuwar da ya rasa. Tare da Fudail suka koma sai masu kula da abinda zai ci, sam baya son magana ko da kuwa a cikin mutane ne, yafi son ya keb'e kanshi yayi shiru. ---- Merocco. Da wani zai gaya min yadda rayuwata zata koma ba zan yarda ba, dawowar Nimrah bai kara min kome ba, sai damuwa domin tunda tazo bata da wani aiki sai kukan halin da ta sami Mahaifiyarta, ga kuma soyayyar Fudail da ya kamata, kwanciya tayi a jikina. Tana zubda kwalla, tare da gaya min halin da take ciki. Shafa kanta nayi domin ita kukan dad'i take, kuma nasan zata sami abinda take so ni kuma fa? Waye zai bani abinda nake so? Sam mulki da nasabarta bata dace da rayuwata ba, ni rayuwar Yanci nake so. Bana bukatar kome bayan Yanci, shi yasa da zan mallaki Mehran tabbas zamu bar SAMAIND har karshen rayuwar mu, mu shiga inda ba za a kuma ganin mu ba, muyi rayu daga mu sai Yaran mu. Wannan shine tsarin da nake shirya mana,.kamar Yadda iyayena suka bar gidajensu, haka mu ma zamu bar cikin daular mu. Muje mu kafa kanmu tare da boye asalin mu. "Assalamun Alaikum!" Sallamar Rahil ya katse min nazarin da nake. Lumshe idanuna nayi kamar ina barci, shigowa yayi tare da zama yana kallon yadda na sunkuyar da kaina, murmushi yayi tare da cewa. "Toh meye laifin sallamar da ba za a amsa min ba?" Ya tambaye ne ni, tare da tsare Ni da ido. Mikewa Nimrah tayi tare da kallon shi tace mishi. "Barka da shigowa Amir Rahil," d'aga mata hannun yayi yana murmushi, a hankali ta bar d'akin. Dawowa gabana yayi tare da zama ya zuba hannun shi akan cinyata. "Me yasa kika fi son shi akan Ni? Meye bani dashi? Dame ya fini da kike zubda hawayen ki sabida shi?" D'ago kai nayi ina kallon shi sannan nace mishi. "Kai zab'in kakannin mu ne, shi kuma wani shashi ne na rayuwa ta, zan amshi aurenka ne... [5/22, 7:48 PM] Mehkram1256: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat Book3 _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 6.. Cike da mamaki yake kallon yadda nake kokarin gaya mishi gaskiyar da ya kasa Fahimta, so nake lallai ya gane babu dole a soyayya. Kura min ido yayi tare da sake murmushi yace min. "Koda zaki na yankan namar jikina kina ɗona min gishiri zan zauna da ke haka kuma zan kare rayuwata dake!" Murmushi nayi mishi tare da shafa kanshi nace mishi. "So bai maka adalci ba, kamar yadda ya ratsa tsakanin zukatar mutanen da basu shiryawa zanen ƙaddarar su ba, ba zan hana ka ba." Rike hannuna yayi cikin na shi sannan ya matse a hankali, yana murza yatsuna hannun. "Ikram ni na dace dake, karki manta zan zauna dake a duk yadda kike, Ikram ina tsananin kaunar ki" Rike hannun shi nayi cikin nawa tare da kura mishi ido, ina hango iyakar gaskiyar shi. Dauke kai nayi tare da cewa. " Nasan kana sona, amma ya aka ji idan ka taso daga sahara me matsanancin zafin rana, sannan kuma kana murnan zaka tsallake kana hango koramar ruwa, kana isa ka sami ruwan an hanaka sha. Ya zaka ji? Toh haka ka shiga tsakanin mu." Mikewa nayi zan shiga ban daki yace min. "Zan iya hakuri dake har zuwa lokacin da zaki soni amma Tabbas zan aure ki. Kuma zan zauna dake." Cak na tsaya sannan na juya ina kallon shi, kafin nace mishi. "Zaka zauna da ni Tabbas zaka ƙunshi bakin ciki, domin zan zame maka kamar ramin maciji ne, kowani motsi kayi da dafina zaka motsa, bana son mu kai ga haka shi yasa nake gaya maka illar haka." Na shige abuna. Shiru yayi tare da jin babu dadi a ran shi, amma kuma babu yadda ya iya, dole haka ya saka kai ya fice daga d'akin. Tunda na shiga ban daki na fashe da kuka, tare da zama a gurin ina kuka, Tabbas na san yana sona, amma haka bayana nufin zan iya rayuwa da shi bane, Mehran shine zab'i na, Rahil dan uwana ne shi. Ban shirya zama dashi a matsayin abokin rayuwata ba. A hankali na fito daga ban dakin ina sauke ajiyar zuciya, tare da zuɓewa a jikin gadon dakin ina jin kwalla na zuba min. Mehran shine zab'i na, shi din farin cikina ne..idan ana iya musayar so ba zan tab'a musayar Soyayyar shi ba, ina mugun son shi, a lokacin da ba zai min amfani ba. Lokacin ya gama kure mana, dan haka na had'iye kukan tare da kifa kai na a jikin gadon, ina jin wani irin kewar shi. *** Takowa yayi har gaban gawar da masunta suka dauko shi daga ruwa. Babu abinda ya sami gawar, kamar bai jima da mutuwa ba, sai hasken fatar da yayi irin fari fauu din nan. Kallon gawan Nawwas Fudail yayi sannan yaja mayafi ya rufe kafin yace. "Wannan gawar shugaban dakarun daular Umayyad ne, dan haka ba zamu binne shi ba, sai mun san ta yadda aka yi gawar ta wanzu a cikin yankin mu." "Toh shugaba!" Suka amsa mishi. "Kwanakin Baya mun ga lokacin da ya shiga wata jirgi, tare da a yarin daga nan ne na shiga jirgi na, na haura saman Teku, daga nesa na hango lokacin da ake jefa wani a cikin ruwan amma ban sani ba ko shine ba." Gyada kai Fudail yayi lokacin jin da yaji bayanin wani mutum da yaga lokacin da Abrad yasa a wurga gawan Nawwas a ruwa. Murmushi yayi sannan yace mishi. "Toh babu kome zamu bincika." Gaba yayi sannan dakarun suka ɗauki gawar a makara, suka nufi cikin garin SAMAIND da shi. ..... Kallon Mehran Azizatul Nissah tayi tare da toshe bakin ta, tana me fashewa da kuka, da gudu ta nufi hanyar da zai sadata waje, Bin bayanta yayi sabida karta tab'a lafiyar cikin jikinta, zuɓewa tayi a gaban gawar tana kuka da ihu, sabida yadda ta ga gawar shi bata kawo hakan ba a ranta, dakyar Mehran ya d'aga ta, ya koma da ita, sai da aka gama bai bincike sosai, kafin aka nad'e gawar aka mishi jana'iza. "Zan tafi gida, ina ganin babu wanda yasan da labarin mutuwar shi don Allah karka hanani." Shafa kanta yayi tare da maida gashin ta baya, yana me jin tausayinta a ranta, sannan yace mata. "Ba yanzun ba sai kin haihu." Wani irin kuka ne ya kwace mata, bata san lokacin da ta kuma sake kukan ba, ta rike hannun shi tana faɗin. "Toh taya zasu sami labarin mutuwar shi." "Zan aika da sako a gaya musu. Insha Allah" sake rungume ta yayi, ta kuma narke Mishi kamar wacce take cikin tashin hankali na gaske. Haka yayi ta rarrashinta, domin kuwa baki daya ta birkice mishi. Kwana biyu tsakani idan ka ganta zaka Dauka jinya tayi nan kuwa dauke hankalin shi tayi da makirci kamar mutuwar ya dake ta. Duk da kuwa ta kadu da mutuwar amma ba wani jijjiga ta ba, sabida cikin jikinta kar yace dai kwace abin shi, ko wani dalili da zai fito ya fadi gaskiyan cikin nashi ne, Tabbas akwai matsala domin haka zai iya janyo yakin da za a rasa rayukan al'umma, sannan itama bata tsira ba, kisar wulakancin za a mata a gaban jama'a. Dan haka mutuwar Nawwas yazo mata a gaɓɓar da ya dace, dan haka bata ga abinda zai wargaza mata lissafin ta ba. Shima Mehran duk ya damu, domin a tunanin shi da gaske take, dan haka duk ya shiga damuwa duk da yana cikin damuwa, amma sai ya tsinci kanshi da tausaya mata sosai, har yakan zauna yana b'ata lokacin shi akan ta, ita kuma haka sai ta narke tayi ta nuna alamar bata ita fa tana kewar gida, dan haka ya taimaka ya kaita ko da yayya ne yan uwanta sun san yadda take ji gashi babu wanda ya san da mutuwar sa ita. Dan kar ya samu damar da zai nufi gurin Sultanah Fazilatul, yasa ta baki daya ta kawo mishi yanayin da take ciki, yana fita sallah zata ware, ko kuma tayi ta kuka, asalima ta hana shi ko zuwa fada, domin yana fita zata saka rigima haka zai dawo matan da suke dakon shi kuwa haka suke jin babu dadi ga zafin kishinta da suke ji. Wata idan ka nutsu zaka Fahimci burin Azizatul Nissah, bukata take ta dauke hankalin Mehran baki daya, haka da sauran suka gani yasa su hade kan su, suka tsayar da shawara. Akan su shiga jikin Sultanah Fazilatul nisa, sai aka yi rashin Sa'a an sami munafukai a cikin su. Wato Sakeenatu binti Abu Waqqas, ta rubuta wasika ta bawa baiwarta mesuna Munirah ta kaiwa Azizatul Nissah. Ita kuma da ta tashi hada rigima sai ta sauya tsarin labarin tare da kwafe wani ta saka wani abu na daban. Sannan ta bawa Baiwarta me Suna Unaizah takai Fada. Inda Sultan Mehran yaƙe, tare da shaidawa duniya cewa tana dauke da juna biyun shi. Shiru Fadar yayi sannan magatakardan ya cigaba da karanta wasikar kamar haƙa. _Sultan Mehran a halin da nake ciki ina dab da rasa rayuwata, ba dan kome ba sai yadda Fazilatul nisa! Tasa Matan da suke Hareem su dake ni! Sultan MEHRAN ka kawo min a gaji domin zasu kashe ni da goyan bayan Matar da kake mata kallon Mahaifiyarka, tare da amintacciyar baiwar Ikram_ Wani irin lumshe idanun shi yayi tabbas, yana bukatar ya dakatar da Sultanah Fazilatul nisa, amma yana jin wani irin girma da darajar ta a ran shi, shi yasa yake kasa murza mata kome, dan haka ya mike ba tare da yayi musu magana ba, ya nufi cikin gidan. Kallon juna suka yi manyan Fadar. "Kanwar Abrad ce ta samu damar daukar cikin shi? Lallai akwai abinda yake shirin Faruwa, idan har muka dake wata daga wata daular ta haihu da Mehran har abada mulki ya fita hannun Daular Abbasiyyah! A barar da cikin" Dariya Sultanah Hoyam tayi sannan tace musu. "Cikin ba zai tab'a zuba ba! Sabida shi kanshi cikin zan bukaci na tsaya kan shi kamar yadda na tsaya akan uban dab haka babu batun zubda jinin Mehran" "Amma!" "Na yanke kuma ya yanku, babu wanda ya isa ya sauya min ra'ayina, ko kuma dole kubi abinda nace." Ta fadi haka tana mik'ewa daga kujeran ta. Bin bayanta suka yi da ido, Tabbas sun dibo ruwan dafa kansu dan haka su san abinyi domin kuwa har da hannun yaransu a cikin abinda aka turo, wani irin hukunci Mehran zai dauka akan Yaran su? Kuma me yasa ya ajiye FAZILATUL a gidan sarautar? Duk basu da amsar tambayoyinsu dole shi ne zai basu. "Toh ya zamu yi idan da hannun Yaran mu a ciki!" Inji Mir Umdatuddawla, "Sai mu maida laifin kan Fazilatul nisa, ai tafi su hankali, kuma sunanta ya fara fitowa kan nasu, dan haka karka damu sune zasu kwaci kan su." Daga haka suka watse daga fadan. ---- Lokacin da Mehran ya shiga cikin gidan, Ya samu Sultanah Fazilatul nisa tana kokarin shiga tsakanin su Jasrah da Azizatul Nissah, sakamakon fadar da suke yi, wanda dama can tana cike da ita akan zaneta da ta saka aka yi, dan haka ta same ta da bugu, a bangaren Azizatul Nissah itama abinda take bukata kenan Mehran yazo ya same su a wannan yanayin, sabida ta sami damar sharrin da ta kulla musu. Tana ganin shi ta yanki jiki ta fadi tare da rike cikin jikinta. "Wayyo Allah na, wayyo cikina, wayyo Mehran" Ga baki daya ta birkice mishi tare da murkusussu, kallon Sultanah Fazilatul nisa yayi, cikin matsanancin b'acin rai. "Anneh! Sad'akata ce kika sa Jasrah ta sake ta da cikina?" Zaro idanu tayi waje tana faɗin. "A'a Aamaan akan me zan saka su dake ta? Me tayi min da zafi haka da zan tab'a lafiyar ta." "Ya isa! Ki tattara ki bar cikin fadar nan ko kuma." "Sultan MEHRAN!" Fudail ya kira sunan shi da karfi. "Karka hana shi, bar shi ya kore ni barshi ya tura ni waje saboda Azizatul Nissah." Sanyayye ta juya zata bar falon, amma ba haka Azizatul Nissah taso ba, taso idan ya kore ta yasa a kaita gidan horo, b'ata fuska tayi sannan tace. "A haka zaka kyaleta, ba ka hukunta ta ba, bayan so take a kashe ni itama Jasrah hukuncin. Da ya dace da ita kenan, sannan a nuna musu matsayina." Kallonta yayi tare da kai hannun shi kan cikinta yace. "Fudail ka kama Anneh,. A kaita tsohon gida ta zauna a can kar a hada da masu kula da ita, a barta ita daya, Jasrah kuma a kaita gidan horo." Daga haka ya mike tare da Ɗaukar Azizatul Nissah, kura musu ido Fudail yayi, a ranshi yana cewa. *Ikram itace kawai zata iya dakatar da wannan wulakancin* sannan ya raka Sultanah Fazilatul nisa yana bata hakuri, murmushi tayi sannan tace mishi. "Karka damu, tunda Ikram ta bar gidan nan na fahimci babu me iya tankwara Mehran bayan ita, Azizatul Nissah kuma tayi amfani da cikin jikinta ta juya mishi tunani, amma nayi mishi Uzuri." "Yanzun babu abinda za ayi Ikram ta dawo?" Ya tambayi Sultanah Fazilatul, "Itama danginta suna kaunar ta, babu wanda zai so ta shigo wannan rayuwar." Ta faɗa tana share kwalla. Haka ya takata har gidan, sannan ya dawo ya tasa keyar Jasrah. Bayan Mehran ya kai Azizatul Nissah d'akinta, lallab'a ta ya shiga yi har tayi kamar ta fara barci, kallonta yayi sannan ya mike zai bar dakin ta rike hannun shi. "Sultan MEHRAN! Shin kana kaunata?" Kura mata ido yayi sannan ya zare hannun shi cikin nata, sannan yace. "Ina Sonki mana, koda abin cikin jikinki." "Me yasa ba zaka kaunace ba?" Murmushi yayi sannan ya shafa kanta, bayan ya mike zai fita. "Ko har yanzun wancan Yarinyar da maza suka gama hawa da sauka akan ta kake kauna? Amma kuma taya zaka gayawa Al'ummar ka Ikram ta tab'a aure har ta kwanta da wani namijin? Koda yake ai baka san yadda akayi kome ba, domin Yayana ya sha kwanciya da ita ni ganau ce ba juyau ba.... [5/22, 7:48 PM] Mehkram1256: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat Book3 _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 7... "Ya isa haka!!!" Ya daka mata tsawar da sai da dan cikinta ya juya zunzurutun fusata, jikin shi yana kerma ya nufe ta kamar zai rufeta da duka. "Kika sake raina ya b'aci dake, ba zai miki kyau, wallahi sai na baki mamaki. Sai na wulakanta ki a cikin Masarautan nan, sakarya me kike son nayi miki? Ita nake kauna. Ita na fara sani, ban damu ba ko mazan duniyar nan zasu kwanta akanta abinda na sani kaunarta dani gaskiya ce, babu karya a cikin shi. Idan na kuma jin Kinyi irin wannan haukar zan baki mamaki." Daga haka ya fita ya barta, ita a tunaninta Mehran irin mazan nan ne da zaka. Sarrafa su cikin tsarin da ka gindayawa musu sai ya nuna mata shi baya cikin mutanen da zaka tanada domin bukatar kanka. Mehran da Ikram ba tasha ta da a tare da shi ba, duk da kuwa suna kaunar juna Kamar ya, murmushi da farin ciki ne suka rufe ta, kamar zata tashi sama. Ta jefe tsuntsun biyu da Dutse daya, ta sanya shi ya kori Mahaifiyar shi da Jasrah ta kuma cusa mishi jin haushin Ikram, kenan babu amfanin da ba zai mata ba,. Dan haka daga yau tayi ta sanya shi cikin wani yanayi kenan. Kiran Rubina da Unaiza tayi tare da basu silallar zinari akan suje su watsa a ko'ina na farkon da bayi mata suke zama. Tana murmushi, suma cikin farin ciki suka fita suna watsawa. Kallon juna Sawda da suka baiwar ta me suna Atika, cikin yanayin damuwa tace mata. "Uwar d'akina, kamar fa anyi haka ne dan a tinzira zuciyar ku." Murmushi tayi sannan tace mata. "Karki damuwa, dan haka saka ido ki ga yadda za ayi ta." Mik'ewa tayi tare da barin gurin, ta nufi waje, a hankali take tafiya har ta hango Sultan MEHRAN a can yana zaune. Fudail yana tsaye a gefen shi. haka ma Sarwat shima yana gefen shi. A nutse ta isa inda suke, kallon su tayi tare da musu alamar su basu guri. Zama tayi a daya daga cikin kujeran dake gurin na alfarma, a hankali ta zubawa fuskar shi idanu. Kallon ruwan da aka kawo mishi bai sha ba, ta mike da kanta ta zuba mishi tare da mika mishi. Amsa yayi tare da dauke kan shi, sai da ya sha sannan ya cigaba da rike kofin ruwan. "Uwa irin Fazilatul nisa, ba zata tab'a yunkurin abinda zai tab'a ɗanta ba, tunda mutanen duniya suka fahimci karfin Abbana yana tare da Ummina suka saka shi a gaba sai sun raba su, amma kasan me? Uwa irinta ake alfahari da ita, domin duk abinda aka yi domin a raba tsakanin su, Allah bai yarda ba sai da shida kanshi yayi ikon shi da ita. An yiwa mahaifiyar mu kome domin itace Kwarkwarah shi da yafi kauna, amma kuma lokacin zuwa lokacin ana batun matsayin irin na sarauta sai gashi an cilla rayuwarta cikin hatsari, Mahaifiyar mu, ta badda rayuwar ta ne ta hanyar da aka so ta kashe Abban mu, sai ta amshi gubar tasha, kafin ta rasu ta rubuta cewa. Ita bata yi haka dan kowa ba sai dan Ni da Abba na, don Allah kar ya tura rayuwata kamar yadda ita ta tura rayuwarta. Sultan MEHRAN ban baka labarina dan kayi ta kallona ba, na baka labarina ne sabida Sultanah Fazilatul nisa da kasa aka rufe ta a wani gurin. Duk wanda yake tare da kai yasan kana kewar Ikram, amma sabida zurfin ciki ka iya b'oyewa domin fusakarta Al'ummar ka, Sultan MEHRAN ban biyo ka ɗan na cusa maka b'acin rai ba, na biyo ka ne, dan na tuna maka mahaifiyar ka bazata tab'a ganin bayan ka ba. Amma kayi hakuri Insha ALLAH ba zan kuma maka shishigi ba." Daga haka ta mike zata wuce, riko hannun ta yayi tare da kallon yadda take kokarin barin gurin. "Zauna!" Zama tayi tana kallon shi, sake shanye ruwan yayi sannan ya mika mata tare da cewa. "Kara min!" Ta kuma zuba mishi ya shanye, sannan ta kuma zuba mishi ya shanye, kafin yace mata. "Ban taso da kowa ba, haka nayi rayuwa cikin kaɗaici da bani umarni nayi kaza nayi kaza." Shiru yayi tare da lumshe idanun shi kafin ya bude a kanta, yana faɗin. "Lokacin da ta shigo rayuwata ta sha wahala sosai, ta sha ukuba, ni kaina nasan na bata azaba da hannuna, amma kuma ta tafi ta barni da ciwon da ba zai tab'a warkewa ba, ya zaki ji idan aka ce miki abinda kake matukar kauna bai da inganci?" "Idan har kaunar nakewa abun taya zan damu da batun mutane, Sultan Mehran karka daka ta mutanen duniya haka suke su kashe kashe ka, da ranka ba abun damuwa bane." Tagwayen ajiyar zuciya ya sauke tare da kallon ta, sannan yace mata. "Anneh! Tasan ita ta haife ni ta cilla rayuwata cikin gararin? Laifin Anneh yana da yawa, domin Ikram ce ta sani fahimtar kome akanta, shin zan iya yafewa Anneh, ta kashe mahaifina sabida mulki ni kuma tana son ta kashe abin da za a haifa min taya zan iya dauke kai na akan abinda ta aikata? Hada baki tayi da ku zaku kashe abin cikin Azizatul Nissah fa, Kinga kuwa dole naji babu dad'i." Cike da mamaki take kallon shi sannan tace mishi. "Wallahi bana son zama a cikin wannan masarautan amma sanin cewa nan ne zaman lafiya na, ya sani amincewa na zauna da kai. Na rantse da Allah wanda babu wani sarki sai shi, Sultan Mehran, Anneh bata tab'a tunanin tayi maka haka ba, bari kaji abinda ya faru." " Bana son jin kome, tashi ki tafi kawai" ya faɗa mata, babu musu ta mike tare da mishi sallama. Cikin damuwa ta nufi hanyar barin gurin, kallon Fudail tayi sannan tace mishi. "Yaki saurarona, ban san me haka yake nufi ba, dama haka yake da kafiya?" "Rashin Ikram ce ya kuma mai dashi zuwa haka" "Tana ina ne yanzun?"ta tambaye shi. "Tana can Merocco, ana shirin bikinta da Amir Rahil, dan uwanta ne" ya bata amsa, "Toh amma haka zamu zuba ido muna kallon shi babu me iya tankwara shi akan abinda yake aikatawa? Ni yanzun idan nace zan tafi can, zai yi wuya ya barni na tafi amma don Allah kayi wani abu, sannan a kaiwa Anneh bayinta domin jikin girma da damuwa zai mata yawa, idan aka kai mata mutane tana jin motsin su zata rage damuwa." Gyada mata kai yayi sannan yace mata. "Toh ya zamu yi da Mehran idan ya fahimci mun kai mata bayi?" "Karka damu, zan gyara kome Insha Allah. Sannan ka sami lokaci ka bani labarin Ikram, tayu na dauki wani abu daga cikin halayyar ta." Gyada mata kai yayi sannan suka yi sakayi sallama, ta bar gurin. Cike da gamsuwa. Idan baka iya kuka ba aka ce uwarka ce bata mutu ba, dan haka Sawda tayi amfani da wasu dabi'a tare da bin bayan Mahaifiyarshi domin samun kusanci da ita. Tun daga ranar ta maida gurin shi gurin hirar ta, dukda tana yawan mishi shirme haka yasa shi jin zai iya sawa a dawo da Mahaifiyar shi, tunda itama Sawda tayi kokarin ganin ya fahimci gaskiya, sanan itama tana kokarin zuwa har inda Sultanah Fazilatul nisa take, tana zama da ita. ~~ Kallon kakan shi yayi wanda ya haifi Mahaifiyarshi, kafin ya shiga wasa da kofin shayin da aka bashi ya cigaba da cewa. "Insha Allah zan yi yadda kace, sai dai zuciyata ba zata ji dadi ba," "Ka gwada Rahil zaka sami nutsuwa, kuma itama zata girmama al'amarin ka, zata kuma gane kai mutum ne me nagarta, amma idan ka nuna mata kai Kanka kake so zayi wuya baka samu tangarda da ita ba! Amma kayi nazari da kai." Kai kofin shayin yayi sannan ya kurba, mik'ewa yayi tare da cewa. "Zan koma" A hankali ya mike tare da barin gidan kakan shi, wani irin tausayi ya bashi, yana son Ikram amma kuma shi a nashi tunanin ya hakura da ita, badan kome ba, sai dan yadda tazo jiya ta gaishe da kakan da ya kalle ta sannan tace mata. "Bilqisul Ikram! Ya batun shirye shiryen bikin ku, naga anata tura sakon gayyata" Matse hannun ta, tayi tare da sunkuyar da kanta sannan tace mishi. "Ana kan shirin." Murmushi yayi sannan yace mata. "Ke baki shirya bane" Matse hannunta tayi kamar zata karya shi. "Ina kai" Kura mata ido yayi sai ya fahimci bata son maganar auren ne baki daya, dan haka ya jefeta da tambayar da ta sata d'ago kai. "Shin ko kina da wanda kike so ne? Bamu sani ba" Da sauri ta d'ago kai tana kallon shi sannan ta kuma maida kanta kasa,.kwallar da take kokarin dannewa ne ya shiga sauko mata, a hankali ta saka bayan hannunta ta goge. Murmushi irinta manya yayi mata sannan yace mata. "Share hawayen ki, kinji kiyi hakuri da abinda muka zab'a miki,.Insha Allah zaki yi farin ciki." Gyada kai tayi tare da mik'ewa zata bar falon, duk sai yaji babu dad'i musamman yadda ta kasa rike kukanta, dan haka yake ji ba mata adalci ba, dan haka yake ganin koda anyi auren zasu ta azabtar da juna ne ta hanyar amfani da k'iyayyar juna, shafa gemun shi yayi, dan yasan auren kan babu fashi. Kamar anyi an gama ne ma. ....... Kallon sakon gayyatar Masarautan SAMAIND yayi, sannan ya ajiye shi a gefe kafin yace. "Zanje da kaina naga meye Mehran ya fini dashi" Dan haka ya mike tare da nufar cikin gidan, yana shiga ya wuce dakin kakan shi wato Sultan Mu'allim, zama yayi sannan yace mishi. "Ka tura na ko ina amma ni zan kai na SAMAIND tunda ta zauna a gurin Sarkin Daular, ka ga kenan zamu gayyace shi." Murmushi yayi sannan yace mishi. "Allah ya jikan Iyayen ka, ina son yadda kake nuna jarumtar nan,.dan haka ka shirya gobe Insha Allah ka kai mishi!" Gyada kai yayi sannan ya mike tare da yin sallamawa kakan, dakin Ikram ya nufa, ya same ta ta cusa kanta a tsakanin cinyoyinta, tayi wani mugun kyau da cika, shi kanshi sai da yaji a aran shi ya dauke ta ya boye ta shi dayan shi. Sai kace Yar tsana, birkitotta yayi yana sumbatar goshinta. A hankali ya saukar da kanshi zuwa wuyarta. "Ikram me zan gayawa Saurayin ki domin zan kai mishi sakon gayyata na bikin mu." Ban san lokacin da na d'ago da mugun sauri ba, nace. "Mehran? Gurin shi zaka?" Sharr hawaye ya fara zuba, kamar yadda nake tsammanin, kasa tabuka kome nayi, na lumshe idanuna..ina jin wani irin kuka yana zuwa min, shi kuwa abinda yake son gani kenan, dan haka ya zame ni cikin lumana ya fara jagwalgwala ni, rike hannun shi nayi tare da cewa. "Don Allah,.karka min haka duk tsawon lokacin da na kare kaina, bai isa ba sai lokacin da ya rage taki kadan kace zaka kutsa min." Janye jikin shi yayi sannan ya sauka a gadon, tare da fita zuwa dakin Sultanah Balkisu Ikram, sun jima suna hira kafin yayi mata sallama. Tunda ya fita nake kuka. Domin yau nake jin wani irin kewar Mehran, ban tab'a sanin cewa na haukace akan Mehran ba sai da yace min zai tafi gurin shi, naji kamar na cire zuciyata na bashi ya kai mishi, haka Izmah da Nimra suka shigo min itama kallona take, tare da cewa. "Naji wai Amir Rahil zai tafi SAMAIND, amma zan bashi sako ya kaiwa Fudail." Gyada mata kai nayi, sannan na juya musu baya na kwanta ina ajiyar zuciya, har barci ya dauke ni, ban farka ba sai da dare ya raba sannan na nufi ban daki nayi alola, sannan nazo na gabatar da sallar nafilla, na jima i a gayawa Allah kuka na, ina kuma niman a gaji a gare shi, kwallar da nake danne su, suka zuba min, tabbas so masifa [5/22, 7:48 PM] Mehkram1256: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat Book3 _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayena_ 8... "Ya Allah kai ne ka jarabce ni da Kaunar Mehran ya Allah ka cire min kaunar shi a raina na huta" na fada cikin kuka da shashekar kuka, a hankali wani irin zazzaɓi ya rufe ni, kafin wani lokaci na fita hayacina. Shigowar Izmah da Nimra yasa aka fahimci halin da nake ciki har ta kai da an nimo masu kula da lafiyar mutanen masarautan. Haka suka kwana a kaina, Dan koda Rahil ya shigo yaga halin da nake ciki bai hana shi tafiya ba, dan ya san akan Mehran ne, kuma babu fashi akan auren anyi an gama. Sallama yayi musu ya kad'a raƙumin shi dan yace ba zai shiga a matsayin me muƙami ba, zai yi tafiya ce Irinta Sadaukan maza. Sai dai dukda haka yayi tafiyar ce cikin zullumi da damuwa, domin saura kwanaki ƙalilan bikin su, kuma baya Mantawa a watanin baya Ikram da bakinta take cewa. "Ba zan ki aurenka ba, amma Ni kaina nasan cewa mutuwa tace take tunkaro ni, ba zan iya furtawa ba, amma kuma ba zan tab'a yarda na zama mallakar wani ba. A duk lokacin da na Fahimci tazarar da take tsakanin mu sai naji a raina kamar kuskuren nayi aka jarabce ni da samun ahalina me yasa kika bayyana a lokacin da nake shirin zama a Inuwar shi, tabbas mutuwata itace fansa ga kaunar da nake mishi." Lumshe idanun shi yayi wanda yake rufe cikin mayafi me kyau da tsari. Lumshe idanun shi yayi ya bude shi. Murmushi yayi me kyau sannan ya cigaba da tafiya yana ratsa hamada da sahara. "Ba aikata kuskure bane laifi, maimaita kuskuren shine babban laifi, Ya Allah ka gafarta mana kura kuran mu," ya faɗa yana me shan ruwan shi da yake goran shi ya sha. Ya kuma zaburar Raƙumin shi. ~~ Kallon Sultan Mu'allim da Amir Sulaiman da Wazir. Me kula da lafiyar ta yayi sannan ya sunkuyar da kanshi yace musu. "Allah ya taimaki Sultan, Amirah Ikram tana fama da damuwa ne, sannan zucuyarta bugun shi yayi kasa, idan da hali a rage takura mata, domin tana bukatar nutsu a daina takura mata, sannan a daina barin ta ita daya tana zaman kaɗaici haka ma yana taimakawa gurin shiga damuwa." Shiru yayi sannan ya cigaba da cewa. "Na gama duba ta" ya faɗa tare da musu sallama zai tafi. Rakiya Amir Sulaiman yayi mishi. Zama Sultan Mu'allim yayi tare da kallon yadda fuskarta yayi wani irin fayau. Shafa kwantaccen gashin goshinta yayi yana tausayin ta, duk da Wazir ya gaya mishi matsalar Ikram amma gani yake kamar idan anyi bikin su da Rahil zata hakura, abinda bai sani ba kuwa ashe ciwo cinta yake kuma dalilin son ransu. Gani suke kamar duk wani karfin mulki yana tare da Ikram shi yasa basu son rabuwa da ita, Kuma idan tana tare dasu. Shi yasa yaki sauraron kowa kan Mehran haka zata hakuri ayi bikin da Rahil. ~~ Oman. "Baku sami labarin daga SAMAIND ba?" Abrad ya bukaci jin bayani daga bakin wani na hannun damar shi bayan kashe Nawwas, me suna Ukshe. "Eh an sami labarin an ga gawan Nawwas, kuma sun gama binciken yadda gawan ya mutu, sai kuma batun Amirah Azizatul Nissah, Mehran ya amshi cikin jikinta, bayan haka tayi nasarar sashi ya kori Mahaifiyar shi daga cikin masarautan. Sai batu na gaba bikin Amirah Ikram da za ayi da Amir Rahil, nan da kwanaki goma sha biyu." Murmushin gefen baki yayi tare da kallon shi, yace. "Ukshe ina ganin ya kamata a sace min Ikram ranar daurin aurenta a daren da ake shagalin a daren nake son nayi tarayya da ita, yadda zata gane nayiwa maza Zarra" Murmushi Ukshe yayi sannan yace mishi. "Nasan ka kuma nasan zaka iya, shi yasa nake farin cikin kasancewa ta a kusa da kai, Sultan Abrad indai Ikram zata gyara daren ka da Ikram ai babu wani uban da zai hana ayi wannan badakalar." Murmushi yayi tare da gyada kai, domin kuwa yana jin a ran shi an gama mishi kome tunda yaji labarin auren, sannan ya kalli Ukshe yace mishi. " Yarinyar daban ce ga sauran matan ko Kanwar Mahaifiyar ta bata kaita haduwa ba, Ikram haduwa ce ita kanta kome ce." Murmushi yayi sannan ya cigaba da cewa. "Zanyi fatan ba iya dare zan b'ata ba dararrakin rayuwata zan b'ata ina shiga ina fita a jikin Yarinyar nan, so nake nayi ta nutso a jikinta ina jin Yaren da ban tab'a ji ba." Yana tuno lokacin da yake tare da ita a matsayin baiwar shi, idan ya tuna yan madaidaita nonuwarta sai yaji kome ya tsaya mishi gaskiya yarinyar karshe ce, kasanta da yayi yunkurin cusa hannun shi cikinta kasawa yayi karshe itama taki yarda, balle kuma yanzun da take Jinin Sarauta, Sai dai ai Noman ya aureta ko bai kwanta da ita bane? Zare idanu yayi lokacin da yake ji a ranshi babu abinda noman yayi mata tabbas, kuma a haduwar su tabiyu bai ga alamar ta tab'a kwanciya da namiji ba, indai haka ne toh akwai wani abu a lullube da ita, lallai kuwa dole idan ya isa gurin daurin auren ya saka a sato mishi ita yayi daren da yake fata da ita. Idan ba haka ba, tabbas zai iya yakar daular ba tare da ya fahimci abinda suka mishi ba indai akan ikram ce toh kowa ma zai kashe. Duk wanda ya tsaya mishi a gaba zai kawar da shi, ita kanta idan zata kawo mishi cikas, zai iya daukar mugun mataki akan ta, balle kuma wani banza can zai kashe kowa indan akan Ikram ne, zai iya shirya kome dan ya mallake ta. Ba iya ita ba kome ma indai mallakarta ce. Murmushi yayi sannan yayi gyaran murya yace. "Ukshe ka gyara min gidana da yake wajen masarautan nan za a kawo min ita " "Toh an gama Sultan!" Ya juya tare da barin d'akin, yana murmushin jin dadi, dan shima Ukshe bakin Shaidani ne, a gurin. ~~ Alamura sun kuma tabarbarewa a Samaind, domin an sami ɓullowar Farin suna ta cinye abincin mutanen garin, tare da lalata musu amfanin gona, shiru yayi yana kallon yadda kowa yake magana, amma cikanku bai baice ba. "Farin nan kashe mutane suke idan sun je kare abincin gonan su. Kuma Sultan Mehran baka ce kome ba." Sai lokacin ya d'ago kan shi, yana kallon su, kafin ya sauke ajiyar zuciya yace musu. "Toh me zanyi musu? Ko nine zan kora musu farin. Abinda zai faru kawai a tabbatar an dakatar da mutane su zauna a gidajen su, sannan su tabbatar da sunyi rike kayan abincin Insha Allah duk tsanani yana tare da sauki, Insha ALLAH, Ubangiji zai duba al'amarin su." Yana fadar haka ya mike tare barin fadar, yana fita suka dasa gulmar shi da kunshe tsarin shi, dan haka yana fita ya kalli Fudail. "Muna da mutane a cikin gari da makotan mu, dan haka kayi ƙoƙarin gano mutane masu amana ka dibi abinci ayi ta rabawa mutane na yarda da kai ya sani cewa haka, kayi aikin cikin kulawa bana son damuwa kuma bana son a nuna muna da hannu a cikin al'amarin" Gyada mishi kai yayi tare da cewa. "Toh Sultan Mehran." Tunda ya isa yake baza idanun shi ta inda zai ga Sawda, har ya shiga turakar shi, tarar da Azizatul Nissah yayi taci Uban kwalliyar, kallonta yayi sannan yace mata. "Tashi ki fita bana bukatar ganin ki," ya gaya mata haka domin har yanzun yana jin zafin ta da abinda tayi mishi. "Kayi hakuri ba zan kuma maganar Ikram ba, kayi hakuri nabi Allah na bika duk abinda kace zanyi Sultan Mehran." Ganin yadda take kuka ne ya sa shi jin kamar kome ya wuce d'agota yayi tare da cewa. "Karki kuma min abinda kika min na gaya miki, kuma ya wuce amma ki turo min Sawda." A kidime ta kalle shi tana faɗin. "Sultan MEHRAN baka hakura bane." "A'a na hakura ina son ganawa da ita ne " fashewa ta yi da kuka tare da mik'ewa ta saka kai zata fita. "Ke zo nan ya kirata." Jikinta yana rawa ta dawo. "Ki share kwallarki, bana son na kuma jin Kinyi kuka. Maza share kwalla Uwar Yarima" gyada kai tayi sannan ta share kwallarta kafin ta fita, murmushi tayi sannan ta tura aka kira mata Sawda, zama tayi bayan sunyi musayan murmushi sannan tacewa Sawda. " Ki sha ruwa sannan Sultan MEHRAN yana gayyatar ki dakin shi, da Fatan babu wani wanda ya tab'a shigarki." "Ai tsadar da muka dashi ya wuce Musami tarbiyyar namiji, Mace ta rene ni, kuma cikin gidan Sarauta, dan haka mun san yadda ake rike kimar mace, bama wasa da darajar mu." Ta fadi haka tana me mik'ewa zata bar falon, "Ya kamar kinji haushin abinda na tambaya." "Ai nasan koshi Sultan Aamaan Mehran ba zai yi min wannan tambayar ba, balle kuma ke dan ni na taso inda aka samu tarbiyya ne ba inda aka maida mata kamar dabobbi ba" Taji haushin kalaman Sawda, amma dake ta iya makirci mik'ewa tayi tare da mata jagora har Turakar Sultan Mehran. Suna shiga tace mata. "Allah ya baki hakuri, bazan kuma miki magana ba, kuma ai cewa yayi zaku gana da kike gaya min abinda ya shafi rayuwar ki, ban tambaye ki, ban sha'awan na sam me ya tab'a faruwa dake, idan ma Fyade aka miki ai bai dace ki ce zaki gaya min ba, wannan sirrin kice" Shiru tayi tana kallon SULTAN Mehran, sunkuyar da kai tayi murmushi Sawda tayi sannan tace mata. "Karki damu, idan ma maza dubu suka kwana dani ba shine damuwar ba, kasami wanda zai yarda da kai ma arziki ne, ke kika san abinda kike kullawa na sharri da Alkhairi, algunguma kawai." Cikin jin haushi ta kaiwa Sawda duka, aikuwa fada ya kaure a tsakanin su,, daka musu tsawa yayi da sauri suka rabu. "Ku fita min a d'akina" ya fada da mugun karfi, babu musu suka juya tare da barin d'akin shi. Dafe goshinsa yayi tare da jin bala'in ciwon kai. Sabida damuwar mutanen shi da matan da suke kasar shi. Karshe da kan shi ya sauka ya nimo Mahlika. Ya umarce ta ta kawo mishi shayi yana jiran ta, kamar zata yi kuka haka ta tashi ta girka mishi ruwan zafi. Ta kai mishi har dakin, yau haka kawai ya tashi da wani irin fitinnnen bukatar mace, shi yasa yaso kasancewa da Sawda ita kuma Azizatul ta janyo musu rigima. Tana tsaye kamar wata dogariya, yace mata. "Ki shiga ban daki kiyi wanka" a hankali ta wuce tare da shiga, ya jima yana nazarin abubuwan dayawa a ran shi, kafin ya gama sha ya rage haske dakin shi, yana zaune a gurin ta fito tana goge jikinta da gashin kanta. "Barshi kizo kiyi min tausa." A hankali ta ajiye mayafin da take goge kanta dashi, ta haura gadon, rubda ciki yayi, ta haura bayan shi. A hankali take matsa mishi jiki, musamman wuyar shi zuwa kafad'ar shi,. Ruwan gashin kanta yana diga a bayan shi, yana jin saukar ruwan har cikin kanshi, ƙwaƙwalwar shi da zuciyar shi suka fara bashi Ina ma Ikram ce, wani irin yanayi zai samu kanshi. Gabaki daya yaji duniyar shi ta sauya, dan autan wandon shi kuwa sai zillo take tana ihu. Mika yayi tare da juyawa da ita. Saman shi kamar zata fadi. Hannun shi yasaka dukkan biyu ya zare zanin kirjinta, ya kai hannun shi kan halittar kirjinta zuwa ramin Cibiyar ta, wani irin yarrr taji bata san lokacinn da ta sake wani irin ajiyar zuciya ba, hannun shi yakai saman cinyoyin ta, yana murzawa zuwa kirjinta, a hankali jikinta ya fara rawa tare da jin kamar zata zauce. Rike hannun shi tayi tana girgiza mishi kanta, janyota yayi ta faɗa kirjin shi yana matsa mazauninta, jin jikakken gashin kanta ya sauka a fuskar shi bai san lokacin da ta juye mishi Ikram ba, kura mata ido yayi tare da juya ta, yayi tashi zaune yana kallonta. Yana son sauke nauyin da yake damun shi amma zuciyar shi tana hana shi, tare da hasashen ikram, zata zama nashi watan wata rana...... [5/22, 7:48 PM] Mehkram1256: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat Book3 _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayen Mu_ 9.... Mik'ewa yayi daga gadon ya nufi ban daki, ruwa yayi ta kwarara kanshi har ya ji sauƙin yanayin da yake ciki, yana fitowa ya kalle ta sannan ya dauke kanshi tare da ca mata. "Zaki iya tafiya!" Tana fita ya juya ban daki ya kuma alola ya tada sallar nafilla, ya jima yana rokon ALLAH ya kawo mishi dauki a rayuwar shi, har zuwa wani lokaci.. kafin ya kwanta a gurin, yana tuno yadda ikram take zama a gurin, tare da jin wani mugun kewar ta yana taso mishi. A hankali ya gyara kwanciyar shi ba tare da ya kuma koda yunkurin niman wata mace ba. Safa da marwa Azizah take tana kallon kofar da zai sada dakin Mehran, ganin Mahlika tafito yasata saurin fitowa daga cikin d'akinta tana kallon yadda take tafiya ko ta kwanta da Sultan, ganin babu abinda ya sauya a tare da ita ya sata mata magana. "Kina ganin kin isa ne da Mehran zai bukaci haka shimfid'a dake? Ai baki kai ba, haka ma babu macen da ta isa ta haɗa shimfid'a da mutumin da na ware shi domin kai na." "Bani zakiwa iyayi ba, wanda ya kirani turakar shi ma, shine zakiwa kashedi" d'aga hannun tayi zata mare ta, aka rike hannunta. "Bana son hauka, wuce abinki." Ya cewa Mahlika. "Mehran me kake nufi?" Banza ya bawa ajiyarta, sake binshi tayi zata mishi iya shege ya daka mata tsawa, sai da ta shiga hankalinta, fita yayi daga gidan baki daya, ya sami saukin abinda yake ji. Yadda iska ke ƙadaiwa sai yake jin kamar Ikram tana kusa dashi,. Da wutsiyar idanun shi ya kalli gefen da yake tsammanin haka yaga babu kowa, mai da kallon shi yayi inda yake hango kad'awa bishiyoyi. Duk da dare ya fara yi amma kewar Ikram a jinin shi take, shi yasa ya zabi zama a inda yake ganin nan ne zai ɗebe mishi kewa. --- Tun da yamma ya shigo garin SAMAIND, amma kuma yadda zai shiga Cikin masarautan ya rasa, dan haka ya nemi masauki ya kwana a guri, abincin da aka kawo mishi ya tab'a sannan yayi Sallah bayan yayi wanka ya kwanta, Washi gari Da wuri ya isa fadar Sultan Mehran, ya nime iso dashi. Ana gaya mishi ga Amir Rahil yazo yace a kai shi falon ganawa ba baki, tunda ya shiga yake kallon yadda yanayin gurin yake, yana nazarin littafan da aka ajiye su na tarihi da na addini. Da sallama ya shigo, a hankali ya juya tare da amsa mishi. Yana murmushi. "Ya naga kamar Sultan Aamaan Mehran ya faɗa ko jinya kayi ne bayan tafiyar abincin ruhu ka?" Murmushi mara sauti yayi sannan yace mishi. "Me kake tunani? Ai namijin duniya ba a san shi da saka tunani a ranshi ba, domin kullum ana mishi kallon sadaukarwa ne. Meke tafe dakai dan samari?" Ya zauna bayan ya daura kafa daya akan daya, murmushi yayi sannan ya zauna shima yana kallon shi. "Na zata zan zo na samu anyi bikin ka ne da Yayan gwamnonin ka? Ashe ba haka bane. Koda yake babu wacce zata iya da halinka sai Ita, gashi kuma wacce kake so tana can zata zama matar da zan aura nan da kwanaki, toh kasan mata irin su Ikram ba kowa yake samun shi ba domin tsada ne dasu, shi.yasa naki barin damar na rasata na kafe zan aureta, koda yake ba zaka gane haka ba, domin baka bada damar haka ba, ga sakon gayyatar mu nan, ko zaka bikin mu." Duk da ya gama jin haushin abinda yake mishi amma bai ji a ranshi ko zai iya mishi wani abu ba, asalima girmama shi yake sabida ko babu kome a cikin wata uku yaga wani na kusa da Ikram. Murmushi yayi sannan yace mishi. " Ayya kazo a lokacin da bai dace ba domin Al'umma ta, tana faman da fari, ba zan iya tafiya na bar su cikin.wani yanayi ba, ina muku fatan Alkhairi." "A'a kace dai ba zaka iya kallon wani namijin ya auri matar da kake matukar kauna ba? Koda yake ai ba sabon abu bane dan kaki zuwa auren mu, amma abin kunya ne a ce mutumin da Ya rike hannun Ikram na shekara daya ya kasa zuwa bikinta, ban ga laifinka ba, tunda Abrad zai je da sauki. Amma zan gaya mata gaskiya da take damuwa akan ka kai baka dace a damu da kai ba, sabida cikin gidan ka cike yake da Kwarkwarorin. Ita" "Ya isa!" Ya daka mishi tsawa, kafin ya mike yana kallon Rahil. "Kai kamar Ubane a gare ta domin ku biyu ne kuka ragewa Sultanah Balkisu Ikram. Ina girmama Ikram dan haka kai ma haka nake girmama ka, me yasa zaka kawo min shirme? Ba zan sami zuwa ba, Allah ya baku zaman lafiya, na gaya maka ina da Uzuri!" "Uzurin ya kai na wacce take kukan akan ka ne? Ko ya wuce nata ne? Kasan yadda namiji yake ji idan ya fuskanci macen da yake so bata kaunar shi wani take so? Mehran meye kafi ni dashi da Ikram take kuka akanka?" Kura mishi ido yayi a tsannake, yana tuno ranar da yayi mata tambayar meye Noman ya fishi take kuka akan shi yau gashi Rahil yana tambayar haka. Cike da Mamaki yake kallon Rahil. "Dama yana kuka ne akai na?" "Ga sakon daurin auren mu, idan kana son amsar shi ka halarci bikin mu, zaka sami amsar da kake nima." Yana gama fadar haka ya juya abin shi. Tabbas idan ya cigaba da zama a Samaind kome zai faru, dan haka ya juya tare da barin garin baki daya, domin so da kishi sun mishi yawa, idan ya cigaba da tuna Ikram tayi mishi nisa zai iya yunkurin kashe Mehran, haka kuma zai saka a kashe shi. Tausayin kan shi yake, sai dai ya barwa Allah zavin duk abinda ya bashi Alkhairi ne. Tunda ya bar Mehran a falon baki ya shiga rudani domin baki daya ya rasa abinda zai yi ya zama gaskiya, gani yake kamar karya ne Ikram ba zata yi kuka saboda shi ba, ashe kuwa zama bai gan shi ba, ba zai iya wannan sadaukarwa na, ya hakura da Ikram kamar ya hakura ne da rayuwa shi hade da mulkin shi. Lumshe idanun shi yayi bayan ya gyara zaman shi a kujeran da yake, ya zubawa takardan gayyatar, bude lumshasshen idanun shi yayi tare da kankancewa, yana jin wani irin yanayi yana kuma kara tabbatar mishi da kasancewar shi da ita. Duk da yana kewar ta haka sai ya shi jin kamar ba gaskiya bane da Rahil yake gaya mishi tana kuka da kewar shi, Kenan itama tana jin yadda yake ji akanta, kenan dukkan su suna yiwa juna kurman Kauna? Toh indai karayar da ya gani akan idanun Rahil, haka ne toh ba maka ba zai zare rai akanta ba, ba zai cire samunta ba. Ba zai cire yakinin zama da ita a inuwa d'aya ba. Kai wannan abun yayi mishi dadi bai tab'a jin labari me dad'i irin shi ba kamar na yau. Lallai shi din dan gata ne, ashe akwai lokacin da Ikram zata yi kuka akan shi, murmushi ya sake sannan ya gyada kan shi yana me jin lallai shi din me rabone, dan haka duk me yiwa dole ya tafi ya ganta kodan yadda yaji labarin tana mishi kuka. Murmushi ne me sanyi ya sake ba tare da ya shirya hakan ba, ya mike zuwa fada, kallon manyan mutanen yayi cikin tsantsan farin ciki yace musu. "Kuyi duk yadda zaku yi, sannan Ni zan tafi kasar Yamma domin gudanar da bincike akan maganin da zamu yi amfani dashi na kashe farin, nan da kwana uku ne tafiyar kuma zai kai ni sati biyu Insha Allah. Sannan a rabawa mutane abinci da abin amfani kafin Allah ya dawo dani." Ya faɗa tare da mik'ewa zai bar fadar,kallon juna suka yi kafin suka ce. "Amma dai baka shirya tafiyar ba sai da ka sami labarin Auren Baiwarka da..." A nutse ya juyo yana kallon Zuhair, wanda shi yayi magana, murmushi yayi mishi sannan yace mishi. "Bikin zan je, akwai matsala ne?" Ganin yadda ya juya cikin wani irin izza, yasa duk suka nutsu. Matsalar Mehran ba wai kawai iya magana bane a bakin shi kwarjinin shi hadda kayan jikin shi yana bayyanawa, mutum ne da yasan darajar abinda zai fada. Shi yasa yayi musu zarra, gashi nan dai yaro ne a cikin su,sai Zuhair amma a ruwan sanyi ya kusawa manyan da suka yi jika dashi tsoron shi. Suna masifar shakkar abinda zai biyo baya, shi yasa idan yayi magana kamar yankan wuka jikin shi har rawa yaƙe. "Akwai abinda ka ajiye min ne?" Ya tambayi Zuhair bayan ya dawo fadar ya zauna, kallon manyan fadar yayi sannan ya cigaba da juya zoben hannun shi na azurfa. "Tambayar ka nake?" "Kayi hakuri Sultan Mehran! Yaro ne bai san kome ba." "Nasan da haka" ya faɗa tare da jingina kan shi yana me kumshe idanun shi, kafin ya tsinkayo Muryan Zuhair yana faɗin. "An gaya mishi gaskiya, shi waye da zamu ji tsoron shi, mulki hauka ce, ko aba a bashi yan mata bane? Sannan meye Jasrah tayi da za a kai ta gidan Azaba?" Murmushi yayi sannan ya kuma kallon Amir Hood da hankalin shi yayi mugun tashi, danne Zuhair yake amma fir yaki shiru zai da ya tsinka mishi mari yayi shiru. Mikewa Amir Hood yayi zuwa gaban Mehran. "Kayi hakuri kasan Yarone kuma bai da hankali, duk abinda ya fito bakin shi yake faɗa." Bude idanun shi yayi akan Amir Hood, sannan yace mishi. "Meye ya faru?" Jikin kowa ne yayi masifar sanyi. "Kayi hakuri Mehran" Kurawa Hood idanu yayi sannan ya tab'e bakin shi, sannan ya kalli Fudail ya gyada mishi kai. Ya fita. Tare suka fita. Kallon shi Fudail yayi sannan yace mishi. "Sultan me yasa kaki amsar hakurin da yake ba? Sannan kuma baka hukunta shi bayan kuwa sunyi maka laifi." Murmushi yayi sannan yace mishi. "Kasan me yasa na tura Mahaifiyata daga jikina? Kasan me yasa naki magana akan Mutuwar Mahaifina? Shi yasa naki kula batun shi, Amir Hood yayi laifi bana son na hukunta shi idan na tab'a Zuhair har abada ba zan iya hukunta kowa ba, sabida zasu ce ina amfani da mulkina ina zalinci, Babban Damuwa na talakawa na, suci su koshi..bana son na bar garin suna cikin wani yanayi na wahala. Sannan idan na hukunta shi ,.daga baya suka sami labarin naje daurin auren Ikram zasu rena ni, amma da nayi shiru zanyi magana ba, ai ya wuce.. koda sunji labarin ba zasu zarge ni ba, kaina Yana ciwo sai magana nake, kuma ban gama ba." Haka suka koma dakin shi, yana yiwa Fudail bayanin abinda yake shiryawa, tare da tsarin da zasu bi a taimakawa Talakawan shi. ---- Kwance nake hawaye na zuba daga rufaffen idanuna, ina jin kome da ake yi amma bani da ikon na amsa musu, sai dai ina jin su da tattaunawan da suke a kaina. Suna son na bude idanuna amma fir naki, sai ma kara rufe shi da nake yi..shafa hannuna Sultanah Amrah take yi tana gogen min zufar da nake. "Ikram meye yake damun ki?" Ta tambaye ni kumshe idanun na kuma yi, ajiyar zuciya na sauke,.a sanyayye sannan na bude idanuna akanta kafin nace mata. "Mehran!" "Shin ba zaki hakura dashi bane? Mutun kamar wanda yayi.miki asiri na fara gajiya." "Amma dani ko? Domin ni bana gajiya da Mehran. Kuma ba dan tab'a gajiya dashi ba har karshen rayuwata, Mehran naso Mehran zan cigaba da so. Koda kuwa haka zai zame min.rayuwa da mutuwa amma Mehran wani tubali ne a rayuwata,.da zaran na rasa shi na rasa kome na duk na Shine." Buge min baƙi tayi iyaka razana na razana, kuka na fashe da shi ina kallon ta, nace. "Me yasa kike son Rabani da rayuwata? Me yasa kuke son tirsassa min? Da iyayena na raye ba zasu tab'a min dole ba, kowa zai bani abinda nake so ne? Ko tausayina matsayin mariniya baku yi amma kuna son nayi muku biyayya bayan nima ba bani abinda nake so kuka yi ba, sannan ku Fahimci ni da ku akwai bambancin ra'ayi da al'adu. Ku mulki ya ginaku, kun taso cikin al'adar shi.ni kuma na taso inda aka boye min asalina me yasa ba zaku kyale Ni ba, wallahi nayi imani matukar kuka bani damar zama da Mehran zan yi farin ciki har karshen rayuwata, amma idan kuka bani wanin shi zan amsa da nayi muku biyayya ne ba dan na fahimci irin gatan da kuke min ba. Ya dace ku duba ni ku duba maraicina, Mehran wani yanki ne na rayuwata. Ba zan iya samun wanda ya fishi ba, ya koya min son shi tun ban kai haka ba, shine namijin da na zauna dashi bai tab'a yunkurin keta min mutuncina ba. Shine namijin da kome zanyi baya kallona da idanun shi sai ma ya dauke kanshi wani namiji ne kuma basarake za same ni bai kwanta dani ba, tunda baiwar shi ce Sai Mehran, sabida ba jikina ne a gaban shi ba, Ni ce abar son shi. Shi kenan shi kenan, shi kenan na hakura dashi domin nayi muku biyayya.... [5/22, 7:48 PM] Mehkram1256: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat Book3 _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayen Mu_ 10 "Ba hanaki farin cikin ki muka yi ba muna hango miki abinda yake tattare da wancan daular ce, kiyi hakuri iya gatar da zamu miki kenan." Girgiza mata kai nayi tare da kallon yadda take kokarin nuna min gaskiya, "Ba zan Fahimta ba, ba zan tab'a Fahimta ba, zuciyata kawai nake fahimta bayan ita ba zan iya fahimtar kome ba, idan kuka bani damar zama da wanda nake so zan yi alfahari da haka da akan. Amma ba kome ba kome. Shi kenan." Na fada tare da juya mata baya, tabbas wannan shine abinda ake cewa an b'ata goma daya bata gyaru. Yarinyar duk ta fita hayacinta, sai dai gaskiya barinta tayi aure a Samaind kamar kashe ta da rayuwarta suka yi. Kukan da nake ne yake kuma tab'a mata zuciya, shafa bayana tayi sannan ta mike tare da barin d'akin, tana jin kamar tayi kuka. Fadar Sultan Mu'allim ta nufa, inda tace Mishi. "Sultan ina son ganawa da kai" Jinjina kai yayi sannan yace mata. "Ki shiga cikin gidan gani nan zuwa." "Nagode!" Ta juya tare da komawa gida, tana jiran shi, bayan wani lokaci ya shigo suka sake gaisawa. Sannan ta gaya mishi abinda ya kawo ta, shiru yayi sannan yace mata. "Kiyi hakuri! Na rigada na yanke shawara, ta shiga hankalin ta karta sake nayi fushi da ita aure ne babu fashi." "Allah ya huci zuciyar ka." Ta gaya mishi sannan ta tashi tabar falon sai yanzun take kuma hango kamar akwai son zuciya akan auren domin dai ba wai dan suna son Yarinyar bane sai dan kawai ta biya musu bukatar su. Allah ya kawo mata dauki, ta faɗa a ranta. Domin kuwa bata hango yadda zata iya taimaka mata. Da wannan zancen zucin ta isa cikin gidan, tasa bayin da suka rakota fara shirya tafiyarta zuwa wani sati su dawo. **** A hankali yake takawa har cikin haramtacciyar fada, zama yayi tare da kallon Sultanah Fazilatul nisa, kan shi a sunkuye. Sannan yace mata. "Zan tafi bikin Ikram" "Allah ya tsare hanya." Mikewa yayi tare da barin gidan. ..... Haka suka shirya cikin.dakaruk karta kwana da Sarwat da kuma Fudail bayan ya barwa Zunnoon garin shi, a karo na biyu. Ana bikin saura kwana biyu. Suka nufi Merocco. Tafiyar da ta dauke su wuni daya da rabi. Dan sun yi tafiyar ba tsayawa, sun shiga garin ana shagalgular bikin. Duk da dare ne sosai, amma ana akan shagali. Masauki aka kai shi yayi wanka tare da hutawa, sannan ya fito kamar yadda kowanni sarki yaƙe, ya nufi gurin shagalin. ...... Tunda aka shirya Ni sanye nake da zinari bayan kayan da aka sami, sai zinarar da aka min wanka dasu, hannu da wuyana. Kai na har da kafana, ko yayya nayi motsi sai kaje karar su. Kaina a sunkuye ina me kallon zobben Mehran karamar azurfa wacce ta kuma kara haska hannuna da yake dauke da zinarai. Riko hannuna Rahil yayi tare da cewa. "D'ago kanki mana na nuna miki wani abu" Kamar ba zan d'ago ba. Na dai d'ago ina kallon shi. Nuna min wani guri yayi da idanun shi. Mehran na hango a zaune fuskar shi tayi wani irin kyau, kasa dauke idanuna nayi. Sannan na juya ina kallon shi. Bakina cike da tambaya. "Yaushe yazo?" "Kina son ganin shi ne?" "A'a;" Na fada a sanyayye ni daya nasan yadda nake ji akan shi, dan haka na kuma riko hannun shi nace mishi. "Zan koma cikin gidan na gaji." "'a'a kice baki son ganin shi dai" "A'a ba haka nake nufi ba!" "Toh me kike nufi?" "Shi kenan" Haka ya mike tare da cewa. "Barka da zuwa manyan bakin mu, kama daga manyan Sarakunna zuwa shuwagabannin yankunan jazziratul Arab,.muna muku Barka da zuwa. Ina kuma yiwa babban Aminin mu Barka da zuwa Sultan MEHRAN. Barka da zuwa a kurarren lokaci. Sai Sultan Abrad wanda shima ya iso akan lokaci,.muna muku Barka da zuwa. Dan haka zan raka Amirah Ikram cikin gida ta gaji." Kallon Juna Abrad da Mehran suka yi, murmushi Abrad yayi sannan yace mishi. "Kazo ganin abinda zai faru ne? Idan da Ikram tana cikin lardin ka ne, Yanzun tana cikin inda zan gudu da ita, nayi ta cinta ina kuma shan nonuwarta wanda suka cika tam din nan" "Toh ina ruwana da kai, idan ka gadama ka ɗauke ta mana, hana ka nayi ko tsorona ne Yasaka gaya min abinda zaka aikata?" Ya tambaye shi yana murmushi,.domin tabbas bai zata Mehran zai zo ba, shi yasa ya kasa fahimtar abinda yake fada. "Hmm!" Yacewa Mehran. ..... Fisgo yayi tare da rungume ta, sannan yace mata. "Ki kula min da kanki ban son naji labarin kin je inda yaƙe" Kura mishi ido nayi sannan na kwace kaina nayi gaba abuna, sabida nasan dai zuciyata tana kwaɗayin ganin Mehran amma bana ganin zan iya zuwa gare shi . Gabaki daya daren kasa barci nayi, ina ta juyi kamar zan yi yayya. Har gari ya kusan wayewa sannan na tashi nayi wanka da alola, ina idar da sallah barci na dauka na. ...... Dakyar Fudail ya samo Izmah, zama tayi tana dariya tare da cewa. "Nimrah kake son na kawo maka?" "A'a gashi ki kaiwa Amirah Ikram, Sultan MEHRAN yana son ganinta." "Toh amma zata iya fita kuwa? Domin an zuba matakan tsaro fa akanta" ta faɗa mishi. "Ki bata zata iya!" Juyawa tayi tare da nufar hanyar gidan, koda ta shiga dakin ta samu Suna cin abincin tare da Amir Rahil, irin cin masoya din nan sai hira fita tayi tana mamakin yaushe suka shirya haka, nan kuwa ba kome bane sai yadda Ikram ta sake jiki dashi ganin Sultan Mehran ne ba kome bane. Bayan sun gama ya sumbaci goshinta sannan ya fita, yana fita Izmah na shiga d'akin, mika mata wasikar tayi, ta buɗe. *ina fatan zaki zo gare ni ina ji ranki mako har kullum Bawanki Mehran* Tausayi ya bani, tare da nad'e takardan, murmushi jin dadi nayi ko babu kome zan kuma ganin Mehran, sai dai kuma har ga Allah abinda nake ji akan shi, zai sani na iya bashi kaina, Insha Allah da na bawa Rahil gwara na bawa Mehran, koda haka zai zame min abun kunya na karshe a rayuwata. Dan haka kayan gyaran jikin da suke bani bana sha duk su na kama na shanye tass, sannan na gyara jikina ko ina na, da kaina nayi ta gyara, har dare gyaran jikina nake ana min ina yi da kaina, wasan al'adar masarautan aka fara suka ce naje nace ba zani ba, dan haka kowa ya fita sai masu tsaron kofar aka bar min, jakuna aikuwa na bude taka na zarga zanin gadon na sauka abuna, tunda na sauka na nufi hanyar da zata kai Ni wajen gari. Dakyar na sami masaukin shi..shima bai fita ba, dake shigar maza nayi ina zuwa na buga kofar ya taso ya bude, kurawa juna ido muka yin, kafin ya bude min kofa na shiga, ina shiga yana rufe kofar, fisgo ni yayi kirjin shi. Cikin wani irin azazzaben SOYAYYA ya dauke ni cak, makale shi nayi tare da lallubar fuskar shi ina sake mishi sumbata, jingina yayi da kofar, muna yiwa Junan mu wani irin shegen sumbatar da ta sani ji kamar zan narke a jikin shi, hannuna suka biyu suna keyar shi, nashi kuma yana bayan, yayi min kyakyawan riko, zare mayafina yayi ya wurga tare da kallon yadda na tattara gashin kaina, a Keya, sannan ya shiga sumbatar wuyana har kirjina, ji yaƙe kamar bai tab'a mu'amalantar wata mace ba,sake kan shi nayi tare da warware rigar jikina, dama ban daure kirjin ba, idanun shi ya sauka akan abinda bai taɓa tsammanin zai gansu cikin sauki ba, kifa kanshi yayi a tsakiyar su. Yana jin wani irin yanayi yana ratsa shi. Gadon ya nufa dani, ban ji ko dar ba. Kayan jikina ya raba ni dashi, sannan ya zare nashi yayi min rumfa, cikin wani irin salon da ban tab'a ji ba, yake goga min kirjin shi akan nonuwana, rike zanin gadon nayi da mugun karfi na rintsa idanuna, kafaffuna suna manne da juna sai murzasu nake, Mehran zai kashe ni da salon shi, yana goga min yana sumbatar bakina, yana goga min yana lasar haɓɓa na, cikin wani irin fitar numfashina, nace. "Mehkram!" Harshen shi.ya kai wuyana yana lasar shi tare da sumbatar shi, hankali ya sauko kan cikakkun tsayayyun nonuwar da suka tsaya kam, ya kai harshen shi. Rungume kanshi nayi tare da sake ajiyar zuciya, gabaki daya na zauce saboda yadda yake lasar saman nonon.yana kuma mirza daya, kuka ne ya kwace min na rasa yadda zan yi ina azabtuwa da kewar shi, hannun shi ya kai saman cinyata, ya shafa har zuwa, kogin maliya yaji hannun shi jike, bude kafar yayi tare da kallon yadda nake zufa, zanin gadon yaja tare da cewa.. "Innalillahi wa'inna ilaihi rajioun, Ubangiji ka kare mu daga sharrin shaidan." Ya mike tare da nufar ban daki ya barni a wannan yanayin, kuka ne ya kwace min, na tashi tare da saka kayana, bai fito ba nayi tafiyana, sabida abinda yayi min mugun wulakanci ne, taya na kawo kaina gare shi zai nuna min wani abu na daban. Haka na koma gida har d'akina, na shiga na cigaba da kuka, shigowa Rahil yayi sannan ya kalle ni. "Kin hanani kanki amma kin bawa wanda kike so ko? Dama gashi ya saka ki kuka." "Waye ya gaya maka gurin shi nake?" "Ai Ni ba yaro bane. Ko ance miki ban san kin fita gurin shi bane" "Toh naje sai me? Kai na, na bashi sai me? Idan ka ji haushi ka fasa aurena." A fusace ya fice daga dakin, nima kuka ya kuma ni, haka ya nufi gidan shi shima yana jin haushin kome, amma kuma idan ya tuna soyayyar da ya ga suna yi sai yaji kamar ba zai iya ba, ..... Tunda ya fito ya samu bata nan, dai dai kuma ɗan abin daure gashin kanta, tayi mugun bashi tausayi, sabida ta kawo mishi kanta, kuma yaki amsa. Haka ya shirya ya ficce daga cikin gidan, zuwa gurin taron. Duk wanda ya gansu, ya san yana cikin damuwa, abu biyu yake damun shi,.bukatar mace da kuma damuwar rashin Ikram da yake dab da riskan shi, yasan zai rasata shi yasa ya hakura bai kasance ta ba, domin kuwa yasan darajar yadda ake tasa kima yake. Domin anyi amfani da rashin kimarta an tinzira kishin shi, don haka ba zai tab'a barin haka ya faru da Rahil ba, kuma idan ya duba ai haka ba dai dai bane. Ko da yaushe musulunci tayi mishi gata, ba zai iya lalata musu auren su ba, domin idan yayi haka tamkar ya haramtawa Rahil Ikram sai tayi idda, Tausayin kan su da makomar soyayyan su yasa shi, jin kwalla me zafi ya sauka mishi, tabbas yayi kuskuren a baya, amma a yanzun ba zai kuma aikata hakan ba, koda kuwa Ikram zata bashi kyautar kanshi ne sau dubu sau dubu, damke hannun shi yayi yana me jin kamar zuciyar shi zata buga. --- Washi gari. Aka tashi da shirin daurin auren, tunda aka fara shirin babu wanda bai shirya ba, masarautan kowa yasan ana shirin daurin auren Dan haka Abrad shima gefen shi.yana sawa a shirya dauko mishi Ikram, sabida zai tafi da ita sannan daurawa Mehran sharrin shi ya sace ta. A hankali fadar ya fara cika, kafin lokacin yayi fadar ya cika makil babu matsala tsinke. Ana ta shirin daura auren, har takai da Sultan Mu'allim ne kawai ake jira, lokacin na ta tafiya kowa sai magana yaƙe, can wajen mintinan arba'in da wani abu ya fito, aka fara hidimar daurin auren, "An daura auren Ikram da.. Hahhhh zuciyar mutane yana bugawa sai dummm kake ji, ana jiran shi waye Angon... Hhhh koda yake ina jiran💓💖😻🚶🚶 [5/22, 7:48 PM] Mehkram1256: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat Book3 _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayen Mu_ 11.... Ya dauke ni awa biyu da wani abu ana kwara min ruwa, sakamakon sumar da nayi, tun kafin a daura auren nake wannan sumar. Shafa kaina Sultanah Balkisu Ikram tayi tana murmushi. "Ta Isa haka, sumar ya isa haka ko babu kome zaki rayu dan masoyinki, ba dan mu ba, mun gaza fahimtar ki amma shi ya fahimci sakon ki, ba son kai bane ya samu muka kafe, Bama son kiyi nisa da mune. Kuma bamu yi kokarin hanaki farin cikin ki ba, duk iyaye na gari zasu so dan su yayi farin ciki a rayuwar shi, ba zasu tab'a barin shi yayi bakin ciki ba, mu iyayen ki muka haifa ba ke ba, amma har abada ba zamu tab'a saka ki kuka ba, dan haka kiyi hakuri da abokin rayuwarki, kiyi hakuri da duk wani abinda zaki gani akan shi, sannan ki zama me biyayya da saka shi a hanya na kwarai, karki sake mutane su shiga tsakanin ku, domin a halin yanzu kowa zai so shiga tsakanin ku. Ikram indai faffutikar da kika yi akan SO gaskiya ce, karki sake wasu suyi amfani da zuciyarki gurin ruguza miki farin cikin ki, mutane dayawa suna niman wannan damar ke kuma kin samu, me yasa ba zaki gane darajar da Allah yayi miki ba, sai yanzun na kuma fahimtar dalilin da yasa kuke son juna, ba kome bane ya rayu da maraici kema kin rayu da maraici, kunsan halin juna, indai har haka ne Toh kuwa karki sake wani ya sauya miki kaddarar ki, karki sake ayi kuka dake. Karki sake kiyi kuka da su, kiyi kokarin kin biye damuwarki duk wanda ya kawo miki ɗauki ki nuna mishi Allah ya riga shi, Yanzun idanun duniya tana kanki, amma kiyi kokarin jajjircewa insha Allah ba zaki yi kuka da abinda muka baki ba, Allah yayi miki albarka, karki manta kiyi tattalin farin cikin mijinki sama da na sauran mutanen da zasu kewaye ki, Ubangiji ya baku zaman lafiya da Zuri'ar dayyiba." ---- "An daura auren Ikram da Sultan Aamaan Abdus Samad Mehran na biyu, na kasar Farisa, karkashin daular Abbasiyyah, Amir Rahil ne ya amshi auren shi. Sultan Mu'allim ya amshi auren Ikram." Duk da yana cikin fadar ake daura auren sai yaji kamar duniya tana juya mishi, ji yayi kamar maganar tana dawo mishi bibiyu, sakamakon yadda abin yazo mishi ba zata, mik'ewa yayi zai bar fadar, Fudail ya rike shi tare da cewa. "Barka muna taya ka murnan samun Ikram Allah ya baku zaman lafiya da zuri'a dayyiba, barka." Kasa magana yayi yana me kallon mutanen da suke taya shi murnar, ana gama daurin auren ya fito, dafa mishi kafada aka yi ya juya a hankali tare da tawowa gaban shi. Murmushi yayi mishi sannan yace mishi. "Lallai na tayaka murna, sai dai jiya kamar kai ma ta kawo maka naka kason ko? Ai haka take ita ke bin namiji ba dai namiji ya bita ba, yarinyar tana da dadin mu'amala, gaskiya tunda nake cin mata ban tab'a cin mace me dadin irin Ikram ba, ai jiya nasan kaji yadda nake ji a duk lokacin da na shiga tsakanin cinyoyinta. Sheeeeeeee" ya wani ja iska, tare da had'iye yawun. Sannan ya cigaba da cewa. "Ai yanzun ta manta da kwakular nake mata da hannuna, ina kuma turawa cikin gabanta ina karkaɗa mata, zaka ga har kuka take tana jan gashin kanta ko shima Amir Rahil sau nawa yana kwanciya da ita ko ce maka aka yi yawon da tayi tayi nan kafin ta dawo bata yi mu'amala da maza bane. Maza sosai suka yi ta kwanciya da ita, shi yasa na bashi shawarar da mu bar maka sauran ka karasa, domin maza hudu sun dauke abinda kake ta tattalin shi. Yoh kowa kan shi ya sani jiya ba gashi da ramin yake mata kaikayi ai kai ta kawowa ka susa mata, kuma nasan kayi ta zura mata kana nishin dadi, itama tana kukan dad'i. Duk girman ka matukar ka zura mata azzakarinka magana ya kare zaka ga shegiyar ta dauke k.." Wani irin naushi Mehran ya sakewa Abrad, tare da kai mishi mahaukaciyar duka. Jikin shi yana rawa, dukar shi yake kamar Allah ya aiko shi, dakyar aka shiga tsakanin su. "Idan na kuma ganin ka a tsakanin mu sai kashe ka kai sunan Ikram ka ambata sai na kai ka lahira na kashe ka a can," "Kuka ka ke? " Ya kuma matsowa kusa dashi. "Ka tambaye ta, sau nawa ina kwanciya da ita, Ko mijin da ta aura bashi ya amshi budurcin ta ba, ni ne na zuba ba mata gwatso, naci ta na kuma sha nononta kayi abinda kaga zaka yi. Kuma na rantse da Allah sai kasake min Ikram, duk abinda za kayi kayi amma sai ka sake min ita. Macen da ba a cika samun irinta ba a duniya ka mallaka, macen da take da zubin halittar mata dubu, kwayar idanun ta ko bata daka kwalli ba haka take halittar ta ce, dasashenta baki yake ko bata sha wani abu ba lema take, yatsar kafarta dogo ne dan haka tana da zurfi, sannan bakinta dai dai yake da ramin gabanta kace na bar." Wani wawan naushi ya kai mishi tare da kifar dashi a kasa, dakyar aka janye Mehran, daga kan Abrad. Aka nufi masaukin shi da shi. Zama yayi, tare da kurma Uban ihu yana ji kamar ana hura mishi wuta a kirjin shi. Kuka ne yake son yayi amma ya kasa yi, zama yayi yana dauke ajiyar zuciya. Sannan ya kwanta yana ambaton Allah. Sai lokacin hawaye ya shiga zuba mishi. (Kai kishi masifa ce, da ace maza akewa kishiya tabbas wata rana zasu kona gida domin kuwa basu da juriyar kishi) Kuka yake shar shar kamar karamin yaro, ya kasa yin kome, idanun shi sai zubda kwalla yake, yana ambaton Allah, lokaci guda farin ciki da bakin cikin sun mishi zuciyar shi. Dama haka take shi yasa jiya ta kawo mishi kanta tabbas Ikram kinyi kuskuren ba irina ake yaudara ba! ---- Kallon su nayi tare da jin labarin da suke baddawa. "Eh fada akayi da Sultan Aamaan Mehran, da kuma Sultan Abrad, yanzun haka Sultan Abrad bai san Inda kan shi yake ba." Cikin matukar tsoro na miki tare da cewa. "Ina Mehran din yaƙe." "Yana masaukin shi." Da sauri na saka kai zan fita, suka tare ni. "Amirah, kuskure ne babba ki fita kafin a kai ki gidan mijinki!" "Ku bani hanya " na daka musu tsawa, da sauri suka bani hanya, na fita ina me tattare kayan jikina dan doguwar riga ce irin ta kasar hindu, da babban mayafinta, tare da manyan gwala-gwalai da aka Kawata min jikina da shi, duk inda na ratsa karar kawai kake ji, koda na isa bakin kofar da zata kai Ni wajen gari suka hanani fita, kallon su nayi tare da cewa. "Ku bani hanya yanzun zan dawo." Basu min musu ba suka bude min kofar, na nufi masaukin shi. Ina zuwa naga Fudail a bakin kofar shiga gidan, kallon juna muka yi sannan ya bude min kofa cikin tsantsan girmamawa, har cikin dakin na shiga yana kwance. "Meye ya kawo ki? Karuwa karya wacce ta gama rabawa maza gindinta. Ballagaza bola dattin kazamta, me yasa jiya kika kawo min kanki?" Ya daka min tsawa, mik'ewa yayi tare da kallona, hawaye na zuba mishi kamar yadda yake zuba min. "Da kika auri norman ban tab'a jin zafi ba, Amma kwanciya da mutanen da basu kai ni daraja ba, Ikram ki kashe ni zai fi min sauki da ace ina raye amma zuciya ta ba zata huta ba. Wato kin ji dadin yadda maza suke zura miki azzakarin su, baki tab'a kyamar su ba, me yasa duk suka gama kalle min sirrina. Na zata da nace miki Sirrintacciya na iya ni nake da damar shiga wannan bangaren ashe akwai mutanen da suka rigani. Ikram Nagode sai dai kuma" dariya yayi sannan yace mata. "Ki shirya ganin ukuba har rayuwarki, kazama datti bola, shaddar kasuwa, karuwa ballagaza kawai ficce min daga gida bana son ganin kazamar fuskar ki, wacce bata iya kome ba sai kaiwa maza tallar kanta." Murmushi ne me hade da kuka suka zo min amma na had'iye tare da cewa. "Nagode ko babu kome na ji dadin zuwan ka aurena,.kuma Nagodewa Allah da bai bani kai a matsayin miji ba, sabida ya dubi maraicina ya bani Dan uwana a matsayin mijina, imma ya sami maza a kaina toh tabbas nayi imani da Allah zai rufe kuma zai zauna da ni, Alhamdulillahi da ban kai kaina rayuwar ka ba, da na sha kunya har karshen rayuwata. Na Barka lafiya" "Sakarya sha-sha-sha, wawuya ki je ki tambaye su waye mijin da aka baki, kin iya saka kayan banza ki biyo namiji amma baki iya bincikar meke faruwa ba. Kuma ki tabbatar Fudail ya raka ki har cikin gidan da kika fito, karuwa kawai." Ajiyar zuciya kawai nake tare da fatan Allah ya kai ni gida, ina fita ko ta kan Fudail ban bi ba, nayi tafiya ta, duk da Yasaka dakaru raka ni, sannan ya shiga cikin dakin. "Amma Sultan wannan bai dace ba, matar ka kake zargi da wasu abubuwan, wallahi ban yarda da abinda Abrad ya faɗa ba, domin kowa yasan Ikram kin tsantsiyya ce. Bata ji kama da irin matan da suka watsar da mutuncin su ba, Haba Sultan yau kome aka gaya maka akan Ikram bincike shine akan gaba, zata baka hadinka." "Kai ma ina zargin ta baka kanta, ai tun tana Madinatul Mah nake ganin kusancin ka da ita." "Subhanallahi Ubangiji yayi mana tsari da mugun ji da mugun gani ban tab'a aikata abinda zai dame Ni ba, kuma da kake ihun kana jin haushin Ikram matar da nake so da bakinta ta gaya min maza sun yi mata fyade, da na bincika na samu haka ne nace ina sonta, ba dan kome ba, sai dan ƙaddarar da ta haura kanta." "Ai kace matar ka sauran wasu karti ne shi ne ni zaka bani shawaran na zauna da wata dattin." "Aamaan idan yayi maka ka zauna da Ikram idan bai maka ba ka rabu da ita, tana da masoya bila'adadin. Ba kanta farau ba, ba kanta karau ba. Amma ka sani kana dab d kuka da idanun ka." "Fitar min a daki, ka je ka zauna da Ikram. Tunda baka ganin laifin da aka min. Allah ya isa tsakanina da ku har da Ikram da duk wanda suka ci amanata kuma ka gaya musu yau zamu wuce idan sun gadama su bani ita idan basu gadama ba su bar ta tayi ya bin mazan da ta saba." Kallon da Fudail yake mishi baki sake sai dai ya rasa bakin magana, kallon shi yake. Yadda fuskar shi tayi ja, idanun shi ya kad'a jajjur. Girgiza kai yayi sannan ya juya tare da barin d'akin, yasan sharrin kishi ne da kuma shaidanin mutum irin Abrad. Lokacin da na isa gida, ana ruwan sama me ƙarfi, a hankali naje bakin kofar shiga shashin Sultan Mu'allim na zauna ruwa na sauka a kaina, kuka nake mara amfani, gashi duk bayin da suke shashina sun fito nima na, tare da Rahil hango ni suka yi na zauna tare da kifa kaina akan gwiwata,na saka hannuna na rungume gwiwar. Kuka nake tare da jin kamar zuciyata zata buga, ji nake kamar zan mutu zunzurutun bakin ciki, gabaki daya na rasa inda yake min dad'i, ji nayi duniyar tayi min zafi. Kai na har yana min wani irin bugawa kamar ana buga min da guduma, komawa Rahil yayi ya tawo da Sultan Mu'allim, juyawa yayi tare da cewa. "Ku kyale ta, karku mata magana idan ta gama zata bar gurin, a yanzun kuma tana iya kin kula kowa, an jima idan bata bar gurin ba kai min magana " Ya fada tare da nufar cikin dakin shi, yana jin kamar zuciyar shi zata buga, yaji labarin ta tafi gurin Mehran,kuma an gaya mishi fadar da suka yi akan ta ne, toh meye ya faru a tsakanin su ukun? 🤣😹 Am always love Chakwakiyya 🤦🏼‍♀️🤨 [5/22, 7:48 PM] Mehkram1256: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat Book3 _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayen Mu_ 12... Ruwan da ake yi ne ya kare a kaina kaf, lokacin kuwa ana shirin shiga sallah azhar. Ruwan ya dauke idanun sun kumbura sosai dakyar na mike ina rawan sanyi, ko gabana bana gani, na isa kofar shiga falon sultan. Dakyar na tura kofar, na zube a gurin yana zaune a kilishi dauke kan shi yayi yana karanta Alqur'ani, rarrafawa nayi har gaban shi. Bakina yana rawa hawaye na zuba daga idanuna. "Atta! Don Allah ka saka shi ya sake ni. Na fada auren." "Don Allah Atta kace mishi na fasa auren, kaji Atta. Don Allah na fasa auren na zan auri Mehran ba." Na fada ina kuka. D'ago kai yayi yana kallona..sannan ya mike tare da rufe Alqur'anin ya fita abun shi. Da sauri na bi bayan shi ina ihu. "Wayyo Allah na, Atta don Allah karka tafi ka bar ni don Allah ka saurarre ni!" "Karku sake ta fita." Ya bada umarni ga dakarun da suke bakin kofar falon shi, nayi kuka nayi danasanin kuntatta musu da nayi akan Mehran. Ta kofar dakin shi na fita, tare da nufar cikin gidan ina kuka. Duk inda na wuce bayi ne ke zuɓewa, ina shiga na same shi tare da sauran yaran shi da jikokin shi. Har da kakata Sultanah Amrah, zuɓewa nayi a gaban su ina kuka tare da rokon su. "Don Allah Karku kai Ni gare shi wallahi na fasa auren, ku bani koma waye. Ni ku zab'a min ko a cikin bayi ne zan zauna dashi bana son Mehran, don Allah Atta. Ummyn ki saka baki bana son, Ummana,"(wato Sultanah Balkisu Ikram) da sauri na rarrafa gaban Rahil ina kuka. "Yayana don Allah na fasa karka yarda ya tafi dani." Kuka nake shima kuma daurewa yake baki daya kukan da nake yana d'aga musu hankali. "Ka tafi da ita a rufe kofar d'akin ta, kazo muyi magana." "Don Allah Karka tafi dani ka bar ni a tare da kai, don Allah Yayana kar a tafi dani. Wallahi mutuwa zan yi. Mehran ba Masoyina bane na gaskiya. Yayana karka tafi dani." Haka yake jana. Ina ihu tare da cewa na fasa auren, Sultanah Amrah kasa hakuri tayi sabida kuka ya ci karfin ta. "Toh meye amfanin rashin jin maganar magabatan ki, kowa sai da ya gaya miki illar abinda kike so, amma kin ki kula kowa gashi tun ba a kaiki SAMAIND zaki fara fuskarta matsala wani irin taurin kai ne gare ki, baki jin magana. Ke daya kin dagula mana lissafi. Haba wannan wacce irin ƙaddara ce take bibiyar rayuwar ki, daga wannan sai wannan a nimo mana Mehran din ya sawwake mata. Na gaji ita daya ta rage min a duniya, nake jin sanyi idan wani abu ya same ta wallahi ko Askandariya zata zama toka sai na yaki Mehran me yake ji dashi! Yarinya karama ya addabi rayuwarta na gaji da wannan wulakancin. Ko wacce amarya murnan rabuwa da dangi take zata fara rayuwar yanci amma dubi Jarumar yarinya ta koma tana tsoron auren shi meye yayi mata haka da zafi. Rahil Maza ka kira." "Koda ya kira shi Sultanah Amratu, koda Mehran yazo sai dai ya tafi da ita amma na zai tab'a yarda ya rabu da ita ba, ne nasan haka zai iya faruwa naki yarda da auren shi. Amma ita ta saka Rahil a gaba da fitina, gata nan jiya masaukin shi taje karya ne? Meye ya kai ki? Kinsan abinda kika min?" Jikina ne ya dauki tsima. Yana kallona cikin madaukaciyar fushi da damuwa, ya nuna ni da yatsa. "Kamar ki dauki takalmin kafarki ne ki mare ni dashi haka kika karya min alfahari na, Ikram kika bi dare kika tafi har gidan Sultan Aamaan Mehran! Da mijin da zaki aura yayi magana kika ce mishi bashi kanki kika yi" ya karshe maganar cikin tsannanin takaici. Tasowa Sultanah Amrah tayi tare da rufe Ni da duka, basu hanata ba, domin sun san kimar da na lalata, tarbiyyar su na watsawa kasa, darajar su na keta. "Ku bani takobi na sare kan karya! Mu zaki lalatawa darajojin mu? Mu zaki lalatawa kimar mu? Me muka miki haka da zafi." Kasa magana nayi kukan ma yatsa cak, haka tayi ta dukana har aka ce ga dan sako daga gurin Sultan MEHRAN. "Kace ya shigo." Da sauri ya fita ya gaya mishi.ina kwance a kasa, Fudail ya shigo cikin nutsuwa, gani na a kwance ya sashi karasowa da sauri. Rike rigar shi nayi cikin kuka nace mishi. "Fudail don Allah kace mishi ya sawwake min, don Allah kace mishi na fasa auren shi. Fudail wallahi dan uwana nake so. Na fada auren shi. Don Allah ka saka baki ya rabu dani." Ina fadan haka ina kuka wanda yafi nada. "Amirah, ke shugaba tace. A duniya baki daya babu abinda Aamaan yake so sama dake, babu abinda Aamaan yayi mishi kuka sai ke, Aamaan ya bar mulkin shi sabida ke, yau mun tawo mun bar Samaind cikin halin fari da yunwa ya tawo ganin ki bai tab'a saka rai zai sami auren ki ba. Wallahi sharri aka miki tare da kishi ya rufe mishi ido, idan da ina da yadda zan nuna mishi gaskiya Amirah Ikram wallahi da nayi, kiyi hakuri." "A'a baya sona, ya daina sona ya kira Ni ballagaza, ya kirani karuwa, ya kirani datti ko don gidan da nafito Mehran ya d'aga min kaf...." Kifa min mari Sultanah Amrah tayi. Tace mishi. "Meke tafe da kai." Wani irin kuka nake me mugun cin rai. "Ni Ko kashe ni zaku yi don Allah karki bar shi ya tafi dani domin yayi min alkawarin azaba da ukuba." "Yace ina bukatar tafiya yau ko za a bashi ita." "Sultanah Amratu! A bashi ita su tafi Allah ya basu zaman lafiya." Wani irin ajiyar zuciya na sauke tare da zuɓewa a jikin ta, ban kuma sannin meke faruwa ba, dukkan su basu damu ba, sai ma shine da yace musu. "A'a bar wannan al'amarin zuwa gobe Insha Allah, zan mishi bayani yadda zai fahimta." Suma kuma sai suka ga da cewa haka, dan yana fita aka kira masu kula da lafiyar mutanen fadar aka dukufa a kaina. Sun jima kafin Allah baya basu Sa'a na farka amma kuma suka goga min abinda zai sani barci. A hankali barci me nayi yayi gaba dani. "Gaskiya ku duba lamarin yarinyar nan, karku tsannanta mata." Sannan suka yi sallama tare da barin d'akin. --- Lokacin da ya isa gurin ya same shi yana shirya jikin shi. Kallon tambaya yayi mishi. Dake shima a cike yake da shi yace mishi. "Bana tunanin Ikram zata yarda ta zauna da kai domin gata can tana kuka a raba auren ku, cin mutuncin da kayi mata kuwa ta faɗa a gaban danginta. Dan haka sai ka san abinyi idan zaka saketa ne na kai musu shedar haka, toh bismillah rubuta ka bani na kai musu. Domin na barta Sultanah Amrah tana dukarta." Jikin shi yana wani irin rawa ya fice daga dakin. Ya nufi cikin babban gida, yana shiga Rahil ya hana shi wuccewa cikin gidan. "Ba zaka goranta mata kimarta sannan ka biyo ka ga bayan ta ba, ina tunanin ko ita ce magajiyar ƙaruwai dai haka, ka zauna ka ci mutumcin yarinyar da take mutuwar son ka. Wallahi ban zaci zaka iya amfani da haka ka kuntatta mata ba, Allah sarki so bai san inda ya dace ba. Inda yasan inda ya dace da babu wanda ya isa ya tozarta mana ita, yarinyar da yau ya dace tayi barci cikin farin ciki da soyayya, amma kuma zauna ka juya mata baya a daren farkonta. Idan zaka iya ka turo mana sakon rabuwa da Ita." "Kai ka isa raba ni da ita? Duk duniya babu wanda ya isa raba ni da ita, dan haka ka bani hanya na ga mata ta" ya bangaji Amir Rahil ya wuce, shi kuma ya bashi hanya ne sakamakon hango Abrad. Ya tun karo su shine ya bashi hanya, Abrad na isowa a kidime yake tambayar shi. "Ya jikin Amirah Ikram?" "Abun da ka aikata bai maka bane kazo karasa mana ita, Shaidani wallahi ka wuce ko na saka a maka tijara." Ganin da gaske yake yasa Abrad juyawa yana murmushin nasarar da yayi ko babu kome wallahi ya raba masoya saura yanzun.... --- Lokacin da ya shiga cikin gidan, jikin shi a matukar sanyayye, kunyar su da abinda ya aikatawa Ikram yasa shi kasa motsi, yana kallon ƙasa. Ya kasa magana sai shirun da yayi. "Tana wancan Dakin." A hankali ya nufi inda aka nuna, ya shiga, da sallama hangota yayi tayi fayau gwanin tausayi, a ranshi yake jin tausayinta, amma a zahiri kallonta yake kawai dan gani yake kamar ta rasa hanyar da zata kare kanta ne ta bige da kwanciya babu lafiya, kallon kirjinta yayi wanda take numfashin yana d'agawa, abinda ya faru jiya ya dawo mishi. Sake tuna yadda suka fada duniyar jin dadi da ita, harbawa wandon shi yayi, cikin sauri ya matse ta. Karasawa yayi tare da zama a bakin gadon, yana shafa fuskarta. Wani irin azazzaben SOYAYYAR ta yake ji yana yawo a ranshi. Kafin ya shafa goshin ta wanda yayi zafi, riko hannunta yayi tare da kallon ta, sumbatar hannun yyi yana jin wani irin tausayinta a ran shi, hannun ya kai wuyar shi yana faɗin. "Sirrintacciya na, ba zan iya hada ki da kowa ba, kishinki girma yake dashi, shi yasa na kasa jurewa, ba zan iya yafe miki ba, domin kuwa zan hukuntaki da laifin da kika aikata min, ina nan ina jiran ki har ki farka." Ya fadi haka tare da sumbatar goshinta, sannan ya fita daga dakin. Yayi musu sallama, sannan ya bar gidan baki daya, yana jin zafin abin a ranshi. Tabbas yayi karfin hali da ya iya shiga cikin gidan, domin kuwa ba kowani namiji bane za a ci mishi fuska yayi hakuri amma yanzun kowa ganin laifin shi yake gani. Su kuma abin da ya basu haushi akan me zai shigo bai jajjajta halin da take ciki ba, kuma ya bude baki yayi magana yaki basu hakuri duk da yasan sun san abinda ya haɗa su, dan haka suma suka dauka da zafi sosai sun dauki zafi ainun. Shi yasa da ya fito babu wanda ya saurare shi. Kuma shima ya dauki fushi akan abinda suka mishi, sai ya zamana an sami rashin fahimtar juna a tsakanin su. ....... Bayan na farka na fara shaƙar kamshin turaren shi, hawaye ne suka zubo min a lumsassun idanuna, na kuma gyara kwanciya na, "Sannun tashi ki ci abinci." Girgiza mata kai nayi alamar bana jin yunwa. "Toh ai sai ki kashe kanki shi kan yana da wasu Kwarkwarorin bila'adadin." "Sultanah don Allah kice." Girgiza min kai tayi tare da cewa, "Ba a saki a gidan sarauta, kiyi hakuri ba zai iya rabuwa dake ba, da ace abinda yake zargin ki kina gidan ne, toh ba makawa za iya sake ki, sannan kuma Kinga haka laifi ne babba, dan haka kiyi hakuri kiyi hakuri kiyi biyayya Allah zai baki hakuri." Kura mata ido nayi kwalla na zuba min, rike hannun ta nayi sannan nace mata. "Sultanah. Ya tsane ni fa" Shafa kaina tayi sannan tace min. "Karki damu kishi ne, kuma nasan Indai Abrad yana raye ba zaku taɓa zaman lafiya ba keda Mehran, dan haka kiyi hakuri Insha Allah zaki yi farin ciki sosai." Kifa kaina nayi a kirjinta ina kuka, tana shafa bayana, tare da cewa. "Kiyi hakuri Insha Allah Ubangijin yana tare dake " Girgiza kai nayi ina fadin. "Umma zan sha wahala ne kawai a hannun shi, domin ya gaya min ga bakin shi, don Allah kiyi wani abu. Zai wulakantani, Mehran baya fadan abu bai tabbatar ba. Sultanah kiyi kokarin raba Ni dashi dan Allah kiyi hakuri ki taya ni rabani dashi bana son shi yanzun na rantse miki da Allah bana kaunar Mehran... 🤔🙄Kuma dai... [5/23, 8:16 AM] Mehkram1256: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat Book3 _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayen Mu_ 13.... Murmushi tayi tana shafa kaina, tare da cewa. "Fadan masoya ne ya gaji haka, kuma ba zan iya hanawa a kaiki gidan shi ba, saboda muna son ya fahimci nagarta mu. Kiyi hakuri" Mai da kaina nayi saman ma tashi, hawaye na zuba kamar magudanar ruwa, fita tayi itama. A hankali abinda ya faru jiya zuwa yau, ya sani jin tsanar kaina da kaina, bana fatar na rayu ma, ga baki daya ji nake kamar na mutu dan bakin ciki. Bayan na kai MISHI kai na,.sannan ya jefe Ni da kalmomin masu zafi da ciwo. Da taimakawan bayi nai wanka tare da gyara jikina, kasancewar yau da asuba haila tazo min, kwanciya na koma, har dare ina kwance. Daga ni sai wata riga mara nauyi doguwar ce irinta sakar kasar yamma, shigowa yayi da sallama,.kai na a sunkuye ban d'ago ba dukda kuwa zuciyata tana wani irin bugawa. Zama yayi daga cikin kujerun da suke dakin, ya kura min ido. Rigar jikina irin shara shara ne, dan haka ya kura min ido. Kafin ya dauke kan shi yana me shiru yana nazarin abinda zai gaya min me zafi. "Naji ance kina bukatar rabuwa dani?" Da sauri na d'ago kai na, na kura MISHI ido. Tashi yayi yana zaga d'akin. Tare da bin yadda aka tsara kome na dakin. "Kina bukatar rabuwa dani da gaske ne ko kina kokarin b'oye min cewa kin tab'a kwanciya da maza ne? Idan har da gaske baki kwanta dasu ba me yasa zaki ce ba zaki aure ba? Kenan Abrad yayi gaskiya da yace ya saba saka hannun a jikinki yana wasu abubuwan dake?" Hawaye ne suka fara zuba min, na kasa koda d'ago kai na kalle shi, a hankali na mike tare da isa bakin kofa zan fita na bar MISHI dakin, taki biyu yayi ya saka min kafa. Tare da d'ago ni zuwa bakin gadon ya wurga ni sai da na bugu da bayana da kai na. Wani irin marayan kuka na sake tare da nishi a hankali. Ina me rike kai na, sai jinin da na fara aman shi ta baki. Abinda ya tsorata shi kenan. Ya karaso da sauri jikina zai tab'a ni na ja baya, sake hawa gadon yayi naje garin matsawa na fadi daga gadon, na buge wani sunduki da kaina. "Ikram!!!!" Ya kira suna na da mugun karfi. Tare da isa gurin ya dauke ni, ganin yadda jini yake zuba yayi bala'in d'aga mishi hankali, kara rungume ni yayi tare da shafa bayana. Kwantar dani yayi, sannan ya nufi ban daki. Ya dauko ruwa da tsuma. Yana fitowa ya same ni a bakin kofar zan fita. "Amma baki da hankali" ya dangwara da ruwan yayo kaina kamar zai dake ni domin ya d'aga hannun, aka bude kofar d'akin, Rahil ne ban san lokacin da na fada jikin shi ina kuka. "Yayana don Allah Karku kai ni SAMAIND wallahi kashe ni Mehran zai yi" Kallon Mehran yayi sannan yace min. "Kiyi hakuri, duk abinda zai miki wata rana sai labari, Atta ya hana mu magana. Muje na gyara miki ciwon da kika ji." Ganin yadda nake kuka tare da damukar Rahil, yasa baki daya kishi ya kuma turnike shi, ya zuciya tare da barin d'akin, haka Rahil ya taimaka min yayi min gyaran ciwon, sannan ya kawo min shayi nasha, kafin na kwanta. A hankali daren ya zame min dare mafi munin da bala'i a rayuwata, burina na Auri Mehran amma yanzun na zama mara amfani. ....... Lokacin da ya isa masauki sai fushi da fada, tare da kwallo da kome, yana ganin ai cin amanar shi ake shi yasa nayiwa Rahil kyakyawan riko, dan haka sai ya dauki mata, a ranar dai haka muka kwana zuciyar kowa babu dad'i. Dake tafiyar sakamako ne za ayi. ..... Ina ta jin motsin mutane ban san cewa, a dakin bane sai da na farka naga an kwashe kome nawa an fita dashi, a hankali Izama da Nimra suka taimaka min na nayi wanka, ina fitowa aka shirya min abun karyawa, ina gama cin abincin dakyar naci domin kamar magani nake jin shi. .... Bayan na gama aka bani kaya na saka, sannan na fito. A hankali nake tafiya ina dafe bango har na isa babban shashin Sultan, inda kowa yake zaune. Kallon Amirah Laylah nayi tana murmushi, tare da mik'ewa ta taimaka min na zauna a daya daga cikin kujerun falon, ina haki. "Toh Ikram Allah ya bada zaman lafiya." Iya haka suka yi ta faɗa min, ban tab'a ganin abinda yayi min ciwo kamar yadda naga basu damu da ni ba, dan haka ana ce musu Mehran yana waje, suka rakoni baki dayan su, za a raka ni da kanshi ya sauko daga keken dokin yana kallon yadda nake tafiya ina niman Izmah ta rike ni, dake kofar cikin gidan akwai matakala,.jiri ne ya fara dibana. Dakyar nake sake kafana, ina kokuwa da numfashina. Duhu ne ya Mamaye idanuna, kafin na kai kafana kasa naji kamar an tunkude ni ta baya. dukkan su kiran suna na suka yi da mugun karfi. "Ikrammmmmm!" Shi kanshi bai san yadda aka yi ba, sai tsintar kan shi yayi ya tare ni tare da mun kyakyawan riko, jin yadda nake numfashi ga jikina yayi zafi ya sashi daukata tare da isa gurin iyayen na, yayi musu sallama da godiya har ya juya zai tafi dani Rahil yace mishi. "Karka manta mariniya ce bata da uwa bata da Uba, bata da kowa A SAMAIND sai Allah. Masoyin gaskiya kokarin zama adali yake koda yake ita ai masoyiyyar gaskiya ce, duk wanda zata mu'amalance shi sai ta mishi adalci da zuciyarta tare da gangan jikin ta, dan haka ga Amana nan. Idan ka kula da ita Allah yana ganinka idan ka wulakantatta Allah yana ganinka. Muna sonta muka bar maka ita ba tare da duba waye kai ba, sai dan duba meye take so. Iya mu biyu muka ragewa kakar mu idan ba zaka iya zama da ita ba, ka dawo mana da ita kar ciwon zuciya ya kashe mana ita bayan bamu more ta ba." A karon farko da yaji kunya ya kama shi, sunkuyar da kai yayi sannan yace mishi. "Insha Allah zan rike amanar da ka bani, kayi hakuri da abinda na aikata laifukan da nayi mata, amma ba zan iya hana zuciyata kishin abinda nake masa so sama da kome ba, iya wannan zan gaya maka gaskiya." Daga haka ya juya tare da sauka daga matakalar ya nufi cikin keken dokin dani, muka bar masarautan. _Yadda ta ji dadin namiji ne ta kawo maka kanta? Ni kaina nasan ta manta da kwakular da nake mata_ Juya min baya yayi tare da kallon waje, yana ji kamar zuciyar shi zata buga. Juyawa yayi yaga yadda nake zubda kwalla. Duk sai jikin shi yayi masifar sanyi. Shafa kaina yayi cikin nutsuwa yace min. "Me yasa kika zab'i zubda kimar ki sama da kome? Kinsan yadda nake burin zama da ke? Ina miki wani irin kauna ce me wuyar fassaruwa. Kaunar da nake miki gaskiya ce ban tab'a hadaki da.." "Mehran kaunar da kake min karya ce, baka kaunata baka bukata na a rayuwar ka, idan da kana kaunata ba zaka tozartani daga auren mu ba, amma ka zab'i cilla rayuwata cikin ukuba." Fusata yayi tare da d'ago ni zaune, ya shiga gaya min magana marasa dad'i, tare da goranta min abinda a ka gaya mishi.. "Ni ba karuwa bace, idan har dan ya kwana dani a daki daya a gado daya shine karuwanci toh ai kai ma kayi haka dani ko ka manta ne? In tuna maka" na tambaye shi ina zubda hawayen bakin ciki. Marin bakina yayi tare da shake min wuya. "Ni zaki tsinkawa mutunci kiyi laifi ba zaki bani hakuri ba , sannan ki nuna min ai ba sabon abu bane a gurinki." "Eh na fada karya na maka na gaji zaka kashe ni da rayuwata ta, meye nayi maka da zafi da ka zab'i cilla ni cikin damuwa?" Ban san meke damun shi ba, domin kamar mara hankali ya koma min tare da marin bakina da fuskana, sai da yaga na fara tarin jini,. yana fita ta hanci da bakina ya sa shi barin abinda yake min. Rungumo ni yayi tare da cewa. "Matukar kika ce zaki mai da min raddi zaki yi kuka ban tab'a d'aga hannu akan mace ba amma nayi a kanki. Kun cuce ni wallahi kuma ban yafe miki ba." Haka yayi ta niman magani na, har ya gaji sannan yayi magana aka tsaya, dakyar aka samo maganin a gurin Izamah. Haka muka Cigaba da tafiya har dare, sannan muka yadda zango sabida dare, tunda ya gyara min kwanciya, yasa kai zai. Ban kula shi ba kawai abinda na sani zan gyara jikina, daukar abin gyaran nayi na fita daga tantin yana kallona, na nufi dajin, bin bayana yayi tare da tsayawa a kaina na wanke jikina tare da saka sabon abin tare jinin, sannan ya haƙa rami ya binne wanda na cire, kafin ya saka ni a gaba zamu bar gurin. Sai ji muka yi an zagaye mu. "Mun zo daukar Amaryarka ce ka bamu ita zamu dawo maka da ita idan Maigidan mu yayi abinda zai iya da ita, idan kuma kaki zamu maka rubdugu" "Nayi muku alqawarin duk wanda ya tab'a ta ba tare da na yanke hannun shi ba, toh wallahi yayi tafiyar shi da ita, babu kome na bar muku ita, idan kuma na sare hannayen ku zan kashe ku baki daya." Zare takobin shi yayi tare da kallon su, yace musu. "Bismillah;" Aikuwa suka kawo min cafka, mara imani kamar ba yan adam ba, haka yayi ta sare hannun su, sai da yayi musu illa. Kafin aka sami wanda ya buga mishi itacce a keyar shi, ya fad'i. Yana kallon mutumin ya kai hannun shi ya dauke ni bayan ya fesa min wani abu na zube a jikin shi. Lumshe idanun shi yayi sannan ya bude a hankali ya hango mutumin yana tafiya a cikin dajin, sake lumshe idanun shi yayi ya cigaba da hango. Cikin wani irin zafin nama ya mike da mugun gudu, yayi bayan mutumin, kafin ya fahimci abinda yake faruwa a bayan shi Mehran ya buga shi da kasa,, wasu mutanen biyu suka kuma bayyana tare da ɗaukata da gudu . Haka suka yi ta bashi wahala, har suka b'ace mishi, sakamakon watsa mishi kasa da suka yi. Murmushi Abrad yayi tare da kallon kyakyawan fuskar ta wanda yake cike gwanin ban sha'awa, tayi kyau fatar ta ta murje, sumbatar bakinta yayi tare da kai hannun shi saman kanta. Yana maida gashinta baya,. Ihun mutanen shi yaji dan haka da sauri ya, saka wuka ya yaga kayan jikinta bayan yayi arba da kirjinta, wani irin dadi ne ya kama shi, jin Mehran yana tunkaro shi yasa shi yaga tantin ya fita ta baya, ki babu kome ya kuma cusa mishi zargin Ikram. Lokacin da ya shigo ya samu babu kome a jikina kayan duk an yaga, cire rigar shi yayi na alkyaba. Ya lulluba mata. Yana jin kamar zuciyar shi zata buga. Haka ya dauke ta ya fito da ita, tare da komawa inda suka yadda zango. Duk abinda ya faru yasan shirin Abrad ne, amma bai tab'a kawowa zai bi matar auren shi ba, dan haka ya saka a ranshi duk ranar da ya kama Abrad zai mishi kisar da ba a tab'awa wani mahaluki ba. A tantin ya kwana yana kallon yadda take barci, cikin nutsuwa da kamala, har gari ya waye. A hankali na bude idanuna na same ni a jikin Mehran mun makale juna,kallon shi nayi yana barci cikin nutsuwa da alamun ma, tunda yayi Sallah asuba ya dawo kusa dani, kewar shi da kaunar shine suka kuma kama zuciyata gyara kwanciya nayi a jihar kin shi. Dake jiya bai rintsa ba, sai gashi shima ya gyara min kwanciya na. Ajiyar zuciya na sauke. Jin na jika jikina yasa ni tashi tare da hayewa gefe, shima kuma kamar a mafarki ya tashi, yana kallona. Kamar zanyi kuka nace mishi. "Zan yi wanka da gyara jikina." Wurga min kayayyakina yayi muka fita, Nimra da Izmah suka tawo tare da amsar kayan muka nufi wani koramar, sai da aka gama duba gurin tsaf sannan dakarun suka koma, ina kallon shi ya cire kayan shi ya shiga ruwan ya zauna. A hankali na cire kayan jikina da ya yage, sannan na koma gefe na wanke jikina, kafin na zauna a cikin ruwan, nutso yayi tare da zuwa inda nake, kallon shi nayi na dauke kaina,.ina goga sabulu a jikina, fisgo ni yayi muka shiga cikin ruwan sosai, inda kafana bai isa cikin ruwan ba, rungume ni yayi yana shafa fuskana, tare da nutsar da kanmu cikin ruwan muna kallon juna. A hankali ya d'ago ni sannan ya shafa bayana, kurawa kirjina ido yayi sannan ya kira kan shi a tsakanin su, yana me jin wani irin yanayi yana ratsa shi. Ni dai nawa ido. Har muka gama wankan..... [5/24, 7:22 AM] Mehkram1256: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat Book3 _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayen Mu_ 14.... "Yaushe zaki gama jinin?" Ya tambaye ni tare da d'aga kan shi a kirjina, shiru nayi mishi ina me Cigaba da wasa da gargasa jikin shi. Matse ni yayi sai da nayi kara sannan ya kalle ni. "Dan iska kika mai dani?" Nan ma shiru nayi mishi, ya kuma jin haushi sama da ta Farko. "Ina magana kin mai dani sakarai ko?" Kokarin kwace kaina nake ya kuma matse ni sosai. "Meye nayi miki kike azabtar da ruhina haka?" Kwalla ne suka cika min ban san lokacin da dariya ya kwace min, tare da kallon shi, sannan na janye daga jikin shi zan fice daga ruwan, Rigani fitowa tare da kwashe kayana ya rike. "Tambayar ki nake?" Murmushi nayi tare da juya bayana na cigaba da wasa da ruwan, indai nice yanzun muka fara, da yaga ba zan mishi yadda yake so ba, ya ajiye min kayan ya kawo min kayan na sauya sannan na fito na gyara jikina muka dawo sansanin mu. Har muka karya muka bar gurin niman abinda zai min tijara yake ban bashi kofa ba. Mun isa SAMAIND da kusan azhar, dan haka kafin mu shiga garin aka shelata akan Sultan MEHRAN ya dawo da Amaryan shi, haka yasa aka tare mu sosai. Ana bikin murnar har muka shiga cikin masarautan, kowa jira yake yaga Amaryan. A kofar shiga gidan aka tsayar da keken dokin da muke ciki, ya rigani fita sannan, na fito tare da taimakon shi ya rike min hannuna. Muka nufi cikin gidan. Duk Kwarkwarorin shi sun zaku su ga wacece, ganin Izmah da Nimra yasa fahimtar Ikram ce. "Wato auro Ikram yayi bayan muna jiran shi?" Inji Jasrah, ta faɗa a sanyayye, domin abin ya bata mamaki. Babban shashin Sultanah Fazilatul nisa na da shi aka ware min bayan an kawo kayan da yake mallakina anata jera su, har dare sannan aka gama, daga nan muka shige cikin ɗakin Ni da bayina, nuna musu dakin su kayi dan basu da yawa, su uku ne Izama da Nimra da kuma Ruwaida. Kafin na shiga ban daki nayi wanka tare da gyara jikina dan nasan gobe zan tsarkaka. Kwanciya nayi a fankacecen gadon da aka mallaka min ni daya, ina tuna irin kaunar da ake min a cikin dangina, kwalla ce ya zubo min, haka ka kwana ina kuka. Sai goshin asuba Bauchi ya sauke ni. *** Lokacin da ya shiga turakar shi, bin bayan shi Azizatul tayi cikin kuka da bakin kishi. "Me yasa mu ka ki auren mu? Wato sai Ikram ko?" Ta faɗa da karfi, hawaye na zuba daga idanunta. Tare da kafe shi da idanunta, duk matan da suke cikin masarautan bata kishin su, bata jin zasu sami Mehran, Amma a duk lokacin da ta tuna da Ikram itace Muradin Mehran sai wani irin tsoro da shakku ya kamata, Uwa uba duk mazan da suke tare da ita haka suke tare da ikram. Idan d'an uwan ta, babu macen da yake so sama da Ikram, Nawwas shima haka,.haka ma Norman shima Ikram duk mazan da suka shiga rayuwarta Ikram sai ta kwace mata shi. Yau ga Mehran da ya shigo rayuwarta ta samu Ikram ta kwashe casa'in da tara na soyayyar shi. Sai ka shi daya ta bar musu, shima bata da yakinin zata samu. Fita tayi daga dakin ta na jin tabbas zata dauki mataki. Kayan shi ya fara kokarin ragewa, bai kulata ba ya shiga ban daki. Bayan ya haɗa ruwan wanka, sannan ya shiga cikin ruwan, ya zauna yana tuna wanka da suke yi yau da safe, ji yayi baki daya kome na shi ya tsaya cak,ya shiga zuba ruwan a ko ina na jikin shi musamman inda ya lura ikram tayi ta tab'a mishi, wato kirjin shi zuwa kan tarin surar jikin shi da suke murɗe, sai yau ya kuma tabbatar da tana mugun son wannan surar jikin shi. Murmushi yayi sannan ya gyara zaman shi cikin ruwan, kamar wanda yake tare da ita, sai mik'ewa yayi tare da. Daureye jikin shi ya fito. Saka jallabiyar shi yayi tare da nufar d'akinta, taba kwance ya shigo mata kai. Dake ta rage hasken d'akinta tana kallon shi, ya hauro mata gado, janye rigar shi yayi tare da kwanciya yana kallon inda nake kwance. "Zoki min tausa!" "Kaje kamilan matan da ka tara su maka ni shara ce" d'agowa yayi tare da kallona. "Ki zo ki min tausa!" Ya faɗa a sanyayye, domin abinda na Fahimta ya gaji, ina kyautatta zaton ko abinci bai ci ba, amma yazo niman magana. Juya mishi baya nayi tare da cewa. "Nayi alƙawarin da kaina ba zan tab'a maka kome ba." Fisgo ni yayi tare da kallon fuskana. "Duk sauran matan basa iya min magana na rashin ɗa'a amma ke, kin masifar rena ni, dan kin saba masu kananun azzakari suna goga miki a gabanki shine bari ki min rashin kunya." "Toh Me babban azzakari an hanaka goga baka ne? Ni ban zata ma kai cikakken namiji bane sai dai ina ganin ka cikin suffar maza." Sake baki yayi yana kallona, tare da kasa min kome. "Ni kika gayawa magana Ikram?" "A'a magana ce fa idan kasan na fada baka san na maidawa ba." Na fada ina me juya mishi baya, "Ni kika gayawa magana?" "Mehran ni bayan gaya maka magana ba, kawai kuskuren fahimta Ce." "Ikram!" Ya mike tare da saka kayan shi zai fita, dan ranshi yayi masifar b'aci, ko a jikina gyara kwanciya nayi, tare da cewa. " Sauka lafiya" Tunda ya saka kai ya fita, ya hadu da Azizatul Nissah, kallon shi tayi tare da cewa. "Sultan MEHRAN!" Wani irin kallon banza ya watsa mata," sannan ya wuce. .... Washi gari. Bayan na tashi ni dasu Izmah muka shiga gyara d'akin, bayan mun gama muka saka turarukan wuta, masu shegen kyau da dad'i. Sannan nima na dauko kayan gyaran jikina, sabida hailata da nake ganin Yau zata dauke. Cire riga nayi tare da daure kirjina da wani mayafi, suka shiga shafa min. Abun gyara jikin. Tare da da goga min A bayana, a hankali suna min hira, duk da ina sauraron su, amma hankali na, yana ha Mehran da yau bai shigo ba. Duk sai naji na damu saboda bai kai fadar da muka yi a masarautan mu ba, amma kuma haka muka yita mu'amalar juna har muka iso. Daga ni har shi bamu da zuciya domin mun kasa hakuri da juna, kuma ba zamu iya zama ba tare da mun yi fadan ba. Shafa abin nayi a kirjina, tare da gogawa a hankali, sake diban abin nayi naga sun mike. "Barka da safiya, Sultan Mehran" "Hmm" yace musu, take suka watse daga d'akin, ga uban kamshin da dakin ya dauka, mik'ewa yayi tare da juyawa ya rufe kofar, sannan ya dawo tare da zama yana kallona. Cire kayan shi yayi tare da zama ya saka hannun shi ya zare min mayafin jikina, da sauri na kai hannuna ina me kare kirjina. Kamar zan yi kuka. Diban kwabin yayi yana shafawa a jikin shi tare da zubawa a kirjin shi. "Mehran kayan gyaran mata ne fa?" Na gaya mishi a tsorace, banza yayi da ni, a hankali ya janyo matashin da suka saka min a bayana, sannan ya kwantar dani. "Ba kin rena ni ba? Ba kin mai dani mara mutunci ba? Haka kawai an cusa min b'acin rai kuma kema kina kokarin cusa min." Hayewa kaina yayi tare da jibge min nauyin shi, yana kallon yadda nake nishi ina kokarin ture shi. "Bakin ce ban kai namiji ba, wallahi sai na saka ki kuka yau sai kin gane duk mazan da suka zura miki azzakarin su kai ni ba, dan haka yau." "Allah ya taimake ka, dalla sauka akai na, an ce maka nayi wanka ne da zaka hake min." Na fada kamar zan mare shi. Dan yayi mugun bani haushi. Bakin shi ya kai saman nawa, na kauda kaina ina jin kwalla na zubo min, haka kuwa ya saka min da karfin tsiya. Ya shiga niman harshe na, yana samu naji ya sauke ajiyar zuciya. Tunda nake ban taba ganin irin wannan sumbatar ba, wallahi sai a gurin Mehran, domin kuwa kamar zai cire min harshe bakina har wani irin zafi yake min, tuni kwalla suka cika min idanuna, jin abin ya fara min ne, ya sani lumshe idanuna, tare da biye mishi muka Cigaba da sumbatar juna, yadda yake goga min hadin dake kan kirjin shi a kirjina yasani kai hannuna keyar shi tare da kara rungumo shi. Lumshe idanuna nayi ina kuma narkewa a jikin matashin, kara narka min soyayyar shi yake tare da taimaka min kamar yadda yasan zan iya taimaka mishi. Mehran yasan yarda ake bin mace cikin ruwan sanyi, kamar zan yi kuka haka yake bina, bakin mu yana hade da juna, hannun shi naji yana zamar da daurin dake kasana na yi maza na rike hannun shi ina girgiza kai. Cire bakin shi yayi a cikin nawa yana kallon idanuna. "Meye nufinki?" "Ban gama ba" "Hakkina nake so?" Ya tambaye ne ni, "toh ban gama ba zan baka kazamta ne?" Na shiga ƙoƙarin rabuwa dashi, sake riƙe Ni yayi. "Me yasa baki iya gaya min magana da tausassan kalamai?" "Sabida haka ka koya min, ni tarbiyyar kace, kai ka maidani yadda nake. Kuma zaka Cigaba da maida Ni yadda kake so" A hankali ya mike tare da nufar ban ɗakin, ina jin abu na zuba min, nasan ba iya jinin bane har da ruwan jaraba da muka mannewa juna, tashi nayi tare da nufar ban daki na samu ruwan da su Izmah suka hada min, ina ƙoƙarin cire abin jikina ya shigo, ban kula shi ba na zare farin tsumar jinin da nake na samu babu kome sai ruwan da nake zargin haka. Ji nayi an dauke ni cak tare da saka ni cikin ruwan. Ya bini tare da zama a bayana. Ya shiga dauraye min jikina, tun bana so har na hakura, juyar dani yayi muna kallon juna, a cikin ruwan kuwa hannun shi ne yake yawo a bakin kofar arewa, yadda yake min ne ya sani juyar da kaina, na kasa kallon shi. Shafa kirjina yayi tare da kai bakin shi kan daya daga cikin abinda yake mugun kauna, jin yatsar shi zai saka min a gurin ban san lokacin da na ture shi ba, zan fita a ruwan, jikina yana wani irin rawa, zunzurutun zafin da naji shi har cikin raina, sake dawo dani yayi da karfi ya juyar dani zai daura Ni akan, sandan girman shi, ihu na saka mishi tare da yunkurin guduwa. Sake dawo dani yayi, shi a tunanin shi ina ina gudun shine sabida kawai na ji haushin shi, bai san akan azabar da yake kokarin nuna min bane, juyawa nayi. "Don Allah." "Akan me zaki hanani hakkina, dake mazan banza ne min iya basu kanki babu wani abu a ranki ni kuma mijin aurenki, kin hanani hakkina, wallahi sai bayinki sun fiki daraja a gidan nan tunda kika zab'i tozartani da hakkina, mara mutunci kawai." Ya ture ni, tare da fita abin tana tsaye kam,saka kayan shi yayi a waje ya fita, abin shi. Daga nan bai tsaya ba, sai dakin Jasrah, tana barci ya shige har cikin uwar d'akinta, tayi baja baja, yana shiga yayi tozali da cinyoyin ta, masu haske da ɗaukar idanu, dan haka ya haura gadon, tare da d'aga rigar ta sama, ya shiga lallubar nonuwarta yana matsawa, yana jin ina Ikram ce ma a wannan yanayin, baki daya sai mika take ta zata mafarki yake, sai da ya shiga lasarta yana kuma goga mata kayan aikin shi. Saman cinyoyinta ta bude idanunta. Zata yi magana ya zira mata harshen shi a bakin ta, ta kama da sauri, tana kuma dauke ajiyar zuciya. Cikin matukar bukace, ya gyara mata kwanciya tare da kallon cikin idanunta ya danna mata, sandar girman shi. Wani irin kara ta sake tare da ture shi, ya kuma kara wani irin sauri wanda ya sata sake kuka a cikin wuyarta, a karo na uku ne ya jishi cikin jikinta sosai, ya ji yadda take da dad'i, amma wani abin mamaki bakin shi Ikram yake ambata, zungure ta yake yana kuma karawa da raruke ta, [5/24, 4:25 PM] Mehkram1256: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat Book3 _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayen Mu_ 15... Cikin rashin tausayi da jin kamar itace Ikram din ya shige ta, sai da ta sake wata irin kara tare da nutsata sosai, sai da yaji shi daidai a cikin jikinta sannan ya shiga aikin da ya dace, ihu take tare da dukar shi yana faɗin. "Duk duniya baki rena kowa ba Ikram sai ni, Ikram meye nayi miki da kika rena ni, yau..." Da sauran maganganun marasa fa'ida. Mehran ya gama fusata da abinda Ikram tayi mishi dan haka haushinsa ya sauke baki daya akan. --- Dake kusan su Kwarkwarorin suna kusa da juna ba kamar Ikram da take nesa da su ba, dan haka suna jin abinda yake faruwa, kasa zaune Azizatul tayi tana jin ranta kamar zai fita. Tana. Kuka ne ya zo mata tana kallon wani sunduki ta ja a hankali, ciro wani batta tayi tare da ajiye shi hawaye na zuba mata . "Na rantse da Allah babu wacce ta dace da ɗaukar cikin ka..kuma dole na haifa maka cikin jikina a matsayin naka" ta faɗa tana kuka me tsananin zafi. Fitowa Sakeenatu binti Abu Waqqas tayi tana kallon kofar Jasrah, tausayin kanta ne ya kamata, a hankali ta juya zuwa d'akinta. Sannan ta haɗa duk abinda take bukata ta juya tare da barin gidan baki daya,. Ta nufi lambu a can ta zauna tayi ta kuka. Kafin wani lokaci gidan ya dauki bushe bushe da algaita, ana murna Yau Mehran ya yi kwantar amarci da daya daga cikin matan shi, kafin kace kwabo an saka biki sosai. Ina daki naji ana ta buga tambura, kallon Ruwaida nayi da Izmah nace musu. "Meke faruwa?" "Bamu sani ba sai mun leka dai." Girgiza musu kai nayi tare da bude baki zanyi magana, sai ga Mahlika ta shigo tare da wasu dakaru. "Lafiya kuka shigo cikin?" "Waye ya baki gubar ki sakawa abincin Jasrah. Idan Sultan Mehran ya fito d'akinta!" "Amirah Ikram" ta faɗa kanta a sunkuye. Cike da mamaki nake kallonta tare da cewa. "Ni yaushe kika" "Ke kuka turo wannan wadar ta kawo min, idan Mehran ya fito dakin Amirah Jasrah, idan za a kai mata madara a saka mata a cikin abincin ta" Kura mata ido nayi kafin ba kalli dakarun na bude baki zan yi magana Mehran ya shigo. "Ku tattara bayinta ku tafi dasu, ita kuma ku barta anan." "Babu inda zasu tafi tunda nayi ce nayi laifin, ba zan bari a tab'a lafiyar su ba." Na faɗa. "Ku fita dasu." " Baza su tafi ko ina Ba Aamaan" na fada mishi. "Ka kira min, Azizatul Nissah." "Idan ba zaki bari a kai su gidan horo ba, zan saka Kwarkwarah ta zane min ke" d'ago kai nayi tare da sake murmushin takaici nace mishi.. "Aamaan.duk abinda kaga yayi maka kana da damar yin haka lokacin ka ne, Ni." Shigowa tayi tana me kaskantar da kanta. "Ku fitar da ita ki zane daidai laifin da ta aikata." "Ba sai sun fitar dani ba, Mehran zan iya fita da kafana." Haka suka fita na gyara zaman rigana tare da saka kai zan fita ta finciko ni. "Sai kin biya kamar yadda na gaya miki" "Sai me? Ka sake a kashe ni shine zai sani fahimtar kaji haushin ban baka gindina kaci ba." Na gaya mishi a fusace. Haka na fita a gaban sauran bayi da Kwarkwarorin, ina fita ya dunkule hannun shi tare da kai naushi a jikin bango. "Bilqisul Ikram! Meye nayi kike azabtar da ruhina? Meye na miki haka?" Yana jin yadda Azizatul Nissah take zane ni, tare da jin kamar finciko duk wani jijjiyar da take hade da zuciyar shi, lumshe idanun shi yayi yana jin sautin bulalar. Tun yana kirga bulalan har ya kai da ya rud'e, ita kuwa tana yi ne da haushin ta tare da mugun kishin da yake cinta. Haka ta gama sannan ta wurga da bulalar, sannan ta zauna rike da cikinta, zuwa Izmah da Nimra da suka yi, suna kuka. Suka d'aga ni, Ruwaida ta juya tare da min alamar zata goye ni, lokacin ya fito daga shashina. Girgiza mata kai nayi tare da cewa. "Karki damu, zan iya tafiya da Kafa na." A hankali na fara takawa har zuwa daidai inda yake, murmushi yayi min, nima na maida mishi. "Ki iya harshenki, sannan ki iya furucin ki, uwa uba ki iya kishinki, idan na kuma jin labarin kinyi wani abu, hmm" Ban mishi magana ba, na wuce abuna, ina shiga daki na yanki jiki na fadi. Rigana suka fara cire min domin ta bayana ya fashe sosai, haka suka taimaka min da ruwan zafi, bayan sun saka min ruwa na farfaɗo, a hankali suka gasa min bayan tare da shafa min magani. Tun daga ranar Mehran ya gane dadin matan da suke kasan shi, yayi ta binsu yana kwana dasu. Domin bayan Jasrah bai kuma bin wata d'akinta ba, tsakanina dashi sai dai idan na shiga lambu muke haduwa shima, kowa sabgar gaban shi yake yi. Abin yayi mugun b'ata mishi rai. Domin ranar da Yasaka aka zane ni, da dare liyafa suka yi tare da gabatar da ita a matsayin, shugaban Kwarkwarorin wanda ba haka suka so ba, burin su a bata matsayin magajiyar sarauta. Amma yaki magana akan haka. Cin mutuncin da naga Jasrah da Azizatul zasu fara min ranar na kamata na mata shegen duka, ta hanyar zane ta, wato Jasrah. Yana fadanci aka je aka gaya mishi, shiru yayi tare da cewa. "Ku tawo da ita." Lokacin da aka tawo dani, a nutse na shiga fadar. "Amirah Bilqisul Ikram! Meye kike nufi da kika daki Amirah Jasrah bayan ana kyautata zaton juna biyu gare ta?" "Rashin kunya tayi min naga ba zan iya kyale ta ba na dake ta?" Na fadawa Amir Hood, "Baki iya magana cikin hikima bane?" "Ba a koya min shi ba" "Baki da da'a ce?" "Ban san shi ba?" "Ke Yar gidan Uban waye?" Had'iye yawun bakina nayi sannan nace mishi. "Almustapha Mu'allim, nasan kana da tarihin shi ai. Kwararren mai sarrafa kwari da baka." "Fudail ka kai Ikram haramtacciyar fada." Ya fada min yana kallon fuskana. Murmushi nayi mishi sannan muka fita da Fudail, sai lokacin na samu damar son yin kuka, dan zuciyata tayi mugun zafi Sosai. Muna shiga gidan naga Anneh, da sassarfa na isa gare ta, tare da zuɓewa a jikinta. Kuka nake mata tare da rokonta. "Anneh kice ya sauwake min, wallahi na fasa zama dashi" Na fada ina kuka me cin rai. "Kukan abinda suke mike kike ko kuma kukan abinda yake miki kike?" "Ba zan taba musu kuka ba." Na goge hawayen ina me zama tare da kallon su. "Sultanah, ko zaki taimaka mana tayi kokarin koyar halin su." Ya faɗa tare da juya ya fita. Abin da Mehran yayi na banzatar da Mahaifiyar shi ya sani jin tsanar shi. Sai da na kwashe kwana goma sha biyar, sannan Mehran ya taso da kan shi yazo ya zai fitar dani. Ganin yadda Annerh take gyara min gashina, yasa shi zuba min ido, muna cikin farin cikin, tunda nazo take gaya min yadda zan samu nasara a cikin gidan. Murmushi tayi mishi sannan tace mishi. "Zakina Sannun da zuwa." Zama yayi tare da gaishe ta, sannan ya nutsu. Wani daure fuska yayi tare da amsa mata a dakile,, dauke kai nayi kamar bana gurin, "Idan kin gama ki tashi." "Babu inda zani" Tasowa yayi da nufin ya dauke ni tare da nufar kaina, kallon shi nayi domin baki daya sai wani fitar da huci yake kamar wanda ya sami sa'an shi. D'agani yayi tare da jijjiga ni, "Kin isa ina magana kina magana, kije kika ga yadda matan da suke kasana suke kyaytata min" "Aamaan matsalar ku ragagge ne bani da lokacin ka, kaje." Rigima ce ta sarke a tsakanin mu, sosai tare da lallai sai na bishi nima kuma nace bani binshi. Karshe haka Mahaifiyar shi ta bashi hakuri, cikin masifa ya juya kanta zai mata nace mishi. "Kul! Uwa tafi gaban haka ka kuskura ka gaya mata magana wallahi sai na bar gidan kuma na yake ka naga yadda zaka yi dani. Ka godewa Allah da ya barta a raye, ni ina son nawa na rasa su, dan haka bani hanya na wuce." Na gaya mishi tare da juyawa ba dauki mayafina, na tafi gidan,tun daga ranar, na sake fadawa matsala da shi, domin kuwa duk abinda ya faru nice Mehran baya bincike zai hukunta Ni. Yau na fito daga dakina zan fita naji suna ta hira Azizatul tana gaya musu. "Karuwa ce? Kuma baiwa ce a masarautan mu, dan Sultan Mehran ya aureta aka kaita wata masarautan. Amma Ni na sha ganin yadda Yayana yake kwana da ita." Juyawa nayi tare da ɗaukar tufa na gutsira sai da na tattauna shi, sannan na amayar dashi dan har na had'iye na zuba a kasa, ina juyawa na janyo wuyar rigarta na kifa kanta a kan aman nawa, sai da na sata ta lashe. kan Uban Bala'i, amai take son yi na tushe mata baki, sai da ta had'iye ba juya ina kallonta kafin na fita ba bar musu gidan. Aikuwa aka kira Mehran, yazo ina lambu. Ya shigo Kamar zai tashi sama. Abinda ya kawo shi bai ishe ni ba, na cigaba da abinda yake gabana, yana ganin naki kula masifar shi. yasa kai ya fita. Haka muka cigaba da gara juna, tare da wahalar da juna, tun yana, watan cikin Azizatul Nissah shida wata ifitla'i ya dame ni. Ba kome bane sai Mehran ya sani dafa mishi mishi abinci, ina gama abincin kafin na shiga daki na dawo an zuba mishi guba, koda na juye abincin na kai mishi, zai fara ci naga kamar kasan abincin yayi bakikkirin. A tsora ce na kalle shi. "Guba kika saka min?" "Tun tuni ban saka maka guba ba, sai yanzun?" Kafin kace me maganar ya bazu, ina shiga d'akina, na sami wasika . _Ina da yakinin Kinga abinda ya faru! Ki fito daga Masarautan ina jiranki idan kika sake yaci abincin dare yau gobe zaku shiga takabar shi ABRAD_ Haka na dauki mayafina, tare da bin ta bayan gidan na fice, har wajen gari na fita. Kamar yasan da zuwa na, na hango shi a kofar wani gida. Kamar zanyi kuka nace mishi. "Meye nufinka? Meye yasa kake bibiyana?" Takowa yayi tare da tsayawa a gabana, ban san lokacin da na mare shi, cikin kuka nake cewa. "Kanwarka ta hanani sukuni, kai ka hanani sukuni meye ka maku ne?" Na durkushe ina kuka. "Ina Sonki ne?" "Babu soyayya a tsakanin mu, Kanwar mahaifiyata ka aura ta ina zaka soni?" Shiru yayi sannan yace min, "Ina kaunarki har yanzun ban cire rai da ke ba, ki rabu da Mehran ko tawo gare ni, idan ba haka ba wallahi zan kashe shi." Kwalla ce ya zubo min cikin iyakacin kuka nace mishi. "Karka sake wani abu ya same shi dan wallahi zan hauka ce maka" Takowa yayi gabana tare da cewa. "Ina jin zafin kukan da kike yin nan ko hakura kizo." "Wallahi gwara na mutu bani da aure da na bika, na gaya maka ka rabu da Mehran." Sannan na juya na bar gurin, har na shiga ban cikaro da kome ba, sai da na shiga d'akina, na same shi zaune yana kallona. "Ina kika je?" Toh me zan gaya mishi, nace na tafi gurin Abrad. "Na tafi gurin Anneh ce" wannan karyan ya fado a kaina, murmushi yayi sannan yace min. "Ina tsoron kar na sami wani abu da zai tab'a kimar masarautun da kika fito ne, shi yasa na miki magana, kuma na fahimci ana min wasa da igiyar aurena, zan iya kome dan na tabbatar da kare hakkina. Dan haka ki fita ba tare da iznin na ba kuskure ne babba." Ya saka kai tare da barin d'akin, zama nayi ina jin babu dadi a rai, kamar na gaya mishi gaskiya, sai dai kuma yana fita aka gaya mishi daga wajen gari na fito. [5/25, 9:43 AM] Mehkram1256: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat Book3 _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayen Mu_ 16... Zai juya cikin gidan, Fudail ya rike shi tare da cewa. "Idan ka shiga me zaka ce mata? Kace daga ina ka fito bayan ka gama niman ta? Ka gama birkicewa daga fitar ta, shine zaka kuma komawa cikin gidan ka titsiye ta, bayan ka san ba hakuri ne da ku ba. A gaskiya bai dace kana zubda mata da matsayinta a gaban abokan zaman da basu kaita ba, domin abun kunya kake shafa mata ka duba magana ta." Shiru yayi sannan yace. "Daga yau ka saka ido akan fitarta" "Ni ba zan saka idanun akan fitar, ba sai dai Ko Nimrah" kallon shi yayi kafin yaji jikin shi yayi mugun sanyi, tare da juyawa ya shiga cikin gidan. Tun daga lokacin sai wani irin zargi ya kuma kulluwa, wanda takai ko ban daki ta shiga fahimci kamar ana bibiyarta. ....... Dan haka aka kuma ninka matakan tsaron gidan tare da saka ido a kaina, ko ina na fita sai na fahimci ana bibiyata, har ranar nake tuntubar Fudail ko ya san dalilin da yasa Mehran yayi min haka shima ya nuna bai sani ba. Kuma naso muyi maganar da Mehran yaki bani damar haka, shi yasa na ajiye abin a gefe. Zaman Cikin gidan babu dad'i ga munafuncin bala'i domin anata rad'e rad'e, Jasrah ciki da da ita, gefe guda cikin Azizatul ya tsufa bata cika shiga hidimar ba, sai wani abu da yaso hada su da Jasrah har ta kai sun yiwa juna su habaici da bakakken magana. Ina kwace, naji ina son fita zuwa haramtacciyar fada, dan haka ban gaya mishi ba, na shirya na fita abuna, koda na dawo na samu ana ta nima na. Kallon su nayi ina kuma kallon Mehran da yake zaune a kan darduma. "Sultan MEHRAN kayi mata iyaka da bibiyar rayuwar d'an uwana, ban da jaraba da karuwanci. Sai kace karya da auren ki ma ba zaki daina bibiyar Abrad ba, toh wallahi wani abu ya faru sai kin biya wallahi dan ba zan lamunci haka ba" Ta watsa min takardu a fuskana, rubutuna ne tare da tambarin masarautan. Kwalla ne ya cika min idanu, domin har da kwanan wata, da kome kallon Izmah da Nimra sai Ruwaida, sunkuyar da kai suka yi. A hankali na juya tare da kallon shi. "Nayi laifi Sultan Mehran, duk hukuncin da ya dace ka yanke min" na fada hawaye na zuba daga idanuna. Bai iya cewa kome ba sai kallona yake ya ma rasa abinda zai ce, mik'ewa yayi tare da cewa. "Daga yau ku ninka Dakarun SAMAIND sama da wanda suke waje, sannan a nimo min Abrad a mace ko a raye a kawo min shi domin nayi alƙawarin idan ya kuma bibiyar Mata ta sai na kashe dan iska." "Akan me? Meye laifin shi? Ga wacce take bibiyar shi ba a dakatar da ita ba sai, shi wannan ba adalci bane Sultan Mehran, wannan ba adalci bane, akan me zai bibiye ta, bayan yana da wacce ta fita, Sultan Mehran don Allah karka cutar min da shi, dan shi daya ya rage min a duniya. Idan ka kashe shi waye zan ƙalla na jin sanyi, amma ita tayi karuwanci baka ji haushi ba sai shi, karka manta Mehran shi da shugaba ne guda fa, al'umma yake jagoranta, don Allah karka kashe mana shi, don Allah ka karka kashe min d'an uwana. Idan ba haka ba kuwa zaka dauko abinda zai dame mu." "Kiyi min shiru? Yau ne ya fara bibiyarta? Meye ya kawo shi SAMAIND? Meye ya hana shi zama a kasar da yake mulki tabbas idan muka hadu zai gaya min abinda ya kawo shi SAMAIND har yake bibiyar matar da nake aure." "Amma wannan matakin ba zai yiwu ba, sabida." "Idan kika kuma wani magana wallahi sai na saka an shafe min daular ku baki daya." Ya fada a tsawa ce, wannan dalilin yasan ya ta yin shiru. Hawaye na zuba mata, kallon Ikram tayi cikin kuka tace. "Ki saka a ranki daga yau zaki fara fuskarta matsala da sai kin gwammaci mutuwa da rayuwa." Ta juya a fusace, tana kuka tana shiga d'akinta wani irin ruwa ya faso mata, kafin kace me, haihuwa tazo, babu shiri aka shiga niman unguwar zoma, suka cika d'akin. Ni kuma wuce ni yayi tare da ja min tsaki, haka na shige cikin shashina, na zauna ina kallon inda nake da yakinin an ajiye min Abu dan ba hakan na fita na bar gurin ba, shigowa su Izmah suka yi tare da zuɓewa kasa, suna kuka. "Kiyi mana afuwa." Cikin matukar karfin hali nace musu. "Ku shirya ku tafi Askandariya," "Don Allah kiyi hakuri, ba zamu kuma ba." "Bana son damuwa ku shirya ku tafi Askandariya" kuka suke nima kuma hawayen nake gogewa. "Ku shirya nace" da sauri suka shiga hada kayan su, tare da kuka domin. "Wallahi Ikram bamu tab'a cutar dake ba. Bamu san me ya faru ba, don Allah kiyi hakuri." Hawaye ne ya zubo min, tabbas basu nuna min sun san kome ba, amma taya aka samu wasiku haka a d'akina? Taya aka samu abinda nima ban san dasu ba, kwalla ne ya zubo min na kuma cigaba da sharewa. Zasu Fita Mehran ya shigo dakin, ganin sun hadu a babban falon yasa shi zuba musu ido. Kafin ya shigo dakin ya same ni a zaune ina kuka. "Ina zasu?" "Zasu koma Askandariya" Gyada kai yayi sannan yace min. "Babu inda zasu" "Zasu tafi fa" "Idan na isa babu inda zasu" kallon shi nayi sannan na sunkuyar da kaina, ban ce mishi kome ba. "Me yasa kika zab'i tozartani?" Ya tambaye ni tare da matse hannuna. "Me yasa kai baka bincike?" Na mai da mishi tambayar shi. "Laifi na kike gani?" "A'a ban ga laifin ki ba, sai na lusari irina, haka kike son na fada?" "Duk yadda yayi maka Mehran zaka iya fadi!" Jinjina kai yayi tare da juya, kanshi yana jin kamar zai fasa ihu, amma bai ce kome ba, ya mike tare da cewa. "Na barki Lafiya, idan kika sake wani abu ya kuma faruwa, Ikram karki yi kuka dani, kiyi kuka da kanki." Sannan ya juya ya bar d'akin, bayan yayi mata kashedin kar ta sake bayinta su tafi, zama nayi ina son nayi kuka, amma na kasa, dan haka na yi shiru ina kallon hanyar da yabi, kamar na fasa ihu. haka nayi ta jin kamar zan mutu, wasikar na gani da sauri na dauka. _Mijinki ya hanaki fitowa ko? Har da saka matakan tsaro? Ikram tabbas zan baki mamaki gobe zasu fita rangadi idan kin iya ki zo idan ba haka ba zaki sha mamaki_ Na karanta sakon ya kai sau goma sha biyar, na rasa yadda zan yi da raina dan haka na zuba ido na ga me zai faru. Har dare tunda nayi sallah na kasa ko kai loma daya na abinci cikina, na zauna ina kallon abincin, karshe daukar abincin suka yi tare da fita dashi. Ina zaune sai ji nake kamar zanyi kuka. Washi gari. "Ina kwance ya shigo dakin da shigar zai fita, kallon shi nayi domin yayi masifar kyau. Shima kallona yayi babu yabo babu falasa, yace min. "Azizatul Nissah ta haihu ki shiga ki duba ta, kuma ki manta da abinda ya faru, ta samu mace." ."Allah ya raya." Takowa yayi gaba na, tare da d'aga ni tsaye muna fuskata juna. "Yaushe zan ajiye miki nawa Yarona? Kamar yadda na ajiyewa Jasrah." Ya faɗa tare da kai kan shi wuyana, yana shinshina ni. "Gaskiya babu rana" "Akan me? "Sabida Zubewar darajar gidan nan ba zai yiwu na dauki cikin Yarima me zuwa ba, sabida Ni baiwa ce da na rayu a tsakanin dauloli biyu." Murmushi yayi sannan yace min. "Haka yayi ai" Sannan ya juya zai fita nace mishi. "Ka kula domin za a iya farmaka ka" "Waye me zarar farmakar zaki irina?" "Ai yadda kake shiri haka kowa yake shiri akanka" "Toh maji magani" Kwanciya nayi abuna, sabida iskar da yake kad'awa, alamar zamu iya samun ruwa, haka shima ya juya tare da barin d'akin. Ina zaune a gurin har aka fara ruwa, me shegen ƙarfi. ---- Tunda suka fita yake bin talakawan shi yana ganin abinda ya faru, tare da sakawa ana daukar sunayen su. Dandazon mutane aka gani dan haka suka tsaya ana tambayar lafiya, babu wani abu. Kawai shiri aka yi akan shi, dan haka yana sauka tare da kutsawa, cikin mutanen sai ji yayi an soka mishi wuka. _Kayi a hankali domin ana shirin farmakar ka_ Sake suka mishi aka yi ta dayan gefen, rike hannun su yayi sai da ya karya hannun, ihun su ya saka aka watse, jini na zuba a jikin shi ya zare takobin shi tare da sarar wuyar dayan mutumin dayan kuma ya kai zai sare shi yace. "Abrad ne ya saka mu" Faduwa Mehran yayi, Fudail ya karasa tare da ɗaukar shi, a baya suka nufi cikin masarautan da gudu, lokacin ana sake musu kibau ta ki ina, dab zasu shiga masarautan aka harbi Fudail a kafa, dan haka suka hantsila tare da faduwa, sake tashi yayi ya dauki Mehran suka shiga cikin masarautan. Lokacin da aka gansu cikin zubar jini ne aka amshi Mehran, duk wani irin taimakawa da ya dace anyi Mishi, amma babu wani abinda ya faru, dukkan mu muna tsaye akan shi musamman ma Ni da aka kawo shi d'akina, "Sun yi amfani da guba ne a wukar nasu, shi yasa." "Toh meye mafita?" "Wallahi bamu sani ba," Gyada kai nayi sannan na shiga dakin girki, na hada magunguna tare da dafa su, na kawo mishi na fata bashi yana sha. Sannan na kira Sarwat nace mishi. "Ka tafi haramtacciyar fada ka dauko Anneh." Haka na cigaba da bashi kulawa, duk Kwarkwarorin suna shigowa sai Azizatul ce bata shigowa. Haka nayi ta kokarin ganin gubar ya sake shi. Sai da muka kwana muka wuni, sannan ya farka lokacin Anneh tana tare da shi, lokacin da ya farka ya kalle ni. "Taya aka yi kika san za a kawo min hari?" Shiru nayi sannan nace mishi. "Naji haka ne a jikina". ---- "Amma ai ba haka aka yi da kai ba, cewa muka yi Bama son ya rayu shine zaka bashi damar ya rayu." Inji Amir Hood da Hoyam sukewa Abrad magana. "Ya kama min mutane na, sannan kuma zaku min maganar banza, ku yi min sanadin da zan sami Ikram ni kuma zan kashe shi." Ya faɗa. "Wai me yasa kake son Ikram din nan ce?" Inji Amir Hood. "Sabida Ni na kawo ta, kuma akwai sirri a tsakanin mu, dan haka ku kira shi ku tambaye shi ni ita nake so shi kuma zan kashe muku shi." "Amma ka kawo abinda shawara, zamu turo maka ita." Daga haka suka yi mishi sallama. ---- Sati biyu da faruwan Al'amarin, ina goge mishi jikin shi, sai ji nayi hannun hannun shi cikin rigana, ban san lokacin da na make hannun ba. "Baka da lafiya amma hannunka ba zai zauna guri daya ba, dalla sake ni." "Wai ke haka ake aure a garin ku?" Ya tambaye ni yana lashe bakin shi. "Sai dai na tambayo maka." "Amma Ikram amma dai da baki da nono naga yanzun nonuwar suna cika min hannun." Buge hannun shi nayi tare da Cigaba da abinda da nake, haka muka Cigaba da rayuwa, tare da bashi kula, ranar da yaji sauki ya fara fita Fada. "Sultan MEHRAN, meye alakar Matar ka da Sultan Abrad?" Zuba musu ido yayi sannan suka ci-gaba da kawo magana irinta ta shin hankali. "A bisa kudirar masarautan nan, duk macen da aka samu tana da alaka da wata masarautar ta hanyar sirri, toh hukuncin kisa ne akan ta, imma ya kashe ta da hannun shi, ko kuma mu mu kashe ta da hannun mu." "Sannan kun manta ne, nan gaba wacece Sultanah masarautan nan?" Suka tambaye shi. "Ikram! Bilqisul Ikram Mustapha Mu'allim itace Sultanah na gaba" "Ba zamu bata sabida tana da alaka da masarautan da ta kawo maka hari, ta zama munafuka kenan. Sabida muna zargin wani abu na daban." Rigima aka fara a fadar kamar za a daku, Yana shigowa cikin gidan ya mike dakinta...... [5/25, 9:43 AM] Mehkram1256: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat Book3 _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayen Mu_ 17.. Cikin tashin hankali ya nufi shashinta, yana shiga ya samu su Izmah suna zaune. "Ina Ikram?" Shiru yayi tare da fahimtar, bata nan, shiga dakin ta yayi tare da duba ko ina, ya samu bata nan. Fita yayi daga d'akin, aikuwa ya fita tare da nufar turakar shi, ya dauki gatarin shi. Yayi shirin yaki sannan ya saka kai ya fita, cikin fushi. Ya fita daga Masarautan ya nufi wajen gari, tafiya me nisa yayi kafin ya hango su, hadiri ya mamaye garin tare da sake iska. Koda ya isa gurin su, wani sabon bakin ciki ne ya turnike shi domin kokarin da Abrad yaƙe na sai ya kwantar da ikram, ita kuma tana ya kai mishi duka. Kamar zai mutu haka yake ji, dan haka yana isa ya finciko ya, suka fara wani irin dambe na fitar hankali,, ruwan da ake tsulawa ne yayi masifar daga mishi hankali, dambe sosai dakyar wani tsawa ya raba su, kafin Mehran yayi wani yunkuri, Abrad ya gudu, juyawa yayi tare da kallona, yana zuwa ya shiga jana. Ina mishi magana amma fir yaki kula ni haka muka shiga cikin kasuwa Mehran yana jana kamar kayan wanki. Har cikin masarautan bai d'aga min kafa ba, sai da ya dangana ni da dakin shi, kafin ya shiga kwab'e kayan shi, a tsorace naja da baya. "Mehran? Karka tozartani, don Allah karka wulakantani Mehran, don Allah ka tsaya nayi maka bayanin abinda yake faruwa." Rufe kofar dakin yayi tare da kashe hasken dakin sai hasken tagar da take shigowa tare da iskan ruwan da ake, jana yayi tare da cillani saman gadon. Ya cire kayan shi tsaf, dan rashin imani, haka yayi ta yaga na jikina, Kwarkwarorin shi suna jin shi yana masifa da ihu, kuka ne ya kwace min, domin kuwa maka nonuwana yayi ya matse sai da na fasa ihu, me ƙarfi zunzurutun azaba, ya juyar dani, ya ma rasa abinda zai min yaji dad'i, kawai sai saukar dani yayi tare da matse ni da bango, ya d'aga kafana, tare da shuga jikina da mugun karfi, kokarin kwace kaina na fara, sabida naji zai ya galgalani, amma idanun shi ya rufe jikin shi wani irin rawa yake, burin shi ya biya bukatar shi kawai a wuce gurin. Kuka na saka tare da juyawa na kwaci kaina,muka shiga wani irin dambe, tare da fashe fashen duk abinda muka yi karo dashi, dambe me sunan dambe, ganin naki na barshi yayi yadda yake so dani kawai ya kuma juya ji da karfin tsiya, ya danne Ni, sannan ya kifa kanshi, ta shige ni da mugun karfi tare da jin wani irin yarrrrrrr a jikin shi. "Wayyo Allah na!" Iya abinda na faɗa kenan, tare da kifa kaina a jikin matashin da saka min kaina, sake shiga yayi sai da naji abin har cikin cikina, ban san lokacin da na furza da amai ba, sake shiga yayi da karfi, shi da kanshi yasan ya ji min ciwo, domin kuwa abinda yake tsammanin na raba a waje sai ji yayi baki daya ya rasa tunanin shi. Kwanciya yayi a jikina muryan shi na rawa, Yace. "Me yasa kika min shiru? Me yasa baki tab'a kyamar kalmar da nake gaya miki ba? Me yasa kika boye min wannan al'amarin? Nayi ta azabtar da ke baki gaya min kome ba, haba ikram, toh sai ki amshi laifin shirun da kika min" Idan nace Mehran na da Imani, toh ba mamaki ina kaunar shi ne, amma yafi dacewa da layin mugayen karshen karni, domin kuwa sai da yayi min yaga yaga, sannan ya janye daga jikina, kan gadon kuwa ya jike da jini, da ruwan da ya zuba a jikin mu, juyar dani yayi yaga na koma da baya, baki daya ya gama lalata kome. Rud'ewa yayi ya shiga ban daki ya dibo ruwa ya kwara min, ajiyar zuciya na sauke sannan na bude idanuna, ji nayi kamar ba jikina ba, dan haka ina kallon ya koma ban daki, na samu na janyo zanin gadon na rufe jikina, tare da mik'ewa da kyar, na nufi hanyar fita. Ina fita nayi karo da Kwarkwarorin shi suna kallona. Wani kuka ne ya zo min, a lokacin ban iya kukan ba, sai da na nufi d'akina, suna me bin jinin da yake zuba a jikina da ido. A tsorace suna shiga cikin dakin shi. Ganin yadda aka yi barna kafin bukata ya biya, ga gadon shima babu sauki, yasa su cewa. "Wannan karya ce, taya za ayi jinin budurci ya zuba haka sai dai idan akwai abinda aka yi." Fitowa yayi ya same su a tsaye, daure fuska yayi da sauri suka fita, kallon dakin yayi ya tabbatar na fita, dan haka ya saka riga ya biyo bayana, ina shiga d'akina na zube a tsakiyar falon ina maida numfashin da yake kokarin barin jikina. Lokacin da ya shigo ya samu su Izmah suna kokarin kai Ni d'akina, daukana yayi tare da wucewa dani dakin, da kan shi ya taimaka ya hada min ruwan zafi, saka ni yayi ban san lokacin da na zabura zan mike ba, ya kuma danna ni cikin ruwan. "Mehran!!" Na fada ina kuka, shafa kaina yayi tare da cewa. "Qurratulain! Kiyi hakuri kinji Sirrintacciya na, nayi miki laifi. Kiyi hakuri da Mehranki bai da kirki. Sannun kinji da nasan haka ne ba zan tab'a yarda na kusance ki haka ba, da zan kusance ki da soyayya ce yadda kema zaki gamsu ina kaunarki,, Ina me baki hakuri da abinda nayi miki, kiyi hakuri Ikram dina, INSHA Allah daga yau duniya sai ta sheda ina kaunarki, kiyi hakuri kishinki ya sani kasa Fahimtar ki." Hawaye ne ya fara zuba min domin wallahi na tsane shi, burina na gudu matukar na samu sauki zan gudu na bar shi ba zan iya ba, kashe ni zai yi. Haka ya gama taimaka min nayi wanka, sanan na fito. Dakyar nake daga kafana. Ina fitowa Izmah tana mika min madara, dakyar na sha kamar magani, sannan suka bani doguwar riga na saka, sannan suka dauki zanin gadon zasu fita dashi ya amshi abinshi. "Ku kula da ita." Barci me nauyi ne yayi gaba dani. Lokacin da ya shiga dakin shi gyara ko ina yayi da kanshi, wani irin yanayi na farin ciki yake jin shi, kamar bashi ba, yanzun ya san ya hadu da mace, jaruma sai yanzun ya sami abincin ruhinshi, bayan ya gama abinda zai yi ta dauki zanin. Kiran zaman gaggawa yayi tare da gabatar musu da shaidar kwanciyar da yayi dani, take aka nimo kwararru kuma masana akan jinin budurci, suna zuwa suka zuba zuba ma turare akan zanin gadon, ganin kalar bai sauya ba dasu cewa. A kira musu Ikram din, Fudail aka tura, tunda yazo nace su gaya mishi ban da lafiya bazan iya Fitowa ba, haka dai suka tabbatar lallai sai na fito. Alkyaba na saka a saman doguwar rigar, sannan na nufi fadar inda nake tafiya dakyar da taimakawan Nimrah, zamu shiga fadar aka dakatar da ita, na shiga ina jan kafar kamar wata yar kaciya, kunya ta gama kama ni, kai na a sunkuye. Na isa tsakiyar fadar. Kallon manyan matan da aka kawo dan su duba Ni suka yi. ."a shiga a duba mana ita" D'aga idanu nayi zan kalli Mehran ya sunkuyar da kan shi, haka suka kai Ni dakin da yake fadar, suka umarce Ni da na kwanta, haka suka d'aga rigar jikina suka shiga duba ni, hawaye yana zuba daga idanuna. Ina jin dayan na cewa. "Gaskiya baki kyautawa kanki dubi yadda ya farka miki jikinki ke zaki ji dad'i yadda aka ji miki ciwon nan kuwa? Baki ji idan kika yi tafiya numfashin ki yana hawa ba, karki kuma yarda yazo da zafi ya amshi hakkin shi. Babu kyau wallahi." Hawaye ne ya shiga zuba min, a hankali suka shiga gyara min jikina tare da bani kulawa, sannan suna gamawa suka taimaka min na mike, a hankali na fito sai lokacin na ke jin kuka yazo min tasowa yayi tare da riko hannuna na fada jikin shi ina kuka, kujeran shi ya kai ni na zauna, baki daya manyan fadar suka mike tsaye. Kallon shi nayi. Zan bude bakina nayi magana wani daga cikin yan fadan yace. "Amma kuma ai mun sami labarin ta tab'a aure? Sannan kuma ta tab'a mu'amalantar maza" Daga Ni har shi kallon juna muka yi, sannan na mike na sauka a kujeran. "Sai kun tabbatar babu wannan zargin akanta zamu bata damar zama Sultanah a hakan kuma sai ta dauki cikin da namiji zamu kara yarda da abinda zamu bata, dan haka mu ma zamu fara binciken abinda yake yawo a tsakanin bayi na cewa ta tab'a aure." Rike hannuna yayi muka nufi cikin gidan, yana me jin kamar ya kama Abrad ya mishi yankan rago. "Me kika fahimta akan abinda yake faruwa?" Ya tambaye ni tare da daukata, "Su suna son mulki, Abrad yana son ganin na rabu da kai, shi yasa suka hada karfi da karfe gurin ganin bayan ka." "Meye kika sani da hakan?" Kai hannuna nayi kafad'ar shi, ina me kwantar da kaina, nace. " Ba me yawa bane, kawai dai nasan dai akwai wani abu a kasa" "Ya kike ganin zamu yi da Abrad?" Kallon shi nayi domin gaskiya yaki ya kamata ayi dashi, amma sanin cewa SAMAIND suna da karfin dakaru yasani cewa. " Ban sani ba" Haka ya shigo dani, duk Kwarkwarorin suna kallon mu ya kai ni dakin shi, tunda muka shiga ba zance kome ba, amma duk kulawar da ya dace ya bani, Mantawa yayi yana da wani abu a gaban shi, sai da nayi kwana biyu a dakin ranar ya fita, ashe wai yaki aka shirya, zasu rushe Abrad, sannan itama Azizatul Nissah zata kawo mishi wargi ya saka aka kai ta gidan Horo. Kwanta daya aka sakota, tun daga nan muka shiga wani irin rigima da ita, wanda ta kai na kasa zaman lafiya da kowa sun hade min kai, babu zamanin lafiya, haka kuma ba karamin d'aga min hankali yayi ba, koda aka tafi yakin manyan malamai da mutanen Oman suka roki Alfarmar ba zasu iya yaki da Mehran ba, dan haka yayi hakuri idan suka sami Abrad a hukunta shi. Satin shi daya suka dawo lokacin na warke sosai, amma maganar gaskiya, Mehran ya dasa min shakkar shi, wallahi ko muryan shi naji sai na razana, dan haka ina kwance ya shigo shashina, tsayawa yayi a kaina tare da bude min hannu, kallon shi nayi domin nayi kewar shi sosai, a hankali na isa gurin shi, na fada a kirjin shi, daukata yayi tare da cewa. "Ina son kiyi min abinda muka yi ranar da kika zo min a masarautan ku, ina son kiyi min shigar." "Mehran! Baka ji kunyar tambayana nayi maka wani abu ba? Tun daga wannan ranar nake kika da kai, kawai ka kyale ni" na fada hawaye na zuba min. "Kiyi hakuri nace nayi ta baki hakuri baki hakura bane" ya faɗa tare da rungumo ni Sosai. Kuka ne ya kwace min, dan haka ya kai ni kan kujeran tare da zama yana kallona yace min. "Kiyi hakuri! Yadda aka gaya min dole naji.babu dad'i ashe gadar zare aka kulla min, gashi nan Allah ya wanke ki, Amma me yasa baki bawa Noman hakkin shi ba." Kallon shi nayi sannan na share fuskana nace mishi.. "Wancan ranar nayi kokarin ganin na bashi hakkin shi, amma halin da muka tsinci kanmu na sumammen mutanen ka." "Mutanen Abrad dai, shi ya tura Nawwas ya kashe miki mijinki sannan ya daura min." Kura mishi ido nayi domin na tsorata da abinda ya gaya min. "Me yasa Abrad yake min haka?" "Sabida yana matukar kaunarki? Abrad na sonki duk da yasan haramun ne aure a tsakanin ku, shi yasa yake ta kawo min hanyar da zan nisanta taki da ni." Kuka ne ya kwace min, tare da kallon shi. "Mehran! Me yasa ya zab'i b'ata min rai, ka cutar da Ni ba zan tab'a yafe maka ba..... [5/26, 9:26 AM] Mehkram1256: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat Book3 _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayen Mu_ 18... Kura min ido yayi, cikin nutsuwa sannan yace min. "Nasan nayi laifi, amma kishinki ne yake damuna, ina da zafin kishi akanki, don Allah karki azabtar dani da abinda na aikata miki nasan nayi laifi amma don Allah karki rike hakan a matsayin abinda zai zame miki daukar fansa." Tashi nayi daga cinyar shi, zan bar gurin yana kallon yadda nake tafiya a hankali, sai yaji ta bashi tausayi. A zafaffe ya mike tare da bin bayan ta, jin sautin takun shi yasa ta tsayawa cak. Tana me jin kwalla na zuba mata. Yana tawowa ya rungume ta da dukka zuciyar shi, wani irin yanayi suka tsinci kansu, suna masifar kaunar junan su, amma zunzurutun taurin zuciya yasa dukkan su, azabtar da junar su. Juyar da ita yayi. "Kiyi hakuri mana?" "Ba hakuri ne ban iya ba, hakuri ce ba zan yi ba" Murmushi yayi sannan yace min. "Toh hakkina fa?" A razane na kalle shi, kwalla na zubo min, bakina yana rawa nace Mishi. "Mehran! Har yanzu ban warke ba, kuma gurin na..." Rufe min baki yayi da nashi bakin tare da dauka na, yana min wata irin sumbatar da tasa ni jin tsigar jikina ya mike Yarrrr, hannuna na kai keyar shi tare da cusa shi cikin gashin kanshi, a hankali ya dawo damu saman kujeran da ya bari, zama yayi tare da janye fuskana yana kallon yadda na rufe idanuna, hura min iskar bakin shi yayi tare da kallon yadda na sauke a jiyar zuciya. Hannun shi ya saka tare da cire min rigar jikina. Rungume kanshi nayi tare da sauke wata irin nishi, wanda ya samu asali daga cire min nono da yayi ne. Shafa su yayi sannan yace min. "Ikram Kinga yadda nonuwar nan suka kuma cika? Gaskiya ni dan baiwa ne." Lumshe idanuna nayi, tare da kai kana kafadar shi, shafa bayana yayi tare da cewa. "Kiyi hakuri kinji" "Babu batun nayi hakuri, gaskiya dan na cutu." A hankali na sauka a kan cinyar shi na gyara jikina, sannan na bar shi a zaune, sai da na koma dakin na Fahimci yadda na tsira a hannun shi, shigowa yayi tare da kallon yadda nake cire kayana, shima cire nashi yayi yana me takowa inda nake. "Mehran! Don Allah karka dame ni, don Allah ka kyale Ni bani da lafiya." "Ikram ina zan kai bukatar da ta dame Ni? Me yasa kike da taurin kai ne? Toh ki bani hakkina yau kusan sati biyu bana nan, na dawo hakkina sai kowa ya jimu." Kuka na fasa mishi tare da yarfe hannuna, ina girgiza kai na. "Wallahi ba zan iya ba, na gaji ciwo gurin zai min. Na ranar da kai yi ma, ba warke ba." Fisgo ni yayi tare da turani kan gadon ya hauro, ban san lokacin da nayi tsalle zan sauka ya rike kafana. Murmushi yayi sannan yace min. "Wallahi idan baki dawo nayi kome cikin nutsuwa da sallama ba, toh ba shakka idan na saka karfina sai na yaga ki gida biyu na ajiye wallahi tallahi." Kuka ne ya kuma kwace min na kuma yunkurowa zan sauka, kawai ya fisgo ni tare da kamo nono na. "Baki jin magana ko? Bari nayi maganin wadannan marasa kunyar abinda suke auna min rashin mutunci." Mirza min yayi ban san lokacin da nace mishi. "Wallahi zan baka hadin kai" Na fada a raunane, dawowa nayi tare da komawa saman gadon na dunkule guri daya, dariya na bashi, dan mugunta, kallona yayi tare da haurawa saman gadon, sannan yayi min rumfa da kirjin shi, a hankali ya shiga tab'a ni, musamman inda yayi mishi albarka yake saka mishi sosai, kafin kace kwabo ya gama hauka ta min lissafi. Ni da kaina na taimaka mishi. Sai da yazo inda na birkice mishi da kuka ne, ya rufe min baki na da nashi, a hankali yake tafiyar dani, yana bina cikin nutsuwa da adalci, yana kuma kara rarrashina, tare da nuna min sakamakon yadda yake son rayuwa dani, a hankali yake tafiyar da kome, sai da yazo masaraffan ne, kuma na sake wani irin kuka wanda Ni kai na nasan Abu daya ne zafi da kuma shaukin Mehran. "Allah yayi miki albarka gaskiya wannan gurin ba karamin dad'i yake dashi ba, Allah Nagode maka da ka bani damar samun guri me dad'i kamar me? Wai... Wai... Wai, wayyo ikram tsaya kar naji miki ciwo, Kinga tsaya na sha sandar arziki, sandan dad'i me zane yan matan Mehran, wayyo Allah na. Na shiga wallahi karki yi kuka karki yi ihu, Ni daya ne akanki. Ashe rashin kunyar nan da hujja, bude min na shiga. Yarinyar arziki, Sannun Jarumar mata, wai.. wai... Wai ... Me suka saka a gurin nan ne, wannan gurin kowa yake hari. Allah na gode da ka bani gurin Ni daya." Ya faɗa tare da shiga jikina, hawaye ne ya sauko min, tare da sake kara, shima kuma ya sake. Yana faɗin. "Sannun yar Aljannah. Wai kaji dan karamin guri sai dadin bala'i. Na baki kai na, na baki Fudail ke Ni har masarautan na baki." Ya fada yana auna min lissafi, kuka ne ban yi ba shar shar amma kuma na zubda kwalla. Sam babu dad'i shi daya yake kidan shi da rawan shi. Yadda yake wani irin nishi ya sani fahimtar kome ya kawo inda yake bukata, a hankali ya kwanta a jikina yana sumbatar bakina. Kallona yayi tare da shafa fuskata, yana murmushi. "Ikram Nagode!" Ya faɗa min ko kallon shi banyi ba, da taimakon shi, nayi wanka tare da gyara jikina sannan nazo na gyara gadon, jikina a mace. Shafa kaina yayi tare da cewa. "Ina zuwa." Ya tafita, kwanciya nayi abuna barci me nauyi yayi gaba dani. Na gaji ainun, dan haka na jima ina barci, ina farkawa na kuma shiga ruwan zafi nayi wanka, sannan na fito daga ban ɗakin, zama nayi na b'ata lokaci ina tsara kwalliya, ina gamawa na saka wata doguwar riga, sannan na yafa mayafi na daidaita nutsuwata, kafin na shiga cikin kitchen na dauki kayan abincin da aka shirya min na nufi gidan Anneh, tunda na shiga na ganshi a zaune yana me kaskantar da kanshi, d'agowa yayi tare da mika min hannun, kin zuwa gurin shi nayi sannan na wuce gurin Anneh, na zauna. "Ikram Sannun ya jikinki? Yanzun yake gaya min ashe baki ji dadi ba kwanakin baya!" Kunya yasani kasa d'ago kai na, dariya yake min, sannan yace mata. "Anneh ni tsoro nake ji, domin sun kafe akan lallai Ikram bata dace da Sultanah ba, sai dai na bawa daya daga cikin matan gidan." Shafa kan shi tayi sannan tace mishi. "Eh suna ganin matukar suka bawa Ikram akwai yiwuwar samun dukkanin mulkin ka, sannan zata iya lalata musu goben sune, dan haka kayi ƙoƙarin gano inda Abrad yaƙe, ka kashe shi." Da sauri na d'ago kai na, ina kallon ta. Zan mata magana naji an busa, alamar ana shirin yaki, mik'ewa yayi na rike hannun shi. "Ina zaka Mehran!" Durkusawa yayi tare da kallon yadda na b'ata fuska, "Alamar yaki yana tun karo daular mu ce, bari naje masarautan na dawo zan zo daukar ki, karki yarda wani yazo yace Ni na aiko shi." Gyada mishi kai nayi, har zai tafi na kuma mik'ewa na rike hannun shi. "Mehran ina jin tsoro" Saka hannun shi yayi tare da rungume ni, yana faɗin. "Mehran ba zai tab'a barin ki ba, ki kwantar da hankalinki,zan dawo gare ki." Shafa kaina yayi tare da sumbatar goshina, sannan yayi min sallama, haka na koma jikin Anneh na kwanta, ina jin wani irin yanayi a raina, shafa kai na take, tare da cewa. "Zai dawo Insha Allah." *** "Toh ga sakon Abrad sun amshe manyan biranen mu, sannan sun kashe mutane babu adadi. Abu daya yake so ka sake mishi Ikram, ko kuma ayi ta gwabza yaki." Magatakardan. Lashe baki yayi sannan ya kalli manyan mutanen da suke fadar yace musu. "Ba zan iya sake mishi mata na ba?" "Amma yace akwai sirrin da yake tsakanin su, wani irin sirri ne?" Rintsa idanun shi yayi tare da kallon su, sannan yace. "Ban sani ba, amma babu makawa zan shiga yaƙin a shirya dakarun" ya fadi haka yana mik'ewa tare da barin fadan. Gidan Anneh ya tafi, yana shiga yaji kamshin gidan ya sauya, abinci ya samu dan haka ya zauna ya fara ci yana raba idanun shi, fitowa tayi ya zuba mata ido. "Anneh ina son wancan mahaukaciyar?" "Toh ai kuwa ba zan baka ita ba" "Don Allah ki rufa min asiri" "Ai kasan da haka" "Bazan kuma ba" Har na isa gurin su, zama nayi tare da fara cin abincin ya'yan itacce ne ma, na fara ci muna hira. Ina gamawa nasha romon kazar da tayi min da kayan kamshi, ina gamawa na koma jikinta ina faɗin. "Anneh anan zan kwana." "Anneh nima anan zan kwana." "Toh wallahi baku isa ba," Haka muka yi ta hira, da zamu tafi muka mata sallama, wani abu ta bani tana kallona tace min. "Har yanzun tafiyarki bai daidaita ba, amma gashi kina sakawa a ruwan zafi kina tsuguno akai, sannan Insha Allah zaki ji dadin jikinki" Haka ta bani abubuwan gyaran jiki. Muna fita na kalle shi cogewa nai a kofar gidan, juyawa yayi tare da kallona, a hankali ya tako, sannan ya juya min baya na hau, muka fara tafiya ina cewa. "Mehran! Ina son." Cak ya tsaya tare da kallona. "Kina sona" "A'a ni bana son ka!" Na maida kaina izuwa kunnen shi ina lasa. "Ikram kina kunna min wuta!" "Haka nake so, nima ban san me naci a gurin Anneh ba nake jin wani abu." Dakyar muka isa dakin shi, bai sauke Ni ba sai juyo sani da yayi tare da jingina ni da bango, kwaɓe min riga yayi ya cusa kanshi a tsakanin wuyana ina rike da kanshi, murza juna muke tare da cinye bakin mu, kamar zamu haukata kanmu, a babban falon shi, muka shiga harkan arziki, lokacin da da ya shiga a tare muka saka ihu tare da ajiyar zuciya, sannan muka Cigaba daga inda muka tsaya. "Zaki kashe ni, yarinyar nan zaki kashe ni da dadin ki? Da kin san yadda kike ba zaki na kuskuren kara min kwarin gwiwa ba, kai wannan yar arzikin irin albarka. Allah ya jikan Ammyn mu da Abban mu. Da suka haifa min kogin dad'i." Haka ya gama sannan ya kwanta tare da saka kaina a kirjin shi, muka kwanta. Muna sauke numfashin gajiya. "Amma Anneh ta baki wani abu, naji kin kara min dad'i ne!" "Mehran baka da kunya, yadda kake fadan dadin nan kunya yake sani." Shafa nonuwana yayi tare da cewa. "Kece sai a hankali, sai kara girma kike kamar bake ba, wallahi Nagode sosai da kare min mutuncina da kika yi." Haka muka kwanta a gurin, tare da hira har barci, yayi gaba damu. Da asuba ya tashe ni ya tafi masalaci, bayan yayi wanka nima wankan na shiga yana dawowa ya hauro gadon. Zare idanu nayi domin na Fahimci ba gajiya yake ba, nace mishi. "Don Allah." Harshen shi naji cikin nawa, hannuna da na kai zan ture shi ya rike gam, yana me goga min kirjin shi a saman nawa, sai wani jijjiga suke, idan yayi sama dasu. Hannun mu yana sarkafe da juna, kamar zanyi kuka. Amma yadda nake jin shi haka zan yi hakuri da shi. Kasa magana nayi ina jin dumin kwallanna zuba min, wallahi gabana kamar zai tsage, haka ya shiga yana nishin dadi, har ya samu ya tabo ni, hawaye ne ya shiga zubo min ina jin babu dad'i, sai da ya kai ni makura sannan ya samu nutsuwa, yana kallon yadda nake kuka sosai, shafa bayana yayi tare da cewa. "Kiyi hakuri haka Allah yayi ni, wallahi tun daga ranar da na kusance ki, ban kuma jin dadi wata Ya mace ba sai ke, kiyi hakuri dani, idan kika yi kuka kamar kin gaji dani ne." "Mehran gurin ne har yau bai saba ba, idan na cigaba da abinda kake so zan iya illata kaina, dan Allah kayi ƙoƙarin kana gayyatar Kwarkwarorin ka, wallahi ina jin wahala." Dariya yayi sannan yace min. "Shikenan..... [5/26, 9:26 AM] Mehkram1256: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat Book3 _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayen Mu_ 19... Wato abinda na lura Mehran ya zamu abinda yake so, shi yasa yake iya makale mishi sauran Kwarkwarorin baya musu haka, sannan ya kuma damu da al'amarin Ikram, wannan yakin da zai yi dan ita zai tafi, dan haka ya lallabata sai da tayi barci sannan ya samu ya sauka a gadon. Ya shiga wanka, ya gyara jikin shi kafin ya fito, kallonta yayi tana ta barci. Tare da ajiyar zuciya. Yarinya tana da hakuri amma akan hakkin shi sakata kuka yake, fatan shi daya Allah yasa ta sami ciki. Wannan shind addu'o'in shi a kullum, haka ya tafi ya barta bayan ya sumbaci bakinta yana me shafa kwantaccen gashin goshinta, sannan yayi mata addu'o'in kafin yayi tafiyar shi. ---- Bayan na farka, ake gaya min Mehran sun tafi yaki, nayi kuka sosai kafin na ji a raina, ina mishi fatan nasara, tun daga ranar babu wani abinda nake sai Azumi. Tare da Addu'a Allah ya bashi nasara, Azizatul da Jasrah tare da Sakeenatu binti Abu Waqqas, sun hade kan su, sai Sawda ce muke gaisawa, itama ba kullum muke haduwa ba, amma ni ina ƙoƙarin mun fahimci junar mu da sauran su. Sai dai su ba haka bane a ransu babban burin su, mu sami sabani yadda zasu kai karana fada a hukuntani, ana haka wata rana Jasrah ta fito daga d'akinta. Zata wuce ina kauce mata ya bangaje ni, faduwa tayi bata jima ba ta saka ihu, dole aka suka zo aka kai ta d'akinta kafin kace kwabo wai cikin wata biyar ya zube. Gashi Mehran baya nan dan haka Sultanah Hoyam tazo da kanta, ta saka aka kai ni gidan horo, tare da haɗawa har da su Izmah. ---- Sun sami nasarar kwato yankuna Shi, amma Abrad ya gudu dan haka suka dawo gida, bayan sun gama bawa kowani yanki karin mulki, sannan suka dawo. Tunda suka shiga cikin masarautan yaji wani irin yanayi mara daɗi, yana isa shashin sa domin dawowa dare suka yi, ya fahimci akwai matsala basu san zai dawo ba. "Ina Ikram?" Shiru suka yi a tsorace, suka kuma kallon shi. "Ai yau kwana biyar tana can gidan horo darul azab," inji Sawda da take fitowa. Gyada mata kai yayi tare da cewa. "Muje ki rakani" Haka suka tafi, tare har karkashin kasa, suna shiga suka sami Izmah da Nimra suna kuka. Kamar ya fadi haka yake ji, "Me ya faru da ita?" "Yau ne Sultanah Hoyam tazo ta dake ta, har a cikin ta, shine take ta zubda jini!" Kura mata ido yayi kwalla na zuba daga ita, shima abin da yake zuba kenan. "Taya aka yi ta dake ta a cikin?" Ya tambaye su a raunane, "D'azun ne da ta shigo shine Ikram tace mata tana son don Allah a kirawo mata Anneh sabida bata da lafiya,kuma tunda aka kawo mu bata da lafiya, take gaya mata cikin ta yana yawan ciwo, shine ta tambayeta yaushe rabonta da haila, shine tace yau sati biyar kenan, shine ta rufe ta da duka har da naushinta a c..." Daukarta yayi tare da fita daga gidan, gidan Anneh shi ya wuce da ita, yana kaita ya kwantar da ita, aka shiga bata taimako bayan an kira masu kula da su, har goshin asuba, sannan gidan cikin ya fad'i. Ana samun ya fita suka bata magani tare da musu sallama, zama yayi a dakin Anneh yayi kuka ya kuma yin kuka sabida baki daya ya ji tashin hankalin a ranshi. Kai yadda ya rasa cikin jikinta jin shi yake kamar zai mutu, haka Anneh tayi mishi nasiha tare da cewa. "Kaje ta farka nayi mata wanka tana kukan ciwon mara, idan ka shiga ka zauna da ita," Masalaci ya wuce tare da gabatar da sallah asuba sannan ya gaya musu Ikram yayi bari, tausayi ya basu..sannan suka mishi fatan Alkhairi, yana dawowa ya shigo dakin ina rike da cikina. Takowa yayi har bakin gadon. Haurawa yayi tare, da rungumo ni. Yana shafa bayana. "Mehran ciwo!" Shafa goshina yayi sannan yace min. "Kiyi hakuri! Zai daina" "Mehran yarinyar mu aka zubar ko?" "Allah zai bamu wani" "Mehran nafi son wancan, Ni ka dawo min da yarinya na" na saka mishi rigima sosai, shima kuma ya rasa yadda zai yi dani. "Insha ALLAH, Ubangiji zai bamu wani kinji, karki damu."ranar haka na wuni ina mishi rigima sosai. Har dare sannan ya barni a gurin ta, Yana shiga gidan bai ce musu kome ba, sai ya wuce tunatar shi, kallon juna suka yi. Haka ya kwana shi daya, washi gari ya tafi fada, ana nan aka kuma buga tambura alamar yaƙi. Haka yazo tare da zama yana kallona. "Ikram zan tafi yaki" "Mehran!" Na kira sunan shi idanuna na cika da kwalla, "Duk sabida me yasa wannan yaƙin?" "Sabida ke, sabida ke ake shirya min makarkashiya. Basu son ki amshi ragamar Sultanah." "Taya aka yi kasancewa." "Zan dawo ki kula min da kanki." Kwalla ne ya cika min idanuna, tabbas akwai matsala. Haka ya tafi ya barni ina kuka, bayan ya tafi Sultanah Fazilatul nisa, ta saka Ni a gaba da gyara irin wanda zai saka ka jin kamar ka kai kanka gurin mijinka, wannan karon sai da yayi wata daya sannan ya dawo, ranar da ya dawo ne ya dauke ni muka bar Samaind zuwa Makka, a can naga tarin kauna da soyayya, sai da naji duniyar babu wata wacce ta fini sa'ar miji a duniya, sai da muka yi umra sannan muka wuce sudan, kallon shi nake cikin farin ciki. Kwanan mu biyar a jirgin ruwa muka isa, daga nan muna shiga keken shanu sai gezira, lokacin da muka isa garin ya zama alkarya, na rasa gane inda zan nufa. Kallon wani yayi yace mishi. "Gidan su Noman Anwarulkharim,zaka kai mu." Haka mutumin yayi mana jagora, har gidan su, sai lokacin na gane gari, gabatar da kan shi yayi sannan ya nuna mishi Ni. Mahaifin noman yayi kuka sosai, sannan ya saka aka kira mutanen garin aka mana Barka da zuwa, anan aka fara min gaisuwar mutuwar Airan,sai lokacin kuka yazo min, rike hannuna yayi tare da lumshe idanun shi. Bayan mun huta muka nufi gidan mu, wanda ya zama na matar baban mu, tana nan ta haukace tana gani na takama ihuna kirana,ban bi takan ta ba, na shige tsohon dakin mu,na shiga gyara mishi,ko ina sannan aka. Kawo mana abinci daga ko ina zinari na bada aka kawo mana kayan shimfid'a, kallona yake, ina fitowa na kira wasu suka fitar min da matar baban mu daga gidan, zai magana nace mishi. "Karka ce min kome," haka na gyara gidan, murmushi yayi sannan ya zauna yana cin abincin da na kawo mishi, muna ci muna hira, daga nan muka kalli juna kayan yaki ya bani bayan na sauya kaya na muka fita lokacin dare ya fara yi domin sai da muka yi sallah sannan muna fito, babu mutane kowa ya shiga gidan shi. Sabida samarin da suke kawo musu hari, muna isa bakin kogi ya sani na shiga ruwan muna fara wanka, wanda kusan duk soyayya ce kawai muke yi, muna cikin haka sai gasu. "Ranar da aka kashe Mahaifiyar ki, fyade suka mata, ki tattara fansanki ki dauka akan su Aamaan Abdus Samad Mehran na biyu yana bayan ki." Daukar gatarin shi nayi tare da nufar su, na shiga musu wani irin sara tare da kuka ina kashe su, sai da yaga zasu rufa min ya dauki nashi, a tare muka nufe su, bamu kyale su ba, sai da muka ga bayan su. Amai ne ya zo min sakamakon karnin jinin da ya ke jikina, daukana yayi zuwa cikin ruwa ya wanke min jiki. Ikram ba dai wani cikin ne dake ba?" "Ban sani ba Mehran" na gaya mishi haka na kwana da zazzaɓi bayan mun dawo gidan, washi gari ya faɗawa Baban Noman mune muka yi aikin,. Sannan ya saka ka kawo min me magani ta dubani. Murmushi tayi sannan tace mishi. "INSHA Allah muna saka ran Zuwan Yarima ko Gimbiyar kasar SAMAIND." " A'a Gimbiya muke so ko Ikram" Kunya yasani sunkuyar da kaina, haka ya fita shi kuma ya haura shimfid'ar tare da daura akan shi a cinyata, rungume kan nayi sannan na sumbace shi, haka muka kasance a gezira har na sati biyu sabida jikina. Ina jin sauki muka wuce Askandariya. Anan naga gata da kauna, har ina Mantawa da Mehran, amma ina shiga hannun shi nake tunawa dashi, Mehran jaraba. Ko ya muka hadu sai ya zungure ni, kuma ki a jikin shi. Yau ma daura ni yayi akan cinyar shi, tare da aika min sakon shi,. Zaro idanu nayi tare da jan numfashina. "Kiyi hakuri! Wannan yar albarka ne ta kara miki lafiyan dadi." Make bakin shi nayi domin na Fahimci kunya bata wadacce shi ba, haka muka gama kwanakin mu, sannan muka wuce maroko. Murna kamar zasu cinye ni. Musamman yadda Mehran ya makale sai dai mu koma masaukin shi. Sultan Mu'allim sai da ya girmama kaunar da bamu b'oyewa a gaban kowa, kwana nayi a cikin gidan sarauta, aikuwa washi gari Mehran ya birkice min dai da nake ya zungure ni, sannan ya samu nutsuwa, kamar mayye. Rayuwar mu cike yake da farin ciki daga nan sati Daya muka musu aka kuma hadani da wasu bayin, sannan muka dawo Samaind lokacin cikina wata huɗu. Koda muka dawo babu wanda yasan dashi sai ma, sauke Sultanah Hoyam da yayi, zai daurani aka fara samun matsala. Dan haka nace mishi. "Mehran! Ni mulkin nan baya gabana." " Na sani!" Ya faɗa tare da juya min baya. Fushi yayi. Kwantar da kaina nayi. "Kiyi hakuri" Juyowa yayi tare da shafa fuskana, "Ya wuce," Washi gari aka sami sako daga Abrad, abinda ya fahimta abrad na cikin masarautan shi. Dan haka ranar da ya koma gida yace min. "Zan tafi." Shafa kan shi nayi, shi kuma ya sumbaci cikin, sannan ya fita.. ---- Yawo suka yi a cikin garin SAMAIND kafin suka sami wani gidan gona da yake, sannan Suka fuskanci juna. Murmushi suka yiwa juna sannan Mehran yace mishi. "Yau kam babu gudu babu tsira, naso na maka adalci amma baka lura da haka ba, Na so nisanta ka da rayuwar mu amma baka fahimci haka ba, Abrad Mata ta tun tana budurwa kake bibiyarta haka bai ishe ka ba sai da ka cusa min zarginta a zuciyata, bayan kasan karya kake babu namijin da ya ratsa tsakanin ta." Shiru Mehran yayi sannan ya cigaba da cewa. "Ba zan tab'a yarda ka lalata min rayuwa ba, sabida wannan shine damar da nake dashi na bata Sultanah, amma kake yunkurin tozartani, Ikram kusan Y'a ce maka. Amma dattin dake zuciyar ka Ya hana ka fahimtar kome. Zan kashe ka, matar da ka aura mahaifiyar Ikram ce ta sha nono ta bar mata, yau idan mahaifin Ikram yayi maka ko akan Yarka ta zaka ji? Dan haka idan da gaske kaunar Ikram kake ka sadaukar da rayuwar ka domin ita" Yarda takobin hannun shi yayi tare da durkusawa a gaban Mehran, yana kuka. Badan kome ba sai dan tunan da yayi da Yarshi shi da Mehran ya kawo mata misali, kuka yake tare da cewa. "Mehran waye zai kula min da Y'ata? Don Allah karka kashe ni, nasan nai laifi amma So ne silar kome don Allah" "Na baka damar haka a rayuwar ka, kuma na baka damar da fahimtar haka, amma kayi kunnen uwar shegu dani." Dan haka ya tako gaban Abrad ya d'aga shi, tare da zaro wuka a rigar shi yayi ta soka mishi. Sai da yaji yadda Abrad din ya rungume shi. "Mehran! Me yasa?" "Kishi ne a tsakanin zubda jini! Nayi kokarin ganin kauce maka amma kaki, ko a lahira ka kalli Ikram sai na roki Alfarmar Ubangiji ya bani damar kashe ka. Balle kuma a duniya da nake kokarin tsaya mata zaka hanani? Ai baka iska ba, Sultanah Bilqisul Ikram Mustapha Mehran. Shine sunan da nake son ganin yana fita a bakin al'ummar SAMAIND." [5/26, 2:56 PM] Mehkram1256: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat Book3 _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayen Mu_ 20... Hawaye ne ya zuba daga idanun su, lokaci guda sabida yadda suka kasance, d'ago kai Abrad yayi jini na zuba ta hancin shi da bakin shi. "Don Allah duk laifin da Azizatul Nissah zata maka ka dubi girman soyayyar ka da Ikram ka, kayi hakuri. Kar...ka...cu...tar.." Daga nan ya koma jikin Mehran ya kwanta, numfashinsa yana kaiwa da komowa, hawaye ne ya zubo mishi, ya kuma jan wukar ya caka mishi. "Kana son Ikram da yawa, ni kuma ina tsanar duk wanda zai sota, koda kuwa haka yana nufin zan bada rayuwata ne!" Kwalla ne ya zubo mishi tare da rike Mehran, har rai yayi halin shi, sake shi yayi a hankali tare da juyawa ya bar gidan, ya samu su Fudail suna jiran shi, kallon juna suka yi. "Ka ɗauke shi a binne shi. Tarihin shi ya ƙare." Haka suka dawo gidan, ina kwance ya kalle ni tare da cewa. "Ki shirya gobe za a baki matsayin ki." Kallon shi nayi tare da jin tausayin shi, kafin nace mishi. "Toh nagode" Haka ya shige yayi wanka tare da komawa dakin shi ya kwanta, a daren kasa runtsawa yayi yana kukan zuci. Zama nayi ina nazarin abinda muka tattauna da Anneh akan makomar mulkin kasar, da ake nazarin bani, da kuma abinda ta gaya min. Sai da na zubda hawayen dan tausayinta. Da asuba na riga shi tashi, dan haka ina gamawa na nufi dakin shi, na sami dakin da duhu Sosai. A hankali na shiga na same shi yana kuka kamar karamin yaro, a hankali na isa gare shi. Daura kanshi nayi akan cikina, tare da rungumo shi. Nima hawayen na zuba min. Duk abinda Mehran yake sabida ni yake, kuma duk wani matakin da zai dauka duk sabida ni ce, wai wacce irin kauna ce haka da ya gwammaci ya sadaukar da kome na shi sabida ni? Rungume ni yayi yana cewa. "Duniya abun tsoro ne, Ikram karki juya min baya." "Ina tare dakai har karshen rayuwata." Haka muka rungume juna muna kuka, kafin na taimaka mishi akan ya shiga yayi wanka, yana fitowa muka shirya kallona yake, yana murmushi yayi sannan ya ce mata. "Yau da jiya ban duba yallabai na ba!" Tura baki nayi tare da dauke kai na, shafa cikin yayi tare da cewa. "Don Allah" hannuna na zuba a kafad'ar shi. Haka muka haura gadon, daga nan muka cimma matsaya akan ra'ayin mu, kuma ya biyar dani duk da girman cikina, sai da ya sami nutsuwa sani sannan ya kyale ni. Bayan na samu nayi wanka dashi muka shirya. "Wannan mulkin yaki zaki taya ni, kiyi kokarin ganin kin labtar da kowa imma Ni ne, karki raga min. Kiyi hakuri sosai." Haka ya gaya min haka muka fita har inda aka bani mulkin, tare da gabatar dani. Nasha kuka lokacin da aka saka min kambun. "Ni Bilqisul Ikram Mustapha Mu'allim, nayi alƙawarin rike masarautan nan da gaskiya da Amana, zan tsaya akan aikina kuma xan bawa Al'ummar Samaind kariya, sannan zanyi kokarin kamanta adalci da gaskiya. Sannan". Juyawa nayi tare da kallon Mehran. Sannan na cigaba da cewa. "Zan bawa mijina Sultan Aamaan Abdus Samad Mehran, goyan bayan dari bisa dari! Allah ya tayani riko" Na fada hawaye na zuba min, tsayawar da nayi sai da kafaffuna duka kumbura. Kuka ne ya kwace min, haka ya tako tare da rike Ni, muka koma gurin zama, nan aka shiga shagali da bukukuwa, kafin muka koma cikin gidan, a ranar Anneh ta dawo, Daga nan aka shiga turo min gaisuwa da manyan biranen ana gabatar min da sarakuna, Mehran da Anneh suna gaya min abinda zan gaya musu. ---- a hankali kome ya cigaba da tafiya ga shi cikina yana girma dan ya shiga wata shida,ga Sultan Mehran yana tsaye a gefena. A hankali na fara aikina, inda na bankad'o kashe Sultan Abdus Samad. Ana fara wannan binciken, kawai aka sami labarin an kawo maai hari, a wasu kauyukan da suke yankin Samaind, dan haka suka shirya tafiya har da shi Mehran, suka tafi. Zan iya cewa tunda aka fara binciken sai ya zamana na fara. Samun matsala daga yawan kawo min guba a cikin abincin. Ko a ruwan wanka na, yau ma zan yi wanka aka kawo min ruwan kallon ruwan nayi domin sai an kawo min na duba tukun zan shiga wanka. Kallon ruwan sannan na kalli bayin da suka haɗa ruwan. "Gubar furen gulsana, Sultanah" Kallon su nayi sannan nace musu. "Wacece take saka min guba?" Na tambaye su. "Wallahi bamu sani ba" "Nimrah kisaka Sarwat yayi ta dukar su." Haka aka fita dasu, ina kallon ruwan, na koma na hada da kaina, nayi wankan ina zargin Hoyam da Azizatul Nissah, dan haka ina gama wanka na shirya tare da nufar shashin Sultanah Hoyam. Tana gani na ta fara kokarin tashi zaune. "Zauna Sultanah!" Tace min. Zama nayi ina kallonta, sannan nace mata. "Barka da hutawa" "Barka dai Sultanah!" Shiru ne ya ratsa tsakanin mu, sannan nace mata. "Kina kokarin ganin bayana ko? Ban san meye nayi miki ba? Daga guba a cikin abinci sai a cikin ruwan wanka na" "Idan da zan kashe ki, tuni na shafe tarihinki, dan haka bani da lokacin ki." "Hoyam kenan, kin san lokacin da Sultan Abdus Samad ya rasu an kama Sultanah Fazilatul nisa ce rike da wukar ko? Wannan zoben da aka samu a jikin wukar fa? Sannan a ranar kafin mutuwar shi Sultanah Hoyam ta shiga dakin tare da wasu mutane uku suwaye su? Ni nasan su, amma lokacin da ake hada baki da Abrad nasan kome, kawai nayi shiru ne," "Ikram! Kina tono masifa, wanda baki san farkon shi ba balle karshen shi. Abinda kike aikatawa zai janyo zubda jini!" Murmushi nayi domin na Fahimci abunda nake bukata, dan haka nace mata. "Karki damu, idan na fito da dalilin da yasa ake mu'amala da Darakshan duniya zata Fahimta." Daga na mike a hankali, nace mata. "Na barki Lafiya" Nayi tafiya ta, abuna kamar zata yi hauka bata san kunnata nayi ba, sai gata zata gidan Amir Hood. --- Zama nayi tare da tsare Mahlika da ido kafin nace mata. " Haka yayi amma ki sani ba zan tab'a yarda da munafunci ba, dan zan dauki mataki akan ki." Daga haka na sallame ta. Haka na cigaba da kuma da Masarautan har Mehran ya dawo, sannan muka shiga binciken abinda ya faru. *** "Sultan MEHRAN har yanzun ban ji labarin Dan uwana ba" ta faɗa tana zubda hawayen bakin ciki. "Me kike son na miki? Ko na boye shi ne?" "Amma dai ko yayya ne zaka saka a nimo mishi." "Bani da lokacin akan haka" "Amma akan wancan munafukai kana da lokacinta ko?" Zuba hannu yayi yana kallon fuskarta tare da murmushi sannan yace mata. "Zaki iya fita ko yayya" Haka ta saka kai tafiya ina, sannan na shigo dakin.. a hankali da katon cikina tare da kallon shi. "Ya naga tana kuka bayan ta fita?" "Niman magana take, kuma bani da lokacin ta, akan mutumin da na goge tarihin shi." Takowa nayi a nutse ina kallon shi. "Mehran baka gaya mata gaskiya bane?" "Eh ban gaya mata ba" Zama nayi muka Cigaba da tattaunawa, ina bashi labarin binciken da nayi da kuma irin abinda ya faru a cikin masarautan, rike hannuna yayi tare da cewa. "Ina son kiyi aiki. Da zaki bawa kowa mamaki amma kuma yallabai na ya hanaki sakata nima ba jin dadin rayuwa nake ba tunda wannan abun ya fito" Zama nayi tare da kallon shi, sosai na kwanta a jikin shi muna hira, kafin nan ya shiga kawo min Yaren da yasan na kware gurin shi. Sosai muka gurji juna, kafin na kwanta a hankali ina kallon shi nace mishi. "Jasrah tana tare da kai ne sabida ka kashe an kashe mata mahaifi, Azizatul Nissah ce ban san dalilin ta ba,. amma nasan dan ture ni suke tare da kai, idan zaka tuna Jennah lokacin da aka harbeka da guba, itama tazo daukar fansa ne lokacin. Darda yana tare da Sarki Abrad, ya bani horon yaki kafin kai, sai Sakeenatu binti Abu Waqqas, ta haka zo ne sabida zunzurutun tana sonka amma munafuka ce, Mahlika tana nan ne sabida Sultanah Fazilatul, tazo daukar fansa. Sai Hoyam da Amir Hood,wanda suke juya kansu kamar masu gaskiya." "Ikram yaushe kika sami wannan bayyan? Domin na jima ina niman hanyar da zan warware rikicin masarautan nan. Ban samu ba gashi lokaci guda kin fitar da komi." Ya tambaye ni tare da kallon na. Murmushi nayi sannan nace mishi. "Na jima ina zargin haka, amma abin mamaki anan shine wani bayani da na samu akan Azizatul Nissah ya daure min kai, meye laifinka da yazo domin Ni? Dan haka ka zuba ido yadda kome zai wuce, Sawda kuwa tana da masoyinta, domin kuwa sane da ta gaya maka tana da wanda take so shi yasa baka tab'a tunanin mu'amalantar ta ba.". "Eh haka ne, shi yasa na rubuta na ajiye bata cikin Kwarkwarorina, dan haka ki sallame ta taje ta auri wanda take so. Sannan Ina niman auren Nimrah da Fudail, itama wannan yar wadan na tura a dauko mata SAURAYINTA dan haka Nagode sosai." "Mehran kayi hakuri ka rufe idanunka zan yi aiki ne na jahadi, idan kana kallona ba zan iya ba, Mehran karka saka ido akan abinda zanyi don Allah." .rike hannuna yayi sannan yace min. "Ba zan saka ba, zan Barki kiyi aikin da kika fara." Dan haka muka mike tare da shiga wanka, bayan mun fito na nufi d'akina, na shiga tattara bayanai, nasan Unaiza da Rubina suke kawo min sakon wasika daga Abrad dan haka ban kula su ba, abinda nake so bana son na fara dasu. Washi gari. Muna fada Anneh ta shigo tare da zuɓewa a gaban jama'a, tana faɗin. "Sultanah Bilqisul Ikram, na kawo kaina ne abisa laifin kashe Sultan Abdus Samad." Kallon juna muka yi, tare da kallon mutanen fadan. Amma kuma me.yasa Anneh tayi haka, bayan mun gama magana zata bijiro da wannan shirmen, kallon Mehran nayi nace mishi. "Amma kuma SULTAN Mehran." D'aga min hannu yayi tare da nuna min mutanen gurin da ido, hawaye ne ya cika min idanuna. "Tunda ta amshi laifinta a hukuntatta mana?" Inji Amir Hood, "SULTAN Mehran, ina rokon a bar min wannan lamari a hannuna nan da sati daya Insha Allah zan fidda kome cikin nutsuwa da adalci." "Ke Ikram kin fimu sanin ya kamata ne?" Ya faɗa min mik'ewa nayi sannan nace mishi. "Adalci zan yiwa Uwar da ta rasa D'anta na shekaru talatin da shida. Adalci zan nimawa dan da aka rabashi da uwar shi na tsawon shekaru, adalci zan nimawa matar da aka rabata da iyayenta na tsawon shekaru hamsin, adalci zan nimawa Matar da aka kashe mata mijinta. Adalci zan nimawa dan da Yarasa Ubanshi. Adalci zan nimawa Dan da aka lalata mishi rayuwar shi. Idan Sultan Mehran ya bani Damar haka zan duba fiye da haka ma." Na fada ina kallon su, tare da murmushi. Shiru fadan tayi baka jin kome sai numfashin mutane, kallona Mehran yayi sannan ya sunkuyar da kanshi, tabbas zai bada goyon bayan shi, kuma zai tsaya mata koda haka zai iya zama karshen rayuwar shi. Tabbas Ikram tayi abinda yake ganin ba zai tab'a...... [5/27, 9:27 AM] Mehkram1256: +2347035133148 Zahrah Adda Ramlat Book3 _Wannan littafin na kuɗi ne! Idan baka siya ba, karka karanta! Idan ka karanta kuma ka fadi ALKHAIRI ko kayi shiru Allah ya jikan Iyayen Mu_ 21... "Sannan kuma Sultan Mehran ina rokon a min alfarman akan bincike dalilin da yasa Hoyam ta dake ni sai da cikin da na sha wuyar shi ya Zube, iya haka ma ya ishe ni." Na fada ina murmushin jin dadi. Kallon manyan Fadar yayi sannan yace musu. "Me kuka ce?" Zuba mishi ido suka yi tare da mik'ewa daya bayan daya,suka bar fadan. Kuma nasan haka zai faru, shi yasa na amshi Anneh, tun daga fadan aka fara balai. Gamayyar su ce suka taru suka kawo hari cikin masarautan. Ga tsohon cikin da ya hanani yaki lokaci guda suka mishi tawaye, Ni kuma na saka su a gaba nace su yake su, kuma a kamo min su cikin masarautan a kawo su. Zunnon yazo da kanshi suka yi tattauna da Mehran, kuma Alhamdulillahi ya bawa Mehran hadin kai. Shi ya rike masarautan baki xaya bayan tafiyar su yaƙi, haka ba karamin d'aga min hankali yayi ba, dama sun gama shiri sosai, sai gashi bamu jin labarin kome dai ta sakamakon mutuwar dakarun SAMAIND. Abinda ya d'aga min hankali kenan na fara nakuda babu shiri. ----- Ina kwance aka ce nayi bako, dan haka na mike dakyar ruwan haihuwa na zuba min, na saka wani kaya na fito kallon shi nayi sannan na zauna muka fuskanci juna. "Rab kai ne?" Gyada min kai yayi sannan yace min. "Ni ne Sultanah Ikram! Gashi zan tafi nazo duba Yarinyar da Azizatul Nissah ta haifa ne, na cika alkawarin amanar da aka bar min, gashi wannan daga marigayi Nawwas ne." Amsa nayi tare da cewa. "Na gode" ya fita da sauri, kallon shi nayi ya koma wani irin mutum, komawa daki nayi sannan na kwanta tare da buɗe wasikar. _Amincin Allah ya tabbata a gare ki Ikram! Alhamdulillahi ina me sanar miki da Alkhairi, idan Har zaki ga Azizatul Nissah ta haihu cikina ne a jikinta, sannan akwai alaƙar da muka yi da ita, don Allah domin rayuwar abin da ta haifa a mata hakuri sakata aka yi kuma Alhamdulillahi don Allah Karku shegenta min Abinda zata haifa don Allah idan taki ne zaki yita idan ta bada hadinkai toh don Allah ta koma gida Ni kai nasan kafin wannan sakon ya iso miki nayi nisa Ikram wallahi kece macen da na fara Kauna da Aure nayi bakin cikin rigani da Abrad yayi ina miki fatan Alkhairi sosai ya biya miki bukatar ki na Alkhairi. Naki har kullum Nawwas_ Wani abu ne ya tsaya min a kirjina. Tausayin MEHRAN ne ya kuma cika min zuciya ta, dama Andilah ba yar Mehran bace? Me yasa Mehran ya amshi haka? Ko dama yasan da haka ne, wannan sai ya zauna a raina na shiga kokonto akan Mehran har ta kai, wasu kananun magana sun fara fitowa akan Mehran sauran tsirarun mutanen da suka rage, suka shiga kawo min kananun magana wanda ban san ya aka yi na yarda da su ba. Sai dai Darakshan ya kawo min wani sako da ya nuna min wannan yakinin da aka shirya Sultanah Fazilatul nisa da Mehran ne akan tana son matsayinta Na Sultanah. Shi yasa tayi amfani da ni, kuma shima yana son matsayin Mahaifiyarshi. Ta dawo kusa dashi. Kai na ya kulle, gashi Babu Mehran balle ya kare kanshi, dan haka na saka aka rufe min Sultanah Fazilatul, shi kuma Mehran akan Idanun Izmah na mika wuka me guba aje a kashe shi. "Amma baki yiwa zuciyarki adalci ba, akan Me za a kashe Mehran Wallahi nayi imani da Allah karya ce Mehran ba zai tab'a juya miki baya ba, idan da Yana son Mahaifiyarshi ta dawo kusa dashi da tun tuni yayi haka, wallahi Ikram karya ne." "Ku fitar min da ita." Haka suka fita da ita, Ni kuma haihuwar da ban shirya mata bane tazo min domin cikin yayi masifar sauka, ana fita da sakon Ina haihuwar Yarima cikin izinin Ubangiji. Yana sauka can wani ma ya kuma juya min ya diro. Komawa nayi na kwanta, bayin da suke cikin shashina suka rufa min dai da aka shirya mu ni da yaran, sannan suka fito, sanarwar. Kwanciya nayi wani irin barci me cike da gajiya ya zo min. "Jikata me kika aikata? Dama nasan hakan zai faru watan wata rana, Mehran yayi miki so domin Allah kuma ya tafi yakin da yake gab da nasara ki tura a kashe ki. Idan ya dawo karki yarda ki amincewa mulkin da aka baki domin zaki Cigaba da tsabar shine don Allah ki hakura da mulkin idan bai dawo ba,. karki rike mulkin domin jinin al'umma zai zuba ki rike a ranki Uwaisul Qarni yana tare dake." A firgice na farka tare da rungumo yarana, na goye su. Sannan na bada Umurnin a kama Sultanah Hoyam, a rufe min Azizatul Nissah da bayinta, kafin na fita tare da sawa a kai ni inda suke yakin. Bude kofar masarautan aka yi tare da shigo min da Mehran wanda nake kyautatta zaton sun kashe shi. A hankali suka shigo da shi. Tare da sauke min shi an rufe shi da tutar Kasar SAMAIND. Wani irin ihu na fasa zan fad'i,. Na zube dab'as jini na zuba a jikina, kuka nake tare da rarrafawa gurin gawar shi, zan tab'a yace. "Jarumta ga shalelenki nan" Ai ban san lokacin da na dire yaran ba,.na tafi da gudu haka dakarun suka matsamin a hanya ina zuwa na yanki jiki na faɗi a jikin shi. "Mehran!" "Shalele Yarimomin kika ajiye a kasa? Fudail dauko min Yarimomin nan," ya wuce dani cikin gida sannan yasa aka je aka bude Anneh, nan suka rufu a kaina, aka shiga bani kulawar da ta dace, Ina jin su sama sama yake bata labarin An kashe Amir Hood da sauran mabiyan shi, sannan ya maida Zunnoon matsayin shi. Sannan zai karawa Fudail matsayi. Abubuwa dayawa, har barci yayi gaba dani, koda na farka an gyarawa yarana jikin shi. Bude idanun nayi na gannin makale da Mehran. Yana barci a jikina, ban mishi magana ba, na kama dariya sabida.yadda ruwan nono ya b'ata mishi jikin shi. Yana farkawa ya kalle ni sannan ya gyara kwanciyar shi, matse ni yayi nace mishi. "Mehran kana b'ata jikinka fa!" Mikewa yayi tare da zama yana kallon yadda na jika mishi gaban rigar shi, shafa kirjin yayi sannan ya d'aga rigar yana shafa nonon, musamman yadda suke ta zubda ruwa, kai bakin shi yayi tare da lasa yana d'an cizon bakin nonon. "Don Allah karka shanyewa yarana abincin su, kai ma kasha naka lokacin kana jariri." "Kinsan Allah a matse nake ban san ya zanyi dake ba. Kuma ina son na." Rufe mishi baki nayi tare da mishi yar dabarbaru har ya sami nutsuwa tare da wanke ni da madaran shi, wanka muka shiga tare, muna fitowa ya kawo yaran da suke ta zabga ihu, a raina nace . "Haka zaku yi hakuri Mahaifinku jarababbe ne" "Ikram kamar gulmar mu kike?" "Kai Mehran cewa nayi haka zasu yi hakuri Uban su jarababbe ne" "Eh na yarda." . Rayuwa kenan, lokacin da ba bashi labarin Azizatul Nissah, da kanshi ya kaita Daular su ya tabbatar an bata mulkin kasar, sannan ya gaya mata abinda take boye mishi da dalilin da yasa ya kyaleta, sannan ya dawo. Sati na zagayowa aka akayi suna inda aka samu Abdus Samad da Almustapha. Bayan suna Mehran ya sallami duk matan da aka bashi, kallon shi nayi sannan nace mishi. "Mahlika fa? Ba zaka aure ta bane." "Zunnoon yace min yana sonta, dan haka ba zan hana shi ba ya tafi Madinatul Mah ya nimo aurenta, Fudail ma zamu tafi Askandariya. Izmah tunda Firoz yazo shima aje ayi bikin su. Ni kuma Allah ya gani nawa bikin a tsakanin cinyoyinki zanyi." Ture shi nayi tare da hararan shi. "Mehran bana son fitina, yarana basu yi kwari ba, idan sun yi kwari xan nime ka." Turmushe Ni yayi tare da shan abincin yaran shi. Mehran sai du'ai. * Alhamdulillahi bayan cika kwana arba'in, na mikawa Mehran matsayin da ya bani tare da kawo mishi hujjojin da yasa bana bukatar mulkin, sannan aka tafi auren mutanen da suke kusa dashi ana sauro auren aka dawo Samaind aka sha biki, tun a gurin bikin na fahimci me rabani da Mehran sai Allah. Dan haka Yaran suna gurin Anneh ita ke renon su, tunda muka shiga wanka tare ya kalle ni, bayan mun. Shiga ruwan, janyo Ni yayi tare da raba cinyoyina akan Hajiya babban shi, wani irin rungumo shi nayi tare da matse idanuna da kan shi da yake saman Kirjina na sake mishi wani irin kuka, sai da ya shiga sosai. Sannan ya sake ajiyar zuciya. "Wannan yarinya kina kashe ni da kuruciyarki. Nagodewa Allah da yayi wannan kofar domin jin dadina da kuma fitowar kawunan Yarana." Matse ni yayi tare da kafin ya shiga aikace ni, sosai. Na sha kuka a ban daki sannan ya dawo dani yana gaya min maganar cikin wani irin kauna. "Dud duniya babu inda ya kai raminki dadi, ke nifa ban ki na shekara ina Abu daya akanki ba, wallahi naji dadin yadda na same ki, Ikram.ba zaki kuma haihuwa nan kusa ba. Sabida na sha wuyar kwana arba'in. Ina wai dad'i Kenan, duk wanda yace wannan gurin bai da dad'i dai na saka an sare mishi kan shi naga ta rashin mutunci." "Allah Nagode maka Mehran kaci ka bar min na uzurin rayuwa don Allah." Haka ya gama kashe ni da soyayyar shi. Bayan ya nutsu muka shiga wanka, a hankali nake takawa tare da kallon shi. "Wallahi kafi ni girma don Allah kayi hakuri. Ka kara aure." "Sai kiyi kuma, ai shi yasa na lashe kofar da bakina kuma nasha ruwan sabida ki mallake ni" Haka rayuwar mu ta kasance cikin so da kaunar juna, wannan uwar rashin kunyar da taurin kai a dare daya Mehran ya rabani dashi, jarumtar kuwa soyayyar shi ta mantar dani jaruma ce, ina kaunar Mehran kamar yadda nake jin numfashina. Shi yasa kullum muke cinye juna. ---- Bayan shekara daya tsarin mulkin yana tafiya daidai da tsarin addinin musulunci, kuma Alhamdulillahi suma mutanen da basu addinin Musulunci ba a takura musu ba, sannan Nimrah ta haihu, ta sami Ya mace aka saka mata sunan Mahaifiyar Fudail, Izmah itama ta haihu da namiji. Sai Mahlika itama ta haihu, Jasrah tana auren Amidudawlah Gwamna ne a arewacin kasar, Sawda ta auri saurayinta da take azabar kauna, sai Sakeenatu binti Abu Waqqas, itama tayi aure a Bahrain, inda ta da auri wani d'an kasuwa. Azizatul Nissah mulkinta ta Cigaba da yin mulkinta cikin Nasara, yarta da Yar dan uwanta suna girma, haka ma matar shi itama tana cikin masarautan da Yarta. ** Cikin takaici da fada Anneh ta kalle mu. "Yaye yaran kika yi shekara daya a duniya?" "Toh Anneh don Allah yaran da basu shan nono sune abin damuwa kan su? Ni wallahi na gaji kawai gwara a yaye su kowa ya huta." Kallon Mehran tayi da yake ta kunshe dariya. "Aamaan wannan aikinka ne?" Ta gaya mishi a fusace, "Amma Anneh ni meye nawa, ita ta." "Mehran! Kai kace na yaye su yanzun kace babu ruwanka." Aikuwa muka shiga musu, ƙarshe koran mu tayi, muna fita muka shiga dariya, tunda muka shiga cikin shashin mu, muka cinye junan mu. --- Shafa bayana yayi tare da cewa. "Ikram! Meye kike so na miki a duniya?" "Mehran tunda k rabani da taurin kai da rashin ka sanya min tsoronka da shakkar ka, Mehran Nagode ka sauya min ra'ayina ka kuma sauya min ƙaddarata, ka sauya min rayuwa da soyayyar ka, Mehran ka nuna min sakamakon soyayyarka. Mehran ka min abubuwa dayawa da ba zan iya Mantawa ba, Mehran iya wannan abinda kayi min ya ishe ni. Ina sonka. Abinda ka jima kana son jira Mehran rayuwata sadaukar da shi sabida kai, Mehran ban san me zan biya ka dashi ba, Amma Allah ya gani ina sonka soyayyarka itace ta fara sani kuka. Nayi kuka da na kusan rasaka yau da na same ka, sai nake ji kamar nafi kowa dace, Mehran iya haka ma arziki ne da Allah ya nufe ni da samu. Nagode sosai da kaunarka a gare ni." Haka ya kasa cewa kome, sai murmushi rungume ni yayi tare da cewa. "Sonki gaskiya ne a gare ni, kaunarki alfarma ce a gare ni, Yarda dani shine abinda na samu mafi alkhairi, Ikram hakurin da kika yi dani yayi mugun sani jin kin fi kome daraja , kawaicinki abin alfahari ne, juriyarki yasa Maza bibiyarki, Ikram Nagode ki zauna dani kiyi hakuri dani ki kuma soni domin Allah da na kuskura na rabu dake da nayi asara har karshen rayuwata. Ina Sonki ainun."... Gyara kwanciya na nayi sosai a jikin shi muna amayar da kaunar Juna, cikin son gaskiya. .... Mulkin SAMAIND yazama na adalci, sannan ana rike da kome da gaskiya, Sultan Aamaan Mehran ya rike Al'ummar shi da gaskiya, sannan ya mai damu castle din shi dan yace a can muka fara a can zamu karasa, Darakshan kan tunda ya tafi kashe Mehran shi ya mutu Hoyam kuwa yanke mata hukuncin zaman gidan kaso sakamakon tana da hannun kashe Tsohon sarki., Duk wani munafuki min kakkabe shi a Samaind, tsakanin Mehran da Allah ya hanani kara Haihuwa, wai shi ba zai iya da kwana arba'in nan ba, dan Haka Abdus Samad da Almustapha sune muke ganin su muna jin dad'i. Bayan shekaru biyar, sai ga ciki nayi murna shima kuma yayi murna dan yana son karamin yaro, a hankali muka yi goyon cikin har na haife shi, inda na sami Ya mace. Wayyo Allah na. Tun ana mika min ita nace. "Joindatullah! Barka da zuwa." Ana kai mishi ita yayi mata huduba da Joindatullah, akan wannan haihuwar Rahil yazo suna da Laylah da dan su Aliyu. Bayan suna suka watse, wannan karon Alhamdulillahi dakyar Mehran ya barni nayi kwanaki ashirin da bakwai,yana shigowa yaga ina sallah kwaɓe kayan shi yayi ina sallama, yayi juyar dani tare da hauka ce min. "Don Allah bar Ni Salsabila na d'aga kafarki, so nake idan na zura miki sai kin leko hanyar Aljannah.". "A'a Ni dai sai dai na leko kofar Aljannah" Aikuwa haka muka shiga niman lada. Muna son juna kamar yadda nake tsannanin son shi. Kan mu. Allah Nagode maka da ka bamu juna a lokacin da muke bukatar junan mu....... *Alhamdulillahi, masha Allah, Ubangiji ya kara mana hakuri da juna nagode sosai Allah ya hada mu a wani labarin idan da nisan kwana nagode sosai Allah ya jikan Iyayen mu*